0% found this document useful (0 votes)
654 views59 pages

Halacci

The document discusses an interaction between two individuals. It begins by providing context about a lecture and challenges in a class. It then describes a text message exchange where one person asks personal questions of the other. They agree to discuss further in person. The document ends by noting plans to meet again.

Uploaded by

autanmaza07
Copyright
© © All Rights Reserved
We take content rights seriously. If you suspect this is your content, claim it here.
Available Formats
Download as DOCX, PDF, TXT or read online on Scribd
0% found this document useful (0 votes)
654 views59 pages

Halacci

The document discusses an interaction between two individuals. It begins by providing context about a lecture and challenges in a class. It then describes a text message exchange where one person asks personal questions of the other. They agree to discuss further in person. The document ends by noting plans to meet again.

Uploaded by

autanmaza07
Copyright
© © All Rights Reserved
We take content rights seriously. If you suspect this is your content, claim it here.
Available Formats
Download as DOCX, PDF, TXT or read online on Scribd
You are on page 1/ 59

…………kaina yayi matukar kullewa ganin yadda lokaci daya tunani yabar

jikina wanda hakan bakon abune agareni musamman akan mace wanda ada

kamar bera da mage nake kasancewa tsakanina da mace ,na tsammaci zata

fuskanci halin da na shiga a wannan lokaci har naji raina ya baci nayi tsaki wa

kaina kana na girgiza kaina domin in samu In fita daga wannan tunani dana ke,

amma amamakina sai naga ita ko ajikinta hakan yasa na dan ji salama domin na

tabbata bata tsinkayeni ina kallonta ba ballantana har tayi min wata fassarar.

Bayan ta sami wuri ta zauna ni kuma na kuma maida hankalina ga lecturer dake

gabatar da lecture a lokacin ko dayake lokaci zuwa lokaci zuciya ta tare da

taimakon kwakwalwata kan rinjayi tunanina hart a sanyani waiwayawa inda

take saidai aduk lokacin da hakan ta faru nakan yi saurin kauda kaina

alokacinda na farga.

A haka dai har muka gama lecture lecturer ya fit anima na mike na sake

yi mata kallon karshe cikin tsoro tsoro na fice daga hall din . A ranar dai bansan

ya suka kare ba ni dai lokaci azan iya zama awurin da take b a saboda nasan

Adole sai tunanina sai ya canja akanta,

Haka na kasance cikin basarwa da korewa kaina tunani awannan wunin

har Allah ya kaimu dare nayi barci sai na tashi da safe na manta da abinda ya

faru jiya na kuma shiryawa na fita lecture, kasancewa ta bako yasa na fita da

wuri tun kafin lokaci yayi


na kasantu acikin hall, ahankali mutane suna zuwa har ajin ya fara cika lecturer

ya shigo yafara gabatar da darasinsa , na dauko jin dadin darasin kasntuwar

kusan duk abinda ake koya mana na sanshi a baya ina gaba gaba wajen ansa

tambaya, kwatsam sai gata tashigo ajin ta wulka ta gaba na wuce ta zauna sai

kuwanaji kaina ya sara min adai dai lokacin da take wucewa , na dauki kusan

minti biyar ban koma cikin hayyacinaba abin kuma da yake kara ban mamaki

kuma shine akaramin tunani na na kasa fahimtar dalilin da yasa nake shiga

wannan yan ayin asanadiyyarta , ranarma haka lecturer ya gama ya fita na bi

bayansa ba tare da na tsayaba kamar yadda sauran dalibai yan uwana suke yi,.

In takaita muku zance dai haka na kasance cikin gujewa duk wani abu da

zai hada ni da ita saboda in tseratar da tunanina saboda ni har cikin raina bansan

menene dalilin hakan ba kasancewar ban taba tsintar kaina acikin irin wnnan

halinba akan wata daban.

Har na fara rashin lafiya wacce nake kyautata zaton cewa tunanin yarinyar nan

yana da kaso mai tsoka acikin dalilin rashin lafiayar da nake yi, domin kuwa

tunaninta kan sanyani mantawa da halinda nake ciki na daga yunwa ko koshi

har takaiga nakan kai qarfe biyar na yamma ba tare da na karya kumallo ba

sakamakon na fita da safe bann ci abinciba lecture kuma ta riqeni har karfe uku

na yamma , to idan naje daki amaimakon in nemi abinci sai kawai inji ta fado

min arai daganan kuma bani sake sanin wa yake kusa dani har sai na kusa karfe

biyar zuwa shida sai inji kamar na farka daga barci … …


Ahaka dai ina tafe da guntuwar ulcerta wacce ta haddasamin wasu lahani

acikin jiki na …

Aranar da muka dauki azumi na bakwai da yammaci bayan mun fita

daga jarabawar mu ta qarshen wannan rabin shekarar nayi mata kallon karshe

wanda alokaci n tayi matuqar kidimar dani har na kasa yi mata Magana don

kuwa wani bakin tabarau tasan ya wanda da ka ganta kasan ba raini , hakan yasa

ko sallama ban iya yi mata ba , haka na dauki hanyar kano domin kuwa bazai

yiwu in tafi gida kai tsaye ba saboda yamma ta riga tayi sosai dole sai na kwana

a kano kafin da safe in nufi kauyenmu.

Zuwa na gida sai yakasance kamar taki aka zubawa rashin lafiyata don

kuwa said a takaini ga ajiye ajumi gaba daya saboda gazawa, ahaka n a kasance

har aka qare hutu makaranta ta dawo aiki amma ina gida ina famar jinya har

said a na qara almost 40 days ahead sannan na koma makaranta kamar HIV

victim saboda rama , na kasance ko da yaushe cikin qauracewa mutane saboda

matsalar da ke gareni ta tarin tuberculosis wacce nakke kan shan maganinta ….

A haka dai har muka kammala second semester tsakani na da yarinyar

nan sai dai kallo daga nesa ko kuma kiran tsoro ta waya. Dan zaman da mukayi

agida ne har na fara iya jure yin Magana da ita ta waya jifa jifa har dai muka

dawo makaranta, wani abu da yayi matukar dauremin kai shine na rigata

dawowa wanda hakan yasa aranar na kirata da dare n ake tambayarta ra nda
zata dawo sai take cemin sai wani lokaci , kawai sai naji labarin ta shigo

wanshekare.

A wannan karon kuma sai abin yayi worse don kuwa na fara kasa iya

boye damuwata har takai ga mutane sun fara fuskantar akwai abin da ke

damuna wanda nake boyewa , na kasance ko dayaushe so nake in ganta amma

kuma bana son mu hadu face-face don kwarjininta a ido na.

Aranar 2 ga watan April na gagara daurewa kamar an tsunguleni na

rubuta text awayana na tura mata misalign karfe uku na rana bayan na gama

lecture na ranar na tafi hostel… txts din ya kunshi sako ne kamar na neman

shawara akan naga wata inaso amma na rasa yadda zanyi sai nake so ta bani

shawara , hakan nayi ne don inji irin ra’ayinta shin zata bani kwarin guiwa ko

kuwa za ta sarar dani. Abu n mamaki kafin karfe hudu sai naji kiranta awaya

ganin haka yasa na yanke naje na recharge din layi na sannan na kirata , bayan

mun gaisa sai take cewa dani “naga text “ sai na amasa mata da cewa “eh to

yanzu mecece shawaraeki akai” ta danyi shiru da farko wanda hakan yasa na

dan razana kadan kafin daga baya tace “ina ganin…. Kawai ….. kawai ka

sameta ka fada mata” alokacin sai naji kaina yayi min nauyi na nemi in kasa

kara furta wani abu sai dai daga baya nace “haka kike gani?” “Eh mana hakan

zaifi” “idan zan iya kenan?” yar dariya tayi kadan kana tace “eh idan zaka iya

ka sameta ka fadi mata in kuma baza ka iya ba sai ka sami number wayarta ka

kira ta ka sanar da ita” nan ma shiru na sakeyi don kuwa kaina ya daure na rasa
me zan fadi sai daga baya nace “Shikenan nag ode zan gwada in gani duk abin

day a wakana zan baki labari” muka yi sallama na kasha wayata , daga nan na

shiga zullumin wace hanya zan bi in iya fadi mata qudurina ban Ankara ba sai

dai naji an a kiran sallar magrib don hankalina ya bar jikina kwata-kwata har na

manta abinda nake tunani.

Bayan anyi sallar Isha’I kuwa nayi niyyar in kira ta awaya in sanar daita

amma sai taraddadi ya hanani don kuwa na kasa natsuwa da zuciyata sai kusan

karfe tara na dare Na fita don wai in sami wuri kebantacce wanda zan zauna in

kirata amma sai nayi ta yawo cikin makarantar ko ina naje sai inji kamar akwai

wanda zai interrupting dina ahaka har saida na kai Lecture theatre na

makarantar na zauna kan daya daga cikin kujerun dake wajen LT din sannan na

kirata tana fara ringing gabana ya fara fadi kamar sojoji sun kewaye ni da

bindiga. Ta daga wayar da sallama kamar yadda ta saba “salamu alaikum!”

amma ni sai na kasa amsawa akaron farko saida ta sakeyin sallama sannan na

amsa da “wa’alaikumussalam” bayan mun gaisa sai nace “dama akan maganar

da mukayi dake dazune …” sai na tsaya anan ban iya sake fadin wani abu ba

saida taji shirun yayi yawane sannan tace “hello!” na amsa “hello” nima sai tace

“inajinka” na sake dagewa don inyi Magana amma sai na gagara saida ta sake

yin Magana sannan nace “amm…. Agaskiya wannan yarinyar da na baki labari

ba wata bace face ..ke” na fadi hakan cikin karfin hali don alokacin na tabbata

har muryata rawa take, wani babban abinda ya sake karya min wuya shine da
tace min bataji a binda na fadi ba don ji nayi dama ban fara maganar ba da sai in

hakura kawai in bar abin azuciyata don na riga nagama bawa zuciyata tabbacin

bazata karbeni ba. Na sakeyin karfin hali nace “abinda nake nufi shine :kece

wannan yarinyar” still sai naji tayi shiru nayi zaton ko ta gane manufata ne

amma da nace “kin fahimceni ?” sai tace “Gaskiya ban gane ba” hakan da ta

fadi ya matuqar qonamin rai kawai sai nace “ok kiyi hakuri wani lokaci na gaya

miki..” sai tace “to shikenan” mukayi sallama na kashe wayata na kwanta cikin

kujerar duk da kasancewarta simintine amma sam ban kawo hakaa araina ba

haka na cigaba da zama awuri nnan sauro na cizona amma sam bana ji har saida

na tsinkayi kaina cikin wani duhu wanda ya dan fadar min da gaba sannan ne na

Ankara cewa 11:00pm tayi har an kashe Gen. din makaranta, haka na tashi na

nufi daki kamar wanda babu laka ajikinsa alokacin na ji cikina yana min zafi

nan na tabbatar ban ci abinciba adaren ,alokacin na dora tukunya don sama wa

kaina masalaha. Ranar haka na kwana cikin zulumi don na dauki tsawon lokaci

ban yi barci ba

Dagari yawaye na fita lecture haka nayi ta boye boye don kar mu hadu da

ita har muka tashi , da dare yayi misalign karfe goma da rabi na dare na kirata

kuma amma alokacin sai na sami kwarin guiwa nace da ita “na kirata amma na

kasa fada mata kudirina” sai tace “yanxu ya kenan zakayi” ni kuma sai nace

“so nake yanzu zan tura miki sunanta a text da department din da take in Allah

yasa kin gane ta sai ki isar minda sakona gareta” shiru tayi da farko kana tace
“to shikenan Allah yasa na santa” nace “amen”daga nan sai na rubuta sako

kamar haka.

Name: Aisha Rabi’u Ahmad

Department:Maths/Chemistry

(school of science)

Pls contact her whatever you-

discussed you let me know

Na tura mata na kashe wayata na kwanta barci amma sai barcin yaki zuwa har

kusan karfe biyun dare .

Da gari ya waye safiyar alhamis na shiga school sai na kasance cikin

buya don kar mu hadu amma sai ya kasance dole sai mun hadu domin tun

asafiyar da na shiga science complex ina rabe jikin Mathematics laboratory da

sunan na buya ina jira karfe takwas tayi mushiga Practical chemistry na dauki

tsawon lokaci awurin ban ko hangetaba saida na taka da niyyar in nufi

Chemistry lab din kawai sai naci karo da ita zata wuce, kamar atsorace ta

gaisheni na amsa nima atsorace saidai kawai dakewa da nayi ahaka dai muka

kasance ranar sai dai satar kallo muke wa junan mu har aka tashi na koma

hostel cike da zulumi, ina jirace da dare domin in kirata in tambayeta labarin

kasuwa.
Hmm Allah dai shikyauta aikin sabon shiga, tun da na dawo hostel

akwance nake har aka kira sallar magrib sannan na tashi jikina ba kwari na nufi

masallaci don inyi alwala inbi jam’in salla, bayan an idar da salla kuwa sai na

dawo na zauna kan wata waiters seat dake tushen bishiyar bedi (darbejiya)

wacce ke gaban block C na shiga saqe saqen abin da ban ma san taya na faraba.

Ahaka har lokacin sallar isha’I yayi na tashi na koma masallaci don gabatar da

salla, na dade ina addu’o’I don neman yardarm allah da kuma neman zabin sa

akan abinda yafi alkairi gareni bayan dan lokaci kuma na tashi na koma daki na

kwanta sam na manta da cewa rabon cikina da ansar wani abu tun safiya, nan

fan a fara jin ca nji a jikina amma sam tunanina bai kawomin dalilin fuska ntar

wannan chanjin ba ,har wajen qarfe goma sannan na dawo hayyacina bayaga

cewa ba barci nayi ba duk tsawon lokacin da na dauka akwance, hakan kuwa ya

farune sakamakon wani zafi da naji cikina yanayimin, ahankali na tashi na

zauna nayi kokarin mikewa amma sai naji idona yanayi min gizo nan take na

fuskan ci cewa lallai yunwace ke rarakata, alokacin sai na fara tunanin mafita

agareni ,dakyar na sauka daga kan gadon na fara kici-kicin dafa koda rowan

zafine In durawa cikina amma sai na nemi abin kunna wuta na rasa alokacin

kuwa babu kowa adakin duk sun fita zuwa wasu harkonkin nasu ni guma

saboda ganda tare da taimakon yanayin da nake ciki na rashin jin dadin jikina

yasa na koma na zauna said a naga dare ya fara nisa tukunna sannan na yakice

na fita zuwa wani canteen cikin super market din makarantar wato shagon dan

kasuwa na sami maltina da biscuits na aikawa cikina sannan na koma daki na


sake zaman jiran lokaci wato qarfe sha daya na dare domin alokacin na qudiri

aniyar kiranta domin jin ansa.

Zaune nake ina gyangyadi har saida na tsinkayi duhu cikin dakin sannan

na tabbatar da cewa qarfe sha daya tayi don haka na zari wayata na fita na dauki

lokaci kafin inkirata hakanan dana kira tana shiga gabana yafara faduwa don

fargaba bugun zuciyata ya qaru don har rintsa ido nakeyi don dai kawai inji ko

zai sassauta, tana amsawa ta fara gaisheni na amsa mata cikin dari-dari kana

daga baya nayi shiru, itama haka shirun tayi sai bayan kusan 30 seconds sannan

nace

Ni: …am .. dama akan maganarmu ta jiya na kira domin inji yadda kuka

kare da ita…. (na qarasa maganar aciki tare da rakon wasu kalamai

wadanda ni kaina ban san me nace ba).

Ita : (tayi shiru na tsawon lokaci har hakan yasa na sake fadin)

Ni:… kinyi shiru bakice komaiba, kin sameta? Ya kukayi da ita? (duk

wadannan tambayoyin shiru ta sakeyi said a nace) kinyi shiu ko kina

bukatar lokaci ne?

Ita: (cikin sarqaqqiyar murya) Eh!

Ni: kamar tsawon wane lokaci? Awa daya? Sati daya? Ko wata daya?
Ita (a ciki-ciki) sati daya

Ni: hakan yayi miki?

Ita: eh!

Ni: ok shikenan na gode zan cigaba da jira har lokaci n da zaki waiwayeni

Daganan mukayi sallama na koma na kwanta

Haka muka cigaba da yiwa juna kallon tsoro har kusan kwana shida babu

abinda yake hadani da ita sai ko gaisuwa in Allah ya qaddari haduwarmu don

haduwarma sai dai in kirata qaddarar ubangiji don kuwa bana son duk wani abu

da zaisa mu hadu na fison in ganta awani wurin yayinda ita bata ganina . Iya

tsawon wannan lokacin ban kirata ko sau daya bah aka nan itama garama ni

naka tura mata text duk bayan kwana biyu

Ana gobe sati zai cika na tura mata text don tunatarwa da ranar tayi kuwa har

qaguwa nayi dare yayi don inkira inji ansa amma da daren yayi sai kuma na

kasa kira sai juya wayar nake ahannuna sai na dauka kamar zan kira amma sai

inji tsoro in fasa dakyar dai misalin sha daya da mintuna na daure na kira, tana

dauka kuwa ta fara gaisheni bayan mun gaisa na gaya mata ga abinda yasa na

kira , abin mamaki sai ta nuna kamar bata san maganar ba said a taji nadage

sannan sai ta fara yi min wasu tambayoyi wanda acikinsu daya kawai na rike

don ji nayi kamar a mafarki wait a tambayeni “KAI WANE YARE NE?” . Mun

dauki kusan minti ashirin da biyar amma bata sanar min hkuncin da ta yankeba ,
sai ma daga baya tace min tana bukatar Karin lokaci ni kuma sai na maida mata

da martini “in dai likacine na baki daga zuwa koma yaushene zan jiraki, amma

inaso koma dai menene kada ki dubi sanayyar da ke tsakaninmu ko mutunci

kawai kibi ra’ayin zuciyarki don kuwa zuciya keda dammar yanke hukunci akan

abinda takeso ko abinda bata so” daga nan mukayi sallama na tafi na kwanta

amma azuciyata na riga na sadaqar cewa kawai nauyina takeji shiyasa bazata

iya gayamin cewa bata sonaba don haka na fara bawa zuciyata hakurinda sam

bata ma san sunansa ba ballantana ta karbeshi.

Lokaci lokaci nakan kirata mugaisa amma maganar wani campaign duk

na aje gefe don nasan ajin yafi karfina . Awannan tsakanin haka mukayita

artabu da abokaina kan su yarda cewa ba Aisha bace ta sace zuciyata amma sun

doge don sun fuskanci abubuwa awurina da dama amma sai na nuna musu cewa

ita Aisharce kadai tasan yarinyar shiyasa kusancinmu da ita yakaru, don

acikinsu ma akwai wadanda suka ringa fadimin Magana afakaice don dai inji

haushi wasu kuma har kiranta sukayi a waya don su tambayeta amma sai Allah

yasa bata biye ta harkarsu sai ta nuna musu bata san zancenba , ahaka har lokaci

yayi nisa.

Kwatsam sai wani abu mai matuqar firgitarwa ya sameni duk da cewa

nasan Aisha tafi qarfina amma saida naji mugun kishi ya motsa akanta wannan

abin kuwa shine ganin wasu messages da nayi cikin wayar wani course mate

dina mai suna Abdulkadir wadanda ya turawa ita Aishar yana neman soyayyarta
amma kuma bai taba gayamin ba koda dai cewa shima baisan tsakanina da itaba

, yadai san kawai combination daya muke da ita, adaidai lokacin na tuna da

sa’adda yace in bashi numberta amma na ki harsai day a takura sannan na tura

masa, banyi masa Magana ba ganin wadannan messages din sai dai kawai da

nashi na fita barshi da sunan zanje indawo dawowar da banyi ba kenan aranar,

bayan yan kwanaki kuma an bamu wani Assignment based on combinations sai

ita Aishar ta nemi mu tafi library don mu duba answer tare na kuma yarda muka

tafi misalign qarfe takwas da rabi

Bayan mun fito na dan taka mata kadan zuwa kusa da AUDITORIUM

BLOCK wato AU sai nayi m ata said a safe na nufi hostel dinmu, ina gab da

shiga sai naji kira a waya nayi mamaki da naga itace ke kira don ganin yanzu

muka rabu amma kuma saigashi ta kirani, alokacin babu cikakken kudin da zan

kirata ta wayata hakan yasa na cire kunya na daga wayar nayi allama, tun kafin

ta amsa na tambayeta “ya akayi?” na tambayeta kamar a uzurce sai tace “kasan

meh?” “a a sai kin fadi” cikin yar dariya take cewa “nifa na dauka cewa

assignment din special target zamuyi” ni kuwa sai na amsa mata da “hmm, ai ni

kuma tsammanina na mama kike batu akai” sai ta sakeyin dariya kana tace “ai

ni nariga nayi wannan” “ au to ai shikenan gobe naje ni in qarasa wannan din”

na fadi hakan cike da mamaki daga nan mukayi sallama nace saida safe. Har

na kwanta sai na sake ga nin kiranta


Kasantuwar babu wadataccen kudi acikin wayar yasa na fita a daren na

recharging dana kirata bayan ta daga wayar sai na tambayi ya akayi sai tace min

“abubuwane sukayimin yawa” “ bana ganeba me yafaru” sai ta mayar min da

cewa “dama akan maganar ………” bata karasa ba sai tayi shiru tace “kaih..

kawai ka barshi ba saina fadaba” take sai naji gabana ya fadi cikin rashin

fahimtar me take nufi nace “ban ganeba meyasa bazaki fadi ba?” “kawai ka

barshi bazan iya fadi ba” haka ta mayarmin wanda ni kuma alokacin raina yai

matukar baci amma kawai sai na dake nace “ok shikenan tunda bakison nayi

barci sai da safe” da kawowata nan sai na yanke wayar, ko cikakken minti day

aba ayiba sai ta sake kirana, dagawa kawai nayi ba tare da nace komai ba sai da

tace “naji ka kashe” “eh mana in ban kashe ba ya zanyi tunda kince bazaki

fadimin ba?” shiru tayi na dan lokaci wanda har hakan yasa nace “kinyi shiru

me yafaru?” “naji kace bazakai barci bane shine nakeson nace kar ka dami

kanka kayi barcinka ba bu komai” haka ta fadi kamar irin ta damu dani dinnan

ni kuwa sai nace “wannan kuma bai kamata ya dameki ba tunda bazaki gaya

min ba kawai abar maganar anan” jin alamun na damu da gaske yasa ta sake

bani hakuri ni kuma na nuna ban sanshiba, daga karshe ma kawai kasha wayar

nayi na zuba tagumi kamar wanda aka aikawa da sakon mutuwa, ban ankaraba

sai naji karar shigar message awayata , dubawa ta kuwa sai naga “dama akan

maganar Rabi’u musa ne da kuma wannan da yace kabashi number nan a group

dinmu na research” take sai naji cikina yayi wani kara don jin abinda ban taba

tsammaniba, saboda shi wanda take Magana akai din abokina ne don dama
shine na taba gaya muku cewa naga messages a wayarsa wanda keda alak a da

hakan

Bayan da na ja doguwar ajiyar zuciya sannan na daga waya na kirata

bayan ta daga sai na farad a cewa “naga text din da k ika tura m in yanxu”

Sai tad an yi shiru na lokaci kafin daga baya tace “eh dama shine abinda yake

damuna” ni kuwa cikin karfin hali sai nace “toh ai wannan mai saukine tunda

abu ne da yashafi zuciyarki don haka kawai tunani zakiyi ki kuma yi shawar da

zuciyarki akan wanda yafi dacewa da ita hakanan kuma duk sa adda kika yanke

hukunci ki sanar da su duka cewa wani ya riga wani daga cikinsu hakanan

wanda kika zaba din kuma sai kisanar masa domi n dukkansu su sami

kwanciyar hankali” tunda na fara Magana shiru tayi batace komai ba har sai da

na rufe baki sannan tace “toh shikenan na gode mukayi sallama na sake zuba

tagumi awurin batare da na tashi ba bare in kwanta na jima ahaka kafin daga

baya na dauki wayata na tura mata text mai dauke da “Ina mai kara jadda da

miki cewa don Allah duk wanda yayi nasarar samun zuciyarki to ki sanar masa

ki kuma sanar da wadanda suaka rasaki don su san a wane hali suke ciki, kada

kuma kiyi la’akari da yadda kuke da mutum komai kusanci don wannan abune

day a shafi zuciya ba gangar jiki zalla ba.” Na tura mata sannan na tashi na tafi

daki don in kwanta.

Karfe shida saura yan mintuna na safe sai naji wayata tayi qara ina

dubawa sai naga itace ta turo abinda aka rubuta a text din kuwa shine “ akwai
wani abu da nake son sanar dakai wanda baka sani ba, na taba yin aure kuma

ina da da shin zaka iya tarayya da matar aure? Bazan cuceka ba” iyakacin

abinda message din ya kunsa kenan. Hmm babbar Magana nayi matukar girgiza

da ganin wannan sako don na tabbata da atsaye nake sai na sami abin jingina

don akwai yiwuwar in fadi ban sani ba, akwance nake am ma sai da n a rintse

idona na tsawon lokaci kafin daga baya na dawo cikin hayyacina na sake

karanta meassage din sannan na nayi reply kamar haka “toh nana Aisha kinyi

Magana daya mai ma’ana biyu wanda na kasa fahimta da farko kince kintaba

yin aure , daga baya kuma kina tambayata ko za iya tarayya da matar aure, shin

har yan zu kina da aurenne ko kuwa ada kike da auren yanzu baki dashi?” ina

kawowa nan na tura mata na cigab a da kwanciya ina jiran amsa , cikin ikon

Alllah kafin minti biyu sai ta yi reply da “ina nufin zaka iya tarayya da wacce ta

taba yin aure?” hmm abu kamar almara sai naji lokaci daya hankalina ya fara

kwanciya naja doguwar ajiyar zuciya sannan na mayar mata da reply cewa

“Alhamdulillahi naji dadin wannan maganar na kuma gode da sanar dani

gaskiya da tayi don kuwa hakan kara miki matsayi yayi azuciyata haka kuma a

iya sanina addini bai haramta mana auren macen da ta taba yin aureba matukar

hankalimu ya kwanta akanta hasalima a zamanin yanzu dakyar mata ke cika

50% Na quality da suka dace ko wace mace ta mallaka sai gashi ke kin mallaki

90% Na wadannan qualities din don haka haryanzu ina kan bakana in har

zuciyarki ta aminta dani ki sanarmin don in sami natsuwa araina" ina kawowa

nan na tura mata na sake kwanciya na tsunduma cikin tunani, sai can bayan
wani lokaci misalin karfe bakwai da rabi sai naji kira ina bi sai ta fara dariya

cike da mamaki sai na tambayi dalilin dariyar sai tace "da wasa nake" cikin

rshin fahinta nace "me kike nufi" sai tace"abinda na gaya maka da wasa nakeyi"

hmm lokaci daya na dauke wuta har saida na rufe ido sannan naja doguwar

ajiyar zuciya sannan na bude ido nace"alhamdulillah amma fa wallahi kin firgita

ni matuqa, bakya tsoron zuciyata ta buga?" Dariya ta sakeyi tace" ai nasan

bazata buga ba , shiru nayi na dan lokaci sannan nace "to shikenan Allah ya

kiyaye gaba" tace amin mukayi sallama

Karfe shabiyu muka hadu awurin lecture na Gse 122 sai na hadu da Abdulkadir

sai yake ban labari cewa wai Aisha bazawarace sai naji abin ya bani dariya na

sake tanbayarsa wa yagaya masa sai yace wai ita ta gaya masa ni kuwa don

bugun ciki sai nace sai na tambayeta a tsorace ya ce don Allah jar and inje na

ce sai naje na kama hanya na tafi inda take na zauna kusa da ita muka fara hira

amma har aka gama lecture ban gaya mata ba don dama tsokanarsa nake.

A haka muka cigaba da kasancewa bata sanar dani hakikanin abin da ke

ranta game daniba, ita bata fito fili ta gaya min cewa bata sona inyi hakuri ba

haka nan bata kuma amsa tana sona ba, kawai dai abinda nasani shine sakin

fuskarta a gareni ya fi yadda nasani abaya,

Bazan manta wata laraba ba bayan mun gama lecture ta mat 212 wato problem

solving in mathematics muna zaune cikin aji da ita da wasu daga cikin yan ajin

namu ita tana kwafar rubutu daga wani text book zuwa littafinta wanda
yakasance assignment ne da aka bamu a chemistry department, alokacin tsaye

nake jikin bango daga gaban kujerar datake zaune, sai ga wani abokina yashigo

wand azan iya cewa shine aboki mafi kusanci da nake dashi aduk fadin

makarantar yana kuma daya daga cikin masu zargin akwai wani abu tsakanina

da ita Aishar, da shigowarsa ya fara min ba’a ni kuma sai na basar dashi don

kuwa banason ake tashin maganar saboda raina yana baci adalilin haka

kasantuwar nakan tuna da cewa na nemi soyayyarta amma ban sami karbuwa ba

har wannan lokacin kuma bana sa rai cewa zan sami karbuwar, ganin na basar

dashi yasa bai sake ba sai kawai da yaje gurin ita Aishar suka gaisa yake

tambayarta abinda take, ai kuwa kamar dama ajirace take sai tace “daman na

gaji amshi ka taya ni” shikuwa sai yace “a’a ga wanda zai tayaki nan a tsaye

baki bashi ba sai ni?” .. hmm abinda yaso bani mamaki shine sai ta kale ni

sannan tace “nmh ni in bazaka tayani ba bani” tafadi hakan tare da kai hannu

don ta karba, shima sai ya kalleni kamar masu hadin baki sannan yace “a a

barshi to zanyi ko layi ukku nayi miki ai na tayaki” ya fadi hakan tare da karbar

biron hannunta ya fara. Ni kuwa ina tsaye agefe ina dan murmushin dole don

kuwa zuciyata ni kadai nasan abinda takeji, bai dade yanayi ba sai yace “nagaji

gaskiya kai anshi kayi mata ai dama kai yakamata kayi bani ba” ya fadi haka

tare da miko min ita kuwa sai ta bishi da kallo yayinda na karba sai ta kalleni

muka hada ido sai ta yi kasa da idonta, nikuma kawai saina fara rubutu tana

zaune da wayarta a hannnu tana sauraron waqar naja’atu ta annabi wakarta ta

dandali
Ina rubutu ina satar kallonta ayayinda ita ko aka bata kawoni ayadda na

fuskanta, ahaka har computer students suka shigo zasuyi lecture a wurin muka

fita muka basu wuri yayinda muka shiga ajin da yake opposite to wanda muka

fita muka zauna seat daya da ita ina rubutu tana wasa da wayarta yayinda wayar

yayanta(wanta) wato bishir ke rike hannunta, ina cikin rubtu ban Ankara ba sai

naji tace “kaga hoton baba” saurin waigawa nayi don inga me take nunamin sai

kuwa na tsinkayi mutum zaune cikin mota cikin shiga ta mutunci tare da

karamci wanda da zarar ka ganshi zaka fuskanci cewar bahaushene ne kuma

mai kamala duba da yanayin suturar dake jikinsa. Murmushi nayi kawai wanda

ya kasance iyakarsa kan fuskata don atake gaba nay a fadi don hakan ma wata

alamace dake nuna cewa Aisha ba class dita bace sai nace “na gani hoton yayi

kyau” kawai na cigaba da rubutu na yayi n da rabin hankalina baya jikina har na

tsaya ban ma saniba sai naji muryarta tace “ka gaji kaima?” dan guntun tsaki na

saki na cigaba tareda cewa “a a wani abu kawai na tuna , a haka dai har lokacin

lecture mu yayi na wani course one of the two elective courses we offered in

chemistry department wato Gaseous state da kuma Nuclear chemistry wanda ni

n ake offering din Gaseous state ita kuma take offering din nuclear chemistry

sai muka fita dukkanmu yayinda ita kuma ta nufi hostel.

Allah dai ya kyauta aikin qaddara bayan mun tashi daga lecture muma

mun tafi hostel can misalign karfe biyar na yamma sai na kirata bayan mun dan

gaisa sai na ke tambayarta ya take sai tace min bata lafiya tana fama da ciwon
ciki, hankalina yayi matuqar tashi jin cewa bata da lafiya har ma na rasa me zan

ce da ita bayan istirja’I da nayi sai kace wanda ya fadawa wata masifa kana na

bita da sannu ta amsa yawwa “yaya jikin naki yanzu” ta amsamin cewa “da

sauki” “to Allah ya baki lafiya ya kuma kiyaye gaba” mukayi sallama take sai

na tashi na bazama yawo don kuwa jinayi zaman hostel din ya gundureni kawai

saboda jin cewa bata da lafiya ina tafiya ina saqar zuci wanda azuwa yanzu ban

iya tuna ina da ina naje alokain da na fita yawon nan nasandai na fita agalawa

zuwa gidansu Kailani bayan na fita na shiga wurin Adam shi kuma alokacin

daya dameni da ba’a saina tashi na fice na kama hanyar komawa makaramta

wanda ina kan hanya aka kira sallar magrib dpn haka sai na zarce masallaci

nayi alwala nabi jam’I.

Bayan na tashi daga shago wanda n a saba zama lokaci lokaci bayan

sallar isha’I zuwa abin day a sauwaka sai na kuma kiranta don in tambayeta

yanayin jikin sai take cewa dani “hmm jiki Alhamdulillahi na warke” ni kuwa

sai nace Alhamdulillah naji dadi sosai Allah ya kara lafiya ta amsa amin kafin in

kaiga yin Magana sai ta fara bani labarin abinda ya haddasa mata ciwon cikin,

abin kamar wasan kwaikwayo tana fadi tana dariya yayinda tace “kasan me?

Dazu da rana bayan kun shiga lecture ni kuma na kama hanya zantafi hostel

kawai sai naji ina sha’awar garri harda zan wuce ta wurin masu saida gyada

nake cewa da ban cinye gyadata da na siya dazuba da nasa aciki , ahaka na

qarasa ina zuwa kuwa na jika na sa sugar da madara na sha nagama kenan
cikina ya fara ciwo saboda dama ban yi breakfast ban a fita….” Haka ta cigaba

da labarta min abinda ya faru tanayi tana dariya ni kuwa tsitttt nayi tausayinta

ya kamani har saida taji shirun yayi yawa sai tace “hello” na amsa da “hello

inajin ki” “naji kayi shiru.” “hmm kawai tausayi kika bani, amma meyasa ma

kika fita baki yin break fast ba ? dama ancemin baki cin abinci sosai gashi kuma

kika cusawa cikinki abinda be saba dashi ba.” Duk abinda na fadi shiru tayi tana

jina wanda har dariyar da take dan yi shiru tayi ta dena ban kuma san daliliba

wanda hakan yasa na tsargu nace “kinyi shiru bakice komai ba dagaskene kenan

baki ci n abinci sosai” sai ta amsa da “Nhm ai ba koda yaushe bane kuma ni

bawai cine banayi ba kawai irin ikina kenan bana cin abinci da yawa”…..

Kar dai in cikaku da surutan iska, abu kamar wasa ciwon ciki yaki ci yaki

cinyewa har takaiga an samata drip dag a karshema har saida ta koma gida,

hakika komawa gidan da tayi ya nunamin ainahin kujerar da nake awurinta

domin bata gaya min zata tafi ba saida ta tafi tukunnan na tambayi kawarta

Raihana take gayamin ai ta tafi. Sai daga baya na kirata nake mata ya jiki

sannan naked an tambayarta ya akayi ta tafi bata sanar dani ba take cemin wai

tayi la akari da cewa Raihana ta gaya min, shiru kawai don kar inja abin da

tsawo har akaiga ta fadi wani abinda zai iya sawa inji ba dadi nabi ra’ayinta

nayi mata allah ya sauwake mukayi sallama satinta guda cif agida ta dawo

school wanda wannan sati dayan da tayi babu wanda bai shaida hakan ba

sakamakon canji da bayyan atare dani ana gobe za afara azumi ta shigo
makaranta, aranar ji nayi kamar anyi min wani albishir duk da dai ban sami

ganinta aranar ba domin ko aranar da zata dawo saida nace in ta shigo ta gaya

min amma sam bata juyo ta kaina ba sai misali n karfe tara na dare sannan ta

kira tana tambayata wai me yayi zafi ta dawo ban yi mata sannu da zuwa ba, ni

kuwa sai na kafa hujja da cewa ai ban san ta dawo ba saboda nace in ta shigo ta

sanar dani kuma bata gaya min ba don haka nake tsammanin ko bata dawo ba

ne nan dai muka dan zanta mukayi sallama abayan na tambayeta ya nayin jikin

nata.

Rana daya takk wacce na tabbatar bazan taba mantawa da ita arayiwata

ba itace ranar 15-05-2019 wannan rana kuwa itace ranar da ko a mafarki ban

taba tsammani zata zo min ba, kar dai in cika ku da surutu ainihin abin daya

faru shine ranar da muka dauki azumi na goma misalign kkarfe shida na safe ina

kwance kawai sai na ji karar shigar saqo a cikin wayata da sauri kuwa na duba

sai na tsinkayi sako daga wata number da sanyawa suna Nana Ayeesha, cikin

sauri na bude ina tsammanin zanga rubutu cikin screen sai nag a wani dan

kankanen rubutu wanda ko layi daya bai cika ba amma tasirinsa yafi karfin

kundi guda , abin da rubutun ke bayyanawa shine

I Luv you
Iyakacin abin da sakon yake nunawa kenan, na sake dubawa da kyau har saida

na tashi na zauna na share idona sannan na sake dubawa amma dai banga canji

ba abinda na gani da farko shi nasake gani cik, zuciyata ta tsaya tunaniya ya

tsaya na koma kamar itace saida na kwashi kusan minti goma ahaka sannan na

farfado nasake duban rubutun naga bai canja ba sai na fara tunanin “wai anya

ma tasan wanda ta turawa kuwa?”, ban sami tabbacin cewa tasan da zuwan

sakonba said a nag anta da nikab aranar haka kuma duk in ta zo wucewa ta inda

nake ko waye awurin bata yarda ta waiga koda inda muke ballantana tayi mana

Magana. hakanan na kasance awannan wuni kamar wanda akayiwa albishir da

cewar an bashi auren wacce yakeso, zuwa dare kuma abinda ya faru na barwa

zuciyata saidai in mutum ya bukaci ya sani sai ya tuntubeni ta lambar wayata

09032287375 don aranar kawai dai don ban ganin iyayena ne yasa bazance

agida nake ba domin babu abinda ya canja.

A haka rayiwa ta cigaba da kasancewa har mukayi azumi kusan ashirin

sannan muka tafi gida kasantuwar an daga exam sai zuwa baya salla.

Bayan salla tazo ta wuce muka koma makaranta domin yin exam, Tunda muka

fara exam har muka gama bamuyi haduwar da ta kaiwa minti goma cikakkiya

ba karewa ma ranar da zamu bar school bayan mun fito daga exam hall saida na

jirata ta fito amma abin mamaki tana fitowa kawai saita wuce kamar bata

ganniba, abin yayi min ciwo amma tunda ni kesonta yasa na bi bayanta

alokacin kuwa suna tafe ne tare da wani course mate dinmu mai suna jibril
sulaiman said a naje gani gata amma sai ta sake nuna ko in kula akaina ta cigaba

da Magana dashi, zuciyata tayi daci matuqa musamman ma da na fuskanci

labari kawai take bashi ba wata Magana bace mai muhimmanci daza ace wai ya

dauke hankalinta, saboda zuciyata alokacin babu 80% daga ciki yasa na cigaba

da binsu kamar wanda aka daurawa igiya har muka kai gate din super market

din school din sukayi sallama har na dan tsaya na tsammaci zata waiwayeni

amma sai naga kawai tasa kai tayi gaba kamar batasan ina wurin ba, hakanan

nima na wuce hostel da niyyar in karasa yan shirye shiryena in karawa motata

mai,

Bayaan na gama tattarayan tsummokina sai na fita neman ani gaye da aka turo

min kuind mota ta account dinsa tun kwana guda da ya wuce amma wai bai

sshigo ba hakanan na cigaba da bibiyarsa don jin labarin kosun shigo ko

basushiga ba Daga karshe ya gaya min cewa har ballance ya duba amma babu

alamar shigowarsu don haka nazo na saba tsohuwr jakata na kira ita Aishar a

waya na sanar mata cewa na fece, ina fita kuwa na biya ta gidan yayata wacce

nake kira da yaya Nafi, na nemi ta bani 500 naira na cemata cikon kudin mota

zanyi snnaan nasa kai na nufi kano. Nasauka kenan a yan kura sai naji wayata

tana kara cikin sauri na uba sai naga number Aisha sai na kyal ban dauka ba da

niyyar sai na sami wuri na tsaya kafin na kirata, na sawa mai napep hannu ya

tsaya nace ya karasa dani unity road dayake nan nake shiga motar Pambegua na

shiga kenan sai na sake ganin kira har sau ukku wanda hakan yasa na kirata tun
kafin nayi magana sai take tambayata "nace ba... ka tafi ne ?" na ansa mata da

cewa "eh na tafi ya akayi?" sai ji nayi tace "kaih gaskiya in bakai nisa ba ka

dawo saboda an fara issueing din Teaching practice foarm kuma sunce in

mutum ya dade bai ansa ba akwa fine due" sai nagaya mata cewa ai harna shiga

kano amma zan dawo kawai in karaba muka yi sallama sai nace da me napep

din ya tsaya in sauka na biyashi ya kara gaba, daga nan sai na sake shiga bus

don inje Gidan wani wan mamana da yake a daurawa wurin mahaifiyar

mamarmu wato kakata kenan don in karbo kudin udin motar komawa Bichi

saboda ko dama niyyata itace innashigo kano kawai zan shiga motar pambegua

in naga an kusa sai in kira a biyoni da kudin motar tasha amma tasowar wannan

maagana ta T.P yasa na canja don haka nayi amfani da naira darin da tarage a

aljihuna na karsa daurawa, wani rashin sa a da akayikuma shine ita hajiyar ta

fita kenan na shiga aka ce dani ta tafi gaisuwar mutuwa , duk nauyin bakina

haka na daure na labartawa aunty wato matar wan mamartawa duk halinda ake

ciki, sai dai kuskure daya da nayi shine da nace nazo wurin hajiyane in ansa

kudin motar komawa sai kuma gashi ba ta nan to inajin da wata kila bata

fahimceni bane sai ta masa min da to kawai, ni kuwa sai na kwashi jikna na

wuce dakin ita hajiyar na zauna, ban dade ba sai aka kawo min abinci naci sama

sama don kuwa na dai cine kawai amma ba dadin sa nak jiba kasantuwar

yanayina don kuwa aduk lokacinda aka ce yau akwai wani abu da na sanya

araina to tabbas in ban sameshi ba hankalina baya kwanciya,


Na dan jima azaune kafin daga baya na fara jjin gajiya ajjikina sai na

shiga daga cikin dakinta na kwanta kan yar doguwr seat dake ciki kafin yan

mintuna kuwa sai bari yya kwasheni, afirgice na tashi don jin wayata na kara

domin dama kiris nake jira ina dubawa sai naga number mamata na dauka tare

da yin sallama cikin muryar barci sai take cewa ya akayi ban tambayi aunty ba

ta bani kudin ? sai na mayar mata cewa kawai dai na gaya mata nazoo ne in

hajiya nanan in karbi kui awurinta sai aka ce dani bata on haka nace bari

injirata daga sai tace inje in karbi kudin wurin aunty, kafin ma in fita inje

dakinata ma sai gata tashigo dakin ta tamabayeni abin da zai isheni zuwa da

komowa nan na fadimata ta dauko ta bani na dauki hanya kafin in karasa school

din ita kuma Aisha ta tafi gida, haka nan na karasa na koma dakin da na zauna

saidai haka na tarardashi kamar anyi yaki aciki na dan tattara abinda zan iya

tattarawa na kawar sannan na sami wuri na kishingida, duhun yamma na farawa

kuwa Arzikin bichi ya fara addabata wato sauro dolece tasa na tashi na fita ina

dan takawa don dai kawai kar in zauna saboda matukar zan zauna tofa sauro ya

ringa ragargazata kenan kamar Aminu ya sami sweet potato.... indai takaita

zancen haka nan na kwana cikin matuqar takura babu katifa sai katako hakanan

babu abin rufa bare matshin kai da gari ya waye na je na karbi form din na sake

auko hanya na nufo kano .. na karasa gida

Nayi kewar Aishatu ciin hutunnan duk da cewa muna waya da ita almost

every night a haka har hutun ya kare sakkamakon dama formally hutun sati biyu
ne kacal, hutun ya karene ana saura sati kamar hudu babbar salla don haka yasa

kai tsaye ita Aishar tace bazata koma ba sai bayan sallar ni kuwa jincewa an

fara karatu yasa na tattara na koma school ana saura sati biyu salla,haka nan

school din takasancemin very lonely boring and the rest of some unfavorability

a haka har sallla tazo ina school don A garin bichi nayi sallar idi kafin daga

baya na shiga kano nayi kwana uku sannan na sake dawowa school.

In brief Aisha ta dawo makaranta lahadin bayan sallah ta fara lecture

ranar litinin bamuyi wata kyakkyawa ganwa da itaa ba har kusan karfe sha daya

bayan mun fito daga micro teacjhing practicum sai na sameta zaune kan waiters

dake karkashin s.l.t kamar abin arziki sai na kaimata wani note nace ta kwafa

saboda amatsayin assignment yake kuma ranar za a karba, definition na wasu

terms akace arubuto kuma ni a wayata babu dictionary sai nace tayi amfani da

dictionary na wayarta tayi nima zanje inyi nawa daganan in karasa assignment

na chemistry da aka bayar, hmm abin mamaki sai kawai ta basar dani, ga page

din danake mata bayani daban amma sai ta bude wani wanda nikaina atake ban

iya fadin meke ciki sai na duba sai take tambayata game dashi , abin ya bata

min rai amma sai na barshi amatsayin wasa na ske cewa “hnm-nmh waike da na

buda miki wurin da zaki kwafa kuma kin bude wani wuri” na fadi haka tare da

ansan littafin na sake bude mata wurin amma sai tace “eh naji ni nan nakeson

gani” alokacin sauri nake inj hostel in dauko foolscap don inyi assignment din

amma sai kuma ga abinda taje fadimin duk da haka sai nace “wai ke zaki kwafa
ko in wuce da abina?” hmm Allah day ya kyauta abin mamaki sai kawai ta ciro

paper daga littafin kailani ta miko min wai “gashi kayimin” babban abinda ya

bani haushi shine yadda kailani ya fashe da dariya yanayimin hannunka mai

sanda harda fadin “a lallai yarinya kin san solution , kai kuma ai sai ka karba

muje” abin ya ban haushi matuka amma sai na basar na nuna kamar ba komai

nace da kailani “rabuda ita dani take” na fadi hakan tare da mikewa tsaye nace

yaxo mutafi abu kamar wacce akayiwa allura kawai sai tayi zumbur ta mik tare

da daukar Jakarta ta ajemin littafin awurin kawai ta dauki hanya kamar ta bace

don ayanayin takunta na gani ga kuma fuskarta kamar zata sa kuka, alokacin sai

nayi dariya nikuma sannan muka tashi muma muka bi bayanta doon tafiya

hostel, shi kuwa kailani tsabar neman Magana wai sai ya bita wait a bashi aron

notebook zai kwafi note, ko waige batayi bat a kai hannu cikin Jakarta dake

rataye akafadarta zata dauko sai nace dashi “kai mujje inashi zan baka” jin haka

yasa ta fasa ta cigaba da tafiya yana zuwa wurina nace masa bani dashi harta

kusa kulewa ya bita da magiya ya karbo littafin.

Bayan misalign sha biyu da kusan rabi n agama nawa assignment sannan

na sami foolscap nayi mata nata amma sai nayi ta kiran wayarta bata dauka wai

tayi fushi dani , hakanan n agama assignment din muka koma school, karfe biyu

muka shiga lecture da shigowarsa kuwa yace a tattara mas assignment na hada

duka na bayar snnan na cigaba da kiran wayarta amma duk abanz daga baya ma

sai ta kasha wayar , iya damuwa na damu ganin ko lcture bata zo ba kuma tun
safe na gaya mata abubuwan da za ayi ranar amma tunda ta koma hostel bata

fitoba kum nasan bai wuce akan maganar safe bace , iyadamuwa na damu

kasancwar na ria nayi nisa cikin sonta ko kadan benison dmuwar tta don haka

yasa banyi zuciyaba naciga bad a kiran numberta amma duk ga banza sai can

misalign karfe goma na dare sannan na kira ta dauka shima ahaka tana dai

maganane amma daji kasan ranta abace yake, duk da nasan kwanan zancen

amma sai na tambayeta “baiwar Allah ba fada me yakawao gaba?” hmm abin

mamaki sai naji tace “akwai mana…” tayi shiru daganan ni kuma sai na sake

tambayar ta “fadar? Yaushe aka fara kuma me yafaru?” akule tace dani

“kamanta da safe?” “oh am sorry kiyi hakuri ni wallahi nama manta na dauka

wasace ai” haka na fadi yayinda na nuna kamar ban san maganarba, ita kuwa

shiru kawai batace komai ba sai na sake cewa “nace kiyi hakuri bakice komai

ba” cikin shagwababbiyar murya tace “to kai shikenan kullum sai dai karinga

batamin rai sannan kace inyi hakuri gaskiya nib azan yarda ba” alokacin wani

abu yazo min wuya na rasa me zance mata don maganar tata dauremin kai tayi

said a ga baya nace “ban gane bazaki yarda ba, baki hakura ba kenan?” sai bat

ace dani komai ba sai na sake cewa “to misali in kince baki hakura ba ya kike

son ayi kenan?” “nima ban saniba” haka ta mayarmin muryarta aciki ciki, nima

shiru nayi sai daga baya nayi ajiyar numfashi nace “baki sani ba?” sai batace

komai ba cikin wata defeating voice nace “to shikenan..” wanda nayi niyyar

daga haka kawai kasha wayar zanyi in hakura da sulhun donnanga alamar bamai

yiwuwa bane, amma kafin in kaiga rufe baki sai ta datseni da “to aikaine ko da
yaushe sai karinga yimin wulakanci, kuma gashi yanzu daga dawowata jiya ka

fara bata min rai” shiru nayi ina mamakin yanayin yadda take Magana kamar

zatai kuka said a ta gama sannan nace “toh yanzudai ai na baki hakuri kuma kin

nuna bazaki hakura bay a kikeson nayi dake?” alokacin sai tace “to amma

gasjkiya sai dai wannan yazama na karhe” nikuwa da abin ya kule ni sai nace

“ok shikenan yanzu sai ki fadimin sharudanki tunda nidai gaskiya ban san wani

abu da na taba yimiki don ya bata miki rai ba don haka kinga in na san sharudan

naki nan dai muka sasanta kamar abin arziki amma daga karshe sai tace wai

“amma gaskiya daga yanzu yakamata kasan lokacin wasa sannan kuma kasan

lokacin daba na wasa ba” jjin haka sai naji taaa bani haushi domin kuwa gani

nayi ita ta fara sako wasa alokacin amma sai gashi tana gaya min cewa wai

yakamat in san lokacin wasa “ok shikenan ba matsala ai hausawa sunce

maganin kar ayi kar afara don haka na sawa raina cewa zan kiyayeta kawai don

kar ma watarana in saki jiki muna Magana tace na wulakantata domin ni nasani

cewa kowaye kuma ko yaushe muka hau da mutum zan iya yi masaa wasa

matuqar zai fahimceni mukayi sallama na kasha wayata na kwanta.

Tun da mukayi haka da ita kuwa sai yakasance ko zan kirata bazan kirata haka

kawai ba sai da kwakwaran dalili haka kuma da zaran na isar da sakona sai in

kashe kawai in jure duk wani yanayi na kewarta dazanyi, haka zalika in muka

hadu sai dai tace dani sannu in amsa da yawawa sannu kawai ta wuce in wuce

sai in ta wuce in waigeta kasancewar bazan iya jurar dogon lokaci batareda na
ganta ba amma ya zama dole in sakaya damuwata akanta ahaka har kusan sati

guda domin tun ranar monday da dare da abin ya faru har sai ranar asabar

kasancewar na saba kusan duk lecture nakan kirata 5 minutes before the time

idan naga ban ganta ba, amma kuma ranar kaewwai sainaji bani da ra\ayin

kiranta don haka ban ko shiryaba sai miisalin karfe tara da rabi dana gama

shirina sai na fito daga block din na zauna kawai a tushen bishiya ina jina kamar

mara lafiya don wallahi kwata kwata bana jin dadin jikina, ina zaune anan

wiurin sai ga kiranta na kashe na kirata sai take cewa "wai baxaka fito bane?"

nikuwa sainace "zan fito mana, ya zone?" "a a bai zoba tukunna amma naga

kowa ya hallarane kuma ban ganka ba uakamata ka taho" haka ta fadi cikin wata

murya ta nuna alamun damuwa (concern) sai nace "to shikenan ganinan zuwa"

na sake shantakewa don ni nafi son inje intadda ya shiga ko kuma ina zuwa ya

shiigo don in har na riga malamin zuwa to fa lallai dole in ringa kallon inda

takke kuma lallai zata gane ni, ba afi mintina biyara ba sai ta sake kira ba kamar

yadda na saba ba sai na daga kawai na kara akunne sai naji tana cewa "ya shigo

fa" ta fadi hakan cikin fada ni kuma sai kawai nayi saurin kashe wayar sannan

na tashi na nufi school din cikin sa a kuwa na shiga bai fara ba, abinda na sani

kawai shine yayi min worning kan kar in sake zuwa masa aji late. sakamakon

yanayin da nake ciki alokacin yasa na kalleshi kawai na wuce naje na zauna,

kazalika tun da na zauna ban yiwa kowa magana ba hasalima ji nayi kawai

kwancitya tafiye min wannan zaman sai na dan kwantar da kaina kan desk din
dake gaba na ina yi ina dan tashi don nkara malamin ya gane cewa ina kwance

ne

Haka dai aka gama lecture babu ko dadi awurina donma dai mafiya

yawancin abinda yake koyarwa is part of my past experience shiyasa ma ban

wani damu ba, malamin na fita sai na tashi zan fita sai na tuna da maganar

micro teaching practical domin kuwa mun forming na group wanda ya kunshi

zallar yan combination dinmu wato chemistry mathematics, kuma ni da na karbi

head na group din sai na suggesting cewa ya kamata mu zauna don mutattauna ,

to gashi kuma banason yiwa Aisha Magana don karta dauki abin wani iri sai na

sanar da kawarta cewa “please ki sanar da Aisha cewa akwai meeting da za

atattauna kan issue na micro teaching practicum amma in zata iya zuwa” kamar

ajirac take sai tace “zama ta iya zuwa kuma in kun gama nima inason Magana

dakai muje ma yanzu” haka ta fadi yayinda ta tafi takirawo ita Aishar muka

sami wani empty class muka shiga saboda kawai bana jin dadin jikina yasa

bayanin nayi musu sama sama muka fita

Bayan mun fito ne muka kama hanyar komawa hostel sai ita Raihanar tak

tambayata kan wasu abubuwa marasa kai bare tushe, amma babban abida ataek

tambaya kai bai wuce akan maganar Ita Aishar ba, ni kuma tun da naji haka na

fahimci me take son fadi, atakaice naso inyimata bayani amm sai naga ta bukaci

dogon zance saina fasa mata komai tun daga farko har karshe domin naga da
farko laifina kawai take gani. Zuwa can dare misalign tara sai ga kiranta muka

gaisa sumul kalau.

Tun daga annan lokacin bamu sake samun wani sabani ba sai ma naga kamar

kulawarta gareni ya dan karu ta hanyoyi da dama wanda ba sai na fadi ba

Haka rayuwa ta cigaba da kasancewa ahankali ahankali tsakanina da ita

babu mai jinmu dukda dai ko ada din ma babu mai jinmu illah kawai da na sani

cewa daga ni sai ita muke sanin ko akwai matsala ko babu donkuwa nidai ba za

a ji abakinaba saboda sirrinane koda kuwa ni na cutu ban fadiwakowa,wasu

lokutanma har assignment take attempting zata yimin amma ni nake nuna bana

son ta wahal da kanta. Kwatsam sai wata safiya ta monday tazomin wanda nayi

matukar raina kaina aranar na kumma debo kokonto na zubawa zuciyyata

agammeda Aisha wanda da farko ni dakaina na san bai kamata zuciyata tayi

wannan tunaninba tunda har abinda yasani wannan danyen aikin bai tabbata

gareniba , wannan al’amari ya farune sakamakon ganin zoben Aisha da nayi

ahannun Rabiu Musa wanda na tabbatarwa da idona cewa baifi kwana biyu

rabona da ganin zoben a hannun ita Aishar ba bayaga cewa ta fadimin cewa

babu komi atsakaninta dashi,wani matsanancin kishine mai radadi ya tasomin

azuciyata duk da cewa ban tabbaatar ba, zuciyata tana bani cewa akwai

yiwuwar asami zoben ya zama iri daya ne bawai natanbane ahannunsa wanda

awannan gabar nake samun sauki araina amma daga lokacin da na sake duban

zoben naga babu wata maraba tsakaninsa da na Aisha sai inji kamar in hadiyi
raina kawai in tafi kowa ya huta don har zuwa nayi muka sake gaisawa na sake

duban zoben sosai don har tabashi da hannuna nayi Amma dduk da haka sai

kawai na sake share lammarin na barshi araina cewa kila guda biyu ne , har ina

fadi araina cewa indai kuwa daban daban ne to lallai zan yi kokari insa ta cireshi

ahannunta don tsananin kishi a haka har suka gama shiga mota suka fita zuwa

wurin excursion din da suka shirya zuwa aranar.

Haka na tattara na koma hostel jikina ba karfi domin wannan ala’amarida ya

faru, don ni ban ma ganta ba saboda munyi waya da safe cewa ba za ayi lecture

da safe ba,

Da gari ya waye ranar talata muka sake fita wurin lecture ranarma saboda babu

wasu qwararan lectures da z ayi aranar yasa bata fito ba. ,misalin qarfe goma na

safen na kirata bayan mungaisa sai na fara bugun cikinta cikin dabara amma

sam sai na lura bata fahimceni ba don hirace muke kamar haka

Ni: sonake in tambyeki amma sai kinyi alkawarin xaki bani amsa dai dai da

saninki gameda abinda na tambayeki

Ita: Toh Allah yasa nasan amsar

Ni: yanzu dai kifara duba hannunki kigayamin menene ajiki

Ita: kamar ya kenan ?

Ni: ki duba hannunki ki bani labarin abinda ke jiki


Ita: (cikin dariya) hmm nidai banga komai ba sai fata da jijiyoyi da suka fito

Ni: (cikin qaramar dariya) a a ina nufin wani abu kamar agogo ko awarwaro ko

makamancin haka

Ita: gaskiya babu komai

Ni: ok da akwai ko babu ?

Ita : dama babu komai

Alokacinda ta fadi haka sai naji kamar ta mareni don jinayi kamar tadan

raina tunanina don ganin na santa da zoben tunda dadewa amma yanxu tace wai

dama babu. Daga nan kawai sai nace “ok shikenan na gode..” kafin in kashe

wayar sai tayi saurin cewa “amma duk me yakawo wannan tambayar?” sai na

mayarmata da “hm babu komai kawai naso inji ko akwai wani abu a hannunne”

“hmm to banyarda ba kawai ka gaya min dalili” haka ta fadi cikin rah anima

cikin raha nace “to shikenan project nake rubutawa shine nake miki interview”

sai duk mukayi dariya sannan tace “to wane irin project ne agayamin inji” “a a

ki bari in nagama rubutawa zan kawo miki ki karanta” nan dai mukayi ta

musayar zance cikin raha daaga karshe mukayi sallama na kasha wayar, daga

nan kuma sai na sake tsunduma cikin tunani MENE NE MATSAYINA

AWURINTA ? ina cikin haka sai na tuno wata shawara take sai na kirata sai

nace ta fito alokacin sai tace wai zatayi wanka sannan ta fito sai nace to
shikenan ya wuce domin dama alokacin nakeda bukatar ganinta sai tace inyi

mata uzuri sai tayi wanka na sake cewa ya wuce.

Daga lokacinne na fara tunanin ko kila ta fahimta ne sai naji abin ba dadi har

matsanancin kishina ya sake motsawa wani abu ya taso ya tokaremin kirjina don

har jinake kamar zan fadi idan na mike, ahaka har kusan karfe biyu sannan na

tashi ko wanjka banyiba nashirya na fita wurin lecture na Organic Chemistry

wacce za’ayi karfe 2:00 pm na fita da wuri na isa science complex amma babu

kowa don haka muka fito nida wani cours mate dina Umar Idris don muje GSE

mu duba result mun fito kenan sai mukahadu da ita da kuma kawarta Raihana

sama sama muka gaisa domin har zuciyata ban wani yi fari cinki da ganinta

kamar yadda na saba ba suka tambayeni venue na gaya musu muka wuce suma

suka wuce batare da Karin komai ba

Zuwa mukayi bamu tarar da mutumin da ke duba result din ba don haka

sai muka dawo zuwa wurin lecture muka taras matar bata ma zoba , zuwa nayi

na sami wurin na zauna bayan na gaisaw da wanda nake ganin zan iya gaisawa

dasu acikin mate din nawa bamu dadeba sai suka tashi zasu fita wai zasu je

wani wuri acikin gari sun fita kenan sai kuma suka dawo tare da lecturer day a

kamata tayi lecture alokacin, nan ma bsu jim ba sai naga sun tashi sunfita koda

dai kafin fitarsu sai da na tura mata takarda mai dauke da “where is your ring?”

alokacin sai naji sunyi dariya dukansu bankuma ji respond ba abin yayi min
ciwo amma sai na share wai sai can da za su tafi sai tace wai agayamin idan za

dauki attendance in rubuta sunanta.

A haka dai yinin yakare inajina kamar an zare min farin cikina don kuwa

ko aiki banyi niyyr yi ba da dare kawai zuwa nayi na sami wuri silent na zauna

donkuwa bana bukatar jinmotsin wani akusa dani, ina cikin haka sai ga kira

kamar daga sama daga dubawa sai naga kirran Raihana wato kawar ita Aishar

na daga sai suke cewa wai don Allah in fito suna on suyi practice na Mat 221

wato Dynamics cikin kuna rai dai na maa musu da cewa to in sunnfita sai su

kirani na kuma zaunawa raina nayimin daci misalin takwas da rabi nafit na

iskesu cikin room a ACL wato area classes, muka fara dubawa a hankali sai na

lura ita Aishar hankalinta na wani wurin sometime ma sai inga ta hda kai da

desk ko in tsinkayeta tana kallona. Da naga abinyayi yawa sai na tambayeta ko

lafiy sai tace min wai lafiya lau, shiru kawai nayi mukacigaba da duba takarda

har kusan karfe goma da rabi sannan sai nake cewa da ita "na tambayeki ina

abin hannunki yake baki bani amsa ba" sai tace "ka bari zan gaya maka"

"yaushe?" "in mun tashi" na amsa da to shikenan muaka cigaba har sai da goma

takai da minti talatin da biyar sannan nace dare yayi muka tashi don tafiya

hostels, nidai ban tambayeta ba ita kuma bata tada maganarba muka yi sallama

na nufi block dinmu suma suka wuce nasu hostel din, aranar sai bankirataba

kamar yadda na saba sai da kamar sha daya tayi sai ta kirani, kasamntuwarba

kudi awayar sai na picking tare da sallama ta amsa sai bata sake magana ba
nima sai nayi shiru don kuwa ni bani da ta cewa alokacin sai daga baya tayimin

wasu tambayoyi wadanda a tunanina bawai sune silar kiran ba kawai dai ta

tambayeni ne don ta bugi cikina in tambayeta. Bayan na amsa mata

tambayoyinta sai tace min ta gode sannan ta kasha waya bayan kamar minti

biyar sai ta sake kira na sake amsawa awannan karon sai ta sake mai mai tamin

tambayar farko da tayi min da sunan bata fahimci amsar da na bata ba bayan na

sake yi mata bayanine sai muka sake sallama ta kasha wayar, ni kuma sai na

sake hayewa gado na kwanta zaman jiran tsammani don kuwa sai dai ince jiran

tsammani don na tabbata komai so na da barci aranar nasan bazai zo ba sai dai

wani ikon Allah kuma, Nayi zurfi cikin kogin tunani wanda yakai extent din da

banma san me nake tunawa ba alokacin sai vibration din wayata dake bisa

kirjina ya dawo dani cikin hayyacina cikin sanyin jiki na dauki wayar na duba

sai nag a sako aka turo da na duba sai naga text kamar haka : “yana gun Rabiu

musa zoben”. Iyaka abinda sakon ya kunsa kenan wani irin abu naji a qirjina

wanda ban ma san y azan kwatanta shiba don har idona sai da naga duhu nay an

sakanni sannan ganina ya dawo normal zuciyata kuwa haka take bugu kamar an

harboni da bindiga na kuskure bullet din nan na saki wayar akan gado na rufe

idona ina jiran ikon Allah ban san sa’ar da nayi barciba nasandai na farka dai

dai lokacin da aka bude kofar dakinmu alokacin kuma karfe biyar tayi,

dafarkawata kuwa wannan sakon dana karanta da dare ya sake dawowa zuciya

ta tacigaba da maimaita shi har nayi sallah na dawo daki na kwanta amma sai

naji zuciyata kamar ana hura min wuta na fara jin haushi ba gaira ba dalili
domin kuwa Magana ma ban son yi, da naji abin na neman wuce gona da iri sai

na tashi na dauki Qur’ani na fara karantawa sai asannan na fara jin dama dama

yakasance zuciyata ta fara rauni don ji nake da nikadai ke adakin kuka zan fasa

ahaka har sai da bakwai tayi sannan na tashin don inje inyi wanka

Bayan na gama shiri tsaf na fita don zuwa lecture sai na sake jin bana son

kowa ya dameni awannan yinin hakan yasa nakoma na dauko wani kyalle na

daure fuskata dashi yakasance iyakar idanuwanane kawai awaje nasake fita

hakan ma sai naji bai gamsheni ba nasake koma na karbo wani bakin Radar (eye

glasses) nasaka wa idanuna sannan na fita awannan shigar na nufi lecture hall

aranar English zamuyi da safe da na isa sai na taradda lecturer bata zo bah aka

nan muka zauna jikin wani dakali dake gefen A.U muna jiran tsammani can sai

na hangi Aisha sun taho itada wasu yammata guda biyu wadanda ban ma san ko

suwaye ba lokacin da suka kusato inda muke sai naga kamar ta gane ni domin

alokacin na fuskanci idonta akaina yake don haka saina ce da Abdulkadir wanda

alokacin ke zaune kusa dani “yakamata mu tashi fa don kasan Karin maganar

kifi ance Zama wuri daya tsautsayi ne” daga nan sai muka tashi muka koma

kusa da central mosque na makarantar muka zauna bamu jima ba sai na sake

hangen ita Aishar sun isa tushen wata bishiyar cashew sun zauna, alokacin sai

naji gabana ya fadi don atunanina ta ganeni yasa ta biyo don ta tabbatar cewa ni

dinne ko bani ba. Atakaice dai haka ranar muka yini bamu hadu wuri daya ba

don ko da muka shiga wata lakcar ta department zan iya cewa ban sata a idona
ba sai dai kawai da muka fita sai na hadu da ita a bakin kofa don ni daman a

barine sai ta fita ta kama gabanta tukunna sannan ni in fita, Awannan lokacin da

na tabbatar ta gane ni yasa na janye kyallen da na daure fuskata dashi sannan

mukayi wa juna Magana bayan mun gaisa ne sai nace da ita inba wani abu za

tayi ba inason muyi Magana, kai tsaye tace “to muje dama hostel zan koma” ta

wuce gaba na bita abaya kamar igiya har wani class dake sashen ISC classes

akasan science complex muka shiga ciki muka zauna, na dauki tsawon lokaci in

ataraddadin abinda zan fadi mata sai daga baya na cire bakin tabarau din dake

idona nayi ajiyar numfashi, ita kuwa alokacin ko kallo ban isheta ba biro ne

ahannunta tana zane ajikin bangon littafinta sai dai na tabbata hankalinta da

kunnuwanta suna tare dani tana jiran taji nayi Magana, Ajiyar zuciya na sake yi

sannan nace “jiya na tambayeki game da zobenki baki bani amsa ba” da suri ta

kalleni tace “nabaka amsa mana” … “dayaushe kenan kika bani amsa” “da

daddare na tura maka ta text, ko be shigo ba” alokacin da ta fiurta haka sai da

na sake tuno abin da ya faru sa’arda message din nata ya shigo wayata, daga

baya sai nace “ya shigo amma ban gane me kike nufi ba” kai tsaye kuuwa tace

“cewa nayi yana wurin Rabi’u Musa” adai dai lokacin da tayi wannan furuci sai

naji kamar ta mareni a tsakiyar kasuwa, shiru nayi nadan lokaci kana na kalleta

shima na dan lokaci wanda hakan yasa ta cewa “me ya faru?” sai nace da it aba

komai kana daga baya na sake cewa “ke kuma haka kawai sai kikaji ya dace ki

bashi zobe?” sai tace dani “a a shi yagani yace yanaso inbashi ni kuma na

bashi” awannan karonma sai da naji zuciyata kamar ta fashe don bakin ciki
kawai basar wa nayi nace “to shikenan tunda ra’ayimkine” awannan karon

batace komai ba sai dai kawai da taga na tsare ta idona yasa tace “meyafaru?”

ajiyar zuciya kawai nayi nace “a! ba komai” saboda yadda take azuciyata yasa

bantashi na bata wuri ba don har ga Allah ji nake babu abinda zata yimin da

zaisa son da nake mata ya ragu acikin zuciyata. Duk kokarina alokacin in tausa

zuciyata domin kuwa maganganu ne da dama acikina ban Ankara ba sai na

tsinci kaina ina ajiyar zuciya duk bayan second biyar sai dakyar da dauriya nace

“amma ina fata kin san matsayin kyautar zobe a al’adar bahaushe ko?” hhhhh

abin dariyar da ya faru alokacin wai sai tace “a’a ban sani ba” a madadin abin

yabani haushi sai ya bani dariya wanda hakan yasa ta kallona cikin mamaki tace

“lafiya?” dariyar nasake yi kana nace “hmm lallaine bamma dai kinsan ke ba

yarinya bace haka nan nima kin san ba qaramin yaro bane da za’a fadi Magana

wacce koda kwakwalwarsa bata gamsu ba zai basar da tunanin kila iliminsa ne

bai kaiba” fuskarta cike da mamaki sai tace “,me yafaru nifa da gaske nakeyi

wallahi ban sani ba” fadin hakan da tayi yasa nayi da nasanin taso da

maganar ,ma don ji nayi aduniya ta gama rainamin wayo, ace kamar ta kuma

bahaushiyab tace wai bata san ma’anar kyautar zobe ba, kallonta kawai nayi na

kau da kaina taree da furta wata maganar da ni kaina ban san me na fadi ba

ganin haka da nayi yasa ta ce “tunda ban sani ba kamata yayi ka gaya min sai in

sani daga yau” “a’a ni bazakiji abakina don komai na fadi zaki iya daukarshi

amatsayin son rai” haka na fadi ba tare da na kalleta ba don alokacinma ji nake

kamar in tashi in bata wuri. Sai tace “wallahi bazan dauka haka ba” “kin ga
manta kawai ya wuce in Allah ya kaimu lokacin da kika sani da kanki sai ki

fahimci yadda nake ji” ina rufe baki naja kyallen fuska ta sama kallo na tayi

tace “to in karbo?” “a’a ba da yawuna ba babu ruwana, ki bashi kyautar abin

sannan kicee zaki karba, kinyi me kenan?” “a a wai tunda bakaso sai in karbo”

“to ni bance ba in kuma neman izini kike ban amince ba” cikin fada fada na

furta hakan don raina ya fara baci. Cikin wani yanayi kamar na damuwa ta

kalleni kana ta kauda kanta sannan tace “don Allah ka fadamin” “ki bari ki

tambayi Raihana zata gaya miki” da jin haka sai tace “dama ita nake jira kawo

wayarka in kirata sai tazo yanzu ta fada min” ban ko kalli fuskarta ba sai kawai

na tura mata wayar ta dauka ta kira number Raihana sukayi Magana ko kadan ni

ban kai hankalina wurin ba, bamu jima ba sai gata ta iso bayan mun gaisa sai ita

Aishar take tambayar ta game da abinda muka tattauna da ita da buda bakin

Raihana sai tace “ya danganta da yadda kyautar takasance don ka bawa mutum

kyutar zobe ba wani abu bane, kawai mutumci ma zai iya sawa” “hmm daman

nasan za’aayi haka don nasan bakinku daya” “iya abinda na furta kenan nayi

shiru sai kuwa Raihanar tace “a a wallahi bah aka bane ai ita gaskiya duk inda

take fadin ta ake…” kafin ta rufe bakinta sai nayi hanzarin katseta da cewa “ok

dama gaskiyar haka take ? na tambayeki ainihin ma’anar kyautar zobe kina

cemin mutuncine kawai?” “a’a nace mutumci ma yanasa ayi kyautar zobe” inji

ita Raihanar jin haka ni kuma yasa nace “atsakanin mace da mace kenan ko?”

“a ai ko ma tsakanin waye da….” Saurin katseta nayi da cewa “ya kamata ku

ringa yin adalci aduk lamuranku, ke tsakanin ki da Allah abinda kika fada haka
yake,?” abin mamaki kawai sai ta fara dariya wanda acikin dariyar sai take cewa

“agaskiya in namiji ya bawa mace zobe ko mace ta bawa namiji zobe yana

nufin so ne , ko da dai akan samu amincin da zai sa hakan ta faru koda ba son

bane” tana zuwa nan sai tayi shiru wanda ni kuma hakan yasa nace “kamar

misalign yaya kenan?” “kanar wa da kanwa mana” tana fadin haka sai nayi

ajiyar zuciya nace araina Allah ya kama min ita ta fadi ainihi gaskiya sannan

nace to Alhamdulillahi tunda Allah yasa kin fadi gaskiya yanzu,” ko kallon

Aisha banyi ba nasake kasa da kaina, sai asannan sai Raihanar tace “wai ma

tukunna duk me yakawo wannan?” haka ta tambaya batare da ta tantance wanda

tayiwa tambayar ba wanda ni kuma adalilin haka ysa ban furta komai ba ban

kuma kallesu ba, Kallona Aisha tayi ganin ban nuna damuwata akansu ba kuma

bana da niyyar yin Magana sai ita Aishar tace “waifa akan zoben da na bawa

dan antine ya gani shiyasa yake wannan maganar”, sanda tazo nan sai tayi shiru

ta kalleni ni kuma sannan kunnena kawai na basu don in na kallesu raina baci

yake, Awannan karon sai Raihana tace “to wai yanzu meyake nufi?” “oho nima

ban san me yake nufi ba, to ko yana ganin kamar ina sonshine?,” da tazo nan sia

tace “Raihana don Allah ina son shi?” danaji abin na neman zama fooling sai

nace “kunga ni duk ba wannan ba dama tambayace nayi mata kuma tace bataa

sani ba don haka maganar ta wuce” cikin wata dariya kamar ta tsiwa sai Aisha

take cewa “to yanzudai in karbo kenan tunda nasani” “a a babu ruwa na ba

kuma zan umurceki da aikata wani abu da ya sabawa turbar gaskiya ba don haka

kawai na bar maganar tunda nasan ajin da nake” lokacinda nazo nan amaganata
sai suka kalli junansu sukayi dariya aciki sannan Raihana ta kauda kai ta fara

sakin zance kamar haka “sufa halin maza kenan basu wa mata adalci su da

sunga abu bazasuyi binchike ba sais u fara maganganu shiyasa fan a tsani

soyayya aschool dinnan..” ta karasa magnar aciki wanda nasan ita kadai ce zata

iya fadin abinda ta furta alokacin.

Raina yayi ,matukar dugunzuma yadda naga ga gaskiya kiri kiri amma sai

nine ma nazama mara gaskiya laifin ma gaba daya akaina aka dorashi wanda

hakan yasa na maida kyallen fuskata kana nasanya bakin tabarau din dake

gareni alokacin, kallona kawai sukayi sannan suka kalli junansu Raihana ta kebe

baki sannan tace “Aisha tashi muje hostel yunwa nakeji wallahi” ba tare da mai

da mata martini ba sai kawai ta waigo inda nake sannan tace “tashi muje”

tsamm! Na tashi kamar dama ajirace nake na kama hanya har sai da na kai

bakin kofa basu taso ba, nadan jira su kadan naga kamar tafiyar tasu basu shirya

yenta ba sai nace dasu “naga kamar bakujin tafiyane donn haka sai anjima” ban

ko jira sun bani amsa ba nasa kai na wuce aranar dai bamu sake haduwa ba.

A haka dai rayuwa ta cigaba wani lokacin sai inji kamar ban san

damuwaba amma wani lokaci sai inji kamar ban taba jin farinciki ba, saboda ni

mutum ne mai tsananin kishi wanda na tabbatar da wuya in sami wacce zamu

jitu sosai matukar inada wannan kishin, Akwai wani lokaci ma nakanji indai

ason raina ne ban so ko Magana tayiwa wani namiji in bani ba, ko kuma in ma

yazama dole sai tayi maganar to banso ta cika yawan dariya kamar yadda ta
saba yiwa kowa, amma sai gashi kiri kiri sai ingga tashiga aji ta zauna kusa da

maza, abin yana matuqar qona min rai sosai domin nikaina da sanina nake kin

zama kusa da ita alokacin lecture saboda ban san wani irin kallo za ayi mat aba

in aka ga namiji akusa da ita domin kuwa ita macece mai kamun kai wanda

kowa yasani she is very decent ga addini sannan da kokarin karatu, sannan ni

asanina zan iya cewa ko makarantar za a tara gaba daya babu wanda zai iya

bada shedar cewa gashi yau anji kanta da wata ko wani, tasan mutumcin kanta

yadda ya kamata, hakan ne yasa ban san zama kusa da ita saboda ina ganin

kamar zai iya zubar mata da mutiumcinta kasancewarta kowa yasan tana da

kamun kai sannan zai iya zubar mata da kima saboda kowa ya ganni ya ganta

yasan ta wuce ajina koda kuwa ba a binciki asali ba don haka yasa koda yaushe

nake jin kawai dai ta amsa tana sonane don kar tace bata sona yazama cin zarafi

a gareni, ina matukar shiga qunci alokacinda na tsinkayi wani namiji zaune kusa

da ita saboda koda ace ita ta kame to fa sai ka samu masu takalarta da zance

koda kuwa baza ta maida martani ba ballantana kuma ace ta mayarda martanin,

Nakan zauna nayi ta mazari akan meyasa kusan kowane namiji haka yake

muddin zai zauna kusa da ita saikaga yana kokarin takalarta da zance ko meyasa

haka oho shin sunayi don inji haushine ko don me? In kuma ba haka bane

halinsu ne ahaka meyasa ni ban jin ra’ayin yiwa mace maggana koda kuwa yar

wace ce domin wani lokaci ko dama ace yar uwa ta ce natujar bamu saba soai

bay i mata magna yana matuqar yimin wahala ko kuima halittace hakan oho, to

koma dai meye Allah ya kyauta.


Lokaci yaja matuqa muna tare ahaka duk halayyyata sai da suka canja har

takaiga nakanyi kwanaki sama da biyu batare da mun sami sabani da wani ba

saboda na koyi shanye damuwa koda kuwa wace irice, dalili dayane kuma

saboda aduk lokacin da tayi min wani abu wanda ya bata min rai wanda

atsohuwar halayyata sai na mai da martini matukar aka gayan Maganar da

batayi dai daio da ra’ayina ba, tofa dole zan shanye saboda ina matukar jinta

azuciyata bana kuma bukatar wani abu da zaisa taji ba dadi akaina, domin ji

nake kamar zata daina kulani in na fadi maganar da ta bata ranta, wanda ni

kuma hakan shine abinda yake bani tsoro.

Kwanci tashi rayiwa ta cigaba wata rana mun fito daga lecture Real

analysis under maths department wato mat 223 sai muka jero Da ni da kailani

da Raihana da Kuma Aisha, da farko mai da Magana muke kan abubuwan suka

faru alokacin lecture wanda kuma bayan mungama wannan sai muka cigaba da

tafiya muna wasu indistinct Magana ni da raihana muna gaba sai ita kuma Aisha

suna tare da kailani daga bayan mu kenan sai da muka zo har kusan shagon

agallawa mai chaji sai na ga Raihana ta dan dakata sai asannan ne na waiga

naga me ke faruwa sai asannan ne naga ashe mun barosu Aishar abayane

hasalima shi kailani ya tsaya suna gaisawa da wani gaye wanda ni ban ma san

kowaye ba don kuwa ban sanshi ba, ganin haka sai nace da Raihana “Ni nayi

nan sai anjima” ita ma ta amsa min da cewa “to shikenan Malam Aminu sai
anjima” daga nan sai na nufi hostel din mu don nasan Balallai bane kailani ya

gama abinda yake da wuri saboda sanin halinsa da nayi wajen surutu.

Da zuwa na daki kuwa saina fara kici kicin dafa abinci, ganin har naje na

debo ruwa na dawo na dora abincin ban ga kailani ya iso ba yasa na fita naje

super market don in diba shi ama da naje sai ban ganshi ba nan nasan ya ware

gidansu ne abin ya bata min rai matuqa don haka ne ma yasa ranar ban ko kawo

ra’ayin zuwa gidansu araina ba bayan sallar isha’I kuwa sai kawai na wuce

shago don kuwa ina da kwantain aiki da banyiba, haka kawai bansan me ke

damuna ba sai nake jina ranar rai abace kuma ban fara jin haka ba sai da na fara

typing din wani project wanda erro sukayi yawa aciki na farko spelling mistake

na biyu kuma rubutun duk a cukurkude sai na kura ido nake ganewa gashi kuma

Biology ne ba normal English terms bane aciki balle in ringa rubutawa dai dai

yadda nasan Kalmar nan fa naji raina yayi mugun baci wanda hakan yasa na

saki kida a cikin wasu kananun speakers dake shagon nasanya wasun waqqoki

guda biyu da suke ta maimaita kansu wanda ko kadan hankalina baya gunsu

nidai kawai banason jin wani abu daga ko ma waye, inban manta ba waqar

LOYAL ce ta chris brown tyga da lil wayne sai kuma waqar Ayo ta chris brown

da tyga, ina cikin haka sai nake jin kamar ana sallama sai na waiga sai na iske

Adam yusuf Adam ya gaji da sallama har ya shigo, ko kadan ban rage volume

na wakar ba ban kuma kashe ba haka muka gaisa sama sama sannan yace in

bashi charger yasa chaji, alokacin wayatce ajiki ko 30% bata kai bah aka na cire
na mika masa don kawai banason dogon surutu, yadan zauna na dan lokaci yaji

kara ya dameshi ya tashi yayi gaba aranar dai babu wanda ya jure iya zama

ashagon har kusan karfe goma sai ga Bashir wani room mate dina dan asalin

jihar kano ne shi daga Karamar hukumar takai acikin garin Faruruwa wanda

nake ganin aduk room dinmu babu mai shekarunsa don haka ya zama kamar wa

garemu sai dai shima yana da barkwanci sosai ina zaune yazo yayin sallama

shiru ba amsa don banma san yazo ba sai da yazo ya dafani sannan nasan yazo,

yafara Magana yaji kamar rada yake saboda shi kanshi bajin kansa yake ba

hakan yasa yadan dake ni yace kai da Allah karage wannan karar banzar ko ka

kashe, ban ko kawoshi aka ba alokacin kuwa kokarinake in gano wata kalma da

na kasa ganewa tun shigowarsa, ganin naki kulashi yasa ya dauke takardar

yarike yace ko in kashe ko ya tafi da ita dole tasa na rage, sannan ya fara jana da

surutu in maidamasa atakaice don dai kawai ya rabu dani daga baya sai ya sami

kujera yace in kunna masa film ya kalla don shi ba kallona yazo yi ba, saboda

sanin halin sa sai na kunna masa film din na projecting masa a wani separate

monitor dake shagon ni kuma na cigba da aikina da main screen din dan dole na

kashe waqar gaba daya abin ma bai tsaya iya nan ba sai ya ringa takalata da

Magana domin duk scene da akayi wani abu increadible sai yayi comment akai

kuma sai ya sani ciki wani lokaci in tanka masa wani lokacin kuma sai dai in yi

kamar ban jiba ahaka wasu yara daga kauyen dake kusa da makarantar suka

karu sai muka zama mu hudu ashagon, muna haka har wajen goma da rabi sai

ga kailani yana zuwa yace in bashi ruwa yasha , alokacin banyi niyyar kulashiba
amma danaji abinda yaxo dashi hajace da bata shallake kowa ba sai na dauki

fifty naira na bashi nace gashinan tafi ka kawon canji, ganin haka yasa shi kuma

yace “lallai ne P.G wato yau ni kake bawa hamsin kake gayan mara dadi ko?”

alokacin ya ban dariya amma sai na share nace kaga malam tai kaje kasha ruwa

in ka dawo koma meye ka hidi, dariya kawai yayi ya fita yana cewa ina dawowa

akwai Magana, ban tanka masa ban a cigaba da aikina duk na gaji da zaman da

nake ma har na kosa 11:00 pm yayi saboda akashe gen din makaranta intai in

kwanta, baifi saura minti bakwai a kashe gen din ba sai ga kailani ya dawo da

zuwansa sai ya fara cewa “kai zo nan kaji wani batu” sai nace bari in karasa

aikinnan da yaji haka sai yace “karfe nawa yanxu?” nuna masa agogo kawai

nayi ba tare da fadin wani abu bas hi kuma sai yace “ok an ma kusa kashe gen

bari in ka tashi munyi magnar” shima sai yabi sahun masu kallo,

Ana kashe Gen kuwa ko cikakken mintuna uku banyi cikin shagon

nan ban a tattara na fito na kulle sannan nace da kailani “to uban rashin

mutumci ina kaje dazu bayan mun fito lecture nayi ta jiran ka shiru”

alokacin wata shegiyar dariya yai yace “ka riga kasan halina, bama

wannan ba wata tambaya zanyi maka” “ina jinka” iya abinda na furta

kenan domin alokacin na riga n agama saukowa saboda har ga Allah ko

damuwa na shiga in dai muka hadu da kailani to karshenta kenan, da

budar bakinsa sai yace “dama Aisha ta gaya maka tana da wani saurayine

na daban?” ji nayi kamar an harbeni akirji kaina yayi min wani irin nauyi
nake jin kamar ba da hausa yayi Magana ba sai da ga baya na dan basar

kana nace “kai ban gane ba me kake nuhi?” shikuwa sai sake cewa yai ina

nufin Aisha nada wani saurayine daban bayan kai?” iya fadin maganar

ma kawai ta tayar min da hankali matuka dukda cewa nasan tana iya

yiwuwa yanayine don ya kada min ciki, dan tsaki na saki nace “kai

malam banson tsiyarka don Allah” shikuwa ganin haka yasa yayi dariya

yace “wallahi da gaske nake” rantsuwar sa ta girgizani matuka ammma

sai na maze na sakeyin dariyar yake don kuwa sai dai yake don alokacin

kirjina in banda dukan uku uku baa bin da yake “to naji koma dai meye

way a fadi maka?” “ya zaka ce wa yagayamin bayan na gani da idona”

“to ya isa haka wa ka gani?” “small mana wannan me cafe” yana fadin

haka sai na tuno lokacin da muke waya da ita nake cewa nib azan yi

election na S U G ba sai take cemin tana da candidate data keson in zabar

mata da na tambayeta sunayensu sai tace min da Usman Musa Da wata

Kafila Yususf sai kuma Bellon Hasan Gazara ina tuno hakan araina saina

karajin ba dadi amma daga baya da na tuna cewa dama tun farko nasan

tafi karfin ajina sai na dan sauko sai abin ya koma damuwa daga jin

haushi, ajiyar zuciya nayi alokacin sannan nace “to koma dai meye Allah

yafimu sanin gaskiyar lamari” daga karshe na sake yin dariya nace “to

waima inma saurayin nata ne ai niba wai abin damuwa bane awurima

sosai saboda dama nasan ba ajina bace bare ince dole saini kadai zata so”

kailani kuwa kwafa yayi sannan ya ciji baki yace “lallaima kai.. bai
katraasaba yai shiru yace “amma dai mai daki shiyasan inda ruwa yake

masa zuba” nima dai dariyar kawai nayi ta yake sannan mukayi sallama

yayi hanyar gidasu nikuma na nufi hostel dinmu kaina wani girim kawai

nakeji, haka naje na kwanta ko alwala banyi ba, nan fan a zurma ramin

tunani narasa abinda kemin ciwo, na kasa rarrabe wane hukunci zan

yankewa zuciyata shin incigaba da kishina ne ko kuwa in mika wuyane

kawai dominfa ni na riga na san cewa tafi karfina kawai ta amsaminne

don kar yazama ta wulakanta dan adam, to amma kuma aduk lokacin da

na tuna cewa in harfa na rasa ta to tabbas wanine zai sameta hakan sai

yasa inji wani bakin ciki, har infara wani sakaran tunani wanda in nayi

wasa tauhidina zai sami rauni saboda har jinake me yasa ni nakasance

ahaka ASTAGFIRULLAH saboda ina matuqar sonta kamar yadda

bantaba jin son wata araina ba, gashi kuma bias ga alamu bazan sameta

saboda karancin matsayina, Jin da nayi kwanciyar ta dameni yasa na tashi

karfe sha daya da yan mintuna sai na kira number Raihana domin wayar

Aishar ta sami matsala sai nai sa’a kuwa batayi barciba mun dan gaisa

sama sama sai take cewa dani Aishar tayi barci, to daman ni bba Aishar

nakeson Magana da it aba ita Raihnar ce, sai na fara Magana kamar haka

“a a karki damu dama ke nakeson muyi wata Magana dake” “to ni

kuma?” sai nace “eh kedin amma don Allah ina rokonki duk maganr da

mukayi dake banason ki fadawa Aisha komai nafison ni in gaya mata da

akaina bayan mun tattauna” haka na fadi mata abinda yasa na fadi haka
kuwa shine banason taji magnar daga wani harr anta y abaci dominkuwa

na tabbata bazata ji dadi ba shiyasa, take kuwa tace kar ka damu insha

Allah bazataji abakkina ba” “to nagode.. am dama sonake inji ko kinsan

meke tsakanin small da Aisha?” “small mai CAFÉ wai?” “eh shifa”

amaimakon ta bani amsa sai naji tayi wata tambaya wanda da farko saida

gaba nay a fadi cewa tayi “ban gnae ba me yafaru ?” sai naji hakan kamar

yana nuna alamun ta sani ne,sainace a a ba komai wallahi kawai jita jitace

naji yasa nake son inji kar inyi abinda ba daidai ba” ajiyar zuciya tayi

sannan tace “kaih nidai gaskiya bansan me ke tsakninta dashiba sama da

kawai tana kai masa photocopy kuma baya amsar kudinta amma nidai

gaskiya bansan akawai komai tsakaninsu ba” “to shikenan Raihana

nagode dama wallahi magna ce tayi yawa kan wai shi saurayin Aisha ne

shiyasa tun ina share wa har abin yafara damuna saboda rashin tabbaci

akai” haka na fadi kana ita kuma daha baya tace “gaskiyane dole abin

zaio dame ka, amma ka tambayeta mana kaji daga bakinta” “a a basai na

tambayetaba tunda har kema baki da labari hakan na nuna cewa ba

gaskiya bane” haka na fadi cikin sauri don karma tace ita xata gayamata

in shiga uku domin ji nake muddin labara ya isketa zan iya shiga matsala

“to shikenan Al-ameen insha Allahu ma bagaskiya bane” “to Allah yasa

haka, nagode sai dasafe” “to sai da safe Allah ya tashemu lafiya” nan

mukayi sallama na koma daki na kwanta awannan lokacin nasami saukin

tunani domin jinake tunda har Raihana bata saniba to lallai jita jitace
kawai, nan nayi barci na harda dan guntun mafarkina wanda kafin safe

ma na manta abinda na gani acikin mafarkin da gari ya waye sai na fita

makaranta da sunan in Allah ya hada mu zan tambayeta cikin dabara da

wayo don 9nji gaskiyar abinda ke faruwa amma amamakina sainaga

lecturw farko da akayi da safe ban ganta ba nayi ta jira duk da dai na dan

tsorata da zancen da kailani ya gaya min amma sai nayi ta duban kofa

kozan ganta ta shigo amma shiru har lecture ta kare kafin mu fita wani

lecturer ya shigo muka dora da wata lecture daban, harm un kusa kare

lecture sai ga kira daga number Aisha dayake raina ya far abaci saboda

rashin ganinta da banyi ba kuma nayi ta kiran wayarta bata shiga sai nayi

kamar bazan dauka ba sai daga baya sai na dauka na kara a kunne sai

kuwa naji sallamar Raihana nan fa sai naji gabana ya fadi na fara

tambayar kaina me yasa ita Aishar batayi Magana da kanta ba sai da

muka gaisa sannan sai tace “wallahi Aishace dama bata da lafiya tunda

safe muna asibiti da ita” wani rin sarawa kaina yayi naji kamar an buga

min wani abu saida na dauki yan sakanni ina istirja’i sannan nace “a wane

asibitn kenan?” sai tace dani clinic din makaranta, har na yunkura zan

mike sai na tuna cewa a cikin class nake sai na koma na zaun nace da

Raihana “ok in sha Allahu ganinan zuwa yanzu ina lecture ne zan nemi

excuse in fita” dan basarwa nayi kadan naga abin fa bazai yiwu ba don

zuciyata takasa daurewa kawai na mike na excusing kaina na fice daga

class din dsauri nayi asibitin makarantara don inje inganta don inga halin
da btake ciki domin dagaske hankalina yayi matukar tashi bias ga rashin

lafiyar tata nidai kawai fatana shine inje intarar cewa jikin yayi sauki

saboda a mafiya yawn lokuta in naji wani abu ya sami Aisha jinake

kamar ana cizona in kuma naganta acikin wani hali sai’inji kamar an zare

lakar jikina yadda tafiya ma adole nake yinta cikin hanzari na isa asibitin,

ina shiga kuwa na isketa kwance cikin wani irin yanayi don ni aganina

ma kamar bata san nazo ba muka dan gaisa da wadanda ke tare da ita

wadanda acikinsu ma babu wanda na sani sannan na sake duban ita

Aishar cikin tausaywa nace “sannu ko” tayi min alamun taji kuma ta

amsa tahanyar motsa kanta kadan duk da cewa akwance take, ji nayi

kamar inyi kuka alokacin sai da na daure nace da ita ya jikin ta sake yin

alama wanda ni azuciyata naji kamar tace “da sauki domin kuwa

kunnuwana basu jiba kasa sakeyi mata Magana nayi har sai da Raihana ta

iso daga inda take domin alokacin da na shiga bata ward din muka dan

gaisa da ita sama sama sannan na tambayeta ya jikin Aishar tace min da

sauki. Har da wani iyayi nawa don kuwa nasan a matsayin iyayi zasu

dauke shi dukda cewa ni har cikin rainana fadi yadda na ce “amma an

dubata kenan ahaka?” “eh sun dubata kenan gama maganin da suka bata”

“oh God” haka na tsinkayi kaina ina fadi sai daga baya nasake duban

Aishar ina ji araina kamar in cire mata abinda ke damunta kawai ta tashi

mubar wurin da ita sai da na sake yin ajiyar zuciya sannan nace to

charges fa nawa suka chaje ku?” sai kace irin ina jin karfi dinnan dominfa
a sannan ko cikakkiyar five hundreds babu ajikina amamakina sai naji

tace “ai tana da file anan kuma kasan in mutum yana da file kyautane”

“ok..” iya abinda nasake iya fadi kenan nayi shiru “wai kinga nifa ina

ganin kamar gara akaita cikin gari don a running over all test a kanta

domin naga abinnne yaki ci yaki cinyewa” haka na furta bayan na dau

tsawon lokaci ina tauna maganar araina don gudun kar suga kamar na

raina musu abinda sukai ita kuwa Raihanar sai cewa tayi “eh haka ne

nima nayi wannan tunanin amma yanzu tunda sun bata magani mu gwada

mu gani tukunna in yaso in abin yan cigaba sai akaita cikin garin, duk da

dai muna sa rai zata sami sauki” “toh Allah yasa hakan don munfi sonn

hakan dama” na furta hakan cikin wani yanayi dani kaina ban san yazan

kwatantashiba nan dai na dan zauna shiru kafin daga baya na fita atsarge

nace bari in dawo, abinda yasani tsarguwa kuwa shine ganin yadda na

taradda ita Aishar cikin wannan hali sannan babu abindama yafi bani

takaici ma sai yadda na tuna cewa asannan babu wasu cikakkun kudade

ajikina ballantana in dan yi mata saye saye wanda suka kamata, haka na

nufi super market kamar wanda babu laka ajikinsa shiga kasuwar nayi

nadan sai wani abu wanda kunya zata hanani furta muku shi sannan na

sake nada kwana na koma clinic na sake zama kamar wani mai gadin

wani abu sai dai in dan duba inda ita Aishar take in sadda kaina kasa

kamar wani munafiki saboda ni kadaine namiji awurin har sai da na duba

agogo naga na kusa share mintuna talatin zanne sai na tashi nayi musu
sallama sannan na fice na nufi hostel na kwanta duk da cewa lokacion sha

biyun rana tayi kuma akwai lecture da yakamata in halarta amma sai naji

bazan iya zuwa ba don nasan ko naje ba abinda zan fahimta, na kusa

mintuna sha biyar ahaka sai wata zuciyar ta ce dani gara in tashi in yaso

in naje ko attendace nay i mana ni da Aishar zai fi sannan na tashi na tafi.

Muna tasowa kuwa na yiwa Raihana waya ina tambayar yanayin jikin

Aishar sai tace ai an rigaya an sallamesu ma yanzu zasu tafi hostel ne

alokacin na dan yi ajiyar zuciya sannan na kara da cewa to Allah ya kara

sauki, Raihanar ta amsa da amen kana tace “munga abu mun gode” fadin

hakan da tayi sai da gabana ya fadi don nasan kwanan zancen domin ance

mara gaskiya ko acikin ruwa jibi yake sai na dan basar nace bangane ba

“eh nace ne munga abu mungode” haka tasake mai maitawa nikuma sai

nace to shikenan tunda an fara haka sai anjima banma jira tayi Magana

ban a kashe wayar sannan na nufi masallaci.

Aranar jumua’ah kuwa bayan mun fita sallar jumu’ah sai muka dawo

muka taradda anyi mana shashanci a hostel din mu domin acikin dakin

mu an dauki katifun mutane biyu da kuma wasu yan kayayyakin da ba

arasawa, hakan yasa muka raka wadanda abin ya shafa security division

don suyi report don gudun tashin maganar wata rana, muna kan hanyar

mu ta tafiya sai na hangi Aisha zaune kan gabar wata gada gab da school

clinic tun daga nesa na gane cewa itace don haka na kasa dauke ganina
daga gareta don da ganinta kaga marar lafiya hankalina dai bai kwanta ba

amma saboda tunanin kada mutanen da muke tare dau suyi wani abinda

bai dace ba yasa sai banyi wa Aishar Magana ba illa iyaka da mukayi wa

juna murmushi sannan a daga mata hannu afakaice itama alama tayi min

da kanta muka wuce, bayan mun bar security division din sai sauran suka

fice daga makarantar don shiga gari ni kuma sai nayo kwana na dawo har

da gudu gudu don saurin inzo inga switch din duk wani mood da nakan

iya shiga azuciyata wato wacce ako yaushe nake daukar kaina kasa da ita

don ganin matsayinta da nake, nake jin cewa alfarma ce kawai tayimin da

har take iya kulani don kuwa ban cancanci koda gaisuwa ba ma bare har

wani batu soyayya ji nakeyi koda ace zatace dani ta jingine ni gefe bazan

taba ganin laifinta ba hakanan bazan taba daina wani abu gareta ban a

daga kyautatawa don kuwa na riga nayiwa kaiana alkawalin cewa ko tana

sona ko bata sona baza ta taba neman wani danake da ikon yi matra shi in

kasa yimataba don na tabbata azuciyata da anyiwa dan adam bauta da

babu shakka zan bauta mata, ko da acikin kawayenta naga suna Magana

koda kuwa kuwa tarahace na tsani inga anyi mata wani abu wand aba

daidaiba ballantana kuma ace daga bangaren maza, wanda da farko wanta

ma saida na fara jin haushinsa kafin nagane abinda ke tsakaninsu,

Cikin rashin sa’a sai ban insketa awurin ba nan danan sai n adage

waya na kirata nayi sa’a kuwa ta daga bayan mun gaisa sai na tambayeta
abinda take awurin da na tarar da ita sai tace dani sun fito daga clinic ne

sai sauran suka fita main gate don suyi siyayya ita kuma sai ta tsaya

hutawa da nasake tambayarta “yanzu kin koma kenan?” sai tace “a’a ina

nan in ashan iska a kusa multi purpose hall(church)” “ok to yayi kyau, ke

kadaice ko ke da wasu?” “a a nikadaice zakazo ne?” asa’adda ta fadi

haka sai da naji kaina yayi kato cikin zumdi kuwa nace “in dai kin bani

daman zuwa me zai hana?” “to kazo mana ain i kadaice kuma ba wani

abu nake ba kawai hutawa nake” haka tafadi wanda sannan na mayar

mata da cewa “to ba ki ganin in nazo zan dameki?” “hmm kai dai kawai

in akwai inda zakaje shikenan amma ni bance zaka dameni ba” abinka da

mai neman kuka da aka jefa da kashin awaki ban ko jira ta rufe bakiba

nace “to shikenan ganinan ahanya” na fadi hakan gami da kashe wayata

na kara sauri.

Da isata sai na taradda ita zaune kan yar kujerar karfe daketushen

bishiyar wata bedi(darbejiya) bata san na isa wurin ba dayake ta baya na

isa wurin, sallama nayi wacce ta fargar da ita har ta waigo don taga ko

waye sannan ta amsa, ganin na coge a tsaye sai tace “ka zauna man aka

tsaya atsaye?” alokacin yar kunyace ta kama ni don dari dari nake da ita

shiyasa na coge ganin kujerar ba wani girma gareta ba sai kuma gashi ta

cedani wai in zauna, jikina har wani bari yake slightly ayayin da na dan

matsa kadan na zauna kusa da ita tazarar dake taskanina da ita baifi 1feet
ba wato 12 inches, kwatan kwacin 30cm kenan, muka dan gaisa

samasama na sake yi mata ya jiki ta amsa cewa da sauki kafin daga baya

muka dan fara hira sama sama dai mun kai kusann mintuna 40 har ta

turamin wasu pics dinta, sai can da na fara rasa abin fadi sai nace da ita

“akwai wani abu da yake raina na kasa mantawa dashi duk da cewa ban

yi imani dashi baamma ya hanani sukuni, wanda har raihana ma sai da na

kira amma ban sami mafita ba” bata ko kalleni bat ace “to mekenan haka”

sai da nayi ajiyar zuciya sannan nasami damar sake budar baki nace

“wani labarine mara tushe ya isheni cewa wai usman small saurayinkine,

amma kiyi hakuri fa da wannan maganar kawai dai na gaya mikine

saboda kore tanttama,” sa adda na fadi haka sai tayi shiru bat ace komai

ba sannan ta juya kanta wani wurin kamar ba da ita nake ba, wanda hakan

ya dan sa gaba nay a fadi na dan kalleta na tsawon lokaci sannan nima na

kauda kaina na koma kallon wayata araina nace bazan sake tambayarta ba

don naga alamar ranta ya baci kuma gashi dam aba cikakkiyar lafiya take

da itaba har na fara tunani fara bata hakuri sai naji tayi ajiyar zuciya

sannan tace “maganar gaskiya munyi soyayya da usman amma ada ne ba

yanzu ba” wani abu naji azuciyata kamar an dokeni akirji dakyar na

hadiye yawu sannan nace “hmm ok amma ni abin tsoro ya bani domin

naga bantaba sani ba” kafin in sake furta wani abu sai tace “gani nayi ai

ada ne shiyasa kaga ba bukatar in gaya maka” ajiyar zuciya na sake yi

sannan nace ita ma Raihana da na tambayeta cewa dani tayi bata sani ba”
“ai alokacin bama tare da Raihana shiyasa bazata sani ba domin kasan

NCE I lokacin bamu san juna da raihana ba” da fadi haka sai tayi shiru ta

dan kalleni har muka hada ido kafin ta kauda idonta, nima alokacin sai

nayi shiru na dan lokaci sannan nace “kar kice na dame ki da tambaya,

amma meye silar rabuwar ku dashi?” bata ko jira ba sai naji tace

“halinssa yasa muka rabu” daga nan ban sake tambayarta wani abu ba har

aka fara kiran sallar la’asar mukayi sallama na tashi na nufi masallaci ita

ma sai ta nufo masallacin domin tayi sallah kafin ta koma hostel, amma

ni azuciyat kawai na bar maganar ne saboda ganin halinda take ciki na

rshin lafiya don har ajikin a jinake yi kamar nine bani da lafiya, domin

har ga Allah ban taba jin son wata ya mace da gaske da zuciya daya ba

kamar yadda nake son Aisha ba haka kuma bana tunanin akwai wacce

zata kuma samun wannan damar domin kuwa zuciya ta gaba daya na bata

kuma nasan bazaiyiwu ta dawo gaba daya ba babban abin bakin cikin ma

shine duk kokarin da nake wajen ganin na faranta mata sam sai kaga

kamar bata san inayi ba wani lokacima sai in ringa mamaki araina “me

yake kawo haka? Saurayi gareta daban ni kuma irin kumfar kogi nake

awurinta kokuwa zuciyar tace babu shauki aciki take rayuwarta

emotionless?”

A haka muka kasance rayuwa dai gata nan sai daikawai ayi

alabarce

You might also like