Mar&rsquo Adam&rsquo S Book 2 Complete Hausa Novel by Hausanovels001
Mar&rsquo Adam&rsquo S Book 2 Complete Hausa Novel by Hausanovels001
MAR'ADAMS
💖💖💖💖
💗💗💗💗💗💗
Book 2
*AYSHA A BAGUDO*
WATTPAD @HAUESH
AREWABOOKS USERNAME
AYSHAABAGUDO
bismillahirrahmanirrahim
Page 1
...nan da nan hankalin ma'aikatan dake fitowa yayi kansu duk suka tsaya suna
kallon ikon allah yayinda zukatansu ya cika da mamakin DG m.malik "dan Allah ku
taimakeni saceni yake qoqarin yi karku bari ya saceni dan Allah "maryama ta fad'a
cikin tsananin kad'uwa ,duk yadda taso ta kwace hannunta daga cikin nashi ta kasa
dan ba qaramin riko yayiwa hannunta ba ,abinda yasa mutanen dake tsaye suna
kallonsu basu taimaka mata ba kuwa shine basu ta'ba gani DG m.malik ya kula wata
mace dake cikin ma'aikatan ba bare har hannunsa ya kai gareta ba sai yau ,dan
haka suka kawo Idanu suka zuba suna kallon sarautar allah domin dai sun tabbatar
akwai wata matsalar da tashi aikata hakan ."
hankalin maryama ya sake tashi fiyye da tunanin mai karatu ,kai tsaye wani office
ya nufa daita ya tura ya kofar office din ya shiga daita sai alokacin ta saki qara
mai sauti tana sake neman agajin mutane kafin ta qara wani sautin taga ya bud'e
wani d'akin acikin office din wanda yake ajiye zanenta ,turus tayi tsaye tana bin
d'akin da kallo yayinda zuciyarta ke wani irin bugawa da sauri sauri ,numfashi
kawai tayi ta saukewa sakamakon tafiyar saurin da tayi yayinda kwakwaluwar kanta ta
shiga yamutsawa sakamakon abinda idanunta suka ci karo dashi ."
gabadaya d'akin hotunan zanenta ne da mai gidansa yake zanawa a duk lokacin da yayi
mafarkinta kallon d'akin kawai ta cigaba yi hankalinta na qara tashi "ya kalleta
sosai ya kalli zanen hotunan dake manne da bango
ya qara tabbatarwa kanshi ita ce, muryarsa na rawa ya soma magana "ki taimakawa
rayuwata ki biyoni zuwa wajen mai gidana"
"wani kallon tsoro tayi masa tana ja da baya jikinta na wani irin rawa dan a yanzu
tsoro ya shigeta matuka sakamakon ganin zanen fuskarta ."
"Mai gidana ya dade yana nemaki ,mai gidana ya mutu a soyayyarki ,mai gidana yana
matukar sonki so kuma na hakika ,dan allah ki auren shi idan ba haka ba zai iya
rasa ransa akanki matukar kika yi kuskuren butulcewa aurensa dan ba qaramin so yake
miki ba ,akanki zai iya komai ya qara maganar yana qoqarin kamo hannuta akaro na
biyu" muje na kaiki wajensa .."wallahi mutuwa zai yi idan ya rasaki ."
saurin ja da baya tayi agigice tana girgiza masa kanta cike da matsanancin tashin
hankali , yanayin bugun zuciyarta kuwa sai ya baka mamaki"dan Allah ki fahimceni
bazan ta'ba cutar dake ba wallahi kawai gidansa zan kaiki ya ga abinda ya dauki
shekara da shekaru yana mafarki ,ina kaiki zan kama gabana wallahi kinji na rantse
bazamu cutar dake ba ,mai gidana yana qaunarki zai iya mutuwa idan har bai sameki
ba "kallon taba'b'be dakiki mara hankali take masa daga tsayen da take acikin
d'akin kafin daga bisani muryarta na rawa tace " a she kuwa zai mutu tun wa'adin
mutuwarsa bai kusantosa ba ."
"kai kuma hakika ka shiga d'imuwa ko nace ka haukace da har ka amincewa zuciyarka
da rudin daka shiga ,kai yanzu a ganinka nice nan ?"ta fad'a cikin tsananin tashin
hankali dan tabbass zanen fuskarta ne har ma da yanayin tsarin jikinta sai dai a
nata tunanin wata ce dabam mai irin surarta amman ba itace bace aka zana ,dan daman
kuma ance mutane biyu biyu allah yake halitta a duniya wata killa ma aljanace tazo
masa da siffarta a mafarki dan babu abinda aljanu basa yi dan haka bata ga dalilin
da zai sa ta amince wa kanta cewar itace ba bayan mafarki ne ita a yanzu ma wani
sabon tsoro da tashin hankali ya sake lullu'beta ."
Jikinta na rawa ta cigaba da magana " idan hauka kake yi kayi maza ka dawo cikin
hankalinka?idan kuwa dimuwa ce ta sameka akan mafarkin mai gidanka kayi hanzarin
dawowa cikin haiyacinka, dan bani bace wannan ,banza sha sha dakiki kawai dabba
wanda bai san kima da darajar mace ba ,kawai akan wani zanen banza zaka jawo mutun
zuwa nan alhalin mutane na kallonmu ,ni yanzu babu abinda zance maka sai allah ya
isa hannuna daka ta'ba da zubar min da mutunci da kayi tana gama fad'ar haka ta
juya zata bar d'akin taji ya biyota yana qoqarin rikota dan bazai yarda ta gudar
masa ba , duk runtsi duk wuya sai ya kaita wajen mai gidansa ai kuwa tana juyo ta
dauke shi da maruka biyu ajere ji kake tass tass !!! ."
Nan da nan ya shiga ganin double acikin kwayar idanunshi saboda wani irin hasken
daya gilma a cikinsu tsayawa yayi cak dafe da kuncinsa bazai iya tuna lokacin daya
sha mari haka ba , a fusace ta shiga nunasa da yatsan hannuta tana huci tamkar
numfashinta zai bar gangar jikinta sannan tace "karka sake gangancin kai wannan
banzar hannun naka jikina ,jikina mai daraja ne tayi maganar cike da zafin rai da
kunar zuciya , jiki a sanyaye ya zube k'asa bisa gwiwowinsa a gabanta yana rokonta
da sauri ta fito daga office din tare da murda key ta rufeshi aciki ,ta fito
gabadaya zuciyarta na wani irin rawa ganin idanun mutane akanta zuciyarta ce ta
karye sai hawaye sharrrr tasan wani kallo mutane suke mata ,wata killa ma suyi
tunanin yayi wani abu daita ne ."
Cike da tashin hankali ta soma d'aga kafafunta cikin sauri kamar zata tashi sama
Kallo daya zaka mata ka fahimci bata cikin natsuwa da kwanciyar hankalinta, tana
fitowa bakin get din ma'aikatan bata sha wahala ba ta samu mota ta fad'a cikin
tashin hankali sai da motar ta tashi sannan ta tuna da wata aba subai'a sun yi
tafiya mai dan nisa ta sauka a oshodi under bridge, tana tafiya hawaye na bin
kuncinta ,ai har abada bazata sake dawowa wannan ma'aikatar da sunan aiki ba, duk
yadda zata dojewa zuwa zatayi sai dai a maye gurbinta da wata ."
tafiya kadan tayi ta qaraso inda zata shiga mota mai zuwa agege allah ya taimaketa
mutun daya yayi saura motar ta cika ta fad'a da sauri suka wuce wani sanyayyen
ajiyar zuciya ta sauke dan sai alokacin ta d'an samu natsuwa ta sauka a capito road
ta d'auki titin unguwarsu sai dai har lokacin bata daina jin mummunar fad'uwar gaba
ba adalilin zanen halittarta data gani ,ahankali ta shiga gidansu tana shiga
idanunta ya sauka akan umma data fito da wata qawarta ladin na amadu umma na ganin
maryama ta saki fuska tana murmushi tace "kar dai sai yanzu kika dawo?".
Maryama ta fesar da numfashi tace "wallahi umma sai yanzu na dawo" tô sannu da zuwa
amman dai yau kin jima gsky " yau muyi busy ne a wajen aiki gashi yau har apapa aka
watsamu sannu da gida ".sannu da zuwa maryama ya aiki ta sake maimaita wa akaro na
biyu ?"alhamd mun godewa allah mun dai kusan qarewa mu huta."
" ina wani hutu tunda ga aiki a gabanki Allah dai yasa mu dace kina qarewa ki samu
aiki"
"Ameen ummah na gode allah ya bar girma ." Ladi na amadu tayi shiru tana kallon
maryama , ta d'an rusuna ta gaisheta ta wuce su zuwa bangaren su "kamar maryama
ko ?inji cewar ladi" Eh! itace "kai girman dan mutu ba wahala kalli yadda ta
girma ,wallahi kam ta girma Kmr fa jiya jiya aka haifeta "ai shine mamakin da nake
gata ta girma masha allah har ta kai ga bautar kasa kun tsaida mata miji ne ".?
"Masu neman auren suna zuwa sai dai da zarar anyi magana mai karfi sai su gudu
amman dai yanzu ta samu wanda bazai gudu ba ,d'an aminin abban sadam Ke sonta kuma
da gaske aurenta zai yi "kash ."! ladi ta fada cike da damuwa ,umma ta kalleta a
natse tana cewa "ya naga kin yi wani iri ko akwai wanda zaki nemawa aurenta ne ?
ladi ta girgiza kai tana cewa "ko daya wad'an nan ya'yan nawa da duk suka zama
abinda suka zama dama lafiyayyu né basu saka rayuwarsu a shaye shaye ba ai sai kayi
masu kamu dan naga yarinyar natsuwa ."
"Sosai kuwa maryama akwai natsuwa su kuma allah ya shirya mana su "Ameen ya hayyu
ya qayuyum "amman me yasa zaku bawa wani ?bazaki tsaya an bawa d'ana sadam ba ?a
gsky sunyi matukar dacewa da juna "wannan sarkin shiriritan ni kaina nayi masa
shaawar auren yarinyar amman ganin gashi gata na dauka shima zai wa kanshi shaawar
aurenta amman sai naga shi sam bama maganar aurene a gabansa ba ,amman da zaku
had'asu da sai kun fi samun saukin hada kayan aure tuwona maina ba wani abun kirki
zaku kashe ba "umma tai murmushi tana cewa "wato auren arha kuke nema ?ladi ta
gyad'a mata kai alamun eh !
"ai kuwa sai dai kuyi gaba dan maryama kam sai wanda aljihunsa zai yi kuka"
ahankali suka cigaba da takawa suna tautaunawa a tsakaninsu."
Aunty na fitowa daga daki ta iske maryama tana zaune tana hawaye da hanzari ta
qaraso wajenta tana tmbyrta "Ke lafiya me kike ma kuka ?"wani matsanancin kuka ya
sake zoma maryama hakan yasa hankalin aunty ya sake tashi "wai me ya faru ne kike
kuka haka ? rarrashinta ta soma yi a tunaninta ko mutanen gidansu suka ta'bota daga
dawowarta da kyar ta samu tayi shiru ".
"Bari na kawo miki abinci kila kina jin yunwa ta mike ta kawo mata abinci da ruwa
sai dai ruwa kawai maryama ta iya sha nan taji zuciyarta tayi sanyi "wai meke
faruwa ko abinci kin kasa ci cikin natsuwa ta fad'awa aunty duk abinda ya faru
daita yau a wajen aiki "shiru aunty tayi tana dubanta a tsanake kafin ahankali ta
soma mgn "zanen mai kama dake princess?."
ta gyada mata kai alamun "eh! "to shine zaki daga hankalinki akanshi ? aunty ai ni
bama zanen bane tashin hankalina ba kamar yadda hankalin mutumin ya tashi
matuka ,wai shi sai ya kai ni wajen mai gidansa wallahi aunty yau Allah ne kawai ya
taimakeni da sai dai wata bani ba ,wama ya sani ko masu satar mutane ko masu shan
jini haka kawai yaje ya saceni su zuke min jini ."
."aunty tayi murmushi tace "masu satar mutane da shan jini ne zaa basu office
acikin babbar maikata haka? wata killa dai maigidansa mai kama dake yake mafarki
kawai shine kuka yi aran gama dashi Ke kuma kika tsorata" maryama tayi murmushi
wallahi nayi matukar tsorata dan bazan qara zuwa aiki wannan maakatan ba "baki da
zabi princess dole idan an sake buqatarki kije ke dai kawai ki dinga addua kafin ki
bar gidan nan "wallahi aunty ina yi ban ta'ba barin gidan nan batare da nayi addua
ba ."
"To shikenan Allah ya qara tsarewa yanzu dai karki saka damuwar wannan abun a ranki
har kizo ki rame dan yanzu ma duk kin canza kin rame ba kamar kwanakin baya ba dama
ya lafiyar kura" murmushi maryama tayi" allah aunty ba wani rama da nayi ina after
dad ? na fita da safe bangansa ba gashi na dawo ma banji motsinsa ba da alamun ya
baya gida ?"bai jima da fita ba "bana son ina gida baya nan duk sai gidan yayi min
wani iri gida ya dawo kamar gidan mutuwa"ni kuma nafi son shi haka bakina ya huta
kwakwaluwata ta huta dan duk abinda akayi akan idonsa bai masa ba sai ya tanka
shiyasa idan ya fita sai naji kwanciyar hankali haka sukai ta hira har Maryama ta
wastsake daga damuwar da take ciki ."
Shi kuwa bangaren m.malik cikin dauki ya shiga neman layin mai gidansa, daman
abinda yasa tun farko bai nemesa ba so yayi yayi masa suprice sai dai kawai ya
gansa daita ,duk da ya rasata yau amman sai da yayi dariyar farinciki , lallai
mai gidansa dan bawa ne shi da mahaukaci ma ya daukeshi a she dai mafarkinsa zai
zama gaskiya ko
babu komai a yanzu sun tabbatar ita din gsky ce kuma dole su basu nemanta "ahankali
ya zauna akan daya daga cikin kujerun office din hankalinsa yaji ya dan fara tashi
sakamakon abinda computer sadawar ke fad'a masa number a kashe take ."
cigaba yayi da kiran numbobinsa sai dai amsa daya ake bashi wayar is switch off "oh
my goodness wai me yasa ya kashe wayoyinsa?wani yaronsa ya kira ya budesa yana
fitowa direbansa ya taso cike da girmamawa yana qoqarin ya bude masa mazauninsa ya
mika masa hannu alamun ya bashi keyn motarsa "yalla'bai ka bari na kai mana "ya
fadi haka ne saboda ganin yanayin da yake ciki kai kawai ya gyada masa ya shiga
gidan baya direba yaja suka wuce "ina muka nufa yalla'bai?"
"Babana esatate zaka kai ni direba ya d'auki hanya, duk bayn second sai ya kira
layin a kashe a karshe dai ya yanke shawarar turawa ATA sako kamar haka "Slm sir
Please call me sir I have gist for you." tafiya kadan sukayi suka kawo bakin
tafkeken get din
gidansa ,sai dai kash basu samesa ba dan tun daga bakin get aka sheida masu baya
nan "shiru yayi yana tunanin jiya ne fa aka d'aura masa aure kuma ya kamata ace ya
tare da amaryarsa "kenan baa nan ya tare da matarsa ba ?yayi wa kanshi tmbyr ."
Ko da yake mutun mai tarin arziki haka ai yana da gida bilaadadin duk kusan yasan
rabin gidajensa sai dai bai san wanda zai nufa ba ahalin yanzu dole yana bukatar
yayi waya dashi kafin ya nufi kowanne daga ciki ,cike da tashin hankali ya bawa
direbansa umarnin su wuce zuwa apapa gra yasan dai dole mahaifiyarsa ko cikin
yan'uwansa zasu san inda yake tafiya kad'an sukayi suka hadu da wani matsiyacin go
slow tsaki m.malik yaja yana dafe kanshi."
Bangaren ata kuwa yana can kwance shame shame ya sha whiskey Kmr yadda ya saba
yayi mankas yana ta sharar bacci a kasan d'akinsa wannan dalilin né yasa m malik
yaji gabadaya wayoyinsa akashe dan sai daya kashe wayoyinsa sannan yayi
mankas,hakan bai sa m malik ya hakura ba duk wucewar mintuna sai ya kiran layin mai
gidansa amsar daya ake bashi ,ganin har zuwa wannan lokacin bai samesa ba yasa yayi
qoqarin kira salim ko suna tare dashi shi kuma kiran na shiga baya dauka haka
zalika number hisham ."
Wanda a wannan lokacin m.b ,salim ,yaya Ibrahim amar kai har ma da hisham suna
tsaye akan ATA cikin tsananin damuwa ,hisham ya fito da wayarsa ya duba number m.
malik ya gani bai dauka ba dan nan take ya fahimci magana yake son yi da ATA ya
sake kallonsa yadda ATA din Ke kwance wani iri tamkar mara rai ya maida wayarsa
cikin aljihu gabdayansu zukatansu cike yake da tashin hankali halin da yake ciki
tunanin kawai hisham yake me zai faru idan mami tasan halin da yake ciki dan shi
bai san iya kwanakin daya dauka yana shan giya ba sai yau da mb ya kira salim suna
tare salim din ne ma ya takura masa yazo ."
wayarsa ta sake ringin ya fito dashi ya duba still m malik ne dan haka ya sakata a
silet ya sake maidata aljihunsa "ku kama min shi mu daurashi akan bed inji cewar mb
daya kai hannunsa jikinsa yana zubar da hawaye "he don't want to loose him at
all ,shi bai san ma soayyar mafarkinsa ya kai haka ba wallahi duk tunaninsa da
zarar an daura aurensa shikenan komai ya zama tarihi agaresa a she komai zai yi
worst ne atare dashi wani irin tausayin abokinsa ne ya lullesa ".
"Me Ke damun tunanin adam ne ?he's so much in love with his dream ,what will happen
idan bai sameta ba? "zan iya mutuwa for real." salim yaji sautin muryarsa cikin
maye yana bashi amsa da haka "farincikina na ganta I just love her with all my
heart "gbdy suka suke numfashi suka daurashi akan katifa ya kwanta sharaf yana
sauke wani wahallalen numfashi "yanzu me zamuyi mu raba rayuwarsa da wannan damuwar
?" yaya Ibrahim ya fad'a "yana dubansu."
Amar ya numfasa yace "ni dai idan son samu ne a rabashi da auren nan na maryam yaji
da matsala daya "idan kuma ita yarinyar mafarkinsa ba gsky bace fa ?inji cewar
hisham, kawai mu tayashi da addua, yanzu bari mu sheidawa mami halin da'ake ciki
saboda idan ya farka karta bari wani ya shigo inda yake ko shi ya fita zuwa koina a
tsareshi zuwa na wani lokaci adai samu wanda zai zauan tare dashi da zai dinga kula
dashi kamar zai fi "mb ya fad'a yana dauke hawayensa ni bansan wake zuwa siyo masa
giya ba dan dai da kanshi bazai iya zuwa ba wallahi muddin naga mai siyo masa giya
sai naci uban kowa waye ya qarasa mgnr yana naushin iska ."
"kun fa san halinsa, kunsan halin taurin kanshi babu wanda zai hanashi abinda ya
ga dama inji cewar hisham "duk da haka dai a samu mutun biyu zuwa uku su tsaya tare
dashi wannna karon bai isa ba matsawar bazai daina shan giya ba ya zama dole mu
dauki mataki akanshi haba nifa na fara tunanin aljana ce yarinyar mafarkinsa duk
suka zuba masa ido " to idan ba haka ba kamar adam me zai tsaya batawa kanshi
lokaci akan wani mafarki diya ko ta uban waye ai zai samu, kawai aljanna da yake
gani nata salon kenan ,amamn da yarda allah qarshenta yazo sai muyi 'bata 'bata
daita da ayoyin Allah yanzu dai bari na kira mami "inji cewar yaya Ibrahim ."
Mami kam dake cikin mutanen da suka zo mata biki suna ta'ba hira acikin damuwa take
dan duk wanda ya kalleta yaga yadda take abubuwanta yasan tana cikin damuwa mai
tsanani sam sam ma babu kuzari ajikinta kawai she's thinking of abubuwa daywa abu
biyu yafi damunta rayuwar adamcy bata san yadda zatayi dashi ba, ga kuma ta uwar
maryam da kawayenta suna buqatar amarya ta tare a gidanta kafin su wuce ga ango
baya cikin natsuwar da zasu tare,yanzun ma da take zaune addua take allah ya
saukowa danta tilo da kwanciyar hanakali da natsuwar zuciya."
tana cikin wannan halin wayarta ya fara ringim ta dauka ta duba "sunan yaya
Ibrahim ta gani yana yawo akan screen din wayarta da sauri ta dauka cikin tsananin
damuwa tace "Ibrahim yaakayi .? "mami adam ne yake cikin wani .."bai kai ga
karasawa ba ta katse masa hanzari ta hanyar mikeww tsaye ta nufi kofar fitowa daga
dakin dan ba wayr da zata iya amsawa bane a wajen da take ta koma d'akinta tun da
taji ya ambaci sunan adam ta fara karanto duk wata addua data iya a can bangarensu
kuwa wayar yaya Ibrahim tana loudspeaker har sanda mami tace "yauwa Ibrahim ina
jinka yanzu me ya faru da adam din ."?
"Mami da akwai matsala "mb ne yazo ya iske shi cikin wani yanani adam yana son
kashe kanshi saboda wani banzar mafarkinsa I think ya kamata mu dauki mataki akan
wannna matsalar nifa nama fi tunanin mafarkinsa jinu ne ya dace mu sa ayi masa
rukiya ya fad'a mata, tashin hankali mami ya qaru ."
Muryarta na rawa ta soma furta kalmar "inna lillahi wa inna ilaihi rajiun ."kardai
giya ya sake sha ?numfashi ya sauke kana yace "eh mami daman kinsan ya fara sha
ne ."
Kuka ta fashe dashi tana cewa "shekaranjiya nan ya fara sha ban san me adamcy yake
son maida kanshi ba ace mutun bazaiyi tawakali da hukuncin allah ba"mami ki kwantar
da hankali in sha allahu komai yazo karshe da ikon allah zamu yaki koma menene da
karfin addau ,nifa bansan abun nasa ya kai haka ba sai yau din nan "ya kai Ibrahim
na shiga uku ni zulai wani irin jarabawa ne wannan ?"ta fad'a tana sake fashewa da
kuka saboda tashin hankali."
" yanzu dai mun d'auke shi daga inda yake kwance a kasa mun maidashi kan bed kizo
muna son mu wuce muje muyi sallah amaman bama son abarshi shi kadai zamu barshi da
salim da amar sai ke idan ya tashi ya ganki a kusa dashi ya fad'a mata "ok ganin
nan zuwa "ta fad'a tare da kashe wayarta ta fito tana goge hawaye tana shigowa suka
matsa suka bata wuri ta zauna kusa dashi tana fashewa da wani kuka ta riko hannunsa
cikin nata ."sosai yake jin sautin muryar kukanta cikin kunnenshi da zuciyarsa
"hannunta dake cikin nashi ya damke yana cewa "so ..sorry sweetheart!so sorry for
putting you through this it's all my princess fault da bata bayyana min kan...."
bai qarasa ba yayi shiru daman maganar can kasa kasa yake fitowa kuka mami take
sosai suna bata hakuri ."
"Wannan princess anyi shegiyar princess bazan ta'ba yafe mata ba "no no karki sake
zagar min ita kawai ku nemo min ita a duk inda take shine kwanciyar hankalina da
samun kwanciyar hankali zuciyata if not I will kill my seif dan bazan yi rayuwa da
wannan guntuwar yarinyar ba, ga gara na mutu "ya rabbi anya kuwa ban jefa dana
cikin matslaa ba ?kin jefani , ni bana son auren nan tunda kika min auren nan kika
jefa rayuwata cikin matsla ai da bana shan komai sai sigari itama na dawo nace na
daina shanta yanzu kuwa gbdy komai na samu zan sha ina matukar son yarinyar
mafarkina I can't live without her ban ta'ba soyayya ba sai akanta I don't know
what's love but I love her with all my heart please give me that love sweetheart
ita kawai nake so ku nemo min ita ya fda cikin murya maye ."
"Gsky ta tafka kuskuren ba dan kadan ba wajen hada wannan auren to kuma idan batayi
masa haka ba me zatayi tunda babu tabbas din samun yarinyar mafarkinsa ? ya Allah
ka ceceni ka yayewa dana wannan damuwar da yake ciki ,ya Allah ka kwantar masa da
hankali "naunayen ajiyar zuciya ta sauke tare da waigowa bayanta sai lokacin taga
duk sun fice sun bar dakin sai ita kad'an da d'anta."
ta gyara masa kwanciya tana shafa sumar kanshi dake kwance luf tana tofa masa
addua byn ta gam ta runtse idanunta gam wasu sabbin hawaye na zubo mata ."hannun
tasa ta goge hawayen sannan ta yunkura ta mike tsaye ta fito zuwa falo nan ma taga
babu kowa acikinsu dan haka tayi tunanin kiran layin Ibrahim wayar ta soma ringin
alokacin yana zaune zai yi alwala sallar magriba yana d'auka tace "kun wuce sallah
ne?" okay to shikenan bari na jirasu sai nima naje nayi sallah na gode kwarai da
gaske Allah yayi ma rayuwarku albarka tana gama wayar ta koma cikin d'akin ta zauna
tana duban kwakkyawar fuskar danta dake zagaye da saje ."
Tafe tafe motar m.malik na moving har suka qaraso karkashin bridge din Liverpool
anan suka tsaya cak domin cunkoson ababen hawa dake wajen manya tankokin mai ne ta
koina ,su kansu motarsu a tsakiyar manyan tankokin mai take m .Malik yayi kasa
kadan da glass din hannun da yake zaune yana gyara zama dan gbdy duk zaman ya
gundireshi sakamakon cunkushewa da titin yayi sai ma yaji kamar ya fito ya taka da
kafafunsa ko ya hau mashin zai fiyye masa da wannan zaman da suke ."tsaki yaja ya
sake neman layin ATA still dai a switch off yake ya sake neman na hisham kira daya
ya dauka ."
wani naunayen ajiyar zuciya ya sauke yana cewa "yalla'bai barka da wannan lokacin
daga can bangaren hisham ya amsa masa da "barka !atakaice "ya kuma akaji da taro
allah ya sanya alkhairi jin haka yasa yaji wayar ta gundireshi dan da yasan allah
yasanya alkhairi zai masa bazai dauka ba "ammm daman na kira layin mai gida ne baya
shiga shine na kira ko kuna tare dashi "eh amman yana bacci "yana gama fad'ar haka
yayi disconnecting din kira yana jan tsaki ."
m.malik yayi shiru rike da wayar a hannunsa yana mamaki "bacci by this time ? sai
dai ya dan samu kwanciyar hankali kad'an najin halin da mai gidansa yake ciki amman
tabbas yaji ajikinsa babu Lfy ,a hankali ya motsa bakinsa yana cewa "saed ina ganin
idan mun qaraso karshen titin nan mu juya zuwa gida dan bazan samu damar ganin
wanda zanje wajensa ba "okay sir ."saed kaga wani maseefafen go slow ko ?wallahi
yalla'bai wajen nan kullum a haka yake ko zaka sauka ka hau mashin ya qarasa da kai
gida ".shiru yayi yana tunanin maganarsa dan shima tunanin da yayi kenan yana
ganin haka zai yi ya huta da wannan zaman ."
Fitowar salim kenan daga massalaci ya ciro wayarsa yana dubawa nan yaga missed
call's din m.malik kusan guda goma ajere dan haka ya shiga nemansa alokacin da yake
qoqarin fitowa daga motar ya d'auki mashin ya qarasa gida ganin salim ne ya koma ya
zauna tare da d'aukar wayar bayan ya d'auka suka gaisa a mutunce ,bayan sun gaisa
salim yace "naga missed calls dayawa fatan dai lafiya ?"
"lafiya lau daman ina son nayi magana da mai gida ne to kuma muyi waya da yalla'bai
hisham yace min yana bacci "eh haka ne bacci yake yanzu haka ma wajensa zanje "to
dan Allah kayi min qoqari idan ya tashi ka fad'a masa ya kirani duk da dai na tura
masa sako amman nasan ba lallai bane daga tashinsa ya nemi gashi kiran ujila ne "in
sha Allahu zan fad'a masa da zarar ya tashi "nan sukai sallama adaidai lokacin da
motocin dake tsaye a saman gada suka soma tafiya."
wata mota dake dauke da kwantena ta kwaso da gudu ai kuwa kwantainan data d'auko
tayi wani tsalle tayo kasan gadan nan mutane dake tsaye a titi suka fara darewa
suna ihu da kururuwar kowa ya soma yin ta kansa ,zo kuga gudun ceton rai nan da nan
na cikin motoci suka dinga firfitowa domin ceton ransu m .malik ya yunkura ya fito
agigice shi kuwa direbansa kafin ya fito tuni kwantainan ta fado kansu tare da wasu
motocin nan take motoci suka lotsa tuni direbansa ya tashi aiki shi kuwa garin
fitowa ya ceci ransa kanshi ya bugi gefen wata tanka nan da nan ya zube kasa a sume
wajen ya kaure da ihun mutane iri iri wasu kiran Jesus wasu na kiran sunan allah
yayindai mutane bilaadadin sun shiga tashin hankali most especially ganin yadda
jini ke mamala a kasa ."
*******
skarfe goma sha d'aya daidai mami na zaune shiru a bakin gadonta tare da zabga
tagumi hawaye na gangaro wa bisa kuncinta "ta had'a wannan auren ne da zumar kowa
karshen komai ga rayuwar tilon d'an a she bata sani ba wata wutar tashin hankali ta
kunna arayuwarsa da zuciyarsa "ya zatayi da wannan tashin hankalin daya kunno kai
cikin rayuwarsa?addau ce kuma kullum ta Allah tana yi masa babu sallahr da bata
masa addua , shi acikin yaranta ma tsameshi take tai masa tashi adduar dabam ."
sosai tayi zurfi cikin tunani a yanzu ta yarda aljana ce ta auri tilon d'anta kuma
take barazana da rayuwarsa dan dole ta mike tsaye ta nemo masa magani kafin taga
karahensa ta runtse idanunta gam tana sauke numfashi,tana cikin wannan halin
ya'yanta mata uku suka shigo d'akin dan tunda suka zo biki basu koma gidanjensu ba
sai zuwa jibi kowacce zata kama gabanta ,a matukar agigice duk sukayi kan mami
saboda ganin yadda taKe cikin mummunar yanayi dan suna iya jiyo sautin kukanta
gabdynsu suka zagayeta kowannensu na qoqarin son jin abinda Ke damunta duk da sun
san damuwarta bazata wuce akan dan'uwansu bane ."
"Ku taimakeni rayuwar adamcy tana cikin garari adamcy nah na cikin wani hali
dan'uwanku na bukatar adduaku ,muddin rayuwar adamcy ta cigaba a haka hakika zaku
rasani domin zuciyata na daf da tarwatsewa ,ku tayani dawo dashi daidai bazan iya
cigaba da kallon rayuwarsa haka ba ."ta qarasa maganr tana fashewa da wani kuka mai
ta'ba zuciyata "bazan ta'ba yafewa wannan aljanar ba sai allah yayi mana hisabi
daita domin tayi silar ruguza min rayuwar d'a"kiyi hakuri mami in sha allahu komai
zai daidaita zamu cigaba da yi masa addaua yanzu adamcy yana ina dan tun jiya
daya sauko ban sake ganinsa ba? ".inji cewar aunty khadija."
Cikin murayar kuka mami tace "yana d'akinsa ya sha giya babu yadda yake "hankalin
aunty shahida aunty khadija zabiba idan yayi dubu ya tashi a wannan lokacin, cike
da kid'ima suka mike tsaye suka fita daga cikin d'akin mami cike da tashin hankali
suka nufi saman d'akinsa byn fitarsu mami ta biyo bayansu salim da amar na zaune a
falonsa suna jiran farkawarsa suna ganinta suka gaisheta "sannunku da qoqarin allah
yayi maku albarka".
suka amsa da "ameen mami "halan bai farka bane har yanzu ?eh bai farka ba dan duk
bayan minti goma sai mun shiga mun dubashi yana nan kamar yadda kika barshi " allah
ya kyauta "ta fad'a tana kutsawa cikin bedroom dinsa ,yaranta na tsaye akanshi suna
kallonsa ta shigo "a lissafina awanni shida kenan yana wannan baccin dan bansa tun
lokacin daya sha ba "lallai nima na fara tunanin akwai sharrin jini ajikin adamcy
idan ba haka ba ina shi ina giya ? "me ma zai kai shi ga shanta? inji cewar zabiba"
allah dai ya yaye masa wannan maseefar koma menene bai fi karfin addua ba kuma zamu
dage iyakar karfinmu."
ahankali ya soma motsi sai dai gbdy ilahirin jikinsa sunyi masa nauyi dan ko d'an
yatsansa baya iya d'agawa gashi dai yana d'an jinsu sama sama idanunshi ma yake
qoqarin bud'ewa amman ya kasa tsura masa idanunsu da sukayi ne yasa suka fahimci ya
fara motsi nan suka kira salim da amar suka shigo atare "kamar yana motsi "suka
had'a baki gurin fad'ar haka amar da salim suka qarasa suka hau saman gadon dake
kwance salim ya kai hannunsa daidai hancinsa yaji saukar numfashinsa ya daidaita
dan haka yace "ya soma dawowa daidai "
"Ku dagashi ku zaunar dashi " inji cewar mami suka dagashi suka zaunar dashi
aunty shahida ta janyo pillow ta mika masu suka amsa suka saka masa a bayansa mami
duk ta sallamesu zuwa parlour ta shiga bathroom dinsa ta fito hannunta rike da wata
qaramar roba dake dauke da ruwa dumi sai towel ta janyo kujera kusa dashi ta ajiye
ta cire masa gbdy kayan jikinsa ya saura daga shi sai boxcer da tsufan mami hakan
bai hanata aiwatar da nufinta ba wankan towel tayi ma adamcy da kanta ya bude
idanunshi da kyar ya kalleta , ta dauko wasu kaya ta saka masa , ta gyara masa
kwaciya ta leko ta kira y'yanta atare suka shigo d'akin".
Sun sha mamakin ganin abinda mami tayi lalla d'a da uwa sai allah wato abinda take
son tayi masa kenan yasa ta korasu parlour adduar take tofa masa dan haka suma
basuyi sanya a gwiwa ba suka shiga tofe masa addu'a ,wanda kuma zuwa lokacin wani
bacci ne yayi gaba da ATA mai cike da mafarkai da ya saba barkatai marasa kan
gado !suka fito daga d'akinsa zuwa qaramin parlour mami suka zauna hira ,anan suka
ga ana hasko abinda ya faru cikin akwatin talabijin!! sosai suka jinjina wannan
abin wanda har cikin zuciyarsu tunani suke kan halin da ahlin wadan nan bayin allah
zasu shiga ? fatan su dai Allah ya jikan musliman dake ciki wannan mummunar tashin
hankali."
Ana gama gabatar da labarai suka mike gbdynsu suka sake komawa samansa Karfe biyu
daidai ATA ya tashi kamar wani mahaukaciya sabon kamu sanadiyyar mafarkan da yayi
da princesa dinsa tana masa ihu kan yayi aurensa ya barta har da ikirarin sai ta
kasheshi tare da matar da ya aura ,da k'yar suka samu sukai controlling dinsa ta
hanyar addu'ar da sukayi cikin ruwa suka bashi ya sha kuma suka shafa masa a
jikinsa sai faman lumshe idanunsa yake ."ga dukkanin alamu hankalinsa ba jikinsa
yake ba sabida maganar da sukayi tayi masa amma sai dai yabi su da ido kawai alamun
bai ma san mai suke fad'a ba."
Idanunshi ya bude sosai dan da zarar ya runtse idanunshi fuskarta yake gani ga
kuma wani masifaffen ciwon kai da ya sakoshi a gaba saboda sigarin da yawaita sha
acikin kwanakin ! ATA wanda kansa yayi masa nauyi ya dafe kanshi da hannuwansa
duka hankalin mami da yaranta ya qara tashi ganin yadda yaki cin duk wani abinda
suka ajiye masa ,sai dai kawai ya dinga bisu da idanu acikin daren aka je aka
taho da likitansa dan jikinsa yayi zafi sosai likita yayi masa allurai wadan da
zasu saukar masa da zazzabi shima da kyar aka samu ya bari akayi masa".
wannan dare gaba d'ayan mami da ya'yanta sun yishi ne cikin hidimar ATA daya kwana
cikin mawuyacin hali sun kula dashi sosai washegari bayan yaya Ibrahim ya tafi
sallar asuba yayi ma limamin dake shigowa basu sallah bayanin akan matsalar ATA
wanda hakan yasa tare suka shigo dashi a lokacin mami ma ta idar da sallar asuba
sannan kuma ATA ya samu bacci karatu suka farayi masa baji babu gani a wannan
lokacin har wayewar gari sannan suka samu ya motsa daga inda yake kwance."
nan take suka fuskanci bawai aljanu ne dashi ba,illa damuwa da yake faman dashi
akan wani abinda ke damunsa bayan sun tafi liman ya aiko masu da wani ruwan zam-zam
cikin gora kan su tabbatar da sun bashi yasha da zarar ya farka da yaddar Allah
komai zai zama dai-dai! ai kuwa suna basa ya koma ya kwanta wani nannauyen bacci
yayi gaba dashi wanda cikin baccin nashi sai faman had'a zufa yake baji ba gani
tsawon lokaci ya d'auka yana baccin kafin ya fardad'o,wanda kuma cikin ikon Allah
garas ya farka babu wani alamu komai attare dashi."
Sallah suka fara sakashi yayi kafin suka bashi abinci yaci,had'i da bashi
magungunan sa na daren jiya yasha nan da nan kuwa wani baccin ya sake gaba dashi
sabida akwai maganin bacci cikin magungunansa ,tsawon kwana uku mami suka d'auka
suna bashi tsaftatacciyar kulawa shi karon kanshi ya tausayawa halin da suka tsinci
kansu ciki adalilinsa ,duk sun zube sun fita haiyacinsu sai dai kallonsu kawai yake
yana tunanin yadda ajiye damuwarsa ya basu farinciki ."
Mmn sudais
💗💗💗💗💗💗
MAR'ADAMS
💖💖💖💖
💗💗💗💗💗💗
Book 2
*AYSHA A BAGUDO*
WATTPAD @HAUESH
AREWABOOKS USERNAME
AYSHAABAGUDO
bismillahirrahmanirrahim
Wannan littafin na kudi ne mai bukatar karantashi byn na kammalashi zai biya 1000
ta wannan account number din 1438775094 Aishat abdullahi access idan an tura sai a
turawa wannan 09136918331 alert domin tabbatar da an tura domin sauraron littafaina
a tuntubi chaneel dina (Hausa bakwai ) a YouTube.
Page 2
Zaune yake acikin d'akinsa ya bala'i surawa bangon d'akinsa idanunshi yana sake
zurfafa tunaninsa , acikin kwanakin da'aka d'aura masa aure komai nashi ya sake
sauyawa fuskarshi a d'aure ya cigaba da kallon bangon d'akin, sosai rashin
maganarsa ya qaru fiyye da yadda yake a abaya zaka masa magana sau d'ari ba zai
amsa ba, hatta mami a yanzu da yake cikin tsananin damuwar nan ba wani kulata yake
ba haka zata tasa shi gaba da nasiha da kuka amman har tayi ta gama bazai ce mata
uhm ba bare uhm ."
ransa duk a jagule kamar ya kashe maryam haka yake ji ya huta da muguwar tsanar da
yayi mata ,
gabad'aya bai ga ta yadda zai kawowa rayuwarsa farinciki ba, shi dai yasan muddin
yana jin yarinyar amatsayin mata agaresa tabbas haka rayuwarsa zata qare cikin
qunci , gbdy yan'uwansa na shigowa zuwa inda yake har mahaifiyar maryam din da basu
koma ba ,mrym kuwa da zarar ta shigo yake yiwa yan'uwansa alamar ta bar masa
d'akinsa mahaifiyarta kuwa duk sannun da take masa idan ta shigo baya amsawa
hassalima kawar da kanshi wani gefe yake dan kamaninta da diyarta nasa shi jin wani
irin tsanarta ."
Alokacin aunty shahida jiki a matukar sanyaye ta dawo inda fuskarsa take tana cewa
"meye haka adamcy ?"ka amsata mana ummu habiba nayi maka sannu" yayi shiru yaki
motsawa " ko ka manta wacece ita da matsayinta ne ?sai lokacin ya motsa labbansa
"wacece ita da kuma matsayinta?"cike da matsanancin mamaki aunty shahida Ke
kallonsa ko dai kwakwa luwarsa ta ta'bu ne ? kafin tayi yunkurin sake cewa wani
abu taji amon muryarsa cikin zafin rai "you better tell her to leave my room I
don't want to see her face ".ya fad'a a matukar tsawace "zai iya cewa tun daga
ranar data bar d'akinsa bai sake d'aura kwayar idanunshi akanta ba, yan'uwansa kuwa
gaba
d'ayansu suka sauya masa fuska."
Sosai kwakwaluwarsa ta sake lulawa cikin tunani neman mafuta yana buqatar kawowa
rayuwarsa canji da sauki idan kuwa har haka ne dan dole yasan abun yi kafin
mahaifiyarsa tayi maganr tsarewarsa da yarinyar, tashi yayi daga zaune da yake ya
tura hannuwan sa duka cikin aljihun wondonsa zagaye d'akinsa ya fara kafin ya soma
zance shi kad'ai "adam dan dole ka nemowa kanka mafuta to me zanyi ?me zanyi dole
dai ina buqatar nayi nisa da rayuwar kowa to ina zan koma ?wata kasa zan tattara na
koma ?
"ko kuma wani gida zan koma acikin gidajena na cigaba da rayuwata ?yayiwa kanshi
tambayar yana cizan gefen lip's dinsa ."
shiru yayi yayinda ya koma ya zauna akan katifa numfashi yake saukewa kamar wanda
yayi gudun tsare kanshi ya shiga ya mutsawa ."muddin kayi haka baka kyautawa sweet
heart ba, zaka sake jefa rayuwarta cikin tashin hankali ne,karka duba kowa ka duba
halin damuwar da mahaifiyarka zata shiga
a lokaci d'aya ya sauke wani naunayen ajiyar zuciya sakamakon saukar hannun mami da
yaji akan sumar kanshi ,wani zazzafan numfashi ya sauke sannan ya kalleta batare da
yace komai ba " tunanin ya isa haka ka tashi kayi sallah ". ta fad'a sannan ta
ajiye masa flaks din tea ta fito zuwa sallahr magariba ."
Wannan halin da ake ciki ya qara sa hankalin maryam ya tashi matuka ,da gaske dai
yaya adam baya sonta dan gabd'aya ta fahimci halin da yake ciki duk akanta ne,uwa
uba wulakanci da yayiwa mahaifiyarta dan umma ta fad'awa faiza ita kuma faizar
bata boye mata ba ta fad'a mata komai kafin su bar garin "tana kuka take sheida
mata" hakika yaya maryam ni kaina banji dadin abinda yaya adam yayiwa ummammu ba,
koma menen wannan ai tsaknin ke dashi ne ita meye laifinta zai koreta acikin mutane
?."
ada can baya ni kaina yaya adam yana matukar burgeni amamn a yanzu qiyayyar da yake
nuna miki da abinda yayiwa ummammu ya dasa wani mummunar tsanarsa mai girma acikin
zuciyata a karshe tace "to yaya maryam ni dai sai dai ince miki allah ya qara miki
hakuri zama dashi ? shiyasa tunda suka wuce kullum bata da wani aiki sai na kuka a
karshe ta killace kanta acikin 'daki ta kule ta dinga kuka kwana biyu kenan da yini
amman bata fito ba tana daki tana faman kuka sallah ne kawai ke tashinta."
buga kofar mami take da karfi tana kiran sunanta amman mrym bata bud'e ba ta kira
layinta tana ringing amma taki 'dauka daga baya ma ta kashe wayarta gabadaya."wani
kuka ta fashe dashi dan ita wallahi da gaske son ATA take so kuma wanda bazata iya
rayuwa babu shi ba, dan lokacin da mami ta zatar da hukuncin aurensu dadi taji
sosai kawai dai ta boye abun ne acikin ranta saboda sanin halinsa allah ya sani
tana matukar qaunarsa bil hakki so wanda bazai misaltu ba, tun kafin tasan kanta
take fama da wahalar dakon qaunarshi sai gashi adaidai lokacin da take murnar ya
zamo mallakinta ya tsiro da wani sabon salo da nuna kyama ga mahaifiyarta "umma
Kiyi hakurin abinda yaya adam yayi miki haka rayuwarsa take karki yi fushi dashi
kuka take Sosai tana sambatu ."
Tana cikin wannna halin taji ana qoqarin balla kofar d'akin dauke numfashinta tayi
ta tsaida kukanta sai dai fa hawaye bai daina gangarowa ba kofar na gama budewa
mami ta shigo d'akin gigice ta rungume maryam ajikinta tana tmbyrta "me akayi miki
marym da kika dauki matakin cutar da kanki haka ?wasu hawayen masu zafi suka sake
zubo mata cikin muryar kuka tace "mami yaya adam ne!"mami ta sausauta rungumar da
tayi mata ta zuba mata idanu tana kallonta atsanake "yaya adam kuma ?ta fad'a tare
da yin shiru ."
Maryam tayi shiru tana shesheka "Kiyi hakuri diyata ki fad'a min me yayi
miki ?"still dai shiru tayi kafin ta fad'a mata duk abinda ya faru ."dafata mami
tayi kana ta soma mgn "hakika adamcy bai kyauta ba amamn Kiyi hakuri,sai data
numfasa kana ta cigaba da magana "ahalin yanzu adamcy sai kina hada masa da addua
"kai kawai mrym ta gyada mata karkice zaki janye jikinki dashi sakamakon abinda
yayi saboda yanzu ba kamr lokacin baya bane, a yanzu kusa dashi zaki yi ki fara
nunawa mijinki kulawa sannan dole ki koyi juriya akan komai daga garesa har Allah
yasa muyi nasara akanshi ."
" nasanki da hakuri maryam zaki iya yin komai Kiyi qoqari ki fara janyo hankalinsa
gareki ni kuma zan cigaba da addua in sha Allahu Allah zai sausata masa wannan
zafin zuciyar" sannna zan kira ummanki da kaina na bata hakuri .sannan shima adamcy
dole ya kirata ya bata hakuri dan haka kar na sake ganin kinyi kuka ko kinsa kanki
cikin damuwa idan ba haka ba zamu samu matsala still kai ta gyada mata tana goge
hawayenta ,babu laifi ta dan ji sanyi aranta jin zatasa ya kira mahaifiyarta ya
bata hakuri ."
Bayan fitar mami daga d'akin tashi maryam tayi tai wanka ta shirya cikin atafa
Yellow me flower green ta dauko veil green ta fito zuwa parlour'n tayi breakfast
sannan ta shiga neman layin ummanta Allah ya taimaketa bugu daya ta dauka ta
gaisheta ''maryam me ya samu muryarki haka ?"bana dan jin dadi ne jiya da ciwon
kai na kwana gashi banyi bacci ba" "sannu Allah ya sawake, kinsha magani?"eh na sha
sukai shiru can maryam ta cigaba da magana "umma dan Allah Kiyi hakuri da abinda ya
faru "
"Ai maryam ban san wannna mijin naki dan iskan mara mutunci bane sai daya gwada min
cewar shi kwallon tattacce ne,wato giyar kudi na dibarsa shiyasa zai taka duk wanda
yaso to wallahi ni bazan taku ba "dan girman allah umma Kiyi hakuri mami ma tace
zai kiraki ya baki hakuri "wa ?wannan kwallon shegen ne zai kirani ya bani hakuri ?
ai irin tarin qiyayyrki da nagani acikin kwayar idanunshi bazai sa yayi ba "karki
ce hka umma tunda mami tace zai kira ki zuba ido kigani zai kira "to wallahi
wallahi wallahi nasan adamu bazai kirani ba ko mutuwa zanyi bare ma ya rike
hakurinsa bana buqata."
shiru mrym tayi cikin rashin jin dadin saurin rantsuwar da mahaifiyarta tayi ."sai
dai hakan bai sa taji tsanarsa a zuciyarta ba ."yaushe ne tariyarki ko a gidan zaki
cigaba da zama ?ban san yaushe bane amamn nasan mami zatayi komai akan haka "to
walalhi a san abun yi dan bazan sake lamuntar wulakanci ba bayan wanda akayi min
"ko da zinari aka kerasa dan ubansa idan da wulakanci dole a raba auren dan bazai
yuwa ba ni uwarki ban sha wahala a gidan miji ba ,ba zai yuwu tun da kuruciyarki ki
fara hadiyar bakinciki d'a nmj ba ".
"ai na dauka abun nashi na mutunci ne na yarda da zabin yaya ashe tantiri ne ,da
shegen kansa Kmr ball hankalin maryam duk ya tashi sai hakuri take bata"ke wai
hakurin me kika bani ai murna zakiyi tunda daman bakya son aure gara araba auren
tun baa je koina ba kar azo ana cewa Kiyi hakuri saboda ya'ya ."mrym ta sauke wani
wahallen numfashi ."aranta tace umma bazaki gane yadda karfin soyayyarsa yake
kwance acikin zuciyata ba "dan dakatawa umma tayi taji me zata ce sai dai shiru
tayi batare da tace komai ba ,a tunanin umma ko maryam bataji abinda ta fad'a bane
yasa taja bakinta tayi shiru dan haka ta soma fadin hello hello kina kina jina kuwa
.?"
dan numfashi taja ta sauke tana jin yadda soyayyar ATA Ke kwarara ajinin jikinta
"maryam !Na'am umma!" kinyi shiru ko kina son zama dashi ne da wannna mugun halin
nashi ?"wani numfashi ta sake saukewa "umma Ke ba wacce zan boyewa bace tunda ke
mahaifiya ce ko babu komai zaki tausaya min tayi shiru tana faman sauke numfashi
cike da zaku wa ummah tace "uhm ina jinki !
"allah ya sani umma na dai nuna maku bana son aurensa ne a zahiri amman a bad'ani
ina matukar qaunar yaya adam so wanda zan iya rasa raina akanshi "inna lillahi wa
ina ilahi rajiun shikenan yayi galaba akainmu na shiga uku ni habiba madadin mu
juya shi shine zai juyamu sai ta fashe da wani irin kuka tana kiran ta shiga uku ."
rarrashinta mrym tayita yi a kashe tayi mata sallama ta kashe wayar ."tunda ta
kashe wayar take rike da wayr a hannunta cike da damuwa ta rafka uban tagumi diyana
ta shigo assalamu alaikum shiru mrym bata amsa ba kasancewar ta lula duniyar tunani
dan girgiza ta tayi ,a sanyaye ta dubi diyana "maryam lafiya kuwa "?murmushin yake
tayi tace "lafiya diyana "Aa mrym karki min karya tunani fa na samu kina yi ki
fad'a min gsky me Ke damunki amarya?."murmushi ta sake yi duk yadda diyana taso
taji damuwarta taki sai ma shigo da wata hirar tayi byn tafiyar diyana ta kira nana
hauwa'u hira suke kowannensu na fad'awa danuwansa yadda yayi kewarsa ."
***
ATA na tsaye a gaban mirrow yana kallon sansar jikinsa ya rame sosai ,kallo daya
zaka masa ka fahimci irin ramar da yayi wanda Ke tattare da tsananin damuwa tsawon
lokacin ya d'auka tsaye yana kallon kansa ta mirrow kafin daga baya ya sauke
naunayen ajiyar zuciya ya janyo wata qaramar stood dake gefe ya zauna hannushi ya
d'aura a saman faffaad'en qirjinsa yana shafa kwantaccen gashin qirjinsa hade da
lumshe tsumammun idanunsa ,shi kansa yasan duk matar data mallakesa matsayin
mijinta bak'aramin lucky tayi ba ".
cike da sanyi jiki ya soma shafe jikinsa da body lotion yana qoqarin binne
dukkanin wata damuwa da tunanin ,a yanzu yasan bashi da wata damuwa ko tunani sai
na rashin princess amman yana jin lokaci yayi da zai raba kanshin da tunaninta
wani dogon tsaki yaja yana furta "muguwa daga yau babu ni babu tunaninki ,mikewa
tsaye yayi cikin tafiyarsa ta kasaita ya nufi wordrobe dinshi dan saka kayan
shiryawa yayi cikin wasu had'add'un kananan kaya blue jeans with white t shirt "
wani irin kyau kayan yayi masa na d'aukar hankali, ya sake komawa gaban dress
mirrow ya d'auki turare ya feshe ilahirin jikinsa sannan ya kwashi wayoyinsa da
sukayi kwanaki hud'u akashe ya kuna."
nan da nan sakonni sukai ta shigowa ya zuba hannunsa daya cikin aljihun wandonsa
"ya sanya silifas fari sol ya fito yana taku kamar baya son taka kasa a natse yake
saukowa daga step koda ya gama saukowa da maryam idanunshi ya soma cin karo tana
zaune sanye da atamfa ja kayan sun yi mugun haskata abuka ga farar mace sai dai
kallo daya yayi mata ya dauke idanunsa daga kanta yayi tamkar bai ga wata halitta a
wajen ba ya maida hankalinsa inda mami Ke zaune rike da jarida ita kuwa mrym
idanunta kyam akanshi har bata son kifta idanunta idan tana kallonsa wani abu take
ji yana fexgarta mai kama da shoking."
jikinsa ya basa idanunta na kanshi dan haka ta kasan idanunshi ya kalli inda take
tare da jifanta da wani irin kallo wanda yasa tayi saurin dauke kwayar idanunta
akanshi ta sunkuyar zuciyarta na wani irin luguden bugu ,tana son ta gaishesa
amman tsoro da firgici sun taru sun hana , ya cigaba da taku cike da izza da jin
kai da jin shi wani ne ya qaraso ya ajiye wayoyinsa a kan qaramin tablet dake ajiye
a gaban mami ya zauna a kujerar da sweetheart dinsa take zaune ya daura kansa kan
cinyarta batare da yace uffan ba ".
Mami ta'ajiye jaridar dake hannuta wanda tun soma jin kamshin turarensa da takunsa
ta daina karatu da take muryarsa a kasalance yace "gud afternoon my sweetheart"ta
daura hannuta akan kwantaccen sumar kansa tare da fadin" afternoon my adamcy fatan
ka tashi lfy ? ya dan tabe baki "nut bad !"
maryam dake zaune a wajen tamkar mutun mutumin zuciyarta banda bugawa babu abinda
take tsabar firgici ita kanta tana tunanin yadda zaman aure zai kasance a
tsakaninsu ta koina ta duba matsala ne tattare dashi idan aka barta da matseefaffen
tsoron da take masa ma kawai ya isa ya kasheta a gidansa mutun sam babu saukin kai
hatta mahaifiyarsa shan kamshi yake mata ."
ATA bai sake cewa komai ba ya dauki daya daga cikin wayoyinsa daga kwance da yake
yana duba sakwanin mutane da akayi ta turo masa a cikin kwanaki hud'u data gabata
sakon m.Malik ne na farko farko ya tsurawa sakon ido yana karantawa a hankali yana
jin wani iri a gbdy ilahirin jikinsa lumshe tsumammun idanunshi yayi kana ya soma
qoqarin nema layinsa wayar tana ringing baa dauka kusan sau biyar ya kira wanda a
dabiarsa baya kiran mutun sama da sau daya yayi shiru yana cigaba da kallon sakonsa
"adamcy nah!"mami ta kirasa cike da kulawa."
"Hakika mahaifiyarka tayi .."stop sweetheart !" ya fad'a yana kai idanushi inda
maryam take zaune tana kallonsa Kmr zata cinyesa wani mugun kallo mai hade da
harara yayi mata wanda yasa ta mike tsaye da sauri ta nufi hanyar dakin ,mami ta
sauke numfashi tana cewa "me yasa zaka korar min yarinya ?"idan ba rashin kunya
irin nata ba da munafurci zaman me take ?"kuma ma ni bana son kina min fad'a a
gabanta ai sai ta qara raina ni ."wa ya fad'a maka fad'a zan maka "?ni babu fad'an
da zan maka hasalima rokon gafararka zanyi adamcy nasan na cutar da kai akan auren
nan ."
"Adamcy bani da wani zabi ne yasa na yanke wannan hukuncin akanka wanda bansa cikin
maseefa zan jefa rayuwar d'ana ba." ka yafe min "haba sweetheart ki daina bani
hakuri da neman yafiyata wallahi baki min laifin komai ba "wallahi nayi maka laifi
tunda gashi a fushin da kayi dani yasa ka min hukunci mai zafi da radadi na sha
wahala sosai acikin kwanakin nan da ka jefa rayuwarka cikin maseefa "wannan bashi
yake nufin nayi fushi dake ba " yayi maganar Kmr zai yi kuka ".
"Shine mana idan ba fushi kayi ba me yasa zaka min hukunci da shaye shaye bayan
kasan shine abu mafi muni da zai kassara min rayuwa ?shiru yayi kawai yayinda
maryam ta lallabo ta fito daga cikin dakinsu ta rabe tana son taji tautaunawarsu
"dan allah karka sake kai giya bakinka "shiru ne dai ya sake biyowa baya yayinda
mrym ta sake kasa kunne sosai ko zataji mami ta cigaba da mgn "ka min alkwari
adamcy bazaka sake kai giya da duk wani kayan shaye shaye bakinka ba "
"Naji !"
"Ba maganar kaji ba ka bud'e baki kayi min magana "nayi miki alkwarin bazan sake
shan giya ba daman ni ba mashayinta bane damuwar da zuciyata take ciki ne silar
fara shanta na bar giya har abada amman zan sha sigari."mami tayi shiru tana duban
fuskasa "wato dai shi fad'i ka hutu ne kome zai faru sai dai ya faru amman sai ya
fad'a abinda ke ranshi ahankali taji ya kamo hannunta cikin nashi tare da tsaida
kwayar idanunshi akanta "sweetheart ki yafe min domin na kasa miki biyayya akan
abinda kike so nima ba laifina bane ,wallahi da zan iya tursasa zuciyata da zan so
yarinyar nan ko dan saboda darajarki ."
Ta zare hannunta cikin nashi ta daura a sumar kanshi tana cewa "na yafe maka duniya
da lahira" "daman kuma mami ba me iya dogon fushi da tilon d'anta bace dan tun yana
yaro idan yayi mata laifi tayi fushi dashi tofa dare nayi zata tashi tayi alwala
tai nafilfili da masa addua tare da nemammansa sauki da afuwa a wajen Allah shiyasa
rayuwarsa ta cigaba, dan tasan a yadda Allah yayi sa da baud'ad'dan hali irin
wannan tace zata yi fushi dashi to rayuwarsa zata lalace rayuwar bazata masa kyau
ba kuma akarshe dai itace acikin matsala cike da kulawa tace "adamcy me kake son
kaci akwai dish iri iri akan dinner wanda matarka mrym ta shirya maka."
turo baki yayi cike da izza har zai yi magana " kome ya tuna sai Kuma ya fasa cewa
komai sai dai yaji zafin mgnrta matarsa a ina shi baya son ana had'ashi da yarinyar
aure dai an daura bashi da yadda zai yi amman sai ta gwamaci mutuwa da rayuwa dashi
da kanta zata zo tace araba auren idan taji wahala
mami ta tsurawa fuskarshi idanu kana tace"adamcy nah kayi shr "ya lumshe idanunsa
kawai " muje kaci wani abu , ahankali ya ware idanunshi akan mami yana dubanta
sannan ya motsa labbansa da kyar yace "sweetheart na koshi fita ma zanyi
yanzu ....."
"fita zakayi byn baka sakawa cikinka komai ba ina fa hankalce da kai duk kwanakin
nan bakason cin abinci, ina zaka ma tukuna da naji kace fita zakayi byn kana cikin
hutun angonci ?ta fad'a tana hade fuska tamau hade da zuba masa idanunta."ya d'an
ytsina face dinsa har dimple dinsa ya lotsa" kyawunsa ya sake bayyana" ya mike daga
kan cinyarta ya zauna sosai shima yana kallon yanayin Sweetheart dinsa yana jin
soyayyarta fiyye da komai "yana sonta baya son damuwarta, itace duniyarsa sannan
itace ke tattare da duk wani farincikinsa tana tsantsar sonshi da nuna masa duk
wata kulawar da uwa kad'ai zata iya yin haka kawai inda tayi masa ba daidai ba
hadashi aure datayi da mrym shima kuma ya yafe mata yasan batayi hakan dan
kuntatawa rayuwarsa bane ."
Hannuta ya kamo duka cikin nasa ganin yadda ta damu muryasa a sanyaye kmr koda
yaushe "am so sorry my sweetheart zan dan fita ne amman muje zanci tayi murmushin
jin dadi "alhamdulillah! ta furta acikin ranta da alamun adamcynta ya fara dawowa
daidai tace" kai ko hade da dan dungure masa kai " kai komai zakayi sai kayiwa
mutun kwalisa ai naso ace mafarkinka gsky ce ta canza min kai byn ta canza min kai
ta juya ka son ranta "haba sweetheart kina ganin akwai wannan matar da zata iya
canza miki ni daga yadda nike ko juya ni ?akwai mana idan nmj na son mace babu
abinda bazai iya yi akanta ba "banda wannan d'an naki dan bazai jiyu ba duk son da
zan yiwa mace bazan ta'ba bata wannan chance din ba ."
"Allah ya shirya min kai" ta fad'a tana d'aga murya ta kwallawa mrym kira ". ATA ya
yatsina fuskar sannan ya langwa'bar da kai yace "sweetheart ki barta kawai ki
zuba min da kanki nafi son naci daga gareki dan ma banson wahalar dake ne da sabon
girki zaki min ya karasa fadar maganar yana had'e rai ,mami ta dubesa ta sake yin
dariya cike da jin dadi tace "Allah ya shirya min kai adamcy "
"Ameen !ya amsa yana kashe mata idonsa daya " yau kawai ka wanke min zuciya ka
sanyani ciki farinciki mara misaltuwa allah yayi maka albarka yasa ka gama da
duniya lafiya ."
byn ya gama cin abinci duk da ba wani abin kirki yaci ba "amman hakan ya yiwa
sweetheart dadi, ko ba komai ya dan saki ranshi ba kmr kwanaki ba. wayarsa ce ta
karade parlour da qara wanda tun soma cin abincinsa yake jin ringing dinta amma ya"
share, ahankali yasa hannu ya dauki wayar yana kallon screen din wayar " sunan mb
ya gani rubuce yana wayo "tabe baki yyi kana ya manna wayar a kunnenshi ."Mb najin
alamun an daga wayar cike da natsuwa muryarsa babu wata alamun damuwa dan daman
kuma salim ya sheida masa ya samu sauki yace" yayi angon maryam da girma
kujerarka ."
ATA yaja tsaki yace" ya'akayi sarkin matsala.?
bangaren mb kuwa shekewa Yayi da dariya sannan yace" meye abun tsaki malam ka
saki jiki ka morewa angonci"enough mb !"banaso I don't like it please "shiru sukai
gbdy kafin ATA ya cigaba da mgn kana ina yanzu ? "okay kazo yanzu , eh zaka iya
zuwa ka jirani a waje kuma karka sake kayi min westing time dan nasan halinka da
son jikin tsiya fuskar sweetheart dinsa yake kallo har sanda ya gama waya sannan
yace mata shi zai fita sai ya dawo tayi masa a dawo lfy " .
mikewa yayi tsam cikin tafiyarsa ta kaisata ya nufi hanyar kofar fita ya daura
hannushi kan handle din glass door mami ta kira sunansa "adamcy nah !ya juyo yana
dubanta tace "kar kade fa sannan zan turo maka number mahaifiyar mrym idan ka
fita ka kirata ka bata hakuri kaji bai son wani jan mgn dan hk ya gyada mata
kai tare da cewa " love you sweetheart ya sake juyawa ya murda kofar ya fice wani
irin farinciki ya sake lullube mami tasan ba qoqarinta ba ne karfin addua ne kuma
ta lura tunda ya sha tufin limamin nan ya sauya kad'an ba kamar kwanani ba ."yana
fitowa masu tsaronsa duk suka mikewa zagaye dashi yana tafiya suna zagaye dashi
yana masu bayanin inda zashi har ya qaraso bakin gidan baba babba dan tunda aka
samu matsalar nan basu had'u ba shi."
Wasu daga cikin masu tsaronsa suka tsaya a waje wasu suka bishi zuwa ciki a babban
parlour'n ya sameshi byn ya gaishesa ya zauna shi kansa baba yaji dadin ganinsa
kuma hankalinsa ya kwanta yayi masa nasiha akan zama da iyali da kuma hakuri da
rayuwar duniya sun dan jima suna tautaunawa ATA yayi masa mgnr nuzla "ku rabu da
yarinyar nan ,na ma fadawa kowa su cireta aransu tunda ta zabi wannan rayuwar
kenan bata da bukatarmu "bazaa yi haka ba hakuri dai zakayi baba in sha allahu zaa
san abunyi "karka ta'ba kudinka adamu akan nuzla tunda ita da kanta ta zabarwa
kanta haka ni da zaka maida hankali akan hindu ma sai nafi dadi ."
ATA bai boye baba babba komai ba akan hindu abubuwan da suka rincabe ne yasa ban
nemi naji yadda ake ciki ba kuma duk kwanaki nan wayoyina a kashe suke nasan da
zasu nemeni amman dai idan abubuwa sukai sauki zan kira naji yaake ciki dan dole
nasan hindu taje prison domin zargi sun tattaru akanta " Allah ya kyauta ya shige
mana gaba yaran yanzu ne ka haifesu baka haifi halinsu ba allah ya shirya mana gbdy
kiran mb ne yasa yayiwa baba babba sallama ya mike ya fito tsaye ya iske Mb shi
kadai jingine da jikin motarsa hannuwansa rungume da kirjinsa ya mikawa ata hannu
suka gaisa ."
daya daga cikin motocin ATA yansanda masu farin kaya suka bud'e masu suka shiga
yansanda dss suka soma yin gaba sannna motar da ata yake ciki wasu motoci guda uku
abayansu suka fice daga cikin gidan sai da suka hau titi sosai sannan mb ya waigo
ya tmbyesa "wai ina muka nufa ne ? gidana dake ikoyi "me zakayi a ikoyi by this
time kai da baka da lafiya ?"me ya sameni?ya fad'a yana jiransa da wani irin kallo
kai ma kasan baka da lfy amman dai yanzu naga alamun ka samu sauki "tsaki yaja yana
qarawa ."
"fad'a min abinda zakayi a ikoyi dan yamma tayi kasan wannan hanyar babu sauki sai
na kira madam na sheida mata karta ga na dade ban dawo ba ta dauka ko wani abu ne
wani tsaki ata yaja "ku dinga jin tsoron mata kamar su suka kawoku duniya ni yanzu
akwai macen da zan tsaya fadawa inda zani da dalilin jimawata a waje ?"never babu
ita wannan macen a duniya ."Mb yayi murmushi kawai "bazan ce komai akan wannan ba
saboda baka zauna da mace kasan dadinta ba sannan baka da wani experience na zaman
aure zamuyi wannan maganar amman sai anan gaba idan ka zama cikakken mai gida ."
wani tsaki ya sake ja tare da kiran "nonsense sau kuyita yi tunda kun zama bayin
mata kai ma zaka zama bawan mace ne muje dai zuwa ."a natse ya cigaba da motsa
lip's dinsa "wani sako na gani daga m malik to nayita kiran wayarsa baa dauka ba
shine naji hankalina bai kwanta ba nake son naje naji me sakon yake nufi, hakan
naji sakon ya tsaya min arai ,sakon ma yayi three day's da turowa ."Allah yasa
lafiya shiru kowannensu kafin daga baya suka cigaba tautaunawa wanda kusan duk akan
rayuwar da ATA ya jefa kanshi ciki ne ."
suna cikin tafiya daya daga cikin wayoyin ata ta fara Ringim ya dauka ya duba sunan
aunty khadija ya gani kamar ba zai dauka ba sai kuma ya dauka tare da cewa"kanwa
yaaakayi fatan ba da wata matsala kika zo ba ?gsky adam kayi mugun rainani kema
Kinsan shishigi kawai kikayi kika rigani zuwa duniya amman duk da haka dai kece
akasana "tunda kasan da haka ai shikenan ya karfin jikin naka "daman bani da lafiya
ne "baka dashi mana amman yanzu na fahimci ka samu lafiya yanzu daman na kira ne
akan abinda kayiwa ummu habiba wacece haka kuma "bangane wacece haka ba ?ummu
habiba din ce bakasani ba?"
"kiyi maganarki kai tsaye dan bangane ko wacece ba shi yasa nace haka "to
mahaifiyar maryam "tsaki yaja yana sauke numfashi sai lokacin ya tuna mami tace ya
kira "Adamcy ya dace ka kira mahaifiyar maryam ka bata hakuri ."akan wani dalili
kenan ?" akan abinda kayi mata mana "ni bansan nayi komai ba" idan kayi haka baka
kyauta ba dan gsky abinda kayi yayi tsauri dayawa amman zan ari bakinka naci maka
Albasa" ni dai ban sakaki ba idan zakiyi Kiyi da sunanki karki yi da sunana yana
gama fadar haka ya katse kiran ."mb ya dan waiga ya kallesa "kai mai yasa baka son
gsky?" ka bada hakuri shine zai zama wani aiki "amman kai zaka bawa wani labarin
halina bazan ta'ba bada hakuri ba ."
"amman ita wannan ai tmkr mahaifiyace adam yadda zaka girmama mami hk zaka
girmamata "wannan raayinka kenan .
"dole fa ka sauya yanzu bazai yuwu ka dinga bin raayin zuciyarka ba kana aikata ba
daidai ba " dan allah malam karka damu rayuwata raayinka dabam nawa dabam hakuri
ne bazan bayar ba idan dole sai na bayar wallahi sai na saki yarta inga ta tsiya
" a fusace yake maganar yana kaiwa nan yaja tsaki sake girgiza kawai kai mb yayi
tare da yin shiru tafiya mai dan nisa sukayi suka qaraso bakin get din gidan
securities na ganin motocin ATA sukai saurin bude masa tafkeken get din ."
Ahankali suka shiga sukai parking a haraban gidan kusan atare suka fito cike da
girmamawa suka shiga gaishesa inda yake tmbyrsu m malik nan suka sheida masa abinda
ya faru babu bata lokaci ya tmbyi hospital din da yake suka fad'a masa suka koma
cikin mota suka fice ."ATA ya shiga tashin hankali matuka lokacin da yake iso cikin
dakin da m malik Ke kwance yana kallonsa rai hannun Allah.abakin matarsa yake jin
qarin bayanin yadda abun ya kasance hawaye na zuba daga idanunta ".
shiru kawai ata yayi zuciyarsa cike da tashin hankali" yanzu mai likitoci suka
ce ?"wai sai dai a fita dashi waje ya gyada kai tare da cewa "ku shirya at any time
zaku iya wuce yana gama fadar haka ya fito daga cikin dakin zuciyarsa cike da
tausayawa ,matarsa ta biyosa tana masa godiya. da tunanin me m malik yake son fad'a
masa ya baro hospital sai tunaninsa ya kai ga mafarkinsa sai kuma yaji ba haka
bane menene abinda zai fad'a min haka yayita aikawa kwakwaluwarsa tmby karfe takwas
suka dawo gida mb ya shiga motarsa ya wuce gida shi kuma sai da yayi magariba da
ishai sannan ya nufo gidan mami ."
da kyar ata yake daga kafafunsa a natse ya sanya hannu shi ya turo kofar falon
tare da sallama akan lip's dinsa ,mrym na ganinsa ta lumshe idanunta sakamakon
kamshin turarensa da ya bugi hancinta dan ta gefensa yabi ya zauna a kusa da mami
yana kiran "washiii Allah !" sannu ka gaji ko "wallahi sweetheart ya gida ?daga
hk bai sake cewa komai ba yayi shiru "lafiya dai ko naganka wani iri ? "ba lafiya
ba sweetheart ya fad'a sanda yake gyara zama .
" mrym kawo masa ruwa ya sha ta tashi taje ta kawo masa "ga ruwa yayi mata banza
dole ta ajiye a kusa dashi tana jin fad'uwar gaba bayani ya cigaba yiwa mami tana
jimami bai sha ruwan ba ya sake lumshe tsumammun idanunshi byn Kmr second biyar ya
bude idanunshi yaga idanun maryam kyam akanshi tana kallonsa kwayar idanunta cike
da qaunarsa wani abu yaji ya tokare masa makoshi mikewa yayi tsaye dan baya son ya
sake yin wani abu da zai ta'ba zuciyar sweetheart dinsa "sweetheart sai dai safe
"allah ya tashemu Lfy ya nufi step bayansa tabi da kallo har ya bacewa ganinta gbdy
ya tafi da rayuwarta bata son abinda zai sa tayi nesa dashi ."
Yana tsaye a dakinsa yana kokarin cire kayansa yaji anyi knocking cike da mamaki
ya qarasa yana balle maballin gaban rigarsa ya bude kofar , daya daga cikin masu
aikin gidan ne hannunta rike da wani qaramin tire dake dauke da glass cup an rufe
sbd sanin halinsa ta rusuna cike da girmamawa sannan ta mika masa yayi shiru yana
dubanta tare da mamaki, ganin yadda yake kallonta tai saurin cewa "hajiya ce tace
na kawo maka jin tace mahaifiyarsa ce ya kar'ba ya maida kofar ya rufe , madara
ne mai sanyi ya kai bakinsa ya fara shan kad'an wani dadi ya ji dan har sai da
kunnensa ya motsa dan hk ya sake kai bakinsa ya shanye ya ajiye cup ya soma cire
kayansa ."
tabawa mai aiki ta nufi inda maryam take tsaye tana jiranta tana ganinta tasan
adduarta ta karbu tai murmushin jin dadi tana dafata tana cewa "bai miki tambayoyi
ba "yana shirin yi nace hjy ce ta aiko ni" da kyau na gode sosai tabawa mai aiki
ta kama gabanta "ya kwashe kayansa ya zuba a basket ya shiga bathroom ya watsa ruwa
ya fito ya sanya kayan bacci mai budaden gaba ya qara karfin ac dakin kwanta ya
lullube rabin jikinsa ya canza wutar dakin sai dai ya kasa runtsawa m malik ne ya
fado masa ya tashi ya zauna ganin tunanin nason hanshi bacci ya yaye bargon daya
lulluba dashi ya sauko ya dawo falo ya kunna sigari yana zuga Ahankali tunani
sosai yake yana bukatar sanin abinda m malik yaso fad'a masa sakonsa kuwa ya
karanta yafi sau goma amman ya kasa fahimtar akan me ye ?dole dai ya jira har zuwa
lokacin da zai dawo norma.
******
Yau asabar wanda yayi daidai da kwanaki shida kenan da aurensu ata Wanda ya kama
a lissafin hjy zulfa'u Gobe ne nana hauwa'u zata tare a gidanta hisham yana kwance
akan kujera mai zaman mutun uku sai ga hjy zulfa'u ta fito daga dakinta ta kai
idanunta kan agogon dake manne a parlour'n karfe goma har ta wuce gashi tun da nana
hauwa'u take gidan a parlour'n yake kwana baya shiga dakin da take sai dai idan zai
dauki wani abunsa mai mahimanci ranta a bace tace " ka tashi ka shiga daki ka
kwanta ka wani zo ka kwanta anan ka bar nana hauwa'u ita kad'ai" ." babu mutsu ya
mike tsaye dan bai son damuwa har yayi taku uku ta tsaida shi ta soma magana
"hisham ka kular min da yarinya kada ka wulakantar min da 'ya idan na lamunce komai
banda wulakanci bai tsaya jin kalamanta ba dan idan ya tsaya ya cigaba da ji
zuciyarsa zata tarwatse
A natse ya tura kofar d'akin ya shiga tana zaune aka katifa ta jingina bayanta da
abun gado ya zagaya dayan bangaren ya samu waje ya kwanta bai jima da kwanciya ba
wayarsa ta dauki sautin qara ya d'auka ya duba ganin sunan dake wayo akan screen
din wayr ne yasa shi ya zabura ya miki zaune yana daukar wayar tare da kiran sunan
da dan karfi "nuzla !" Kina ina ? tun da ya fara wayar ta zuba masa idanunta kawai
tana kallonsa yayinda idanunta ya ciko da ruwan hawaye "karki damu nace miki ganin
nan zuwa ki tsaya a wajen ya qarasa wayar yana bude kofa ya fito zuwa haraban gidan
yana qoqarin shiga motarsa qarar tada motar ya janyo hankalin hjy zulfa'u dake
tsaye tana shirin kwanciya ta yaye labulen window taga hisham ne kallon yadda yaja
murfin da karfi ya rufe da yadda figi motar zai nuna maka da baya cikin
haiyacinsa."
"Ya allah ka shirya min hisham ina kuma zashi adaidai wannna lokacin ta tambayi
kanta tana jin faduwar gaba hankalin hajiya zulfa'u yayi matukar tashi dan haka ta
kasa kwanciya ta fito daga dakinta ta shiga dakin da nana hauwa'u take ."take taji
zuciyarta ta karye dan koda tashiga dakin kuka take sosai tamkar ranta zai fita duk
yadda taso daurewa ta kasa ta fad'a jikin mumy da kyar ta iya daure abinda take
ji .mumy ta shiga rarrashinta da kyar ta samu nana hauwa'u tayi shiru ."
"Har abada bazaki yi danasanin auren hisham ba muddin ina raye sai kin zama
tauraruwa a gidansa ki qara hakuri ,amamn idan har kika ji bazaki iya zama dashi ba
ki fad'a min aurenku bazai qara koda second daya ba wannan kalmar dake fita daga
bakin mumy yana mata dadi da sanyaya ranta a duk sanda ta furta hakan ma yana sa ta
danne duk wani abu da take ji dan tasan ba cuta tasa ta hada auren da danta
ba ."wani tausashen murmushi ya subuce mata sosai take jin dadin kalaman mumy tana
ganin yadda abun zai zo masu da sauki ta hanyar mumy yanzu ya kike jin zamanki kina
ganin zaki cigaba da rayuwa da hisham ?ta gyda mata kai .
"Yauwa diyar albarka allah yayi miki albarka Ameen ta fad'a tana jin qaunar mumy
acikin ranta "yanzu fad'a min ina hisham ya tafi ?shiru tayi tana neman abind zata
fad'a mata domin ta kareshi a wajen mumy byn Kmr second biyu tace "na dai ji yana
magana akan wani contract "contract? mumy ta tambaya nana hauwa'u ta sake gyada
mata kai tana sunkuyar da kanta kasa mumy tayi mata sai da safe ta juya idanunta ta
zubawa mumy har ta fita daga dakinta ta lumshe idanunta "bata ga abinda nuzla ta
fita ba da yaya hisham ya kasa karbata acikin zuciyrsa yanzu dai tasan sai dai tayi
zaman aure dashi darajan mumy ."
Yana tuki yana jin wani irin bugun zuciya kuka zuci yake wanda yafi na fili ciwo
idan har ya tuna nuzla bata son shi sai yaji radadi sautinta yanzu ma yawo sautinta
yake masa acikin kunnensa yana jin kamr ya juya ya koma gida amman sai yaji bazai
iya ba ko babu komai zataci darajan baba babba salim da yaya Ibrhim yasan muddin ya
maidata gida zasu ji dadi kuma hankalinsu zai kwanta ."yana gama isa inda nuzla ta
kwanta masa yayi parking ya fito cikin tsnanin tashin hankali ya rufe murfin motar
da karfi nan da nan zuciyar nuzla ta karye ta qara sautin kukanta da take akaro na
biyu" allah sarki yaya hisham hakika sai yanzu ta soma jin nadama abinda tayi
masa ."
daga inda take ta fito ganin yana waige waige da qoqarin neman layinta "yaya hisham
ta kira sunansa da sauri ya juyo ya ganta tsaye abayansa tsayawa yayi yana kallonta
tun daga kasa har sama cikin wata atamfa dinki riga da siket kayan sun mata cif cif
ajiki ta rame sosai sai dai baqaramin kyau tayi masa ba wani abu yaji ya tsarga
masa tun daga tsakiyar kanshi har zuwa yatsun kafafunsa ,bai san sanda ya fixgota
jikinsa ya rungumeta tsam kamar zaa kwace masa ita." ahankali ta saki wani kuka
mara sauti ya sake kamkameta ajikinsa yana shafa bayanta "tun tana kuka slow slow
har ta bari kukan ya fito da sauti tun baa je koina ba tayi nadamar rashin
aurensa."
"Me yasa na biyewa son zuciyata ?me yasa banyi hakuri ba ?kuka take sosai wanda
kukan nata yana qara daga hankali da dawainiya da hisham gabadaya ya dawo mata wani
iri sai daya dauki second talatin rungume daita sannan ya sautata rungumar da yayi
mata".bai ce mata komai ba yaja hannunta ya nufi inda motarsa take "ina zaka dani ?
yayi mata banza ya bude gaban mota ya sakata ya maida murfi ya rufe ya zagaya ya
bude mazaunin direba yaahiga "dan allah karka kaini gida "me yasa bazaki gida ba ?
tayi shiru kawai tana wasa da hannunta dan bata san me zata fad'a masa ba ."
"kin gudu akan bakya sona yanzu kuma wannan ya wuce a tsakaninmu, babu wani batu na
soyayya sai na yanuwantaka ne a tsakaninmu, ai gara ki koma gida ki cigaba da
rayuwarki ."tayi narai narai da idanuwa tana dubansa kallon dake tsuma zuciya da
gangar jikin yaya hisham ya numfasa ya cigaba da mgn "yanzu matsayin kanwa kike
agareni ki koma gida ki fara sabuwar rayuwa " daga hk bai kara magana ba yaja motar
bai tsaya akoina ba sai acikin haraban estate dinsu tsayuwar motarsa ya sake daga
mata hankali yayi parking ya fito yana daidaita nutsuwarsa bai mata magana ba yayi
mata alamar ta fito yanayin yadda taga fuskarsa babu annuri ko daya sannan kuma
babu wasa yasa ta fito tabi bayansa ."
Duk da dare ne idanun mutane na kansu kasancewar akwai hasken fitilu ahankali ya
tsaya bakin kofar gidansu alokacin da shadaya da rabi ta buga hannu ya kai yayi
knocking sautin muryar mahaifinta taji yana cewa" waye ?baba hisham ne "hisham kuma
adaidai wannan lokacin Allah yasa lafiya? ya fad'a yana bude kofar ya koma gefe
hisham ya shigo yana gama shigowa nuzla ta shigo tmkr mai jin sanyi da idanu baba
babba ya bita dashi kafin yace "ita kuma wannan fa daga ina ?baba kayi hakuri dan
allah."
hajiya salema kam tuni ta zabura ta mike ganin nuzla ta qaraso ta rungumeta
ajikinta tana kuka "haba nuzla me yasa zaki min haka kin kuwa san halin damuwar
dana shiga "hisham ka dauketa ka maida ita inda ka daukota bazata cigaba da zama
dani ba." dan girman allah baba karkayi haka kai din fa mai hakuri ne kayi hakuri
ka yafe mata nuzla yarinya ce har yanzu idan kaki amsarta ina kake son taje ."?"ta
koma inda tayi kwanakinta amman ba a gidana ba." yana gama fadar haka Ya juya ya
shige turakarsa jin haka yasa hajiya Salema ta saki nuzla ta bi bayansa tana
kuka ."
Cikin fushi nuzla ta nufi kofar fita yaya hisham bai san lokacin daya fizgo hannuta
ba ya sanya cikin nashi ya dan matsota kamar zai shige jikinta ganin kallon da take
masa yasa shi janyota gabadaya jikinsa "kina hauka ne ina zaki ?bakaji abinda baba
ya fad'a ba? shine saboda baki da hanaki zaki fita to me zanyi ? tayi mgnr a
shagwabe "bazaki koina ba kin dawo gida kenan karki sake ganganci sake barin gidan
nan ya rad'a mata acikin kunneta wani iri taji agabadaya ilahirin jikinta "ya
zareta ajikinsa ya nufi dakin hajiya salema daita yana cewa "matukar kika sake
barin gida karki sake marmarin kirana a waya dan haduwarmu bazai mana kyau ba ya
zaunar daita akan gado yana já mata kunne."
ta kallesa shima cikin kwayar idanunta yake kallo yana jin sonta na bin jinin
jikinsa yana son nuzla da dukkanin rayuwarsa rausayar da kwayar idanunta tayi a
cikin nashi kamr da gaske zai iya aiwatar da wani abu akanta idan ta sake barin
gida " sai da safe ki kula da kanki" ta gyada masa kai tana kallon bayansa numfashi
ta sauke "wani irin so yaya hisham yake mata haka ?duk shawarwari da nasihar daaka
sha mata akanshi basu ta'ba tasiri ajikinta ba sai acikin kwanki bakwai kacal da
yayi aurensa ta soma jin wani iri akanshi ."
Mmn sudais
💗💗💗💗💗💗
MAR'ADAMS
💖💖💖💖
💗💗💗💗💗💗
*AYSHA A BAGUDO*
WATTPAD @HAUESH
AREWABOOKS USERNAME
AYSHAABAGUDO
bismillahirrahmanirrahim
Wannan littafin na kudi ne mai bukatar karantashi byn na kammalashi zai biya 1000
ta wannan account number din 1438775094 Aishat abdullahi access idan an tura sai a
turawa wannan 09136918331 alert domin tabbatar da an tura domin sauraron littafaina
a tuntubi chaneel dina (Hausa bakwai ) a YouTube.
Page 3
...... A parlour hisham ya iske hajiya salema zaune ta dafe kanta da duka
hannuwanta tana risgar kuka, cike da tashin hankali hisham ya qaraso ya durkusa a
gabanta yana bata hakuri "dan girman allah hajiya ki daina haka ." "ban san me
Alhaji yake so dani ba hisham, taya zamu haife 'ya acikinmu mu watsata duniya?"
kuskure ne kowa yasan nuzla tayi kuskuren amman tunda ta dawo ai sai kowa yayi
hakuri tunda qaddara tana kan kowa, kuma qaddarar aurenka da nana hauwa'u ce silar
fitar nuzla daga gida."
Cike da tashin hankali nuzla ta fito daga cikin d'akin sakamakon jin sautin kukan
mahaifiyarta sai dai jin furucinta yasa ta qara shiga tashin hankali mai tsanani
cikin rud'ewa ta shiga fad'in "pls umma babu inda zaki sai dai idan nice zan bar
gidan nan amman Ke babu inda zaki." ta qaraso ta zube ajikin hjy salema tana wani
irin kuka dan duk ita ce silar jefa mahaifiyarta cikin tashin hankali ."dan allah
ummah kiyi zamanki bari na tashi na bar gidan nan tun yanzu" ta mike tsaye cikin
rawar jiki zata nufi kofar fita."
wani irin razananniyar tsawa hisham ya buga mata wanda ya firgitata tare da yi
mata alama da ido ta koma d'aki " kina hauka ne ko kin fara shaye shaye ne ?ya
tambayeta a matukar fusace yana tsare gira." Kallonta yake mai had'e da harara "ki
shiga hankalinki sannan ki koma d'akin ko kofar parlour'n nan ban yarda ki taka ba
bare ki bar gidan nan ."babu musu ta juya tsimi tsimi ta koma tana kuka ."Yaya
hisham bai tsaya sake cewa komai ba ya mike tsaye ya nufi d'akin baba babba ."
bakinsa d'auke da sallama ya'isa cikin d'akin baba babba yana zaune yana shan ruwan
tea ya amsa masa sallama ." ahankali hishsm ya k'arasa ya durk'usa har k'asa a
gaban baba babba ,cikin d'aure fuska baba babba yace "a,a har yanzu baka wuce gidan
ba?" cike da fargaban ganin yanayinsa ya d'an sosa bayan keyarsa yace "eh baba
wallahi ban wuce ba saboda na kasa samun natsuwa ."
baba ya sauke numfashi kawai saboda yasan kwanan zance shi kansa yana jin alhinin
rasashi da diyarsa tayi amatsayin miji domin samun miji kamar hisham wallahi sai an
tona ,kaf mazan daginsu yafi su nagarta da hakuri wanda hakan yana d'aya daga cikin
dalilin da shi karon kanshi yake ta bin nuzla akanshi amman taki bin umarninsa dan
ko adam bazai nuna masa komai ba sai tarin dukiya ".
Shiru ya d'an ratsa d'akin can baba ya d'ago ya dubesa sannan yace "hisham ya dace
ace ka kama hanyar komawa gida ko akwai abinda kake so ne...?" ya jefa masa
tambayar domin yaji meye raayisa akan nuzla ." sake shafa keyarsa yayi sannan ya
d'ago cikin yanayin jin kunya ya fara magana "ammm baba .."dama...dama"!! sai kuma
ya fara in ina, shiru baba babba yayi yana kallonsa duk ya wani rikice ahankali
yace "relaxes hisham kwantar da hankalinka kayi min magana ina sauraronka" .
da kyar ya samu nutsuwa sannan ya fara magana "dama baba na shigo ne na qara baka
hak'uri akan abinda nuzla tayi wallahi tayi nadama baba baza ta sake kwatanta
abinda tayi ba dan Allah kayi hak'uri ka yafe mata ka kuma bata wani dama zata
gyara
Still shiru baba babba yayi yana kallonsa kawai cike da tausayawa duk mai hankalin
da ya kallesa yasan yana cikin shaukin só ,koma yace soyayya na tangalili da
rayuwarsa ,lumshe idanunshi yayi kawai dan ba hakurinsa yafi buqata daga garesa
ba,a halin yanzu babu abinda yake bukatar ji kamar ya furta masa cewar zai aure
nuzla ya had'ata da yar'uwarta".
"kayi hak'uri baba nasan kayi fushi sosai daita yanzu idan ka koreta daga gidan nan
ina kake tunanin zata ?".mu godewa allah ma data dawo gida da ba'a nemeta gbdy an
rasa ba" still dai shiru baba yayi "baba bana son rayuwarta ta lalace dan Allah
kayi hak'uri ka barta ta cigaba da rayuwa acikinmu shine kwanciyar hankalina ;;"
yai maganar cikin yanayin tausayi yana zubar da hawaye"..
Hmmm....!!! baba babba ya sauke nannauyen numfashi sannan ya fara magana "hak'ik'a
hisham nuzla ta aikata min babban laifi wanda kullum na kan zauna nayi tunanin
abinda yasa tayi min haka .
"ina tarbiyar dana bata?"wallahi rai na yab'aci sosai akan abinda tayi amma ba
komai komai ya wuce ka daina kuka taci darajanka wallahi banci kai da sai dai ta
koma inda ta fito ka tashi ka wuce gida dare nayi Allah yayiwa rayuwarka albarka ka
gaishe min da matarka tashi kaje"
wani irin sanyin dad'i hisham yaji ya mamayesa bai san sanda ya rungume baba babba
ajikinsa kamar wani k'aramin yaro yana fad'ar "thanks my dad i love you so so much
am very proud of u my dad" nima ina alfahari da kai hisham Allah yayiwa rayuwarka
albarka "ya sakesa ya fita yana murna baba babba kuwa banda murmushi babu abinda
yake yana mamakin irin son da yakewa nuzla "....
karfe d'aya daidai hisham ya shigo gidan kuma akan idanun hajiya zulfa'u da nana
hauwa'u ya shigo bayan ya shigo ya rufe koina yana qoqarin kwanciya akan kujera mai
zaman mutun uku ya ga mumy tsaye akanshi tana masa mazurai da idanunta gabansa né
yayi wani irin mummunar fad'uwa muryarta a kausashe ta soma magana "daga ina kake
adaidai wannan lokacin?"shiru yayi tare da sunkuyar da kai cikin tsananin tashin
hankali dan bai san me zai fad'a mata ba ,gashi shi bai iya karya ba daya girba
mata karya ya huta ."
"Ba da kai nake magana ba kana jina kayi min shiru.?"amm daman ..."sai kuma ya sake
yin shiru yana shafa sumar kanshi alokacin da nana hauwa'u take taku domin fitowa
daga daki "kai nake sauraro ka ji dani bacci nake ji daman me ?".daman mumy nuzla
ce ta kirani shine naje na d'aukota na kaita gida ."
"what ?"!
"hisham kana da hankali kuwa?"ka tsallake matarka kaje ga wata nuzla din banza "
numfashi ya sauke sannan ya motsa lip's dinsa yana mai d'ago kanshi daga sunkuyar
wa da yayi "mumy nuzla fa ba banza bace, bai kamata dan tayi d'an wannan Kuskuren
ba ki d'auki zafi dayawa akanta ,sannan ko babu komai nuzla diyarki kuma kinga dai
irin halin da kowa ya shiga akan rashinta ,"kiyi hakuri dan allah nasan nayi ba
daidai ba dana fita adaidai wannan lokacin amman nuzla tana da matukar mahimanci
arayuwata domin zuciyata ce bazan.."
saukar mari akan kuncinsa ya katse masa maganarsa ,hatta nana hauwa sai da jiyo
saukar marin ajikinta dan tana daf da fitowa parlour'n mumy tayi masa marin ."cak
ya tsaya yana kallon fuskar mumy dafe da kuncinsa yayinda nana hauwa'u ta fito jiki
a matukar sanyaye ta tsaya abakin kofa tana dubansu cike da tashin hankali idanunta
suka cicciko da ruwan hawayen abu biyu rashin son da hisham yake nuna mata da kuma
na dawowar nuzla gida." "hakika tayi farinciki da jin wannan labari dan daman
kullum zuciyarta cike take da tunanin inda take ."
"wallahi wallahi !! sau nawa kaji na rantse idan ka sake min magana akan nuzla
zuciyarka ce sai nayi mummunar sa'ba maka ,idan ban iya tsine maka akanta ba allah
yayi min yadda yake so, kai shashan ina ne ?da zata gudu tayi shawara da kai sai da
zata dawo gida ne tasan da kai ? kai kuma ga shasha tantabara sarkin alqawari ka
girba wa matarka karya an kiraka an contract ka kwashi jiki kaje wajenta ,in da da
wani abu ya sameka fa ?"tayi masa Kmr zata zubar da hawaye ."
"yarinyar nan tace bata sonka bata sonka !! dole ne hisham ?ko dole ne soyayya da
bazaka hakura daita ba "? hisham ya sauke numfashi yana shafa kuncinsa yace
"wallahi mumy sai kin ganta ,tayi nadama sosai "babu ruwana da wata nadamarta tunda
bata min alkunya akanka ba nima bazan mata ba ,kai kad'ai fa na mallaka arayuwata
ni duk yadda muke da mutun yace bai sonka ai sai inda karfi ya qare akan kiyayyarsa
,kasani nuzla diyar dan'uwana ce amman bana sonta da kai tayi rayuwarta kayi naka
allah ya bata wani mijin ."
"Haba mumy take it easy now duk fa abun bai kai haka ba "ka kamin baki anan karka
sake min magana akanta bana són ji ta fad'a à hargitse, tsayawa yayi kawai yana
duban mahaifiyarsa gbdy ta hargitse ta canza masa Kmr wata mai ciwon iska " wallahi
ka sake zuwa inda take sai na ...."saukar hannun abba taji a bakinta yana cewa
"haba my dear wai meye haka ne ?hucin numfashi ta fesar na 'bacin rai tana dubansa
cike da takaici, bai sake barin tace komai ba yaja hannunata zuwa d'akin baccin su
yana rarrashinta."
Ahankali nana hauwa'u ta tako ta tsaya gaban hisham tana kallonsa rasa abun yi tayi
saboda ganin yadda fuskar hisham tayi tana cikin yanayi na tsnanin damuwa dan haka
ta zuba masa idanunta tana canza fuskarta zuwa yanayi na murmushin farinciki shi
kuwa sunkuyar da kanshi kasa yayi zuciyarsa na tafasa"yaya hisham !" ta kira
sunansa ahankali bai amsa ba yaji ta cigaba da mgn "ina tayaka murnar ganin nuzla
hakika naji dadi sosai."
d'ago kanshi yayi ya zuba mata kwayar idanunshi yana kallonta kamar yadda take
kallonsa sai dai nashi kallon mai cike da tsananin mamakin jin abinda ta fad'a ne
sai daya d'auki wasu mintuna sannan ya motsa bakinsa ya fara magana "idan har da
gaske kinji ddin dawowarta na gode "yaya hisham me kake nufi ?". abinda kike nufi
nima shi nake nufi ya fad'a a d'an tsawa ce ."
Ta girgiza masa kai jikknta na rawa tace "walalhi har cikin zuciyata naji dadi
sosai kuma allah yafi kowa sani meye acikin zuciyata ,meye riba ta idan naji dadin
rashin dawowarta?rashin dawowarta ba zai ta'ba canza zani daga halin da nake ciki
ba ta fad'a tare da juyawa ta shiga kitchen bata jima ba ta fito hannunta rike da
qaramin cup ta durkusa gabansa ta mika masa tana kallon cikin kwayar idanunshi cike
da tashin hankali sakamakon rashin sonta da take hangowa acikinsu ."
Yaki amsa ta kai hannunta ta kamo laulusan tafin hannunsa ta saka cup din
ciki ,yaki amsa ya cigaba da kallonta "kayi hakuri kasha zaka ji sauki zugin da
zuciyarka take maka "na sani akwai zafi akwai radadi da ciwo sosai abaka wanda baka
so ,ka sani ni nana hauwa'u bazan takura maka ba bazan hanaka abinda kake so
ba ,idan ma ta kama ka auro nuzla ka had'amu kana da damar yin haka bazan damu
ba ."
Idan kuma bazaka iya had'amu ba zaka iya sakina ka zauna daita kad'ai na yarda na
amince idan kuma zaka iya cigaba da zama dani shima na yarda na amince koda baza
kayi komai na aure dani ba, abu daya kawai nake so daga gareka shine ka bani
kwanciyar hankali." tsareta yayi da oly eye's dinsa masu firgitartata a yanzu ,
hakan yasa tayi saurin kawar da kanta gefe tana danne kukanta."
Bin jikinta da kallo yayi yana mamakin jin abinda ta fad'a ,hakan nan yaji
tausayinta ya mamaye jinin jikinsa tana da matukar saukin kai sannan bata da yawon
damuwa da fari ta tayi qoqarin tsaida mutuncinsa dana iyayensa har ma dana dangi
gabdaya domin auresa, sannnan tayi qoqarin karesa a wajen mahaifiyarsa daya fita
yanzu kuma tana tayasa murnar dawowar masoyiyarsa har ma da albishir din ya aurota
"kai sakarai ka dawo cikin haiyacinka bata son kaga dole zata fad'a haka ,kai ba
haka bane to me yasa taki fad'awa mumy komai bayan taji wayarka da zaka fita .?"
Wani zazzafan numfashi ya sauke yana cewa" idan ni kuma bana raayin aurenta fa? ya
fad'a tare da amsar cup din hannunta yana sauke numfashi "bazai ma yuwu kace baka
son aurenta ba wannan ma ba abinda hankali zai dauka bane nuzla fa zuciyarka ce ta
fad'a tana qoqarin mikewa tsaye zata juya taji ya hard'e mata kafafu nan da nan
gbdy ta juyo ta zubo jikinsa a gigice take kallonsa duk da tasan shine ya hard'eta
amman hakan nan ta tsinci kanta da bashi hakuri ."
"Ka..Ka... kayi haku... "shiiiii! ya fad'a yana kai cup din hannunsa ya ajiye akan
table din dake gefensa ya tsura mata ido suna shakar numfashi juna yayinda ita kam
tuni ta runtse idanunta dan bazata iya jurar kallon ba dan duk yadda take jin
numfashinsa na saukar a fuska da wuyanta hakan bai sa ta bude idanunta ba ."
laulausan tafin hannunsa ya kai saitin wuyanta sakamakon zafin da yaji ajikinta
yayi wani abu yaji ya tsarga masa da sauri itama ta bude idanunta suka tsurawa juna
ido muryarsa a rauni yace baki da lafiya ne ."?numfashi ta sauke da karfi sannan ta
mike daga jikinsa ta zauan a gefensa tana cewa "lafiyata lau nima haka naji yanayin
jikinkina ya sauya."
"Okay yanzu mu ajiye maganar wasa da gaske kin amince na auro nuza ?ta gyada masa
kai alamun eh ! ya gyara zamansa yana kai cup din madara bakinsa "nima zan miki
abinda kike so amman sai kin shawo min kan mumy ta amince na auri nuzla idan kika
min haka zan baki duk wani kwanciyar hankalin da kike bukata daga gareni ".
shiru tayi tana tunanin kafin daga baya tace "dan wannna mai sauki ne zan mata
magana kuma in sha allahu nasan mumy zata amince ."shiru Kawa yyi "gsky nana
hauwa'u tana da kirki da hakuri dan kwata kwata bai ta'ba tsamanin zata amince ba
tunda itama bata sonka ai dole ta amince zuciyarsa ta fda masa haka tsaki yaja
domin sai ya sake tsintar kanshi da jin haushi "muje ka kwanta ka huta dare nayi
bai ce uffan ba ya mike ya nufi kofar d'akinsu itama tabi bayansa ."
Kai tsaye suna shiga d'akin ya fara zare rigar jikinsa bathroom ya shiga ita kuma
ta kakkabe inda zata kwanta ta kwanta tana kokuwa da numfashinta duk da bata son
yaya hisham amman bazata so wa kanta kishiya acikin kwanakin da ko goma batayi a
gidan miji ba ,hassalima bata tare agidanta ba zuciyarta banda rawa da bugawa babu
abinda take wasu siraren hawaye suka gangaro mata ta fara sheshekan kuka tana jin
motsin fitowarsa tayi saurin danne kukanta tana share hawayenta ."
Numfashi ta dinga saukewa sama sama ya dawo gabanta ya tsaya daga shi sai 3 qauter
dake jikinsa duk wani zati dake jikinsa mai daukar hankali ajikinsa ya bayyana wani
tsoro ne qarara ya bayyana akan fuskarta dama zuciyarta gbdy wanda yasata saurin
runtse idanunta gam ji tayi ya kwanta jikinta har tana jin saukar numfashinsa ya
kai hannuwansa ya d'an matsar daita "ki koma wajen baccinki sannan kukan me Kike yi
wa mutane ?"
"Ba kuka nake yi ba " ta fad'a muryarta na rawa "uhm shi wannna kuma ya sunansa?ya
fad'a yana kwanciya "qoqari tayita ta danne kuka ya fuskanceta sosai "alokacin da
numfashinta Ke sama da kasa ya kai hannu daidai qirjinta inda ya suka sauka akan
dukiyar fulaninta wani abu yaji alokaci daya yadda numfashinta Ke sauka da kuma
tsarga wa wani abu da yaji mai kama da shoucking "
"Kina jina zuciyarki tayi nauyi sosai da alamun akwai abinda Ke damunta "ta lumshe
idanunta tana sauke numfashi kuma har lokacin bai dauke hannusa ba "na rashin son
hisham ne ?ta girgiza masa kai alamun a'a "to na meye to?bana komai bane "okay
yanzu ki bude baki kiyi kuka mai sauti domin ki rage nauyin da zuciyarki tayi aiko
kamar jira take ta bude zatayi kuka dan har sautin muryarta ya soma fitowa taga ya
zaro ido tare da bude bakinsa ba zato ba tsanani yaji saukar laulausan lip's dinta
akan na nashi .."
"Tsura mata ido yayi batare daya sake cewa komai ba illa kwayar idanunshi daya zuba
mata yana jin wani irin sauyi ajikinsa tmkr wanda ake jona masa wutar lantarki
cikin lokaci kankani komai ya birkice masa bai san yadda akayi ba ya had'eta da
jikinsa still bakinsu na manne cikin juna , sai fidda numfashi nana hauwa'u take
cikin jin wata irin kunya sam bada wata manufa tayi hakan ba gudun abinda zai fad'a
ne dan yanayin yadda ya zaro ido babu sauki zai iya yin komai ."
Da ba dan period din da nana hauwa'u take ba da babu abinda zai hana hisham saninta
ya mace a daidai wannan lokacin wannan shine abinda ya hana komai faruwa amman
murza kam ta sha gbdy ya manta wata kiyayya jin dadinsa kawai yake da jikinta ita
kuwa babu abinda Ke fitowa daga cikin kwayar idanunta sai ruwan hawaye tare da
mugun tsoronsa tana son hanashi abinda yake tare da sheida masa bafa ita bace
zabinsa amman tsoronsa ya hanata ."
"Yau ne kawai shima nice na jawo ta fadawa zuciyarta hakan, in sha allahu hakan
bazai sake kasancewa ba ,ita dai bata jin wanzuwar tsanarsa ko kiyayyarsa acikin
zuciyarta idan ya shirya yin rayuwar aure daita zata bashi dukkanin farinciki idan
kuma zai cigaba da nuna tsanarta ne zata janye jikinta sosai hisham yazo hannu
gashi babu damar aiwatar da komai lumshe idanunshi yayi tare da komawa gefe ya
kwanta yana mayar da numfashi bai san meke damunsa adaidai lokacin ba domin kuwa
idan yace yasani yayi karya ."
Bayan ta juya masa tana rufe rabin jikinta ya dan waiga ya kalli bayanta wanda
hakan yasa shi jin wani irin ajikinsa gabansa ya dinga tashi tsurawa bayanta ido
yayi shape dinta mai matukar kyau da d'aukar hankali,duk da yasan jikinsa na da
taushi amman sai yaji nata kamar yafi nashi soft kai everything ko dan bambamci
halitta ne jikin ,nuzla ya tuno wanda yasa tunaninsa ya koma kanta itama fa masha
allah tana da sura mai kyau da taushi uwa uba kuruciya dan nana hauwa ta girmeta da
kusan shekaru hudu zuwa biyar ya dauki kusan mintuna talatin a haka bai motsa daga
inda yake ba yana kuma jiyo saukar numfashinta ,numfashi ya sauke ya canza hasken
d'akin zuwa mara nauyi sannan ya zame ya kwanta ya d'an janyo gefen bargon data
rufa dashi ya rufe jikinsa ."
Washegari hisham ya bude ido bai ga nana hauwa'u ba ya kunna wutan dakin tare da
kai idanunshi ya sauke akan agogon dake ajiye akan table it was 9:44tsaki yaja
tsaki sannan ya mike ya shiga bathroom ,bathtube ya shiga yayi wanka ya fito black
boxcer da black singlet ya saka sannan ya daura kaya akai ya fito fuskarsa a hade
ya gaishe da abbansa dake zaune rike da jarida sannan ya shiga dakin mumy domin ya
gaisheta ko kallonsa batayi ba bare ta amsa sallamarsa, ahankali ya qaraso har inda
take zaune juyar da kanta gefe tayi alamun bata son ganinsa "momy Kiyi hakuri nana
hauwa'u ma da kike fushi akanta bata damu ba ."
maganarsa ta sake bata haushi "mumy ina magana "a shake ta juyo ta kalleshi
"maganarka bata da wani amfani agareni fitar min a daki kar na qara ganin ka shigo
min daki sha sha kawai da bai san ciwon kanshi ba korosa tayi daga dakinta ." ya
fito sami abban yana masa complain shima da farko abban bude masa wuta yayi amman
ganin yana bashi hak'uri da janyo masa ayoyi akan masu hakuri da yafiya ya hakura
shima ya daura da yi masa nasihohi yana janyo masa ayoyi da hadisai akan irin
tanadin da Allah yayiwa masu hakuri da biyayya ga iyaye ."
bayan ya gama ya riko hannunsa zuwa dakin da mumy take ya mata nasiha sosai akan
hakuri da yaya nan mumy tace "naji na hakura amman ka fad'a masa kar na sake ji ko
ganin yaje wajen nuzla idan ba haka ba zaka sha mamakina zaka haddasa gabar da baa
san ranar qaresa ba akan nana hauwa'u kuwa zan iya tsine maka "hisham ya dan saci
kallon mahaifiyarsa Kmr zai mata kuka "wai momy me yasa yanzu kike yin haka
ne ?."abinda bakya yi da
"yanzu ka canza shiyasa nima na canza idan ka só abinda nike son zaka cigaba da
ganina a yadda kasani sabanin haka kuwa matsaloli zamuyita samu da kai sha sha mara
hankali "Ke dai kiyi hakuri ki bar mgnrsa da nuzla raayinsa ne idan yana sonta ya
qara daita tunda allah ya halasta masa ajiye mata sama da daya "a ina ?ba dai
wannan yarinyar ba sai dai wata dabam kai watan ma ba dai ina raye ba mu iyayensa
mu ishesa misali tunda muka haifesa ya taso mu biyu kawai ya gani ya koyi example
daga garemu ".
Abba yayi murmushi yana cewa "wannan raayinmu ne ta yuwu shi kuma bashi da wannan
raayin "mumy zatayi mgn abba yayi saurin dakatar daita ta hanyar cewa "abar maganar
haka yanzu dai ki sanya masa albarka tare da kyakkywar addu'a da kuma fatan
alkhairi acikin rayuwarsa " mumy ta numfasa kana tayi Kmr yadda abba ya
umarceta ,hisham sam bai ji dadin kalaman mumy ba ya tashi ya fito ransa a bace ya
shiga d'akin baccinsa ."
Nana hauwa'u na gyaran daki taji an shigo ta dan juyo ahankali domin ganin wanda ya
shigo , yaya hisham ta gani a tsaye fuskarsa babu alamun fara'a ya sha kunu tamkar
bai tab'a dariya ba,tana kallonsa ya qarasa inda durowar mirrow yake yana dube dube
ta bar abinda take ta qaraso ina yake ta tsaya gabanta na wani irin bugawa da
karfin gaske "me kake nema ?shiru yayi har sai data sake maimaitawa, fuskasa a hade
yace "ai Kinsan abinda nake nema ki dauko ki bani "babu musu ta nufi inda ta ajiye
wayoyinsa guda biyu da wallet dinsa daman da zata goge saman durowar ne ta canza
masu wajen ajiya ta dawo ta mika masa tana cewa "fatan ka tashi lfy?bai amsa ba ya
fice daga cikin dakin yana jan tsaki tabi bayansa da kallo ."
lumshe idanunta tayi tana jin damuwa cike da sanyin jiki ta gama abinda take ta
fito yana zaune a falo ."Kusa dashi taje ta zauna tana wasa da yatsun hannunta
"abinci fa yayi ready ? a qalla ya kusa minti goma sannna yace "bana da raayin ci
"tayi shiru ta rasa me zata sake cewa" oh allah ban ta'ba tunanin zan yi irin
wannan rayuwar ba ,sai yanzu take ganin gskyr maryam akan yayanta aure ba abu ne da
zaka iya sadaukar da rayuwarka akanshi ba domin abune da mutuwa ce kawai take
rabawa tashi yayi ya nufi wata kujerar yana dane dane a wayarsa ."
daren ranar da kuma wunin safiyar data waye duk a cikin k'unci nana hauwa'u tayisa
har izuwa yanzu cin abinci kawai ke fito da'ita shima bisa takurawar mumy ce ."dan
kar mumy tazo ta tarar daita a d'aki tana kuka bayi take shiga taci kuka har ta
godewa ubangiji, idanuwanta sunyi jajir kamar barkono, da dare ma da mumy tazo zata
d'auketa domin kaita gidanta sai da mumy tayita rarrashinta dan ji take gara ta
cigaba da zama dasu akan zamanta da yaya hisham mumy ta fito tana bata kwarin gwiwa
sai da abba ya sake masu wasu nasihohi masu ratsa zuciya da kuma gangar jiki sannan
yaya hisham ya d'aukesu suka wuce direban mumy na biye dasu abaya domin shi zai
dawo daita ."
Har suka isa gidan nasiha mumy take masu shi dai yaya hishsm bashi da wani kuzari
saboda har yanzu zuciyarsa ta kasa amsarta dan bai jin zai iya mata irin son da
yake wa nuzla yayinda nana hauwa'u itama jin momy kawai take amman har a zuciyarta
tasan yaya hisham bazai bari su zauna lafiya ba sai 9 na dare sannan direba ya dawo
da momy ta barosu su kad'ai acikin makeken gidansu. d'akin take kallo a tsanake
komai yayi mata kyau most especially parlour'n wanda aka qawata shi da kayan zamani
masu kyau".
Karfe tara da minti shabiyar daidai wayarsa ta soma ringing ya d'auka ya duba, ita
kuwa tunda wayar ta fara ringing ta tattara gabad'aya hankalinta kacokan akanshi ,
bata san dalili ba taji wata irin muguwar faduwar gaba ,ta dan saci kallon inda
yake a zaune a tun sanda suka shigo ,bata dauke kwayar idanunta akanshi ba har
sanda ya dauka yana cewa "wallahi nuzla rigimarki tayi yawa dare fa yayi okay
shikenan ganin nan zuwa yana gama wayar ya fice batare da yace mata komai ba ."
wani irin wahalallen ajiyar zuciya ta sauke tana dafe qirjinta tare da fashewa da
kuka ,ahankali ta durkusa kasa ta cusa kanta cikin qafafunta tana kuka tare da
kankame jikinta ,sai da tayi kuka mai isarta sannan ta mike ta shiga bayi wanka tai
ta fito ta bude wordrobe dinta shiru tayi tana kallo babu abinda babu hatta
kayayyakinta na gida an kawo mata ta
saka kayan bacci wondo dogo da riga mai long sleeve butter colour touch of brown ta
saka hijab sannan tayi sallar shaf'i da witiri tayi addua akan Allah ya zaba mata
abinda yafi zama alkhairi a tsakaninta da yaya hisham ."
sai data rufe kofarta da key ta kashe fitilun dak'in tayi shirin kwanciya bacci ,
koda ya dawo ya tarar har tai bacci yana murda kofar d'akin yajita gam nan da nan
yaji ranshi ya 'baci meye abun kulle kofa tsaki yaja ya juya ya shige d'akinsa ."
Washe gari tana farkawa daga bacci tai sallah sannan ta fito ta wuce kitchen,
had'adden breakfast ta had'a masu naji da gani bayan ta kammala sannan ta d'auka ta
kai dining, d'akinta ta koma tai wanka ta shirya cikin doguwar rigar abaya bak'a
mai ratsin ja tai rolling kanta da mayafin abaya sannan ta saka takalmi silifas
ja , ta feshe ilahirin jikinta da turare tayi kyau sosai abunka ga farar mace ta
d'auki phone d'inta ta fito zuwa falo ."
tana fitowa shi kuma yana fitowa daga d'akinsa sanye da jallabiyya brown , cikin
sakin fuska ta masa barka da kwana ,wani kallo yayi mata mai hade da harara sannan
yaki amsa tsabar bakinciki "meye jiya zaki wani rufe daki ?tayi shiru "me kike
tunani akaina ?"still dai shiru tayi masa tare da sunkuyar da kanta kasa "ko gidan
nan naki ko kuma da kudin wani naki aka gina shi ?shiru tayi tana nazarin maganarsa
,a wannan shirun datayi ta fahimci inda maganarsa ta dosa yana son ta'bo yayanta ne
abinda bazata d'aukar masa ba kenan muddin baya son zaman tashin hankali daita ya
tsaya iya kanta kar ya ta'bo mata wani nata ita dai zata jure komai akanta amman
akansu bazata iya ba ."
Numfashi ta sauke tace "ga breakfast can akan dining idan ka tashi ci ".ta fada
haka né dan kawo qarshen maganar sai dai bata kai ga k'arasa rufe bakinta ba yayi
saurin cewa "to baa ci ina miki magana kina min maganar wani abinci d'an yunwa kika
dauki ne ko me ?" yadda yayi maganar sai da ya gigitata "na fahimci haushin nuzla
kike ji a zuciyarki "idan har fahimtata gsky ne wallahi kiyi maza ki cire a
zuciyarki daman munafurci ne yasa kikace kin amince idan zan aureta na aureta well
idan na tashi aurenta ba amincewarki nake nema ba ."
A natse ta durkushe a gabansa tana kuka "karka min mummunar fahimta bazan iya bacci
ba matsawar na bar kofar a bude tunda kofar shigowa falo a bude take amman kayi
hakuri bazan sake ba maganar nuzla kuma wallahi babu ruwana ko mata goma zaka aura
byn ita kana dama "saboda ga dan iska ba ?"ka rufa min asiri ba abinda nake nufi ba
kenan yaja tsaki ya juya a fusace shifa ba lalla'ba yake son tayi ba so yake ta
biye masa daga nan komai yazo qarshe ."
nana hauwa'u ta mike da sauri ta rungumeshi ta baya tana rera masa kuka mai cike da
jan hankali "yaya hisham dan Allah ka bari na samu natsuwa a gidan nan idan kuma
har baza ka bani wannan kwanciyar hankalin ba kana iya sakina Kmr yadda nace ,sosai
ta shige jikinsa tana goga masa dukiyar fulaninta sannan ta cigaba da magana "nasan
baka sona amman ni ban ta'ba jin tsanarka ba zan iya mutuwa akanka yaya hisham dan
allah me nayi maka da ka tsaneni haka ?"dan allah kayi hakuri ka daina tsana haka
bana bukatar komai bana son kuma daga gareka ni dai mu zauna lafiya cikin sheshekar
kuka ta qarasa mgnr."
Sosai ta rud'a yaya hisham jikinsa sai rawa yake ya juyo ahankali tana jikinsa ta
sake narkewa a qirjinsa "kada ka canza yaya hisham kowa yabonka yake yi akan nayi
saar samun mijin da babu kamarsa gurin kyakkwar halayya kana da kirki bazaka ta'ba
barin nayi bakinciki ko kuka ba , samunka amatsayin miji ba qaramin nasara nayi ba
amman why kake son canza halinka?runtse idanunshi yayi tabbas haka né shi kanshi
yasan ya canza amman duk ita ce silar komai da bata amince da aurensa ba dole
iyayensu su hakura ."
kuka take sosai har da shesheka tausayinta ya kamashi ya soma jin kamar ya bata
hakuri ta daina kuka amman ya kasa magana, dago kanta tayi taga ita yake kallo ta
matso da fuskarta kusa da nashi ido cikin ido suke kallon juna suna shakar
numfashin juna, gbdy wani iri suka dinga ji ajikinsu ya bude baki zai fara magana
ta matso da lip's dinta kan nashi tana kallonsa tana motsa lip's dinta akan nashi
"am sorry yaya hisham I don't mean to hurt you bansan rufe kofar zai 'bata maka rai
ba da ban rufe ba "ta fad'a tana kamo lip's dinsa ta shiga tsosa cikin salo kamar
ta samu sweet ,cikin son qara rusa shi ta kamo harshensa tana mai wani irin sha
tana goga masa qirjinta ."
wani nishi yaya hisham ya saki cikin fitar hankali da mamaki ya zare bakinsa yana
já baya tare da cewa "meye haka ?ya fad'a Kmr bai ji dadin abinda tayi ba sunkuyar
da kanta kasa tayi tana mai jin wata irin kunya "kayi hakuri" lumshe idanunshi yayi
yana jin wani sanyi na bin jikinsa "muje kaci abinci dan allah ba dan ni ba" bai ce
uffan ba suka wuce dining a tare itace tai saving nasa sannan ta zauna ta d'auki
spoon ta kai bakinsa "bude bakinka na baka da kaina mamakin abubuwanta yake wani
lokacin ta nuna masa Kmr tana son shi wani lokacin kuma sa'banin hk most especially
idan tace ya auri nuzla ita kuma ya saketa ko ya qara wasu matan ma a bayan nuzla
yasan ba so bane kawai biyayya takewa mahaifiyarsa "
"kiyi hakuri dai sister har sanda ubangiji zai kawo mana mafuta ta alheri ,In sha
Allah zaku daidaita da yayana, ni dai fatana kullun kenan ubangiji ya daidai taku
damu gabadaya ."wallahi babu wani gara ni sister nima hakuri nike yaya hisham ya
canza sosai fiyye da tunaninki ,duk babu wannan fara'ar da wasan daya saba mana Ke
wallahi tsoro ma yake bani ga damuwa ta qaru daman ba wani samun kanshi nike ba
bare yanzu ga farincikinsa ta dawo jiya fa na tare a gidan nan amman ina ji kuma
ina gani nuzla ta kirasa kuma ya tashi yaje ,tô ya zanyi sister bai dameni ba dan
na auresa ne tsakanina da allah kuma nuzla yaruwata ce da nake so da qauna
"ahankali suka cigaba da tautauna akan abinda ya shafi matsalarsu ."
a round 6pm bayan sun tashi daga aiki ya kamo hanyar gida saboda yau agajiye yake
sosai yana buk'atar hutu ba zai iya zuwa gidan mumy ba ko wajen nuzla."yana isowa
yayi horn gateman ya bud'e masa ya shigo yayi parking sannan ya fito tana zaune
parlour'n sanye da wasu kaya ba wanda ya barta dasu ba ,tana ganinsa ta mike da
sauri ta rungume shi ajikinta sannu da zuwa "yauwa !" ya fad'a atakaice yana
qoqarin zareta ajikinsa dan bazai iya misalta yanayin da yaji ajikinsa ba ."
zata amshi jakar hannusa ya hana ya shige d'akinsa d'akin tabi shi alokacin ya
ajiye jakar hannunsa ta shigo ta tsaya gabansa zata kai hannuta jikinsa ya rike
yana cewa "out pls "Kai tsaye fita tayi ranta a b'ace tamkar wacca akayiwa mutuwa,
tana shiga dakinta kiran maryam ne ya shigo wayarta ahankali ta dauka kuka ta fashe
mata dashi tana furta "sister zuciyarta ta fara min zafi ". duk hankalin mrym ya
tashi tana tmbyrta "sister mun jefa rayuwarmu cikin qangin rayuwa kuka take sosai
maryam na rarrashinta ."
*******
Mami ta kira ya'yanta mata kan tana neman su a washegarin ranar suka kamo hanya
suka zo nan mami tayi masu bayanin abinda yasa ta kirasu batare da bata lokaci ba
suka amince aunty khadija tace "ai idan bai yarda ba mami ki bud'e masa wuta ,uhm
uhm !! aunty khadija kin fa san halinsa mu dai bi ahankali idan aka bishi ahankali
zai iya amince wa "inji cewar zabiba "wannan zaa bi ahankali ai shikenan a kirasa "
babu 'bata lokaci aunty shahida ta kirasa kasancewar weekend ce yana gida ya shigo
cike da izza fuskar nan tashi a had'e tamkar ta zaki yana shan kamshi".
" adamu !"aunty shahida ta kira sunansa tare da mikewa daga zaunen da take ta jawo
hannusa ta zaunar dashi bisa kujera itama ta zauna akan kujerar data tashi , cikin
wani irin yanayi mai cike da tashin hankali da tsoron abinda suke shirin fad'a masa
ya kalli mahaifiyarsu kana ya juyo ya kalli aunty shahida ,yayinda gefen hangunsa
aunty khadija ce wacce fuskarta tafi ta sauran hadewa sai zabiba ya zuba masu ido
yana kallonsu da sauraronsu cikn yin kasa da murya aunty shahida ta soma magana
"yaushe zaka tare a sabon gidanka musan ranar da maryam zata tare ?".
Gabansa ne ya shiga fad'uwa cikin tashin hankali yace "me yasa kuke da damuwa ne ?
ya fad'a tare da jan sayayyen numfashi ya gyara zamansa yayinda ganadayansu har
mami kacokan suka maida hankalinsu kanshi duk hankalinsu a tashe yake kar ya shigo
masu da wata matsala ."wani numfashi ya sake saukewa kana ya cigaba da motsa lip's
dinsa "da gidana da nan duk daya ne a wajena dan haka ta cigaba da zamanta anan
kawai "cikin yanayi na tashin hankali suke kallon mami "mami kina jinsa kinyi shiru
wannan wacce irin rayuwa ce shi babu wanda ya isa dashi sai abinda yaga dama zai yi
"me maryam tayi maka daka zabi ka dinga wulakantata haka ?"inji cewar aunty Khadija
."
"ba maryam ya wulakanta ba ni ya wulakanta Ku rabu dashi kawai yayi abinda yake so
rayuwa ce gani na da yake yi ne a duniya idan na mutu zanga wanda zai cigaba da
wulakantawa "wani irin numfashi mai zafi ya fesar kana ya maida hankalinsa ga mami
"ni ina jin ajikina mutuwa zanyi nan kusa , kawai bakincikina a yanzu bai wuce zan
tafi na barku da matsala ba domin adamcy matsala ne arayuwarku "saurin runtse
idanunshi yayi aunty khadija tace "ai shikenan idan ka kasheta gbdynmu zamuyi
asa.."kafin ta qarasa ya jefa mata wani mugun kallo zuciyarsa na dukan tara tara
idan akwai abinda ya tsani ji bai wuce mutuwar mahaifiyarsa ba "
"Kayi hakuri adam kayi abinda zai faranta ram mami kai kasan mami na matukar sonka
dan allah ko sau daya ne ka faranta mata karka zo byn ka rasata kazo kana danasani,
kazo kana son faranta mata babu hali kasani a yanzu ya kamata ka canza rayuwarka
idan kaki farantawa mahaifiyarka rai ka sani alamuranka bazasu daidaitu ba zama su
tabarbare ne zuciyarka zata qara bushewa ne matukar kaki amsar gsky ."
"Sai abu na gaba ka sani acikin biyayyar da zaka wa mahaifiyarka zai shigar da kai
aljanna domin bazaka shiga aljjana ba sai mahaifiyarka ta d'aga maka kafa kuma zaka
samu wannan damar ne idan ka faranta mata anan gidan duniya ."
yadda maganarta ke shiga kunnensa haka sautin kuka mami ke shiga, hankalinsa yay
matukar tashi "ina ganin lokaci yayi da zan farantawa mahaifiyata domin samun
rabauta "yana fad'ar haka basu jira jin abinda zai sake fad'a ba suka rungume shi
suna jin wani farinciki na mamaye zukatansu yayinda duhun daya tsarke a zuciyar
mami gabadaya ya yaye "da gaske ka amince zakayi rayuwa da mrym ?bai bude bakinsa
ya amsa da "eh ko Aa ba amman aranshi ya amince ta tare a gidansa ".hakika ka
faranta mana rai allah ya yaye maka dukkanin wata damuwa dake damunka yasa alkhairi
arayuwarku "karku wani wahalar da kanku wajen min addua na amince ta tare ne kawai
saboda sweetheart amman fa kusani idan dan farinciki akeyin aure ni bana cikin
farinciki kuma babu wacce zan bawa farinciki yana gama fadar haka ya mike juya ya
bar dakin ."
Mmn sudais
💗💗💗💗💗💗
MAR'ADAMS
💖💖💖💖
💗💗💗💗💗💗
*AYSHA A BAGUDO*
WATTPAD @HAUESH
AREWABOOKS USERNAME
AYSHAABAGUDO
bismillahirrahmanirrahim
Wannan littafin na kudi ne mai bukatar karantashi byn na kammalashi zai biya
1000 ta wannan account number din 1438775094 Aishat abdullahi access idan an tura
sai a turawa wannan 09136918331 alert domin tabbatar da an tura domin sauraron
littafaina a tuntubi chaneel dina (Hausa bakwai ) a YouTube.
Page 4
Kofar suka bi da ido cike da tsananin tashin hankali yayinda mami take kuka me
karfi wanda ke fitowa daga cikin zuciyarta "me nayi wa adamcy da na cancaci wannan
sakayyar bayan nayi masa komai a duniya .?"waigowa sukayi gabad'aya hankalinsu na
qara tashi jin maganar mahaifiyarsu hankalinsu a tashe sosai duk sukai kanta
cikin tsananin damuwa da tashin hankali "kiyi hakuri mami karki d'aga hankalinki
tunda ya amince komai zai zo da sauki munyi miki alqawari muddin muna raye bazamu
ta’ba bari wani mummunar abu ya faru da maryam ba ."
Hawaye yake zubowa daga idanun mami ta runtse idanunta gam tana jin wani iri a
zuciyarta, zuwa wannan lokacin nadamar wannan auren ya shigeta" ina ma zata iya
data bari adamcy ya sawakewa maryam kowa ya huta domin bata son mrym tayi rayuwar
kunci a gidan aurenta ,kuma tasan babu tantama shi zatayi tunda gashi ya furta baya
farinciki da auren dan haka babu wanda zai bawa farinciki tana tunani hawaye
masu zafi na zubo mata ."
Kallon mami suke wacce ita kad’ai ta rage masu a duniyar yanzu idan akwai abinda
suka tsana bai wuce ganin bacin ranta da ganin damuwarta ba hakuri da kwantar mata
da hankali suka cigaba da yi inda mami tayi zurfi cikin tunanin yadda zatayi ta
raba wannan auren ta huta sai dai gbdy ta rasa yadda zatayi "me zatace wa mutane?"
duka aure bai wuce kwanaki goma zuwa shabiyar ba ace ta raba ai sai duniya ta
zageta sam bama raba auren ne mafuta agareta ba .”
Tana cikin wannan tunanin suka dafata suna kiran sunanta a matukar rud'e suna
hawaye da sanyin jiki ta dawo hankalinta tare da kallonsu d’aya bayan d’aya itama
mami hawaye ne ke zuba a nata idanun, ta kamosu jikinta ta damke hannuwansu duka
cikin nata tace "duk naji hakurinku kuma na..na hakura na gode Kwarai da gaske
allah yayi maku albarka allah ya raya maku ya'yanku ,yadda kuka min kuma allah yayi
maku haka ina alfahari daku nasan ko bayan raina zaku duba bayana allah ya tayaku
kula da rayuwar dan'uwanku kuyi masa addua in sha allahu ba zai cigaba da wannan
rayuwar ba zai canza ."
Cikin rauni ta cigaba da mgn "bana son kuyi fushi dashi ina son ku cigaba da yi
masa nasiha da adddu’a dan allah karkuyi fushi dashi kunji ya'yana allah yayi maku
albarka yayiwa rayuwarku data ya'yanku albarka shima allah yayi masa albarka da
rayuwarsa na yafe masa duka laifukan da yayi min wanda na sani da wanda ban sani ba
daga haka tayi shiru tana goge hawayen idanunsu amman tamkar sake qara masu take
sam sun kasa cewa komai su dake rarrashinta sai gashi ta dawo tana rarrashinsu tare
da jaddada masu adamcy bashi da laifi duk laifinta ne data hada auren kuma tayi
nadama
sannan ta bukaci suyi wa mrym nasiha akan yadda zata janyo hankalisa “nan suka
cigaba da tautaunawa kowacce daga cikinsu na qoqarin sake kwantarwa da mami hankali
."
"Karku damu komai ya wuce idan allah ya kai mu jibi da yamma sai kuzo ku kai
maryam gidanta "amman mami dan allah ki daina sakewa adam dayawa tunda Kinsan
halinsa zuma ne sai anci sa da wuta dan wallahi mu bazamu ta'ba daga masa kafa ba
muddin muka ga abinda bai mana ba na tozarci ko cin fuska akan mrym allah bazamu
barshi ba dan bazamu yarda ya wulakanta maryam ba “. inji cewar Aunty khadija mami
tayi murmushi irin nasu na manya kana ta soma magana a natse "Allah dai ya shirya
mana shi ,mu dai cigaba da yi masa addua da kuma fatan alkhairi arayuwar
aurensu ,babu yadda allah baya juya alamarinsa sai kuga komai ya daidaita a
tsakaninsu “wannan haka ne allah yasa mu dace "kuyi qoqarin sheidawa maryam domin
tayi nata shirin ."
A bangaren maryam kuwa wani farinciki ta tsinci kanta ciki lokacin da aka sheida
mata ata ya amince dan bata yi zaton zai yarda da tarewarta ba , a zatonta lamarin
zai zo da gardama ,bayan ta koma d’aki alqibila ta fuskanta tare da yin sujudul
shukur cike da yalwataccen farinciki da yasa hawayen farinciki zubo
mata ,alhamdulillah wannan maganar itace mafi dadin acikin dukkanin abinda ya shafi
rayuwata hakika mami kin gama min komai arayuwata cike da farinciki ta kira nana
hauwa'u ."
Tana d’auka taji ta sauke ajiyar zuciya sannan ahankali ta kira sunanta a can qasan
makoshi wanda ya d’an d’aga hankalin maryam tace"sister lafiya ?a kasalance tace
"lafiya sister bacci na tashi ya kike ?ta lumshe idanunta cike da jin dadi take
fad'a mata batun tariya ranar asabar nana hauwa'u tayi murmushi jin dadi tace "to
sister sai fa kin qara da hakuri akan wanda kike dashi coz gidan aure sai da hakuri
it’s not easy auren mijin da bai sonka domin duk abinda zakayi bazaka ta’ba
burgeshi ba ."
“A tunanina idan akayi aure shikenan kusancinka da miji kan sashi ya canza ashe ba
haka ba, sai yanzu nake ganin gskyrki da kike kin auren yaya adam hakika shawo Kan
yaya hisham ya gagareni bare ya adam” you're my life sister i love you so much duk
duniya yanzu kece kawai wacce zan iya fad’awa damuwata ,ina shakar bakinciki a
gidan yaya hisham most especially akan nuxla “ ni ban hanashi aurenta ba bare ma
ban isa na hanashi ba, kawai ni abinda nafi buqata daga garesa ya kwantar min da
hankalina shine kawai abinda nike so amman yaki kullum cikin d’aga min hankali
yake ,ga yawon wayan da suke daita wani lokaci har asuba .”
“abinda ya bani mamaki daman nuzla tana son yaya hishsm ne? “ kamar tana son shi
sister “idan tana son shi me yasa ta gudu ta barshi?"allah masani nima haka nagani
abun nasu har da gayya amman ni na mika lamarina ga allah kullum shi nake roka ya
zaba min abinda yafi zama alkhairi “ajiyar zuciya maryam ta sauke dan tuni
farincikinta ya gushe ahankali kuma take jin wani irin tsanar nuzla na shigarta
domin duk abinda zai damu sister ya dameta kuma zata iya yin komai akai "bari na
fad'a miki irin abubuwan da nakewa yaya hisham da basu yi tasiri ajikinsa ba amman
ki gwada yi wata kila yayi tasiri ajikin yaya adam "ki rufa min asiri sister kema
kin kasa shawo Kan yaya hisham bare ni?
“ zaki iya nima da babu digon soyayyarsa nayi bare ke da na fahimci tsananin son da
kikewa yaya."
“Kai sister !kai sister ko gsky "baki bazai iya misalta irin son da kike masa ba
you just keep it in your mind naunayen ajiyar zuciya ta sake saukewa tace "haka ne
sister ina tsananin son shi kuma bana jin zai daina wannan son har zuwa lokacin da
numfashina zai bar jikina shine kad’ai muradin raina zan zauna dashi a kowani hali
wannan alqawar ne “ shiru nana hauwa'u tayi tana sauraron bayaninta “uhmm ai
nasani gbdy yayana ya tafi da komai naki ya bar min saura ."harara maryam ta sakar
mata kamar tana gabanta stil fuskarta dauke da murmushi ta cigaba da magana
"sister ko bai sona na kasance dashi hakan zai dangwamar dani cikin farinciki ko
bazai soni ba zan rayu dashi ."
“Ina rokon allah idan har dole dayanmu ne zai samu farinciki samun soyayyar gidan
aure to ya zamanto kece zanji dadi zanyi farinciki domin kece kike tare da abinda
kike so ni kuma daman banyi aure dan soyayya ba ,”ni kuma ina rokon allah
dukkaninmu mu dace mu samu soyayyar mazajenmu so na har abada “mrym ta qarasa mgnr
tana hawaye yayinda itama nana hauwa'u hawaye take zuciyar kowacce na cike da
tunani .”maryam na tunanin halin da zata shiga a gidan aurenta yayinda nana hauwa’u
ke tunanin halin da take ciki a gidanta sun jima suna waya nana hauwa'u na fad'a
mata abubuwan da zatayi domin janyo hankalin yayanta sannan sukai sallama.”
Maryam ta zauna shiru tana mamakin hakurin nana hauwa’u zata iya hakuri akan komai
na gidan miji amman banda hakuri akan wata ko bata dauki mataki akan miji ba lallai
zata dauka akan duk wacce zata ra’bi mijinta ,mijinta nata né ita kad’ai dan haka
babu wacce zata daukarwa rainin” ta dade zaune tana saka da warwara kafin daga
bisani ta mike ta nufi d’akin mami inda su aunty shahida suke,jiki a sanyaye ta
tura kofar dakin ta shiga bakinta dauke da sallama gbdynsu suka maida hankalinsu
gareta cike da girmamawa tace “aunty shahida me zaa daura maku ?.”
Aunty shahida tayi murmushi kana ta dubi sauran yan’uwanta tace “ me zaku ci ? duk
abinda zaki ci shi zamu ci “okay mrym kin iya fankaso?mrym tayi shiru na second
biyu sannan ta gyada mata kai alamun” eh! “tô kiyi mana fankaso na kwana biyu
ban ci ba ,suma kuma nasan zasu ji dadi ahankali tace “tô !ta juya ta bar d’akin
zuwa kitchen tana kiran masu aikin gidan cikin kankanin lokaci suka bayyana
agabanta nan ta fad’a masu abinda take son su tayata ita kuma ta soma qoqarin
kwa’ba fulawa duk abinda mrym tayi ranar cikin sanyin jiki tayisa tare da tunanin
halin da nana hauwa’u take ciki .”
Washegari da misalin karfe shida na yamma ATA ya tashi daga bacci wanda ya soma
tun karfe biyu dan baccin ne ma ya dawo dashi gida, mika yayi tare da salati
sannna ya sauko daga shi sai boxer ya shiga bathroom yayi wanka ya dauro alwala ya
fito kugunsa d’aure da towel yayinda hannunsa ke rike da wani qaramin towel yana
goge sansar jikinsa bayan ya gama ya feshe ilahirin jikinsa da body spray sannan ya
qarasa inda kayansa yake ya dauko blak and whit rigar mai hade da wula ya saka
yayi kyau sosai tamkr wani matashi d’an shekara talatin a duniya ya gabatar da
sallah la’asar ya fito parlour ’nsa ya bud’e fridge ya dauki holladia milk mai
sanyi ya sha sannan ya sauko daga samansa ya nufi gurin mami yana qarasowa ta
ajiye jaridar hannunta tare da mika masa hannu.”
ya qaraso ya zauna kusa daita kallonsa tayi cike da kulawa "shigowata uku ina
duba ka baka tashi ba daman tun da naga irin kwanciyar da kayi nasan ka gaji domin
bacci kake mai tattare da stress ."
numfashi kawai ya sauke batare da yace komai ba "muje kaci abinci kallonta yayi
cike da qauna aransa ,yace "sweetheart na sha hollondia milk bana jin yunwa yanzu
may be kafin na kwanta yayi mgnr yana zuba mata kwayar idanunshi ."adamcy nah !
ta kira sunansa yaji wani faduwar gaba dan duk sanda ta kirasa haka yasan akwai
damuwa.”
"dan allah mar.."no sweetheart karki ce wani abu yanzu we 'll talk later amman
right now karki ce min komai akanta dan allah ki barni na huta da mgnrta
haka ,kullum magana daya kmr wata zinariya "yayi mgnr cikin fushi murmushi tayi
tana dungure masa kai "bazaka bari nayi maka nasiha ba "wani nasiha kuma sweetheart
?nasihar da acikinta muka tashi idan ma nasihar ce ita ya kamata kiyiwa nasiha dan
ni dai kinsan bana son qazanta a gidana , ina buqatar kamshi akoina na shiga
bana son shirme da hauka agidana “ya qarasa mgnr tare da yi shiru "sai me kuma ?
thats all I need bayan wadan nan bana buqatar komai ."
"Sweetheart iya jikokin da kike dasu sun isheki haka ba sai kin samu qari daga
gareni ba” ya fad'a yana zare hannunsa daga cikin nata yana sake kallon fuskarta
ganin yana qoqarin mikewa tayi saurin rikosa za tayi magana ya katseta da cewa "ina
son haihuwa amman bana bukatar haihuwa daga gareta d'an haka tun wuri sweetheart ki
daina tunanin zaki samu jikoki daga gareta dan bazaki samu ba ."
murmushin karfin hali mami tayi cikin tsigar rarrashi tace "ka dai bi ahankali
karka zo kana rage wa diyata murya fa ."na gwamaci mutuwa akan nayi haka "come on
adamcy nah ka daina cika baki karka zo kana min kuka kana sonta fa ."
zare hannunsa yayi tare da barin gurin ya nufi hanyar fita yana cawa “sai na
dawo! bayansa tabi da kallo tana jin wani irin zafi na taso mata duk da ac dake
aiki a parlour'n komawa tayi ta jingina jikinta zuciyarta na tsalle saboda sarai
tunda ya nuna baya só baya só né kuma zai yi wuya ya só ko yayi wani abu da mrym
amman tunda akayi wannan auren babu mai kashesa sai allah, duk yadda zatayi sai
tayi ya só mrym ,shiru tayi tana tunanin dan bata son takura wa d’anta har karfe
goma bai shigo gidan ba mami ta kasa shiga ta kwanta duk ta kasa sukuni saboda bata
son yana dadewa awaje haka ma maryam yadda mami bata runtsa ba itama bata kwanta
ba tana kusa daita "
Suna zaune suna duba agaogo ya shigo tamkar wani zaki ganinta cikin wani yanayi
yasa ya qaraso ya zauna kusa daita kallonsa tayi tana sauke ajiyar zuwa ganin babu
wani sauyi atare dashi "sannu da zuwa yaya "mrym ta fada. yayi mata banza tmkr bai
ji ba yana cewa "sweetheart ba kiyi bacci ba ?cike da kulawa tace “taya zan iya
bacci byn adamcy
nah bai shigo ba “ina kaje.?" naje waya unguwa né amman na dawo since muna tare da
mb né “ baka ci komai ba har yanzu”? numfashi ya sauke daman yasan sai ta
tambayesa "bana jin cin komai sai da safe naci "kana son barin kanka da yunwa mrym
maza tashi zubo masa abinci kafin mrym ta mike ya mike ya nufi samansa ."
Mrym tayi dining ta zubo masa abinci ta dawo mami gashi” yi hakuri mrym ki bar
abincin nan bari na hada masa coffee nasan zai sha tunani tayi tasan halinsa tunda
yace baya ci bazai ci ba zagayeta tayi ta hada masa coffe tayi samansa tana
shiga parlour'n ta taraar dashi zaune idanushi a lumshe "adamcy nah "ta kirasa
ahankali tare d zama kusa dashi gyara zamansa yayi ya zuba mata ido bai ce komai ba
"ga coffe ka sha babu musu ya karba ya soma sha ahankali tana tare dashi har sai
daya shiga wanka sannan ta sauko ta shige dakinta tayi alwala tazo tayi shafai da
wutiri ta kwanta ."
1:00 na dare maryam ta shigo dakin ata cikin sand’a , a hankali ta kai hannu
tana nenan makunnin wutar d’akin tayi saa ta gani ta kunna wutar ta tsaya akanshi
tana qare masa kallo yana kwance ya lullube jikinsa , ahankali ta kai hannunta ta
yaye bargon da lulluba dashi daga shi white pant " wani abu taji ya tsarga mata
tun daga yatsun kafafunta zuwa kanta duk wani zati na jikinsa gashi nan a bayyane
tana kallo har kan jijiyarsa tana gani “ina ma zaka iya bani dama dana bayyana maka
irin yadda nake ji akanka, ina sonka yaya adam tun kafin mahaifiyarka tayi nasarar
had'a aurenmu ,ina da mahimman sako acikin zuciyata.”
ka bani dama isar maka da sakonin zuciyata you are my life ya adam I love you ni
kadai nasan yadda nake jin sonka a zuciyata ,I can't live without you duk duniya
kai ne abinda nake tsananin so kuma nake shiga tashin hankali idan naga wata zata
kusaceka."dan Allah ka soni ko yaya ne "ajiyar zuciya ta sauke tana kare masa
kallon tsab " world can't describe how much I love you ,I love with all my heart
shiru tayi jikinta na qara mutuwa akanshi daya daga cikin wayoyinsa ne ta dauki
qara da sauri ta durkushe kasa ta kankane jikinta wuri daya tana rawa jiki."wayar
tayi ringing har ta katse wani Kira ya cigaba da shigowa .”
ya motsa da kyar ya lulobo wayar ya d’aga batare daya bude idanunshi ba "hello !!!
yaji shiru dan haka ya mayar ya ajiye wayar a gefensa ya sauke naunayen ajiyar
zuciya tare da komawa ya kwanta dan ya gaji sosai ."ahankali mrym ta mike tana
leka fuskarsa bacci ya koma dan hk tasa shi gaba da kallo har da tagumi sai
murmushi take tana ganin tayi nasara arayuwarta tunda ta mallakesa a matsayin miji
sai ta soma kokarin barin dakin wani kiran ya shigo da wani irin mugun sauri ta
hantsila byn kujerar sofa tana rawar jiki wannan karon daukar wayoyin yayi ya kashe
gbdy ya janyo pillow har guda biyu ya matse a qirjinsa ahankali ta fito ta bar
dakin tun kafin asirinta ya toni ta ballowa kanta ruwa dan tasan muddin ya kamata
bazai raga mata ba "..
Karfe shida daidai na yammacin ranar asabar maryam tana zaune cikin girmamawa a
gaban mami ,sanye cikin wata haddadiwa madam gezner fara sol wadda aka yiwa aiki
da yellow zare da stone ,aunty shahida ta yafa mata mayafi fari wanda ya fito da
ainihi shape din fuskarta ta sanya takalmi fari sol tsintsiyar hannunta daure yake
da farin agogo na fata mai baqar fuska,qamshi jikinta ke fiddawa mai sanya nutsuwa
da kwantar da hankali wannan kuma duk aikin ya’yan mami né ."
Gabadayansu ya’yan mami nasiha suke mata mai ratsa jiki,wadda tabi kowacce gaba ta
jikinta,suna sake tunasar daita haqqin daya rataya a wuyanta
cike da gamsuwa cikin sanyin jiki ta soma yi masu godiya,a daidai sanda uban
tafiyar ya shigo,cikin shigar da yafi yi , wato kanana kaya ,baiyi tsammanin zai
gansu a nan ba da bazai shigo ba ,amman babu yadda zai yi kiran sweetheart ne
gashi gbdy sun gansa sallama yayi dai dai lokacin da mami take cewa"mrym ki goge
hawayen,ai bamu rabu ba muna tare duk sanda kike son ganina ki kirani zan zo idan
banzo ba zan sa aka wo min ke ."
Wani haushi ya kamashi dan hk ya kau da kanshi gefe yana maida hankalinsa kan
wayarsa ya isa gaban mami nesa da mrym ya duqa yana mata sallama sanda ta yunqura
zata tashi don basu wuri aunty shahida ta dakatar da ita ta koma inda ta tashi
"Adamcy !"bai amsa ba ka zauna kusa da matarka gefen lip's dinsa ya ciza sannan ya
zauna sai dai nesa daita aunty khadija ta kamo hannunsu ta tsarke cikin juna "adam
ga amanar mrym “ tsaki yaja tare da zare hannunsa cikin nata yana cigaba da danna
wayarsa ita kuwa mrym gabanta ne ke wani irin mugun faduwa wanda bata ta’ba jin
irinsa ba sai yau ."
"Yau zata kwana gida daya wata kila ma daki d’aya dashi ya allah ka kawo min dauki
ka bani kwarin zuciya ka daurani akanshi "adamcy ga amanar mrym nan na damka
maka,kada ka cutar da ita don kana ganin baka sonta ,ko ban gaya maka ba kasan
aure amana ce ta mace da ake danqawa namijinta wanda duk kuma yaci amana Allah
bazai qyaleshi ba,na tabbata diyata mrym bata da matsala,idan naga wata matsala to
daga kaine, ka kuma kuka da kanka don wallahi bazan taba daga maka kafa ko baka
uziri ba,ki kiyaye".
Ya dago idanunshi da suka gama canza kala ya zubawa mami "sweetheart bazan boye
abinda ke raina ba domin idan nace zan rike amanar nan nayi karya dan bazan rike ba
,kice na aureta kuma na aureta amman batun amana kiyi hakuri am sorry bazan iya
rike wata amana ba "ni kake fad'awa haka adamcy ?yayi shiru wai har sai yaushe za
kasan ka girma ka wuce wad’an nan abubuwan?sweetheart babu wani batun girma anan
auren dole fa kika min .”
“da na maka auren dole wa yaja akayi maka ?yayi shiru “allah ya ganar da kai gsky
mrym ki qara hakuri kinji kiyi qoqari ke sauki hakin daya rataya a wuyanki allah
yayi miki albarka "Insha Allahu mami zan kiyaye,Allah ya qara girma, Ameen summa
ameen,Allah yayi muku albarka gbdy ."mami na yin shiru ata ya mike ya fice ,mami
ta mikar da mrym tsaye ta rungumeta tana shafa bayanta ta dauko littafin adduoi
ta mika mata "duk wani maganin damuwa yana cikin nan karki yi sakaci da addua in
sha allahu komai zai zama tarihi wata rana ta mika hannunta ga Aunty shahida suka
fito daita suka sakata a bayan mota inda ata ke tsaye tare da salim da hisham ya
rungume hannunwansa a qirji .”
salim ya dubesa "ata ga amarya can zaa kai maka yau fa zaka shige daga ciki nima
dai bari nazo na lalubo wacce zamu rufawa juna asiri"za dai ka rufa mata asiri ata
yayi mgnr tmkr ba daga bakinsa ta fito ba ."
“Za dai mu rufawa juna "idan baka da hankali kayi daga yau kasa acikin
kwakwaluwarka cewa duk nmj daya auro mace shi ya rufa mata asiri.” salim yayi
murmushi yana cewa "haka né amman dai .."kaga abar mgnr haka hisham ya gyara
tsayuwarsa kawai yana kallonsa batare da yace komai ba "salim ya numfasa yace
"amman dai Ya kamata kaje ka sauya kaya a wuce da kai "zuwa ina kenan ?ba yau zaku
tare ba ?dawa kenan ?ban gane ba kai da mrym mana "Uhm ita kadai dai .”
hisham ya kyallesa kawai ya girgiza kai yana sake gyara tsayuwarsa "su biyu ne
zaune a bayan mota sai aunty khadija da driver a mazauninshi ya tada motar suna
qoqarin barin gidan ." hawaye ya ziraro mata dan wannan lokacin ta kasa daurewa
saboda nasihar aunty shahida ta sunkuyar da kanta tana damqe littafin da mami ta
bata sannu ahankali har suka qaraso tampatsetsen gidan ata dake surulere driver
yayi parking suka firfito har mrym suka sakata a tsakiyarsu cike da nutsuwa
take takawa gabanta na faduwa har suka kawo bakin kofa shiga parlour’n suka ce
"mrym shiga da kafar dama allah yasa kin shigo kenan mutuwa ce zata raba ."
Mmn sudais
💗💗💗💗💗💗
MAR'ADAMS
💖💖💖💖
💗💗💗💗💗💗
*AYSHA A BAGUDO*
WATTPAD @HAUESH
AREWABOOKS USERNAME
AYSHAABAGUDO
bismillahirrahmanirrahim
Wannan littafin na kudi ne mai bukatar karantashi byn na kammalashi zai biya 1000
ta wannan account number din 1438775094 Aishat abdullahi access idan an tura sai a
turawa wannan 09136918331 alert domin tabbatar da an tura domin sauraron littafaina
a tuntubi chaneel dina (Hausa bakwai ) a YouTube.
Page 5
...Kusan minti biyar maryam na tsaye a bakin kofar shiga babban parlour'n gidan
gabanta na wani irin bugawa da karfi, sai da aunty shahida ta sake maimaita magana
sannan ta d'aga kafarta ta dama da kyar bata sauketa a koina ba sai acikin
had'ad'den parlour'n ."
yadda gabad'aya penting jikin gidan yake fari sol haka zalika cikin gidan
yake ,gidan ba wani babban gida bane akan sauran gidajensa domin kuwa duplex ne
sama da kasa ,sama d'akuna uku ne sai d'aki d'aya wanda aka waresa domin baki ,
babu abinda babu acikin wannan d'akin, idan baki suka shiga cikinsa bazasu fito
domin yin ibada ba dan anyi masa tsari na musamman tare da kujerar kwaya d'aya a
d'akin wanda ake kira da (L)."
yayinda kasan gidan babban parlour ne mai d'auke da d'aki d'aya da bayi , sai
makeken kitchen da dining area sai kujera three seter manya manya guda biyu da one
one seater guda biyu na alfarma ga makeken tv bango 80 inches ,iya had'uwa wannna
gidan ya had'u domin kuwa an zuba duk wani kayan qawa na more rayuwar duniya ,kai
tsaye sama suka nufa da maryam rike da hannunta har d'akinta suka zaunar daita a
bakin gado sannan aunty shahida ta shiga kallon d'akin komai kamfani ta tsarashi da
kyau dan bata samu damar zuwa ba lokacin da zaa kawo kayan maryam "
Numfashi aunty shahida ta sauke kana ta soma magana "maryam yau dai allah yayi
ikonsa gashi kin tare a gidan mijinki kuma danuwanki kiyi hakuri da duk wani abinda
zaki gani marriage is sweet and sometimes is not sweet , so idan kikaga dadi kiyi
farinciki ki gara godewa allah ,idan kika ga sa’banin haka Kiyi hakuri wanda daman
hakuri kowacce mace ke yi a gidan aurenta ,matakin nasara a gidan aure ba komai
bane sai addua juriya da kuma hakuri dan haka ki qara hakuri akan wanda kike dashi
ko ba adamcy kika aura ba dole zakiyi hakuri bare kuma kinga irin mijin da allah ya
baki mai matukar wuyar shaani ,amman da sannu idan kina masa abinda yake so zai
canza miki daga adamcy da kika sani zuwa sanyin idaniyanki kiyi duk abinda mijinki
yace abinda yace baya só ki barshi."
muryarta na rawa tace"naji kuma na gode aunty in sha allahu zan kiyayye sai da
suka d'auki wa d'aya da wasu mintuna sannan suka fara qoqarin wucewa durkushewa
maryam tayi a gabansu aunty shahida tasa masu kuka mai ta'ba zuciya, tausayinta ya
kama su, dan sun san kukanta yana da nasaba da irin rayuwa da zatayi acikin gidan
mai tattare da rashin 'yanci ,da kyar suka rarrasheta tare da bata kwarin gwiwa
kafin sukai mata sallama suka kama gabansu ."
Bayan tafiyarsu ta tsaida kukanta tare da sa hannu ta goge hawayenta tayi shiru
acikin makeken d'akin da babu abinda babu na jin dadin rayuwar duniya komai na
d'akin blue ne da kujera sofa kwaya daya ta hade hannuwanta waje daya tana jin
mummunar fad’uwar gaba "ko wani irin rayuwa zanyi acikin gidan nan ?ta yiwa kanta
tambayar kafin a hankali ta yunkura daga zaunen da take ta qarasa jikin window
d'akin ta tsaya tare da kai hannu ta d’an zuge labule tana kallon haraban gidan
ahankali take kallon get din gidan tana jin fad'a uwar gaba mai tsanani ."
Shi kuwa ata daga inda yake a tsaye a haraban gidansu tunanin yadda zai yi da
maryam yake bayan yasan kisan kai haramun ne a addini tabbas daya zuba mata
shinkafar bera cikin abinci taci ta mutu ya huta ,wani naunayen numfashi ya sauke
adaidai lokacin da wayar hisham ta soma ringing ya ciro wayar daga gaban aljihunsa
ya duba ganin mai kiran ya saki fuska tare da d’agawa "hello my nuzlah!okay ina
haraban gidan ma yanzu ,no karki damu anything for you my love a natse ya cigaba da
motsa lip's dinsa “karki manta kece rayuwata kece wacce zuciya da gangan jikina
suka yarda kuma suka amince da qaunarta “ya qarasa maganar yana washe hakora .”
kallon kasan ido ata yayi masa yana mai jin tashin hankali mara misaltuwa."Kai dan
allah manta daita ai kece the best kece first lady ai yana magana yana murmushi
mai tattare da farinciki "wani irin bakinciki ya mamaye gangar jiki ata yayinda
zuciyarsa ta dinga tuttukin bakinciki bai tsaya cigaba da jin wulakanci da hisham
yake yi masa ba ya juya cikin tsananin fushi yana jan tsaki ,kai tsaye inda
motocinsa suke pake ya nufa."
Ya tsaya kawai cikin zafin zuciya yana ciza lip's dinsa na kasa da karfi ma'aikatan
dss da wasu daga cikin masu tsaronsa suka zagayesa yayinda wasu na qoqarin bude
masa mota ."cike da zafin zuciya ya shiga gidan baya ya zauna yana cigaba da ciza
lip's dinsa yana girgiza kafarsa daya."
hisham yayi murmushi bayan wucewar ata sannan ya cigaba da wayarsa "hisham abinda
kayi bai dace ba cin fuska ne ga ata "shi ya'ya mutane da yakewa fa ?ai gara shima
a dinga masa yaji ko da dadi ,ka duba kaga yadda ya bari aka wuce da maryam ita
kadai babu wata kulawarsa sannan kaji irin maganar daya fad'a maka sam sam
maganarsa babu da'a acikinta, baya respting din mace , ka sani na sani kowa hakuri
yake da abinda yazo hannunsa ,shi mai yasa bazai yi hakuri ba ? bana son nana
hauwa'u nuzlah nake so amman hk na hakura daita nuzla dake sauronsa ta sauke
numfashi aranta tace "sai ma ka rabu daita yadda danuwanta ya nuna rashin qauna
gareni itama sai na bari ta d’and’ani qiyayya mai zafi daga gareka dan babu abinda
zai hanani shiga gidan "kaga mu bar maganar mayi daga baya ."inji cewar salim.”
Direbansa cike da girmamawa ya tambayesa inda suka nufa "muryarsa can kasan makoshi
yace "mb ! dan haka kira motar da zata fara yin gaba yayi ya sheidawa direban
sannan suka sa kai motoci biyu ne a gabansu sannan motar da ata yake ciki sai mota
biyu abayansu,cikin kankanin lokaci suka qaraso kan titin oduduwa road inda anan
gidan mb yake ." bayan motocinsa sun shigo cikin haraban gidan sukai parking ,sai
dai shiru ata ya cigaba da zama yaki fitowa sai daya d’auki mintuna shabiyar sannan
ya fito a natse yana shan kamshi.”
Mb na zaune yana kallon tashar labarai yaji sautin muryar ata yana sallama
aciki ,fuskar mb cike da farinciki ya mike tsaye daga zaune da yake ya tarosa ya
rungumesa ajikinsa yana cewa "kai mutumina daga ina haka ?sai daya sauke numfashi
sannan yace "daga gida ! ya bashi amsa atakaice sannan ya samu waje ya zauna yana
fesar da numfashi tare da runtse idanunshi ,amira dake kitchen ta fito hannunta
rike da tray ta gaishesa fuskarta a sake "ango kasha kamshi ina yini ? " ta fada
idanuta na kan tray din dake hannunta tana zuba hadin salad.”
fuakarsa a hade tmkr wanda aka fadawa sakon mutuwa ya amsa "lafiya lau madam ya
gida da yaran ?"lafiya lau muke” tace masa atakaice dan ta qagu ta kammala abinda
take ta bar gun taje ta shirya kanta ."tana sauka daga stares din dining area din
mijinta ya cigaba tambayarsa amaryarsa ."
"Manta da wata amarya na dai baro su aunty sun wuce daita amman zan basu mamaki
"kamar ya zaka basu mamaki ?.”
"bazan ta’ba kwana a gidan ba, aure ne nayi ,tariya ce na basu damar
sukaita ,rayuwa daita kuma bai zame min dole ba haka zata qare rayuwarta batare
dani ba " haba abokina karka yi haka mana ka tausayawa yarinyar nan mana ,”kaga ni
ba abinda ya kawoni kenan ba “ mb ya gyara zamansa yana dubansa a tsanake tare da
cewa “me ya kawoka?“nazo ne akan hisham ".
”hisham kuma ?mai faru dashi ?yayi masa tambayar a jere cikin tsananin tashin
hankali ya sauke numfashi kana ya motsa lips dinsa kadan "hisham yana son mu samu
matsala dashi “a natse ya cigaba da magana ya zayyano masa komai mb ya numfasa kana
yace "gsky bai kyauta ba zan masa magana amman kai kuma ai bai kamata kaji ciwon
abinda yayi ba tunda kaima halinka ne koma nace a wajenka ya koya,kaga yanzu lokaci
yayi da zaka canza” ata ya d’an d’ago kanshi ya tsura masa tsumammun idanunshi “
”wallahi ka canza halinka kaga yadda yaruwarka baza taji dadin aure a gidanta ba
kana cin zarafin ya’yan wasu da kanen wasu amman kai baka son ayiwa naka ai kai ma
kasan hakan ba abu ne mai sauki ba ,kasani duk abinda kayi sai anyi maka “wannan ba
gasky bane yayi maganar yana lasar lip’s dinsa “duk dai abinda mutun yayi akanshi
zai qare ba akan wani ba mb ya bud’e baki zai sake magana ata yayi saurin dakatar
dashi ta hanyar cewa “dan allah na gama da wannan maganar shi kuma hisham ka
nemeshi kaja masa kunne, kuma zan kira auta matukar tana facing din matsala a
gidansa sai kunji tsoron abinda zai biyo baya dan wallahi sai na kashe auren
gabad’aya.”
“idan kuma tana son mijinta fa ? shiru ata yayi batare da ya ce komai ba yana
nazarin maganar mb “ka tsaya ka natsu kayi tunani mai kyau domin kashe auren ba
shine mafuta ba , ka barta tayi zaman aurenta lafiya , babu ruwanka da matsalar
gidanta idan da wata matsala nayi imani nana hauwa’u zata kawo karshensa ,ina baka
shawara ka cire hannunka karka zo kayi abinda zaa zo ana kuka da kai “ shiru ata
yayi ya kasa cewa komai yana nazarin maganarsa har sanda amira ta sake fitowa ta
cika masu table din gabansu da kayan abinci iri iri ta juya zuwa d’akinta ."
"Abokina ..!"rin wannan liyafa haka,gsky ina da rabo acikin abincin gidanka yau
shyasa haushina ya kawo ni gidanka kasan bayan mun shigo haraban gidan nan naji
kamar bazan shigo ba"yanzu dai kanka ake ji sarkin kwad'ayi,ga abinci nan kayi
sarving din kanka ata yace " no bari amira ta fito "ta fito tai maka me ?”yayi masa
tmbyr yana hararasa “hankali kwance ata yace “ta zuba min mana “ai kuwa baka isa ba
sai dai idan bazaka ci ba ,amman matata ni kad'ai zata sarving ,idan kuma lallai ka
matsu da cin abinci kaje ga matarka .”
"uhm !ata ya furta daga kasan makoshinsa sannan yace "banson iskanci fa mb matarka
ko matarmu ? mb yayi murmushi yana dubansa adaidai lokacin da amira ta sake fitowa
yace "darling zubawa wannan gogaggen dan iskan abinci yaci ba dan halinsa ba “
murmushi tayi ta zuba masu tare ."sai da ya gama shan qamshinsa kafin ya soma cin
abinci."mb ya gyara zama yace “gsky abokina karka cuci kanka wallahi kaje
wajen matarka ko babu komai ai ka rage mara “ata najinsa amman yayi masa banza
yayi tmkr ba dashi yake mgn ba ya cigaba da kai abinci bakinsa .”
mb ya ajiye spoon din hanunsa ya zuba masa ido yana kallonsa “ wallahi ata ka
canza rayuwa “me ya faru da rayuwata da zan canza ?abubuwa daya kuwa sun faru da
rayuwarka taya da ranka da lafiyarka ga lafiyayyar mata allah ya baka amman ka
tsaya cutar kanka .”kowa da yadda yake rayuwarsa ni yadda nake rayuwata empty yayi
min .” ata ya fad’a batare daya jallesa ba shiru mb yayi yana cigaba da kallonsa
kafin daga bisani yace “kai ko baka da lafiya ne? ata ya d’ago a natse yana dubansa
mgnrsa ta bashi dariya sai dai yaki yi dan ba aladarsa bace yin dariya .”
”allah ya isa tsakaninmu da kai mb wannan ai cin fuska ne,ko zan so mace sai na
kama wani lashe gabanta gabanta fa? ni adamcy ,i think ka fara hauka ,kai allah ma
ya isa tsakanina da kai ya sake maimaitawa yana ajiye spoon din hannunsa tare da
ture plet din abinci , alokacin da sugura ta fito da mugun gudu daga d’akinsu
mansor na biye daita tana ganin ata ta nufo wajensa ta fad'a jikinsa tana kiran
"uncle !"kaga yaya mansor ko ."
Ya rungume tsam ajikinsa yana kallon mansor dake haki "
”haba yaya mansor mai baby nah ta maka ?textbook din assignment dina ta yaga” ya
fad’a Kmr zai yi kuka ata ya kalleta "baby da gaske kin aikata haka ?tayi shiru
tana sake lafewa ajikinsa "ai tunda kaji tayi shiru ta aikata ne dan barna a cikin
yarinyar nan baa magana babu abinda zata gani bata 'bata ba “inji cewar mb tare da
kai hannu zai zuba mata rankwashi aka ata ya tare hannunsa "yana cewa “haba meye
haka kuma ?wannnan hannun naka koni ka zubawa shi ai sai na tashi aiki bare ita ,mb
yayi murmushi kawai ata ya kalli mansoor yace “kayi hakuri je ka dauko textbook
din na gani ya juya da sauri ya shiga daki ."
ATA ya cigaba da shafa bayan sugura "a duk lokacin dana kalli baby sugura sai naga
kamar princess dina tana yarinya "ko itace? Mb ya fad'a yana murmushi ata ya had'e
rai sannan yace" banason iskanci yau fa naga wasu abubuwa kake min "babu wasu
abubuwa idan itace shikenan sai ka cigaba da jira zan baka aurenta ."ATA bai qara
cewa komai ba ya cigaba da shafa bayanta dan ya fahimci yau iskanci abokinsa yake
ji ."
Bangaren maryam kuwa tana can zaune cikin tsananin tashin hankali gefe guda kuma
jifa jifa tana duba agogo awani suka dinga zuwa suna wucewa ahankali ta mike ta
shiga bathroom din dake manne acikin dakin tayi alwala ta fito tayi sallah
magrib ,haka da ishai tayi ta sake mikewa tayi sallah duk abinda take gabanta
banda faduwa babu abinda yake .”
"nan da wasu 'yan shekaru zamu fara ajiye surukai ,ya dai kamata kasan ciwon kanka
Ata ka rungume aurenka , ko bazaka yi dan kowa ba kayi dan kanka dan rayuwar nan
babu tabbas " karka mutu baka ajiye kowa ba “ muryarsa a matukar sanyaye ya motsa
labbansa “wallahi ina matukar son haihuwa amman bada wannan yaron ba ,bana sonta mb
“kayi hakuri ata ka daina fad’ar haka dan Allah kayi addua kawai “shikenan zan
fad'awa sweetheart tayi min addu tunda addaur iyaye babu shamaki idan alkhairi ce
arayuwarta allah yasa min sonta ko kad'an ne a zuciyata amman wallahi mb I don't
know why ban ta'ba jin son yarinyar nan ba , kullum na ganta kamar na kasheta haka
nake ji , suna tautaunawa mansor ya dawo hannunsa rike da textbook ya mikowa ata."
Ya kar’ba yace “mansor ai yagewar ba wani mai yawa bane kayi hakuri kaji yarona”
kaiwa mamanku zata gyara maka yaron ya juya zuwa dakin amira sun jima suna
tautaunawa har karfe shabiyu sauran sannan ata ya bar gidan zuwa gidansa dake
lekki ." Ita kuwa maryam tana nan zaune har karfe goma sha daya ta wuce babu ango
babu labarinsa ga tsananin bacci tana ji amman ta kasa ko kifta idanunta saboda
tsananin tsoro jiki a sanyaye ta dauki wayarta ta kira mami "maryam ya akayi ya
bakunta? adamcy ya shigowa kuwa ?"a matukar razane maryam ta dago ta kallon
dakin ,sai kuma ta maida kanta qasa kamar tana gaban mami yayinda idanunta suka
qara canza kala sakamakon qwallar data soma dan taruwa mata."
cikin faduwar gaba mami tace "me ya faru maryam ko bai shigo bane ? "mami bai shigo
ba gashi tsoro nake ji mai matukar azabar
Idan bai shigo ba bazan iya bacci acikin gidan ni kadai raina ba " ajiyar zuciya
mami ta saki"oh my god adamcy ,Allah yasa kar ya kasheni ,kawai dan anyi maka
auren da baka so shine zai zama matsala ka dinga wulakanta mutane haka?maryam
Kiyi hakuri nasan dole zaki ji babu dadi ko bama dan tsoro ba ki qara hakuri kamar
yadda na fad'a miki bazaki taba bakinciki da auren nan ba ki barni dashi nasan yana
sane zan sashi yasan aikinsa dan haka ki manta da adamcy kinji kiyi zamanki babu
abinda zai sameki ga masu gadi nan bazasu ta'ba yarda wani ya shigo ba ,kinyi
haquri ina tabbatar miki adamcy zai shigo komai dare ."
Cike da girmamawa tace "to! mami na gode sosai allah yasa kifi haka allah kuma ya
bar min Ke mami ina sonki "nima haka maryam bye take care."yana zaune a parlour’n
gidansa dake lekki phase 1 anjus avenue yana zukar sigari wayarsa ta soma ringing
ya kai hannu inda ya ajiye wayoyinsa ya lalubo yana dubawa sunan sweetheart ya
gani yana yawo a screen din wayar shiru yayi ya cigaba da kallon wayar yana zukar
sigari gbdy yaji gabansa ya shiga faduwa dan bai san me zata fad'a masa ba idan ya
dauka dan haka kiran na katsewa ya kashe wayoyinsa gabdaya ya kwanta rigingine
yana kallon saman parlour'n yana cigaba da zukar sigari sai daya tashi da kwali
daya sannan ahankali bacci yayi awon gaba dashi ."
Bangaren maryam kam karfe uku na dare bata runtsa ba har garin allah ya waye bata
ko kifta idanunta ba balle tayi bacci yadda taga rana haka taga dare tausayin kanta
ya kamata shi kuwa ata ko tunaninta bai yi ba dan babu digon tausayinta acikin
zuciyarsa karfe shida daidai ya tashi ya shige bedroom dinsa ya shiga bathroom yayi
wanka yayi alwala yazo ya gabatar da sallah bayan ya idar ya koma saman gado ya
kwanta idanunshi na kallon saman d’akinsa cikin kankanin lokaci bacci ya daukesa ."
Karfe takwas daidai a gidan maryam tayiwa mami direba bai gama daidaita parking ba
ta fito tana addua" Allah na rokeka ka kawo min sauki acikin rayuwata ka kawo min
karshen wannnan damuwar "ta qarasa fada tana dafe goshinta ta tsaya a bakin kofar
parlour’n tana kiran sunan maryam "maryam !! mami ta shiga kwalla mata kira da
sauri ta miqe a rude ta sauko ta bude mata kofar parlour'n mami ta tura qofar ta
shiga,yanayin fuskarta kawai ta kalla ta tabbatar mata ta sha kuka har gaji "ina
adamcy yake ?cikin mutuwar jiki ta bud'e baki "ammm uhm baa gida ya kwana ba yanzu
Ke kadai kika kwana a gidan nan ?ta gyada mata kai idanunta na kawo ruwan hawaye
"ina masu gadi ?"suma tun jiya da misalin karfe goma ban sake jin motsinsu ba.”
mami bata san sanda ta fashe da kuka mai tattare da tausayinta ba ,da sauri cikin
rawar murya mrym tace"dan allah mami kiyi haquri ki daina masa kuka sai wani
mummunar abu ya samesa maganarta ta katse mata kukanta saboda yadda taga tashiga
tashin hankali ta zubawa fuskarta ido, kawar da kanta tayi gefe tana qoqarin boye
damuwarta dan hankalin mami ya kwanta kusan minti biyar kafin mami ta soma neman
layin ata
Karfe goma daidai ya tashi wanka ya sake yi ya shirya cikin kananan kaya ya kunna
wayoyinsa yana gama kunnawa kiran mami ya shigo.”
jiki a sanyaye ya dauka yaji tace "ni kuwa uwar data kawoka duniya ce ?wani irin
tsinanne yaro ne kai ? cike da tantamar ba mahaifiyarsa bace ta kira numbersa,amman
dan ta tabbatarwa kanshi sai ya cire wayar a kunnensa ya duba yaga tabbas sunanta
ne sannan ya kuma karawa a lokacin da muryarta Ke cigaba da fadin"wai ni kam
sa'arka ce adamcy ? ‚lallai na sakar maka da yawa kaga gadon barcina,wallahi sai na
dauki tsatstsauran mataki a kanka kamar yadda yayana suka bani shawara "jin sunan
yayanta kawai data ambata yasa shi dauke wayar daga kunnensa yana kiran sunan Allah
“yau shi sweetheart ta kira da kalmar tsinuwa wani irin tsinanen yaro ne kai ?”ya
sake maimaitawa kanshi cikin tsananin tashin hankali."
” tabbas akwai wani mummunar bala'i na daban dake son kunno kai cikin rayuwarsa ."
Yana tsaye cikin wannan tashin hankali kiran mami ya sake shigowa jiki a sanyaye ya
dauka "kazo ka same yanzu yanzu ina gidan ina jiranka, sha sha kawai da bai san
ciwon kanshi ba ,iska kawai iya fesarwa daga bakinsa ya kwashi wayoyinsa ya fito
masu tsaronsa na ganin fitowarsa duk suka mike ya shiga mota suka fice a guje tare
da jiniya cike da mutuwar jiki ya shigo parlour'n batare daya kalli inda maryam
take ba dan gaba daya idanunshi na Kan mami né wacce kallo daya yayi mata yasan
tana cikin tsananin damuwa amman km zuciyarsa babu digon nadamar abinda ya aikata
bare tausayin maryam sai ma tarin qiyayyarta data ninku acikin zuciyarsa ."
"sweetheart ta kasa ganewa tursasa zuciyarsa da take akan yarinyar Ke sake hura
wutar qiyayyarta acikin zuciyarsa ,ahankali ya samu waje ya zauan kusa da mami yana
cewa "ina kwana sweetheart!dakata adamcy bana bukatar wata gaisuwarka" shiru yayi
kawai yana kallonta yayinda yaji kanshi yana masa wani irin sara ,"ni zaka wa haka
ko "? bai ce mata komai ba illa ya kalli inda maryam take zaune ya daka mata tsawa
" ke tashi ki bar nan". ta mike da tsaye da sauri jikinta na rawa zata juya mami
tace "Ke koma ki zauna " maryam ta girgiza wa mami kai hankalinta a tashe ."
"ni nace ki koma ki zauan babu inda zaki , ai ya raina ne shiyasa tunda ina masa
fad'a dole ya huce akanki "no sweetheart ni ba haka nake nufi ba but at least ai..
"na rantse da girman allah idan ka sake kwana a wani gida ba gidan nan inda matarka
take ba babu ni babu kai har abada kuma ko mutuwa nayi karkazo Kan gawata zan
sheidawa ya'yana kowa ya sani "haba sweetheart Kiyi hakuri mana "nace kayi min
laifi ne bare ka bani wani hakurin banza ?
"Ina baki hakuri ne dan kin janye maganrki "to bazan janye ,ba dai ka raina ni ba
to wallahi bazaka qara jin dadina ba haka kawai ka dinga gana min azaba kana ganawa
yarinyar mutane azaba, laifi ne dan ta rufa maka asiri ta aureka? "wace azaba kuma
sweetheart yarinyar da babu abinda ya taba hadani daita ya qarasa maganar yana
kallon maryam"ke nace ki bar nan ko ?"ta tsaya tana kallon fuska mami ya sake mata
alamar ta bar gun akaro na biyu a matukar fusace ya mike tsaye "Ke kina hauka ne
ina mgn kina zaune ? ya buga mata tsawa "
"babu fa inda zata karki sake ki bar wajena matsawar bani nace ba "wai sweetheart
me nene haka né ?ya fad'a yana sake kallon maryam dake qoqarin komawa ta zauna yace
"wallahi kika cigaba da zama a wajen nan sai na canza miki kamani"maryam ta kalli
mami cikin tsananin tashin hankali tace "mami dan girman allah kiyi hakuri ki barni
na bar wajena" ai kafin mami ta sake cewa wani abu tuni maryam ta bace .”mami tayi
shiru ta zuba tagumi tana dubansa kawai domin ta rasa me za tayi har kusan mintuna
goma sannan yace "sweetheart kinyi shiru kina kallona "me zance tunda kafi karfina
ka rainani ka nuna min ban isa da kai ba ,duk lokacin da nace ga abinda zakayi
bazakayi ba ,”amman wallahi bazanyi kaffara ba muddin baka cigaba da kwana a cikin
gidan nan ba na rantse da girman allah babu ni babu kai har abada kuma zan cireka
acikin ya'yana sai dai ka nemi wata uwar amman bani zulai ba ."
Mmn sudais
💗💗💗💗💗💗
MAR'ADAMS
💖💖💖💖
💗💗💗💗💗💗
*AYSHA A BAGUDO*
WATTPAD @HAUESH
AREWABOOKS USERNAME
AYSHAABAGUDO
bismillahirrahmanirrahim
Wannan littafin na kudi ne mai bukatar karantashi byn na kammalashi zai biya
1000 ta wannan account number din 1438775094 Aishat abdullahi access idan an tura
sai a turawa wannan 09136918331 alert domin tabbatar da an tura domin sauraron
littafaina a tuntubi chaneel dina (Hausa bakwai ) a YouTube.
Page 6
"Wai meye haka ne sweetheart ?"dan Allah ki daina fad'ar wannan maganar, karki
manta nine fa d'anki wannan yarinyar kuma diyar wasu ce " me yasa zaki dinga
fad'ar wad'an kalaman akaina?me yasa zaki min wannan hukunci ?ya fad'a cikin
tsananin 'bacin rai tunda wannan hukunci kika zartar akaina ai gara ki kasheni
kawai ki huta nasan bani da gata da galihu just kill me sweetheart ko kuma ki
janye wannan hukuncin naki ." yayi maganar Kmr zai yi kuka ."
"Okay haka ma zaka fad'a ko ?ta daka masa tsawa yana qoqarin sake bude baki mami ta
zuba masa lafiyayyen mari tana cewa "kaji magana kawai sannan kayi abinda nace
kuma bazan janye kudirina ba wannan umarni ne na baka wallahi idan ka kuskura ka
sa'bawa umarnina zaka ji abinda yafi haka daga bakina."
Maryam dake tsaye akan step a tun sanda ta bar wajensu jin saukar mari yasa da
sauri ta dafe qirjinta saboda tashin hankalin data tsinci kanta ciki ,ta qara taku
biyu idanunta ya sauka akan mami da ata dake huci tmkr zakuna ,wani hawaye ne
masu zafi suka shiga turereniyar zubo mata ,kuka take sosai tana datasanin kiran
mami datai a daren jiya ,dan tasan da bata kirata ba da hankalinta bai tsaidu
akanta ba har tayi musu diran makiya da sassafe ba ."
" wayyo allah nah ni maryam na shiga uku nah wannan duk laifina ne”. ta fad'a tana
toshe bakinta da hannunwanta duka dan kar sautin kukanta ya bayyana ." cikin
tsananin fushi ata yace "okay sweetheart bazan bi umarninki akan wannan banzar
yarinyar ba "ya fad'a atakaice yana furza da iska mai zafi daga bakinsa ."
"Naji bazaka bi umarnina ba amman kasani daga yau babu ni babu kai ka cigaba da
rayuwarka kai kad'ai har duniya ta nade " tana gama fad'ar haka ta nufi hanyar
step tana kwallawa maryam kira da karfi "maryam !!! mrym ta qarasa saukowa da
sauri ta tsaya cike da fad'uwar gaba tana duban mami "d'auko mayafinki muje
"ina kuma mami ?tayi mata tambayar a matukar firgice ."
"gida mana dan bazan tafi na barki acikin wannan gidan ba "kallon mami take cike
da matsanamcin mamaki sannan ta waiga ta kalli ata dake tsaye taga yadda yake
fidda numfashi har qirjinsa na sama da kasa wanda yake nuna tsananin tashin
hankali".
cike da tashin hankali ta shiga girgiza ma mami kai sannan ta soma magana "mami
dan girman allah kiyi hakuri ki barni kiyi tafiyarki ni zan yi hakurin zama dashi
haka ta fad'a voice dinta na rawa ".
"dan ubanki zaman me zaki cigaba dayi dashi yana wulakantaki ?maryam tayi narai
narai da idanunta tana damke hannuwanta cikin juna ,kin kuwa san babu wulakanci
daya kai miji yaki kwana a gidan amaryarsa a daren farkonta zafi da ciwo ?"nasani
mami dan ni kad'ai nasan halin damuwar dana kwana ciki jiya , tayi mgnr acikin
zuciyarta tana qoqarin daidaita natsuwarta ."
"Ya wulakantanki ya tozartaki ya qunsa miki bakincikin da bazaki iya mantawa dashi
ba har abada amman ki tsaya kina 'bata min lokacin" mrym ta girgiza mata kai tana
mai share hawayenta "amman bake ya wulakanta ya tozarta ba ni yayiwa kuma na gode
masa amman kisani bazan tafi na barki cikin wannan halin ba dan haka ki hau sama
yanzu ki d'auko mayafinki muje an gama wannan auren". mami ta fad'a cikin tsanani
'bacin rai.”
"kiyi hakuri mami duk laifina ne dana kiraki na d'aga miki hankali me yasa ma zan
kiraki ? sannan me yasa zaki hukuntashi ? da kin barshi ni ki hukuntani mami akan
abinda na aikata kina zaman zamanki na d'aga miki hankali " maryam ta fad'a hawaye
na zubo mata ."you're very stupid so you're the one caused all this problems ?
amman dan munafurci kizo kinawa mutane kukan munafurci ."
" ina zaman lafiya da mahaifiyata aurenki ya shiga tsakanina daita sannan dan kin
cika mahaukaciya ballagaza kika kirata kikace ban kwana gida ba ,dan ubanki idan na
kwana a gidan uban me zan miki ? "ya fad'a a fusace ".?a matukar rikice tace
"please am sorry I never know she wil act like this "ta fad'a hawaye na sake zubo
mata, wani irin mugun kallo ya watsa mata sannan yay qoqarin qarasowa inda take
mami na ganin haka tayi saurin taresa da hannunta dan ta lura baya cikin
haiyacinsa "karka soma ta'ba min lafiyar yarinya mami ta fad'a muryarta na rawa
bata ta'ba ganin yanayinsa haka ba ".
"Yau sai na kashe yarinyar nan da uban daya haifeta ya fad'a cikin cigaba da takowa
cikin isa da 'bacin rai jin abinda ya fad'a yasa maryam rungume mami ta baya tana
wani irin kuka tmkr qaramar yarinya "mami ki taimakeni dan girman allah "weetheart
ki bani hanya naci ubanta na ganar daita kuskurenta wanda har abada bazata sake
aikawata wani ba bare ni "ka shiga hankalinka “ita dai tashiga hankalinta “
“ adamcy banason abinda kake min dan babu laifinta ko d'aya idan hukunci ne ni dana
mareka zaka hukunta."
"please sweetheart ki matsa dan babu abinda zai hanani ban hukunta wannan yarinyar
ba akanta fa sweetheart kika mareni “yana qoqarin kamo hannun maryam mami ta sake
sauke masa wasu marukan ji kake tas tass !! har biyu ajere ."wannan karon kam
ata daskarewa yayi awaje d'aya yana kallon mami cike da tsananin mamaki abun yayi
mugun girgiza shi "yau sweetheart dinsa ce tay masa mari har uku kuma duk akan
wannan banzar yarinyar ".?
maryam kam fashewa tayi da wani sabon kuka ganin abinda mami ta sake aikatawa "
matsawar ka ta'ba maryam ban yafe maka ba tana gama fad'ar haka ta juya rike da
hannun maryam sai dai abun mamaki mrym din taki biyota ta turje jikinta na
kyamarrr , dole tasa mami ta tsaya ta juyo tare da zuba mata ido tana neman qarin
bayani, amman mrym tayi shiru sai hawaye dake sauka akan kuncinta"kina ganin irin
wulakanci da yayi min amman da yake ke baki da zuciya zaki ki biyoni wato ke gaki
mai ..."
kafin mami ta qarasa maganrta mrym ta zube kasa gabanta tana kuka tana bata hakuri
.""Kiyi hakuri mami wallahi ba haka bane, ba kuma abinda kike nufi bane ,nayi
nadama dan allah mami kiyi hakuri ki yafe masa ki daina fad'a masa kalamai haka
marasa dadi ,kuma ni babu inda zan biki zan zauna a gidan mijina,da dad'i da babu
zanyi hakuri dashi "tana gama fad'ar haka ta sunkuyar da kanta kasa ganin irin
kallon da mami take mata mami tayi shiru kawai tana kallonta gbdy taji kwarin
gwaiwarta yayi kasa ."
Jin mami tayi shiru hankalin mrym yayi mugun tashi rawar da jikinta yake ya qaru ta
d'ago kanta ahankali taga ita din mami take kallo har lokacin muryarta a sanyaye
tace "kiyi hakuri mami kece fa kike bani hakuri da kwarin gwiwar da har muka kawo
matakin maaurata ,to me yasa akwana d'aya kawai da nayi a gidansa zaki d'auki zafi
akansa alhalin kin fi kowa sanin waye shi ."?
nan kuma jikin mami yayi sanyi ta tsaya kawai tana cigaba kallon mrym , shi kuwa
ata zuba masu ido kawai yayi yana jin zallar 'bacin rai na ratsashi yaji tsanar
mrym ya sake qaruwa da mamaye duk wani sansar jikinsa "wallahi bancin mami dake
tsakaninsu da shi kad'ai yasan irin azabar da zai gana mata amman duk da haka bata
tsira ba zai ganar daita Kuskurenta ,runtse idanushi yayi yana cizan lip's dinsa
na kasa da karfi yayinda hawaye ke bin kuncin maryam , tsaki yaja sannan ya juya a
fusace ya haye sama cikin tsananin fushi yake taka step ."
Yana shiga d'akin daya zamo nashi ne ya soma zariya aciki he's thinking of if
someone else did what his mother did to him today da wallahi allah ne kadai zai
rabasu amman sweetheart rayuwarsa ce yana matuqar qaunarta, yana son duk wani
abinda take so wajen had’in aurensa da wannan bazar yarinyar ne kawai raayinsu ya
sha bam bam tsaki yayita ja tare dafe goshinsa dan wani irin sara kanshi ya cigaba
da yi ."
"Maryam ta kamo hannun mami ta zaunar daita akan kujera sannan ta durkusa kasa
gabanta "kiyi hakuri mami kema fa kinsan halinsa Kmr yadda kike cewa zai canza nima
haka nasa araina wata rana idan allah ya taimakemu sai kiga ya canza, nayi miki
alkwarin zan zauna dashi har tsawon rayuwata sannan kiyi min alkwarin bazaki sake
kai hannunki fuskarsa ba sannan ki daina fad'ar kalamai marasa dadi akanshi nima
kona kiraki karki saurareni akan kowacce matsala ki bani hakuri kamar yadda kike
bawa sauran ya’yanki."
Mami ta qirgiza mata kai alamun bazata iya ba “please mami do the same thing to me
“bafa zan zuba ido ba maryam ,dole nayi mgn idan ma baki fad’a min ba dole zan san
komai “please!..”bafa zan zuba idanu yayi miki wulakanci daya ga dama ba domin Ke
din amana ce a wajena kuma duk abinda yayi miki dole ne ya dameni ko bakya adamcy
ya aura ba dole ne nasa ido a gidansa idan naga zai cutar da ‘yar mutane bare ke da
kika kasance jinina "duk da haka dai mami Kiyi min alkawarin bazaki sake damun
rayuwarsa akaina ba mrym ta fad'a tana sakar mata murmushin dole wanda kana kallo
had'e yake da tarin damuwa.”
"Shikenan bazan sake ba “mami ta fad'a tana kukan tausayinta dana tilon d’anta
data san haka auren zai kasance wallahi data hakura tun farko daya nuna baya so ."
ahankali maryam ta kai hannunta tana goge mata hawaye tana cewa "mami ki bar kuka .
zubar da hawayenki akanshi maseefa ne a gareshi "ta d'aga mata kai kawai dan
batasan me zata ce ba dan kukan ne ya fiyye mata sauki akan mgnr da zatai " daga
nan mrym ta cigaba da kwantar wa mami da hankali ."zuciyar mami tayi sanyi ta sake
amanna maryam itace mace d'aya da zata kular mata da rayuwar tilon d'anta."
murya a sanyaye mami tace "tashi kije ki kirashi yazo ya bani hakuri "maryam ta
zaro ido tana kallon mami a matukar firgice "wallahi mami bazan iya ba he wil beat
me to the exetended sai kin koka min kina kallo fa if bancin kina nan da yanzu ba
wannan labarin ake fad'a ba ."allah bazan ta'ba iya tunkarar sa ba kawai Kiyi
hakuri ki yafe masa "mami am so much in love with your lovely son amman bani da
wannan kwarin gwiwa ." ta fad'a aranta hawaye na gangaro mata ."
hankali ta dora kanta akan cinyar mami tana zubar da hawaye ."tana matuqar sonshi
and she don't want to loose him at all, she don't know what's happening to her
brain, dan tana jin idan ya saketa ko idan mami ta raba auren zata iya mutuwa for
real mami tace "kiyi hakuri mrym ki daina kuka nasan adamcy baya sonki shiyasa
kikaga bana tuna duk wani halin da zai shiga nake yanke hukunci akanshi ta fad'a
tana shafa kanta ."
"Ni kuma kinga bana son abinda kike masa " mrym ta fad'a a fili tana sheshekan kuka
"baki so ?"mami ta tmbyeta ahankali tace "eh mami bana só ina jin ciwo a zuciyata
sosai kinga sakamakon abinda kika yi yau ya qara d'aukar zafi dani tsanata ya sake
qaruwa a zuciyarsa , mami ta sauke numfashi ,gbdy ta gama karantar maryam tana mugu
mugun son adamcy ,ta kuma san muddin ya gano hk zaa qara samun matsala ne ."
"Nima baa son raina bane dan burina bai wuce na ganku tare cikin koshin lafiya da
farinciki ba amman shi adamcy din ne zuma ne sai ancisa da wuta "haka zamuyi
hakuri dashi muyita masa addua allah ya sausauta zuciyarsa ta fad'a tana sake
kwantar da kanta a cinyar mami shiru parlour'n yayi baa jin motsin komai sai na
saukar numfashinsu dana ac dake aiki sai kusan shabiyu mami ta mike tana jaddada
mata tayi qoqarin ta shawo kansa yazo anjima bata hakuri ."ta qarasa mgnr tana
dariyar tsokana ."
"Dan allah mami ki rufa min asiri ina ni ina tarar aradu wannan ai sai ke "mami
tayi murmushi tare da yi mata sallama ta shiga mota suka baro gidan, mami kam da
direbanta ya d'aukota bai wuce koina daita ba sai hanyar gida tana zaune abayan
mota tana tunani abubuwa dayawa abinda yafi komai daga mata hankali soyayyar adamcy
din data ga ya samu kyakkyawan mazauni a zuciyar maryam da kuma qiyayyar adamcy
gareta tasan baqaramin wahala da qalubali zata sha a hannunsa ba dole tana
bukatar taimakonta ,dan dole kuma tasa ido arayuwar gidansu idan ba haka ba maryam
bazataji dadin rayuwar aurenta ba ."
Tana cikin wannan tunanin wayarta ya fara ringing it was nana hauwa'u sai data
sauke naunayen ajiyar zuciya sannan ta dauka tana cewa "auta ya kike ya gida da
fatan kuna lafiya ? to ya zaman naku yake ? "To shikenan ayita hakuri wata rana
sai labari okay zan kirata in sha allahu ,yanzu ma ina Kan hanyar komawa gida ne
daga wajen marym nike "eh to lafiya dai ba lafiya ba "mami ta fad'i haka cike da
raunin murya baangaren nana hauwa'u tace "lafiya mami me ya faru daga tarewa jiya
jiya km ?.”
"Kinsan halin yayanki ai "me yayi mami? "wai akai masa amarya yaki kwana a gidan
wallahi jiya kwana nayi cikin damuwa da tashin hankali amman nima yau nayi masa
hauka dan na nuna masa ba tsoronsa nike ji ba mari uku nayi masa masu kyau ,wallah
i kuwa nasan da zarar ya sauko zai shiga hankalinsa ya dawo ban hakuri ,ku barni
dashi duk zan sauke masa abinda Ke damunsa in sha allahu bazan bar duniya ba sai
ya canza rayuwa ai ko da mutane suke ganin Kmr yafi karfina, ba karfina yafi ba
zan haifi d’a ne nazo ina jin tsoronsa? kawai dai ina lallabashi ne sbd bana son
takurawa rayuwarsa mota na tafiya suna hira da auta har ta kawo gida."
Wayarsa ce ta fara ringing sai data katse bayan ya gama shan kamshinta ya ciro
yana dubawa Hannunsa daya yasa ya rike qugunsa dashi yana takawa zuwa bakin window
din dakin ya bude yana kallon haraban gidan inda masu tsaronsa ke safa da marwa
magana yayi wanda bai wuce ta minti uku ba ya katse ya soma cire kayan jikinsa ya
fad'a bayi dan wani irin zafi jikinsa ya d'auka ga sarar da kanshi yake masa zama
yayi acikin bathtub ruwa na sauka a sansar jikinsa "
ita kuwa maryam ta shiga d'akinta cike da faduwar gaba ta zauna abakin gadonta
tana tunani ta dauki lokaci zaune tana tunani hali irin na mijinta har sai data
duba taga lokacin sallar azahar tayi ta mike ahankali ta shig bathroom ta dauro
alwala ta fito ta gabatar da sallah bayan ta kammala ta koma ta zauna a inda ta
tashi ta tsurawa tv dakin ido sai dai sam batayi shaawar kunnawa ba bare ta debe
mata kewa tayi shiru tana tunanin ya kama taci wani abu dan tun abinci jiya ne
acikinta dan haka ta fara tunanin fitowa ta samawar cikin wani abu ."
Ahankali ata yake saukowa sanye da wasu kaya , jikinsa na fidda kamshi mai
sanyi dadi ya ajiye wayarsa akan center table ya samu waje ya zauna ya d'auki
remut ya kunna tv ya qara karfin ac ya daura kafafunsa akan table yana duban
tv ,ahankali maryam ta fito daga dakinta cikin sanda kamshin turarensa ya bugi
hancinta sam batayi tunanin yana parlour'n ba tafi tunanin ko yana dakin yana
shirin fita ya bar gidan ne, dan haka ta cigaba da saukowa tana saukowa tana sake
jin kusancinta da kamshin turarensa mai sanyi da bugar da zuciya ta lumshe idanunta
tana cigaba da daura kafafunta akan step ai tana gama saukowa kawai taga mutun
zaune tmkr wanda aka dasa ."
Tsananin tsoron data tsinci kanta ciki sauran kad'an ta saki fitsari a inda take
tsaye ,nunayen ajiyar zuciya da numfashi ta sauke alokacin daya ta sanyawa jikinta
jarumta kana ta soma tafiya cikin sanyin jiki zata shiga kitchen, a natse ya d'ago
idanunshi ya zuba mata oly eye's dinsa masu firgitar da mutun dole taja ta tsaya
sakamakon idanunshi da taji suna yawo a gbdy ilahirin jikinta ta hade yatsun
hannunta waje daya ta dago kanta zuwa Kan kujerar da yake zaune taga yayi mugun
hade fuska tmkr zaki yana kallonta a kaskance ."
" zata iya cewa tunda tasanshi arayuwarta bata ta'ba ganin yanayinsa haka ba alama
yayi mata da ido ta koma amman ta dauke kanta tayi kmr bata fahimcesa ba har tayi
taku biyu taji Kmr ya mike ai da mugun gudu tayi Kan step, bata tsaya akoina ba sai
a dakinta har da rufe kofar ta tsaya tana haki da maida numfashi "bayan ta samu
natsuwa kwalla ta zubo mata "bata san tana tsananin tsoronsa ba sai yanzu yaya adam
baya sona gashi ni kuma ina sonshi ta fad'a a fili cike da sanyin jiki ta zauna
jugun tare da dafe kuncinta ."
kusan awa daya taji motsin fitar motocinsa ta sauko da sauri sai dai hawaye ne ya
zubo daga idanunta
Sakamakon ganin ya rufe kitchen din duk inda ta kalla acikin parlour'n babu wani
abu da zata iya sakawa cikinta dole taja jikinta ta dawo daki bayi ta shiga ta
dauro alwala ta gabatar da sallar laasar ta kwanta lamo a saman abun sallah yunwa
na nukur kusanta sai tayi kamar ta kira mami akawo mata abinci sai tayiwa kanta
fad'a ta maida wayar ta ajiye ."
wasa wasa awanni suka dinga wucewa duhu ya fara sako kai lokacin magariba yayi a
daddafe ta tashi tayi sallahr magariba ta dawo ta kwanta a haka ishai tayi wanda
zuwa wannan lokacin ta fara raina kanta tuni hawaye ya fara fareti akan kuncinta
tasan mugunta da kuma hukuntata yasa yayi haka tana daga kwance amman jiri take
gani saboda tsananin yunwa tuni idanunta suka canza kala saboda kukan yunwa da
take bata san yunwa bata da hakuri ba sai yau hatta test din miyon bakinta ya canza
."
Ata kuwa tunda ya fita yana wajen wani abokin kasuwancinsa daya sauka a kasar
yau din nan sun jima suna tautaunawa akan kasuwanci shi kanshi banda coffee babu
abinda yasanyawa cikinsa karfe bakwai daidai a haraban family house dinsu tayi
masa, yana qoqarin fitowa daga mota yaga direban mami na fitowa daga gidanta
hannuwansa duka rike da wasu hadaddun kuloli “ aransa yace “shegiyar yarinya
sarkin rashi hakuri har ta kira akawo mata abincin ,ai da baki kira ba yau haka
zaki kwana da yunwa nonsense girl kawai .”
massalaci dake cikin esate din ya shiga yayi sallah bai fito ba har sai daaka idar
da sallah ishai ya zauna yana azkar yana nadamar abinda ya fadawa mahaifiyarsa
wanda yayi haka ne cikin zafin zuciya gashi yanzu yana dayasani ."ahankali ya dinga
jin rashin kyautatawar da yayi mata , nan da nan kyakkyawar zuciyarsa ta dinga
umartanshi da yaje ya bawa mahaifiyarsa hakuri ya nemi tafiyarta yayinda bakar
zuciyarsa ke gargadinsa har ma da bashi karfin zuciyar nisanta kanshi daita .”
wayarsa dake ringing ya katse masa tunanin da yake ya ciro yana duba wayar sunan
ammar ya gani ya dauka yana cewa "yaakayi ammar ?eh mun gama magana dashi yanzu
haka ina family hausa ,ok bani minti biyar yanzu zaka ganin a gaugauce ya fito ."
Kai tsaye rufar da yake zama da bakinsa ya nufa inda ya iske ammar yana ganinsa ya
washe baki yana cewa ango !ango !! angaishe da ango kasha kamshi"
"A ina kenan na sha ? A wajen ama... "kaga dan Allah malam ka barni naji da abinda
ke damuna dan ni babu wani kamshi dana sha kuma bana saka rai zan sha shi har
abada ".
“kai dai anyi mai cutar kanshi kai muguntar ma har da kanka zakayi wa ?"har kuwa
karshen rayuwata zan cigaba da zama haka ban sha wannan kamshin ba ya fad'a yana
zama acikin daya daga cikin kujerun dake ajiye agurin ."ai ni an gama da rayuwata
an cuceni wallahi amman I think kawai zan samu wata in aura dan bazan iya
rayuwar aure da wannan yarinyar ba dan sam sam attitude dinta is something
else..." ya fadawa ammar yana jan dogon tsaki .”
"hmmm amman da kayi hakuri ka d'an sake daita kad'an kagani ko tafiyarku zatai
daidai "no it can be possible ammar "okay idan haka ne na hadaka da wata sabuwar
mai bautar qasa dake karkashin kamfaninmu yarinyar tana da kirki sosai , koni
bancin bani da wata matsala da salima dana shiga sawun masu nemar aurenta dan
yarinyar akwai natsuwa da kirki ga kamun kai .”
shuru ata yayi without saying a word."Ko baka sonta ?.."ammar ya tambayesa,
ahankali yace
" ammar I don't really know tunda banganta ba amman bani da zabi tunda na rasa
princess zan iya manage da wata "ya qarasa mgnr yana duban fuskar ammar" to kayi
hakuri da mrym din kawai madadin ka qara da wata tunda itama wacce zaka aura din ba
sonta zakayi ba manage ne ai kaga gara kawai ka dinga rage zafi da mrym kawai zai
fi ga tarin ladan aure gana biyayyar mahaifiya" over my dead body ni fa I can't
let the woman I hate touch my fingers balle hannuna har azo ga jikina gaskiya
ammar bazan ta'ba Iyawa ba ."
“Bama zan barta ta ta’ba ni ba bare ni na kai kaina dan rage zafi tayi zamanta haka
nima nayi rayuwata haka amman batun rage zafi ma duk bai taso ba “
ATA sai hakuri fa kuma wallahi irin wannan auren ma ya fi dadi gashi da alamun mrym
din ma tana sonka zakayi yadda kakeso daita har Allah yasa ka fara sonta
“ammar ya fada yana dariya, da sauri ATA ya daga Kai yana cewa "me yasa kace tana
sona ?ai mace idan bata son mutun da wahala ta yarda a daura aure ka duba nuzla
misali ce guduwa tayi har sai byn daaka daura auren hisham da nana hauwa'u ".
“wannan ba gskiya bane , nana hauwa'u ta auri hisham ne ba dan tana son shi ba
hakazalika nima na auri yarinyar nan ba dan ina sonta ba "anya kuwa wata killa fa
nana hauwa’u tana son shi ta boye ne kawai dan bata damar samunsa a wannan lokacin
dan hk kawai ka rike marym dinka kamar yadda hisham ya hakura da nana hauwa’u ."I
can't" ya fada atakaice, dariya ammar yayi yana cewa "Ka bani dariya,irin ku né
da anyi mistake kun kusanci matan da baku so sai ciki."duk fa zaka gama cika bakin
kiyayyar ne ka gama zaka zo ka nemi hakinka ".
“Allah ya tsareni da ganin wannan bakar ranar "kai dai sai idan babu rabo a
tsananinka daita amma wallahi in da rabo komin kiyayyar dake tsakaninku sai kun
jone anyi ciki " ammar ya fada masa hk cike da zolaya ."yanzu ya batun yarinyar
da nayi maka maganarta yanzu zaka aureta na hadaku dan gsky idan dai da gaske aure
zaka qara gara wannan yarinyar ?” wallahi kawai sweetheart nake tunani nasan ma da
wahala ta barni “bayan ta matsa maka ka auri zabinta sai kuma ta hanakali qarawa
gsky ta barka ka qara tunda kana so .”
“Kai dai bari kawai ammar abinda nasani ko banyi acikin lokacin nan ba zanyi a
gaba ko nan da shekara goma ne sai na qara aure "Gsky abun naka na gaske ne
"kai dai ka tayani addua Allah ya bani wata mai kyau kamar irin mace da nike so
“da gudu ma kuwa zaka sameta dan wannna yarinyar da nake maka mgn akanta ta had’u
sosai” ata ya girgiza kai "da wahala haduwarta ta burgeni nifa ina da test "okay
kenan ya kamata ka hakura ka rungume matarka amman kuma wallahi maryama ta had’u
matar manya irinku ce ".
"Maryama !"?ya furta sunan a tsanake yana duban ammar yana jin sunan na ta'ba
ranshi wanda bai kamata yaji hkn akan kowa ba sai akan princess dinsa ,muryarsa a
kasalance yace "sunansu daya da wannnan dolen dolalon yarinyar "wacce kuma haka ?
wannan yarinyar daaka aura min mana“yayi mgnr yana jan tsaki ammar yayi murmushi
yace” eh sunansu daya ko bazaka aureta bane sbd sunansu daya ?kai ban son iskanci
ya kake wani tursasa ni kamar dole to bazaa aureta ba muyi abinda ya kawoka nan da
nan yayi qoqarin canza mgn zuwa ta business dinsu.”
Ammar kuwa sai faman dariya yake “wallahi ata kabani dariya ” wai dolen dolalo kai
ata wallahi baka da kirki nifa ina jiye maka tsoron ruftawa karkazo kana rokonmu
muje maka rarrashin dolen dolalo tace sam bata san da wannan ba “wani tsaki yaja
yana maka masa harara .”bai sake cewa komai ba ya mike tsaye yana cewa “ina ganin
baka shiryawa kasuwanci ba “ko kafin ammar yayi magana tuni ata ya soma taku “ata
tsaya mana dan allah ka dawo muyi mgn tsaki yaja ya shiga bayan mota dan tuni masu
tsaranshi sun bude masa gidan baya .”
Mmn sudais
💗💗💗💗💗💗
MAR'ADAMS
💖💖💖💖
💗💗💗💗💗💗
*AYSHA A BAGUDO*
WATTPAD @HAUESH
AREWABOOKS USERNAME
AYSHAABAGUDO
bismillahirrahmanirrahim
Wannan littafin na kudi ne mai bukatar karantashi byn na kammalashi zai biya
1000 ta wannan account number din 1438775094 Aishat abdullahi access idan an tura
sai a turawa wannan 09136918331 alert domin tabbatar da an tura domin sauraron
littafaina a tuntubi chaneel dina (Hausa bakwai ) a YouTube.
Page 7
Ahankali motocinsa suka fice daga cikin abdullahi estate ,mr ATA zaune a bayan
mota yayi shiru yana sake tariyo tautaunawarsu da ammar shi dai baya jin zai auri
mai kamanceceniya da harafin sunan maryam ma bare mai sunanta, sai kace babu mata
a duniya masu sunan arziki sai nata , tabbas shi yasan dan dole ya qara aure kuma
acikin tsakankanin wannan lolacin amman kuma ba mai irin sunan yarinyar ba .”wani
dogon tsaki yaja sanda ya tuna dole zai koma ya kwana gida d’aya da yarinyar da
yafi tsana .”
Qarfe goma daidai suka qaraso bakin get din gidansa wanda sai alokacin ya tuna
daya sallami masu tsaron get din gidan, hakan yasa ya lalubo wayarsa ya kirasu
su dawo bakin aiki kuma alokacin wanda zuwa wannan lokacin motocinsa sun kutsa
zuwa cikin haraban gidan kai tsaye parking space suka nufa .”sukai parking suka
firfito da sauri ata na qoqarin bud’e murfin kofar motar mutun d’aya acikinsu ya
bud’e masa cike da girmamawa . “
cike da natsuwa ya fito daga cikin motar ya tsaya yana magana can kasan makoshi
“gobe da wuri zan bar gida “ ya fad’a atakaice “okay sir duk suka had’a baki gurin
fad’ar haka, daga haka bai sake cewa komai ba ya soma takawa .”maryam dake zaune
tana cin abinci tana kallon series na turanci my husband my destiny ,title din
series din ne ya d’auki hankalinta har ma yasa ta cigaba da kallo, ahankali taji
ana qoqarin bud’e kofar parlour’n,zumbur ta mike tsaye tabar cin abinci da kallon
da take sbd jin motsin shigowarsa .”
tsumammun idanunshi ya zuba mata masu matukar firgitarwa cikin salo na harara ,
gabad’aya maryam ta gigice da sauri ta d’auki remut din tv ta rage volume ,shi
kuwa wani kallon tsana ya cigaba da binta dashi tun daga sama har kasa “tabbas
zaton shi ya tabba manu direban mami ita zai kawowa abinci .”yadda yake kallonta
yayi mugun d’aga mata hankali dan bata san abinda zai biyo baya ba , jikinta ya
saki sosai yayinda qirjinta ke wani irin bugawa da karfin gaske a sanda ya qara
taku biyu ya qaraso tsakiyar parlour’n ya tsaya still kwayar idanunshi yana yawo
ajikinta .”
“tsoro da matsanancin firgici ne duka suka kamata alokaci d’aya zuciyarta ta cigaba
da bugawa da karfin gaske,yayinda gefe gudu kuma sanyayyen kamshin turarensa ke
neman buwayar hancinta ,nan da nan hankalinta ya sake tashi jikinta ya kama rawa
rawa “wayyo allah nah me yasa na zauna a parlour’n ban koma d’akina naci abinci ba
gashi zan jawa kaina maseefa da tashin hankali?” ta fad’a tana dungurin kanta .”da
kyar ta sanyawa jikinta jarumta tace “san ..sannu da zuwa “.ya jita sarai amman
yayi tamkar bai ji ba .”
a kallon da yake mata yana iya ganin yadda qirjinta ke bugawa da sauri wanda hakan
ke tabbatar masa da tsananin tsoronsa da take ji ne ,wannan ne kawai abinda yake
d’an so daga gareta bayan shi babu komai ,ta koina bai ga ta yadda zai sota ba bare
har suyi rayuwar aure daita .”tsaki yaja tare da d’auke kanshi yana cewa “minti
d’aya!minti d’aya kawai na baki ki tattara ki bar nan kuma daga yau karki sake na
shigo parlour’n nan na d’aura kwayar idanuna akanki dan bana son ganinki “me
nace ?ya tmbyeta yana watsa mata harara “.
“kar na sake ka shigo parlour’n nan ka d’aura kwayar idanunka akaina dan baka son
ganina “ta fad’a idanunta na cikowa da ruwa hawayen tausayin kanta “good idan kuma
kin isa ki fad’a ki janyo wa kanki massefa dan wallahi matsawar sweetheart ta sake
zuwa gidan nan da wata matsala na rantse da girman allah sai na kawo karshen auren
nan bayan na gana miki azaba mai rad’ad’in “.ya fad’a cikin zafin rai.”
“bazan ..”! shut up nonsense girl kawai bar nan yanzu kafin na sauya miki kamani
guntuwa kawai mara fasali ina magana kina magana sa’anki ne ?.”
da sauri ta d’auki basket din da babbar kula da qarami yake ciki ta nufi hanyar
kitchen ,ajiyar zuciya ta sauke bayan ta shiga kitchen din tasa hannu ta share
hawayenta “wani irin mutun né shi da bai da imani haka ?”sam sam zuciyarsa bata
gajiya da fad’ar bakaken maganganu , gabad’aya ko cikaken minti biyar bai yi da
shigowa gidan ba har ya hargitsa mata lissafi .“Oh ni maryam ta yaya zan iya shawo
Kan mutumin nan bare na samu kulawar sa ?ya Allah kasan yadda ka jarabeni da
soyayyarsa ya allah shima ka jarabesa da soyayyata ko dan yaji yadda nake ji
akanshi “ta fad’a a fili tana neman inda zata juye abinci “.
“zaman uban me kike yi aciki ?”ammmm uhmm gani nan fitowa ,ta samu wani kwanon
silver ta juye abincin haka ma stew din ta bud’e fridge ta saka bata tsaya wanke
kulalin ba ta fito da sauri ta d’auki plet din abinci data fara ci tayi d’akinta
tana sauke numfashi .”a natse ya haura sama ya shiga d’akinshi bathroom ya shiga ya
sakarwa kanshi ruwa ya jima ruwa na sauka akanshi sannan ya fito yazo ya sauya kaya
marasa nauyi ya dawo parlour’n kasa ya zauna tare da d’aukar remut ya canza channel
zuwa na labarai yana cewa “useless girl kawai babu abinda tasani sani sai kallon
abinda bazata samu ba .”
bayan kamar minti goma yaji cikinsa ya fara masa zafi alamun yana bukatar ya saka
masa wani abu .”
Wayarsa ya d’auka ya kira d’aya daga cikin masu tsaronsa a gaugauce sale adamu ya
qaraso bakin kofar shigowa ya tsaya yana neman izini shigowa “may i coming
sir”coming! ya fad’a batare da ya kalli kofar ba sale adamu ya shigo bakinsa
d’auke da sallama kasancewarsa muslim ne “ina bukatar abinci da sigari “okay sir”
ya fad’a masa inda yake bukatar yayi masa order din abinci sannan ya mike ya sake
komawa d’akinsa bai jima ba ya sauko ya zauna ya mika masa kudi yana fad’a masa
irin abinci da yake bukata “cike da girmamawa sale adamu ya amsa ya juya ya fice
daga parlour’n .”
Tsakanin gidan da wajen siyar da abinci babu wani nisa shiyasa bai wani jima ba ya
dawo a natse ya turo kofar ya shigo dan yasan halin mai gidansa baya son yawon
kwaramniyya ,ahankali ya maida kofar ya rufe , wanda tuni shi ata idanunshi a
runtse suke yana tunanin mami yana sake jin aransa kamar bai kyauta mata ba ,ko
zata iya runtsawa yau “?shi kanshi idan ya tuna furucinsa gareta yana jin fad’uwar
gaba mai tsanani , yana jin ciwo sosai aransa, idan d’an daya haifa ne yayi masa
abinda yayiwa mahaifiyarsa yau ya zai ji ?ya tmbyi kanshi .
Cike da girmamawa sale adamu ya ajiye ledodin daya shigo dashi akan dogon kujerar
din dake gabansa yana cewa “sir gashi na siyo duk abinda ka bukata” kanshi kawai ya
iya gyada masa ,sale adamu ya juya ya fice ATA ya sauke idanushi akan ledodi kafin
ahankali ya janyo ya fara bud’ewa “yaushe rabonsa yaci abinci daga waje ?”matsawar
yana qasar abincin mahaifiyarsa yake ci amman gashi yau sanadiyyar auren maryam
zai koma cin abinci daga waje.”tsaki ya ja sannan ya bud’e robar abinci inda
idanunshi ya soma cin karo da shimkafa ‘yar waje da gasashiyar kaza ya fito da
robar fresh milk dana ruwan tataccen inibi .
a natse ya soma ci yana korawa da ruwan inibi kusan kazar kawai ya iya ci da ruwan
ininbi da fresh milk bayan ya gama ya kunna sigari ya sha iya shansa ya mike ya
rufe koina ya haye sama .”yana shiga d’akin ya cire kayan jikinsa ya saura daga
shi sai qaramin plan pant ya kwanta flat akan katifa yana kallon saman d’akin yana
shafa kwantaccen gargasar gashin qirjinsa dake kwance luf luf ,lokacin da zuciyarsa
take son hasko masa fuskar mafarkinsa yayi saurin kawar da hakan ya sako tunanin
mahaifiyarsa ,cikin haka wayarsa ta soma ringing bai mike ba har sai data katse
aka sake kira sannan ya yunkura ya tashi ya d’auka yana duba screen din wayar sunan
mb ya gani yana yawo ya d’auka ya koma ya kwanta .”
Acikin wayarsu da mb ne yake koro masa yadda sukai da mami shima dai fad’a yayi
masa sosai tare da nuna masa mahimmancinta arayuwarsa, yayi qoqarin tun abun bai yi
tsawo ba yaje ya bata hakuri ya nemi yafiyata, ya jima yana waya dashi saka makon
baccin daya soma ji ne yayi masa sallama ya sake mike wa ya kashe wutar d’akin ya
bar na bacci guda biyu ya koma ya kwanta ya lullube rabin jikinsa ya runtse
idanunshi yana aiyana gobe daga office direct gidan mami za shi ya bata hakuri ko
zai samu natsuwar zuciya da kwanciyar hankali .”
Lullube jikinsa Ke da wuya bacci ya d’auke masa cak tamkar wutar nepa sakamakon
hoton mafarkinsa bud’e idanushi yayi sosai yana sauke numfashi tare da amboton
sunan allah “wani iri juyi yayi ya canza yanayin kwanciyarsa sai dai yasan tunda ya
fara da tunanin acikin irin wannan yanayin ba lalle bane bacci ya d’auke shi sai
yayi da gaske.” yayi juyi yafi sau d’ari nan da nan ya soma jin haushin kansa ya
kamata ya cireta gbdy arayuwarsa ya samu yayi rayuwa kamar kowani mutun” ko kuma
ka maye gurbinta da wannan yarinyar ba “ wannan tunanin ya fad’o masa arai abinda
bai ta’ba ji cikin ranshi ba Kenan sai a yanzu .”
dogon tsaki yaja yana furta “allah karka nuna min wannna bak’ar ranar .”da dai na
sota ai gara na tabbata ina mafarkina ,a qalla ya kwashe sama da wanni biyu kwance
ahaka yana juyi da tunani marasa Kan gado ,gabansa kuwa banda fad’uwa babu abinda
yake ya kasa runtsawa aiko haushi ya ishesa tunawa da yayi idan fa bai samu
isashen bacci ba alokacin zai samu matsala gobe a office .”ya sake runtse idanushi
ko bacci zai daukeshi amman still dai abinda baya son gani shi yake gani.”
Ya bud’e idanunshi still dai mafarkinsa yake gani live tana kusanto inda yake
ahankali ya mike tsaye ya sauko daga Kan gadon ya kunna wutan d’akin ya d’auki
gajere wondo daya cire iya cinya iya ya saka ya fito daga d’akinsa ya sauko kasa
ya zauna .”
ya d’auki kwalin sigari ya bud’e ya zari kara d’aya ya kai bakinsa ya kunna ya fara
zuqa yana fitar da hayaki ta hanci ta baki nan da nan kwayar idanunshi ya canza ya
dinga lumlumshe idanu alamun bacci ,ya gyara ya kwanta akan kujera mai zaman
mutun uku ya dafe goshinsa yana karonto duk wata addua da ya iya ,cikin ikon allah
bacci yayi awon gaba dashi .”
Kishin ruwa ne ya tada maryam daga baccinta ,ta fito daga d’akinta zuwa parlour’n
kasa mutun ta gani kwance hannunsa d’aya a daidai saman marasarsa yayinda d’ayan
hannun kuma ya dafe goshinsa dashi, batayi tsammanin ganinsa ba dan hk ahankali ta
dinga takawa har ta qaraso garesa ta tsura masa ido kawai tana kallon yadda yake
sauke numfashi ahankali.”ganinsa haka yayi matukar burgeta, ta dinga jin wani iri
yanayi a sansar jikinta,numfashi ta sauke ta kalli center table din gabansa
idanunta ya sauka akan kwalin sigari wani numfashi ta sauke aranta tace “dole
haukanka yayi over wani abun ma ba acikin hayacinka kake yi ba .”
Ahankali ta shiga tattara komai dake kan table din ta nufi kitchen na zubar ashara
ta zubar wanda har da kwalin sigarinsa da yayi saura, fresh milk dinsa tasa masa a
fridge ta dawo cikin sand’a cike da tsoro ta durkushe gabansa tana kallon
kyakkyawar fuskarsa a duk yanayin da yake kyau yake yi wani abu ta dinga yana
fizgarta akanshi har bata san sanda ta kai hannunta saman faffad’an qirjinsa ba
ahankali taji yadda zuciyarsa ke bugawa da karfi kusan minti biyu tayi durkushe
amman bai motsa ba tasan baccinsa yayi nauyi .”
Ahankali ta soma shafa qirjinsa zuwa kasan marasa dake shafe tamkar baya cin abinci
, idanuta tayi kasa dasu bata tsaya akoina ba sai daidai jijiyarsa dake mike acikin
wondo ‘tai shiru tana qarewa halittarsa kallo tsab “kai ata duniya ne komai nashi
mai kyau da tsari ne cikakken nmj ne har da qari hakika tayi sa’ar samu kyakkyawan
miji fatanta allah yabi bayanta ya juyo da hankalinsa gareta su rayu cikin
farinciki.” ta lumshe idanunta tana sauke wani zazzafan numfashi da sauri sauri
hannunta na rawa ta d’aura saman qirjinsa daidai nipples dinsa sai da yayi wata
irin zabura kad’an wanda yasa mryam saurin d’auke hannunta tana qoqarin guduwa ya
koma ya gyaya kwanaciya ya cigaba da baccinsa .”
ganin ya sauke numfashi tare da d’aura hannuwansa duka sama jijiyarsa ya dafe ,ta
sake durkushewa a gabansa ta tsura masa ido “ina sonka adamcyn mami wallahi bazan
iya rayuwa babu kai ba . sonka yayi min mugun kamu I love you my adam, sonka da
qaunarka sun yi min kamun da bazan iya fushi da duk wani wulakanci da zaka min
ba .”ta sake kai hannunta qirjinsa tana adduar allah yasa kar ya farka ya kamata
cike da matsanancin tsoro ta fara shafa qirjinsa tana sauke numfashi .”wani
wahallen numfashi ya sauke yana mai jin wani mugun felings a gabad’aya ilahirin
jikinsa, ita kanta wani iri ta dinga ji ajikinta tmkr ana jona mata wutar lantarki
.”
ta sauke numfashi tana mai matso da bakinta dai dai nashi nan warin sigari ya
bugi hancinta amman cikin ikon allah sai lumshe idanunta tayi tana jin dadin shakar
kamshin sigari da numfashi shad’e ”
Cike da tsoro ta soma tsotsan lip’s dinsa na kasa tana hura masa numfashinta tana
tsotsa lip’s dinsa tana shafa kwantaccen gashin qirjinsa cikin wani irin yanayi ya
kai hannunsa d’aya yana shafa sumar kanta yana ma bakinta wani irin sha yana
juya harshensa tmkr yana neman wani abu acikin bakinta har ya samu yayi nasarar
cafko harshenta ya fara tsotsa cikin kwarewa yana sha yana had’awa da hakoranta da
lip’s dinta sosai ata ya dinga sarrafa bakinta cikin rashin sani .”
Allah sarki maryam wani irin farinciki ne da mugun tsoro ne ya shigeta alokacin
d’aya dadinta yadda yake sarrafa bakinta tsoronta kuma ya farka ya gansu haka nan
da nan dadin take jin yana bin jikinta ta daina jin komai sai tsananin tsoro da
fargaba dan tayi imani muddin ya bud’e idanunshi ya ganta ta mutu sai dai wata
maryam din ba ita ba bayan tozarci ma sai ya kusan kasheta da duka dan haka cikin
tsananin tsoro ta zare bakinta tare da d’auke hannunta a saman qirjinsa tana
rawar jiki .”
Shi kuma jin ta zare bakinsa ya fara motsi yana fitar da numfashi da sauri sauri
yana neman abinda ya kufce masa ya dawo masa domin shi zatonsa mafarkinsa ne .
maryam ta tsura masa ido sosai cikin tsananin tsoro ganin yadda yake fidda
numfashi yana damke jijiyarsa da hannuwansa duka qoqarin bud’e idanunshi yake taí
saurin juya masa bayanta qirjinta na wani irin luguden bugu “.
Idanunshi ya bud’e da kyar yana jin sauyin yanayi a gbdy ilahirin jikinsa bai ce
uhm ba bare uhm illa kallon saman parlour’n da yake batare da yace uffan ba ,cikin
yanayi najin fad’uwar gaba ya sauke idanunshi dake cike da bacci akanta duk da
baya kawai ya gani amman yasan wacece ko dan mugun gajartata, mamakin ganinta yayi
adaidai lokacin da suke tsakar dare” me take yi tsaye ya kai idanunshi ga bangon
parlour’n daidai inda agogo yake manne “hudu saura ya tabbatar karshen dare suke ya
‘bata a qalla minti biyar sannan yayi wuf ya mike tsaye yana tafiya da kyar ya isa
gabanta ya tsaya idanunshi cike da bacci .”
“Ke me kikeyi anan ?ta tsura masa ido tana kam kame jikinta waje d’aya “ko dai
mayya ce ke ?still shiru tayi tana jin mummunar fad’uwar gaba Kmr ta kwasa da gudu
ta haye sama “ina miki mgn kinyi min shiru “mayya ce Ke?okay okay !!na fahimta kin
tashi rawar dare ne ko ?maganarsa taso bata dariya amman tasan muddin tayi mugun
duka ne zai biyo baya “idan ma mayya ce ke sai dai kin cinye kanki da uwarki da
ubanki amman ni namana da daci nonsense girl kawai kizo kin wani tsaya wa mutun
akai zaki shanye min jini “ya qarasa mgnr yana jan tsaki ya nufi hanyar sama .”
Tabi bayansa da kallo qararrawar zuciyarta na kad’awa fiyye da kaida yana shiga
d’akinsa bai koma ya kwanta ba ,ya shiga bathroom yayi wanka dan yana jin jikinsa
wani iri ya d’auro alwala ya fito ya saka rigarsa ya tada sallah .”koda ta hau
sama ta tsaya bakin kofar d’akinsa ta tura kofar d’akin ahankali a saman abun
sallah ta ganshi zaune yana jan casbaha ,ganin zai juyo ta juya da sauri ta shige
d’akinta ta kulle ta kwanta tare da qudundune jikinta tana jin feelings dinsa na
ratsa lugun da sako na jikinta .”shi kuwa bai koma ya kwanta ba sai da yayi
sallolinsa sannan ya koma saman gadonsa ya kwanta bakinsa d’auke da tasbihi ga I
bangijinta ahaka bacci mai dadi ya daukesa .”
bai tashi ba sai wajajen karfe tara da minti talatin ya sauko da kyar ya shige
bathroom, minti shabiyar tsakani ya turo kofar bathroom ya fito d’aure da towel a
kugunsa yayinda jikinsa ke jike da ruwa ya tsaya a gaban mirrow yana goge jikinsa
da gefen towel kamar ance ya kalli cikin mirrow ganinta yayi tsaye tana watsa da
yatsun hannunta wani dogon tsaki yaja yana d’auke kanshi cike da dakewa da daure
fuska tmkr bai ganta ba ya cigaba da goge jikinsa yana mamakin abinda ta shigo yi
kamar ba ita yayi wa kyakkyawan warning ba akan zuwa inda yake ba .”
Bayan ya gama goge jikinsa ya shafa lotion ajikinsa ya bude ma ajiyar kayansa ganin
haka yasa ta juya masa baya tana mai jin nauyi da fad’uwar gaba
madadin ya d’auki kayansa sai ya gyara daurin towel din kugunsa da kyau yayi taku
uku ya qarasa inda take da sauri ta d’auke numfashi sakamakon wata irin damka da
taji ta bayan wuyanta “wani razananniyar qara ta saki wanda yasa gbdy gidan ya amsa
,bai tsaya wata wata ba ya jata kiiiiii yayi waje daita bai tsaya akoina ba sai
d’akinta yayi wuli daita a tsakar d’aki sauran kad’an gefen idanunta ya bugu da
abun gado allah ya kiyaye “dan ubanki me ya shigo dake d’akina “?
ta mike a matukar gigice tana dubansa “ban fad’a miki bana son ganin wannan bazan
fuskar taki ba ?ka..ka !! fad’a min daman ..”tass tasss taji ya d’auke da wasu
maruka masu kyau sai da wani haske ya gilma acikin kwayar idanunta ta fashe da kuka
tana dafe kuncinta“idan kikayi qoqarin shiga rayuwata zaki sha wahala a hannuna
domin kuwa zan bata miki fuska ta hanyar canza miki kamani , tsay a way from me I
don’t want to see your face “yana gama fad’ar haka ya juya a matukar fusace ya bar
d’akin .”
Durkushewa tayi a wajen tana fashewa da kuka mai tsanani “ta rasa wani irin tsana
ya adam yayi mata wani irin kuka take saboda ciwon abinda yake mata ,ta share
hawayenta alokacin da taji motsin rufe kofar d’akinsa “.
Ahankali taji taku takalminsa yana taka step wanda duk takun da yayi daidai yake da
bugun zuciyarta jikinta a sanyaye ta mike ta soma d’aga kafafunta tana zubar da
hawaye har ta kai bakin kofa taji motsin takunsa alamun yana haurowa da hanzari
ta koma da sauri tana jin fad’uwar gaba tsayuwarsa ta gani a bakin kofar yana cewa
“Ke ina kwalin sigarina? muryarta cike da in ..ina tace “amm uhm na ..na ..”sai
kuma tayi shiru ta kasa qarasa mgnr dan tasan tana fad’a masa ta zubar a shara sai
ta gane bata da wayo ya qara taku biyu ya shigo cikin d’akin sosai yana mata wani
irin mugun kallo wanda yasa hantar cikinta kad’awa “ina kwalin sigarina ?akaro biyu
don’t let me repeat my self .”
“Na ..na zubar a shara “ta fad’a hawaye na ganga rowa bisa kuncinta “what !? ya
fad’a a matukar tsawace tayi baya da sauri ta manne da bangon d’akin tana bashi
hakuri “kayi hakuri dan allah .”“sigarin nawa kika zubar ashara saboda Ke dakikiya
ce ?bansan cewar baka gama dashi ba amman kayi hakuri “ numfashi ya fesar tare da
rike kugunsa ya taka ya isa bakin window ya yaye labulan window yana kallon haraban
gidan masu tsaronsa ne suke shawagi da alamun sun gama shi kawai suke jira ya saki
labule da karfi wanda yasa maryam ta firgita cikinta ya duri ruwa. fuskarsa a
murtuke yace “ki tabbatar kin nemo min sigarina kafin na dawo gidan nan idan ba
haka ba wallahi wallahi ki kuka da kanki “yana fita kamfani ya nufa .”
cikin hanzari suna isa ya fito.”kai tsaye ya d’auki hanyar comfrence room domin
wata gagarumar matsala dake son kunno kai cikin kasuwancinsa kuma tunda ya sanarwa
P.A dinsa yasan by this time shi kad’ai ake jira yana shiga ya iske kowa kamar
yadda yayi expecting har ma da ammar da hisham cike da girmamawa manya ma’aikatan
da dake zaune suka dinga gaishesa tare da qoqarin kashe wayoyinsu dan sun san
dokarsa idan yana magana baya son jin motsin kowa bare qarar waya ya mikawa ammar
hannu batare da ya kalli inda hisham yake ba shima kuma bai kallesa ba .”ya samu
waje ya zauna.”
sun dade suna tautaunawa da manyan ma’aikatansa domin kawowa kamfanisa cigaba
ahankali P.A dinsa mustapha umar hassan dinsa ya mike ya kawo masa coffe karfe
biyu daidai ya sallame kowa shima ya fito tare da ammar suka nufi massalacin dake
cikin kamfani yana bawa direbansa umarni cikin harshen tsadadden turancinsa su
juya kan motoci fita zai yi da zarar ya fito .”Ina kuma zaka ?zanje naga sweetheart
dina “ya fad’a cike da jin fad’uwar gaban da bai san dalili ba”.
a natse suka qarasa wajen yin alwala suna magana kasa kasa ATA yace “share maganar
hisham kai bakasan abinda yayi min ba muddin kaga mun dawo kamar da to naga auta
kuma naga kwanciyar atare daita bayan sun idar da sallah ammar ya rigasa fitowa
ya tsaya acikin wata runfa rungume da hannuwan sa a qirji yana jiran fitowar ata
yana tsaye ya hango bayan maryama idanunshi kyam akanta har sanda ATA ya qaraso ya
tsaya kusa dashi yana cewa “me ya d’auki hankalinka da kayi concentre haka ?zubin
halitta mai kyau nake kallo ”ya bashi amsa da haka kana ya cigaba da magana “ kalli
can abokina ka gani tsayuwarta ma kawai abun burgewa ne .”
ATA yaja tsaki yana cewa “nonsense ! ba tsaki zaka já ba ka kalla ka gani kai kanka
zaka fahimci abinda nake nufi, yarinyar da nake fada maka ce, ata da yayi niyyar
kallonta ya fasa ya cigaba da kallon ammar fuskar tashi nan babu wani annurin
kirki sai dai bugun zuciyarsa ya qaru sosai fiyye da duk wani tunanin mai karatu ”
maryama mai kyau !Ammar ya kira sunanta “saurin juyawa ATA yayi yanayin bugun
zuciyarsa bai saisaita ba, maryama kuwa juyowa tayi ahankali sanye cikin kanki
bautar kasa ta nade kanta da qaramin hijab kayan sun matukar yiwa jikinta kyau “ mr
ammar ta hango tare da bayan wani tsaye .”
“Mai kyau qaraso mana mu gaisa “ tayi murmushi wanda yake qara tafiyar da imaninmu
mutun “ahankali ta soma takowa zuwa inda suke tsaye tana wata irin tafiya da mutane
suke ganin tsabar yanga ce tayi mata yawa nan kuwa rashin kibar da bata dashi né ya
janyo haka “kalleta abokina gashi tana nufomu zaka fi qare mata kallo sosai wallahi
yriyar ta had’u” bazan kalleta ba tunda ta had’u ka aureta mana ,duk kabi ka damu
mutane Kmr wanda bai ta’ba ganin mace ba “bai fi sauran taku biyu ta karaso zuwa
inda suke tsaye ba ATA ya soma d’aga kafafunsa bai tsaya akoina ba sai a inda
motarsa take tun kafin ya qaraso masu tsaronsa sun zagayesa .”
Murmushi kawai ammar yayi yana d’auke idanunsa daga kallon bayan ATA “mr ammar
barka da rana ya fama da jamaa ?tayi mgn a natse cikin sanyayyar muryarta “na kusan
sumewa da wannan murya fa “ maryama ta d’an zaro ido tana cewa “wace ni dan allah
ka rufa min asiri kar madam tasamu wannan labarin na shiga uku na “mu shi uku dai
“ya fad’a had’e da murmushi, cikin marairaicewa tace “kaji ba ashe kaima tsoronta
kake ji “yasa dariya adaidai lokacin da motocin ata suka fice yayinda ammar ya
cigaba janta Kmr yadda ya saba .”
kai tsaye abdullahi estate ata yace a wuce dashi ana gama daidaita parking ya
fito ya nufi gidan mami tana daga zaune taji ana yunkurin bude kofar ta tsaida
idanunta akan kofar dan ko baa fad’a mata ba jikinta ya gama bata d’an lelenta ne
ke tunkarota “a natse ya turo kofar ya shigo kana ya maida kofar ya rufe akan mami
idanunshi suka fara sauka bayan ta kallesa ta dauke idanunta akanshi zuwa wani gefe
tana jijiga kafarta tayi tmkr bata ji dadin ganinsa ba alhalin kuwa wani farinciki
ne ya mamayeta domin tun da ta gansa tasan tayi winning yazo ban hakuri ne .”
Ahankali ya tako zuwa inda take zaune akan kujera wanda zuwa lokacin tunin ta
runtse idanunta durkusawa yayi a gabanta yana sauke numfashi tare da d’auran
hannuwansa akan gwiwowinta “Kiyi hakuri sweetheart ki yafe min nasan ban kyauta
miki ba ,ban san abinda yasa na aikata haka ga mahaifiyata ba wacce bani da kamarta
,duk duniya itace take dani nake daita.”nan da nan hawaye ya jike gashin idanun
mami “yanzu zagin wad’an da suka manyanta a zamaninku ya zama wani abun ado shiyasa
kayi min son ranka kuma agaban matarka , me kake tunani idan ba maryam ka aura ba ?
“kaga kenan ka siya min raini ne a wajenta ko kuma nuna mata kofar yi min abinda
ta ga dama .”
“ sweet heart na aikata hakan ne abisa kuskure amman kiyi hakuri dan allah “ ta
d’aura hannunta a saman nashi kawai batare da ta sake cewa komai ba tana jin
tsananin qaunarsa .“Kiyi hakuri kiyi min addua sweetheart ko allah zai sa min son
diyarki a zuciyata ko kad’an ne , sweetheart har yanzu na kasa manta mafarkina ina
tsananin sonta gashi bansan inda zan sameta ba sannan duk yadda naso na cireta
araina na manta daita na kasa manta komai nata .”bugun zuciyarta, numfashinta
fuskarta da kamshinta idanuwanta murmushinta hawayenta sautin numfashinta
sweetheart bazan boye miki ba na sha saduwa daita acikin mafarkina .”
Mami ta tsura masa idanunta tana kallonsa “na fara shan sigari duk dan saboda ita
haka zalika a qoqarin na manta daita ne na fara shan giya ina danne zuciyata
akanta ,nayi iya yina domin na manta daita amman wallahi sweetheart abun yaki aiki
har yanzu koina na juya ciwo nake ji acikin zuciyata “mami tayi shiru zuciyata cike
da tsananin tunani abu daya ne yayi mata dadi acikin magangunsa shine rokon
adduarta na allah ya saka masa son mrym ko kad’an ne wannan abu ya sanyaya
zuciyarta kuma daman tana wannna adduar .”
“Sweetheart nifa abun tausayi ne abun a tausayawa ne akwai ciwo mai zafi acikin
qirjina bana buqatar tausayawar kowa sai taki kece kawai zaki tausaya min domin
kece kawai kika san ciwona kuma kece kawai kike sona tsakanin da allah.“mami ta
numfasa tana cewa “adamcy nah ina tsananin sonka da tausayinka kai ma ka
sani ..”“na sani sweetheart amman akan yarinyar nan kin canza min koma nace kinfi
sonta akaina,mami ta kallesa kawai “sweetheart ki janye maganarki akaina zan cigaba
da rayuwa daita Kmr yadda kika bukata amman batu na samammarta farinciki babu shi
domin ni kaina zuciyata baa cikin farinciki take ba dan haka dan Allah ki janye
magarki akaina .”
Ta girgiza kai alamun a’a “sweetheart kin janye dan idan nayi kuskure kin bin
umarninki wani abu zai faru dani idan kuma wani abu ya sameni kece kike da asara
sam ita ba asararta bace kina ji kuma kina gani zata komawa wani ta bar miki d’anki
da rayuwar daya tsinci kanshi .” muryarta a sanyaye tace “babu abinda zai sameka
adamcy kuma Ina rokon Allah ya kawo maka saukin abinda Ke damunka "ta qarasa fada
tana rufe fuskarta da tafin hanunta hadi da rushewa da kuka .”
“why sweetheart me yasa zaki min asarar hawayenki bayan kin min addua?”addua nafi
bukata daga gareki kuma kinyi min na kuma gode Kiyi haquri don Allah ki daina kuka
ni dai kin janye furucin ki akaina “na janye kai ma kuma kayi min alqawarin bazaka
takura rayuwar maryam ba .”dan allah ka barta tayi farinciki a gidanka wallahi
bancin mutane zasu zageni da na raba aurenku kowa ya huta“
“sweetheart babu mai zaginki kuma da zaki min haka wallahi da naji dadi da samun
kwanciyar hankali “uhmm adamcy taa girgiza masa kai “kayi hakuri kawai adamcy zan
maka addua kamar yadda ka bukata ya sauke wani numfashi yana mikewa ya zauna
gefenta ya zauna yana kiran sunanta .”
“sweetheart!”
“ina jinka adamcy “ina son zan qara aure“bazan hanaka qara aure ba adamcy amman
dan allah ka bari zuwa nan gaba kad’an dan bazan ta’ba yarda ka shigo da wata
gidanka ba alhalin diyata bata da matsayin komai a wajenka “why sweetheart “?mu
bar wannan maganar adamcy muyi wata dan bana son jinta for now shiru kawai yayi
yana mai runtse idanunshi shi kad’ai yasan zafin da ciwon da zuciyarsa keyi .”
“Sweetheart cikin satin nan in sha allahu zan bar kasar nan zuwa holland “da sauri
mami ta kallesa sam maganar bata mata dadi ba ,kuma tasan dan ya nisanta kanshi da
maryam ne “zaka bar kasar nan saboda maryam ko ?tayi maganar kamar zatayi kuka “ko
d’aya sweetheart “saboda me zan yi tafiya saboda ita ?”kema kinsan tafiye tafiye
yana cikin tsarin aikina” mami tayi shiru ya riko tafin hannunta cikin nashi
“sweetheart!”ta sake kallonsa “ki kwantar da hankalinki nifa banki na daina tafiya
zuwa koina ba saboda ke “wa na ajiye a inda zani ?”
“Me zakaje yi a hallond?yayi shiru yana kallonta “naga duka yaushe maryam ta tare
da zaka tsiro tafiya gsky nidai idan son raina ne ka bar tafiyar nan ka wakilta
wani ka d’an zauna da maryam “shikenan sweetheart “ya bata amsa da hakan cikin
halin damuwa ya mike tsaye yana mata sallama murmushi ta sakar masa amman gida
zaka wuce ko ? ya gyada mata kai kawai “to allah yayi maka albarka ka gaishe min da
maryam anjima manu direba zai kawo maku abinci “to !kawai ya fad’a a takaice sannan
yasa kai ya fice daga parlour’n massalacin ya nufa domin gabatar da sallar
laasar .”
Hisham zaune akan kujera yana waya da nuzla “eh har yanzu ina office , allah
kuwa da gaske nike amman bari nayi sallar laasar na tura miki babu mamaki ma idan
na tashi aiki zanzo na gaki kafin na wuce gida , sosai kuwa ya fad’a yana murmushi
kmr yana gabanta ,ahankali yaji ana Knocking din kofar office dinsa amman ya
share yaki bada umarni shigowa ya cigaba da waya da nuzlah har kusan mintuna
shabiyar sannan yace wa nuzla “bari zan kiraki nan da minti biyar acan bangaren
nuzla cike da shagwaba tace “a’a ban yarda ba “okay to shikenan zakiji komai da
zanyi “yana gama fadar haka ya bada umarni shigowa ga diyar aminin abbansa dake
aiki akarkashinsa .”
Zakiya ta tura kofar office din ta shigo ahankali ta tsaya agabansa amman bai
d’ago ya kalleta ba ya cigaba da wayar da yake .”a tsanake ta bude bakinta ta kira
sunansa “hisha…yayi saurin d’aga mata hannu yana cewa alamun tayi shiru dan da
yasan itace bazai bada umarnin shigowa ba “a’a abdull ne ya shigo akwai maganar
da zamuyi dashi shiyasa nace ki bani minti biyar “okay naji da zarar na gama dashi
zan kiraki ya katse kiran sannan ya kalli zakiya yace “yaya akayi ?sai data
numfasa kana tace “akwai matsala fa “me ya faru “ya budurwa zata zauna ta dinga
tayar maka da hankali haka?” nifa abokiyar aikinka ce kuma kusan yaruwarka wacce ko
matarka tasan da zamana bata ta’ba nuna damuwarta ba sai wata can .”
“aa dakata zakiya banason haka matsayin nuzla dabam a wajena tana sama da kowacce
mace a wajena ba wai wata bace kin fahimta ko ?“ kana nufin har matarka ?“eh bakiji
nayi generalizing ba nace kowa , tafi kowace mace dan haka bana had’a maganarta
data kowa ki kyaleni ke bani ma abinda ya kawoki ki bar min office menene ma ya
kawoki “
? ”mr Ibrahim yace ka tura masa idan ka gama “tô naji zaki iya wucewa please ya
fad’a yana nuna mata kofar fita da yatsun hannunsa .”
Ta juya ranta a matukar bace yace “idan kina shiga harkata zan iya sallamarki aiki
, akwai wata mace ne bayan nuzla acikin zuciyata da zaki zo kina wasu surutan banza
?tsaki yaja ya fara duba file din data ajiye agabansa .”tana fita daga office din
hisham office din abdull ta shiga tana kiran sunansa “abdull !! “menene ?ya tmbyeta
tare da barin abinda yake ya dago ya zuba mata ido “wai me abokinka ya taka akan
wannan banzar yarinyar nuzla ne da zai iya ciwa kowa mutunci akanta wai me tafi
sauran mata ne ?kaga irin wulakanci da yayi min yanzu saboda suna yin waya daita
“kinsan me ?ta girgiza masa kai alamun tana jinsa “hakuri zakiyi zakiya dan wannan
yarinyar itace muradin ransa dan ko matarsa baya sakewa daita akan wannan yarinyar
kuma bata son yana muamula da kowace mace “ai kuwa wallahi tayi kadan dan bata isa
ta hanashi muamula da kowa ba .”
“Ita din me ? sannan akan me ?to sai dai idan a gidinta zai tare ko kuma ya
cicibota ya dawo daita office dinsa inyaso duk abinda yake tana gani ko kuma ta
dinga binshi duk inda za shi .”yayi murmushi yace “ko dai kina kishi daita ne naga
duk kin damu ?”“kishi ?meye tsakanina da hisham da zanyi kishi akanshi bayan aiki
da kuma dangantar dad dinsa da nawa ?”kawai dai wallahi naji ina tausayin matarsa
ne yarinyar kirki ce ga hankali ga ladabi shine kawai nake tausaya mata saboda
nasan duk lokacin daya auri wannan banzar yarinyar ina tausayawa rayuwar matarsa
duk da nasan yarinyar nan bazata yarda ta auresa ba wata manufa gareta .”
“Me yasa kika fada haka ?ince guduwa tayi lokacin da zaayi aurensu dashi sannan
yanzu ta dawo masa ai kasan akwai abinda take nufi dashi wallahi , wakilla haushi
taji dan ya auri nana hauwa’u kawai ta dawo ta hanashi zaman lafiya da matarsa
kuma tasan idan batayi amfani da karfin soyayyar da yake mata ba bazata yi galaba
akanshi ba shi kuma dake qaramar kwakwaluwa ce dashi yake wani biye mata yarinyar
daya kamata yaci ubanta laada waje “.
Abdull ya sake yin murmushi wanda dagani na takaici ne “ kinsa me ? kije kawai Kiyi
aikinki zai fiyye miki amman hisham kam bai ji bai gani akan nuzla bancin nasan
gidansu nuzla basa biye biye da ni kaina nace anyi masa wani abu ne “.
“gsky kam amman ni matarsa nake ji ka duba kaga ranar d muka je gidansa baka ga
yanayinta ba kamar tana jin tsoronsa komai a dar dar take yi shi kuma ko kallon
biyayyar da take masa baya yi sai ma wayar da yake da wannan banzar yarinyar ina ma
ni ya samu da naci ubansu daga shi har ita “gsky nana hauwa’u bazata iya ba Ke dai
zai fi kiyi abinda Ke gabanki sarkin shiga abinda babu ruwanta “kana ji ko abdull
“dan allah Zakiya kije na gaji da mgnr hisham nayi masa mgn har na gaji idan zai
canza ya canza idan bai zai canza ba tare dani allah zai wa hukunci ba daga haka
bai sake cewa kala bata juya ta bar office din cike da takaici .”
Qarfe biyar daidai motocin ata suka shigo gidan yayinda maryam ke zaune a parlour’n
kasa cikin tsananin tashin hankali tana waya da nana hauwa’u “wallahi sister duka
fa kwanaki biyu ne kawai nayi acikin gidan nan amman ji nake tamkr a makabarta nike
zagi kuwa acikin kwanakin nan sai dai kawai nace Alhamdulillah ,shi kawai baya
ganin abubuwan da yake min kuskure ne shi kawai kanshi ya sani eh ko jiya ya sha
yanzu haka ma cikin matsala nike dan daren jiya na kwashe kwalin sigarin na zubar
a shara ashe da saura aciki kuma yace lallai sai na dawo masa da abunsa ,ni yanzu
tashin hankalina na aika a siyo masa sigarin baa samo exactly irin wanda yake
sha ba ….”
“Shiru tayi sakamakon turo kofar parlour’n da akayi idanunta data zubawa kofar suka
sauka akanshi sanda yake qoqarin takuwa ,sosai ya dauki hankalinta koda yaushe
fuskarsa tashi a daure take kallo daya yayi mata ya janye idanunshi akanta “sannu
da zuwa” ta fad’a a matukar tsorace tana qoqarin mikewa ta bar parlour’n tun
kafin ya soma cin ubanta , bai amsa ba yace “me na fad’a miki ?bana ce karki sake
na dawo na ga wannan fuskar ba ? ya qara taku biyu taja baya da sauri “dan allah
kayi hakuri ta fad’a cikin tsananin tashin hankali“.ina sigarina ?”
Mmn sudais
💗💗💗💗💗💗
MAR'ADAMS
💖💖💖💖
💗💗💗💗💗💗
*AYSHA A BAGUDO*
WATTPAD @HAUESH
AREWABOOKS USERNAME
AYSHAABAGUDO
bismillahirrahmanirrahim
Wannan littafin na kudi ne mai bukatar karantashi byn na kammalashi zai biya
1000 ta wannan account number din 1438775094 Aishat abdullahi access idan an tura
sai a turawa wannan 09136918331 alert domin tabbatar da an tura domin sauraron
littafaina a tuntubi chaneel dina (Hausa bakwai ) a YouTube.
Page 8
A matukar razane maryam take kallonsa jikinta na wani irin rawa idanunta suka
canza kala sakamakon hawayen data soma d'an taruwa acikin kwayar idanunta cikin
tsananin fad'uwar gaba maryam tace "ga ..gashi can akan table sai dai ba'a samo
exactly irin ..."sai kuma tayi shiru ta kasa qarasa maganarta dan tasan me karshen
maganar tata zata janyo mata, ta tsura masa ido kawai tana cigaba da kallonsa
hawaye na gangaro mata akan kuncinta ."
"exactly irin me ye ba'a samu ba ? yayi maganar a tsawace yana sake had'e fuska "ta
runtse idanunta gam hawaye masu zafi suka biyo kuncinta "irin wanda kake sha né
ba'a samo ba "me yasa ba'a samu irinsa ba ?"ya tambayeta yana tsareta da tsuma mmun
idanunshi masu matukar firgitarwa "tayi shiru tana kallonsa hawaye na faman
turereniyar zubo mata "nima ban....ban sani ba ?"ta fad'a a muryarta na rawa tana
share hawayenta da hannunta d'aya tare da kai tafin hannunta daidai saitin
zuciyarta dake beating very fast ."
Tsumammun idanunshi ya ware sosai akanta yaga yadda ta qara shiga tashin hankali
wanda hakan Ke masa dadi, a duk lokacin daya ganta cikin damuwa yana jin sukuni
aransa, wani abu ya had'iye mai d'aci a makoshinsa kafin ahankali ya motsa lip's
dinsa da kyar "babu ruwana ki nemo min exactly irin sigarina shi nake bukata kuma a
yau dan kinsan halina sai dai ki bawa wani labari ,ban ta'ba d'agawa kowa kafa ba
kuma bazan fara akanki ba yana gama fad'ar haka ya juya a zafafe ya soma d'aga
kafafunsa zai haye sama ."
jiki a sanyaye ta qara taku biyu tana wasa da yatsun hannunta tace "wallahi yaya
Adam ban san yadda zanyi a samo maka irinsa ba sai dai kayi hakuri ka aika wanda
ya saba zuwa inda yake siyo maka ko kuma kayi amfani da sauran na jiya ."wanda
kika zubar a shara kike nufi ?ya juyo a fusace tare da fad'ar haka, taja baya da
sauri tana gyad'a masa kai gabanta na dukan uku uku "you are very stupid ,ki nemo
min ko kuma inci ubanki acikin gidan nan yau ."
"Ubana kuma !?"yes of course ubanki ko zaki rama ne da kika tsaya kina tambayata ?
ta sauke numfashi tana girgiza masa kai "okay ki nemi min abata kuma irin wanda
kika wulakanta min “cikin kasa da murya tace "ni dai gsky ban san yadda zanyi ba
kai dadin me ma kake ji a shan sigari abinda zai cutar da kai ?”
”ni zaki fad'awa haka ? kanta ta gyad'a masa alamun Eh !to ai gsky ne me zakayi da
wani sigari abinda yake saurin kashe mutun "are you out of your sense ?."
"ni kike fad'awa haka "? shiru tayi tana tunani amsar da zata bashi wanda kafin
nan idanunta sun sake kawo hawaye tace "yanzu meye illar maganata bayan gsky na
fad'a maka "?"Are you mad ?"da sauri ta girgiza masa kai alamun a'a "okay iskanci
ne kenan yasa ina magana kina magana ?"ta sake girgiza masa kai idanunta na kawo
ruwan hawaye domin dai gbdy a tsorace take dashi ,maganar ma allah ya sani dauriya
ne kawai take yi da kuma son rage tsoronsa dake kunshe a zuciyarta ".
cikin rawar murya tace "am sorry"!da sauri yace "sorry for your self "amman dai
kuma kasan shan sigari yana da matuqar illa sosai arayuwar d'an adam "so what? ina
ruwanki da rayuwata ?gabanta taji yayi mummunar fad'uwa ta shiga girgiza masa kai
hawaye na sake fita daga idanunta ."ahankali taga ya soma takowa zuwa inda take
tsaye yana mata wani mugun kallo ."nan da nan jikinta ya fara rawa ganin idan ta
tsaya kanta zata cuta yasa ta juya da sauri ta fad'a d'akin dake manne da
parlour'n ta murd'a key ."ta jingina bayanta da kofar ta tsaya tana sauke
numfashi.”
A zafafe ya qaraso jikin kofar ya tsaya tare da runtse idanushi kafin ya dunkule
hannunsa ya kai wa kofar naushi yace "me yasa kika gudu baki tsaya ba kiga yadda
zanyi dake shasha duwaf din banza kawai ?”
”wallahi wallahi da kin tsaya da sai na karya miki kafa sai dai uwarki ta haifi
wata mai kama dake nonsense "muryarta a sanyaye tace "kayi hakuri dan allah bazan
sake ba ."yana jin yadda take kuka take bashi hakuri tana tsaye kusan minti biyar
dafe da saitin zuciyarta dake bugawa da sauri sauri , taji alamun tafiyarsa amman
ta kasa fitowa har sai da minti biyar ta wuce bata sake jin motsinsa ba hakan ya
tabbatar mata ya bar gurin .”
ta bud'e kofar ahankali ta fito tana maida numfashi tare da goge hawayenta ta
hau sama, ahankali ta sanya kai cikin d'akinsa ta leka tsaye ta samesa ya bawa
kofar baya hannuwansa hard'e a saman faffad'an qirjinsa sai huci yake fesarwa tmkr
zakin daya nemi abincinsa ya rasa ,gefe guda kuma duk ilahirin gashin dake kwance a
jikinsa sun mike tsabar bala'i ji tayi kamar taje ta rungume shi ta baya ta sake
bashi hakuri ya sauko dan bata son ganin yana fushi most especially daita ."
Wani dogon tsaki yaja yana sauke hannuwansa ya rike kugunsa da hannu d'aya acikin
ransa yace "wannan wace irin jaraba ce ?yarinya kamar mayya duk abinda zai mata
bata damuwa ko ya zagi uwarta ya zagi ubanta duk a banza baya mata ciwo sai dai
tayita bashi hakuri "ya fahimci mugun hakuri ne daita ,kuma shine dalilin da yasa
mahaifiyarsa tayi masa sha'awar aurenta" tsaki yaja ya soma cire kayan jikinsa ya
fad'a bathroom ya sakarwa kanshi ruwa ya fito ."
Bai sauya wasu kaya ba vest da boxcer kawai ya saka ya kwashi wayoyinsa guda biyu
ya sauko zuwa parlour'n kasa ya zauna ,ya d'auki remut ya canza channel sannan ya
d'auki wayarsa ya soma danne danne yana duba sakwani mutane ringing din waya ne
ya karad'e parlour'n ya bar abinda yake yana yatsina fuska alamun qarar na damunsa
ko ba’a fad'a masa ba yasan qarar wayarta ne ,can gefen kujera ya hango wayar yashe
tsaki yaja , ya d'auke kanshi ya cigaba da abinda yake yayinda aka cigaba da kiran
wayar ,qatar wayar ta dameshi sosai gashi kuma shi bazai ta'ba iya bud'e bakinsa
ya kirata ba ."
cikin haka ta sauko ta shiga kitchen ta soma fito da abubuwan da zatayi amfani
dashi na girki wayarta ce ta sake d'aukar qarar sauti ,ya tsaya cak ya bar abinda
yake ransa na qara 'baci ,da d'an saurinta ta fito tana goge hannunta da towel ta
soma duba inda wayar take ta d'auka taga sunan mahaifiyarta ce ke yawo a screen din
wayar tayi shiru ta kasa d'auka a gabansa ,ta d'an d'ago ta kallesa taga ita yake
kallo ta qasan idanunshi "nan take gabanta ya shiga fad'uwa "mummy ce "ta fad'a
muryarta na rawa."
" yasan zaa rina dan zata fad'a masa ko wacece ta kira ,tsaki yaja "na tambayeki
ne ?ya fad'a yana sake jan wani tsaki "naga kana kallona ne shiyasa nayi tunanin
ko kana neman qarin bayani ne "akan me kenan zan bukata ?duk ma wanda zai kiraki ya
kiraki mana menene matsalata da hakan ?kai kuwa kake da matsala dani tunda zamanka
nake "ta fada tana tsura masa ido taji abinda zai sake fad’a ."bai sake cewa uffan
ba yayi tmkr bai ji abinda tace ba ta juya ta koma kitchen ta kira layin
mahaifiyarta tana aiki suna waya daita wanda duk hirar akan zaman aurenta ne ."
******
Da misalin karfe shida daidai hisham ya shigo gidan a gajiye a parlour'n gidansa
ya zauna yana sauke numfashi nana hauwa'u dake zaune cikin tsananin tashin
hankalin abinda zai faru tsakanin maryam da yayanta tai masa sannu da zuwa babu
yabo babu fallasa ya amsa yana furta "wash allah ! sannu ka gaji ko ?girarsa ya
dage mata alamun “eh ! ko cikakken minti biyu bai yi da zama ba nana hauwa'u ta
mike tsaye tana cewa “bari naje na kawo maka ruwa mai sanyi kasha ya juya
"tafiyarta yabi da kallo ,yadda take jujjuya jikinta yana ta’basa.”
Daman kuma ba tun wannna lokacin ba yasan tana da kyawun jiki sosai fiyye da maryam
dan tana da tsawo sosai , gyara zamansa yayi ya cigaba da kallo every step of
her , .”ya runtse idanunshi sannu ga ruwa kasha da alamun ka gaji dayawa yau "ta
fad'a tana miko masa cup ahankali ya bud’e idanunshi yana kallonta sannan ya karbi
cup din hannunta alokacin da wayarsa ta fara ringing ,ya ajiye cup din ruwan akan
table din gabansa ya ciro wayarsa a gaban aljihun rigarsa yana duba screen din
wayar ."
ganin mai kiransa ya d'auka da sauri yana cewa "hello my dear "
Wani irin bugu qirjin nana hauwa’u yayi da karfi ko baa fad’a mata ba tasan ko
wacece ta kirasa ta samu waje kusa dashi ta zauna tare da janyo kafafunsa ta
d’aura akan cinyarta ta soma mammatsa masa “ no no!! your time is my time my time
is your time am always with you,kowani lokaci naki ne karki damu am always with
you my dear ai tunda nace miki zanzo zanzo ne bari na dan watsawa jikina ruwa ,ko
banzo yanzu ba zan shigo da daddare "tunda ya cigaba da wayar ta kasa cigaba da
massaging din da takewa lafafunsa ta janyo wayarta tana neman layin maryam taji
yadda suka qare da yayanta .”
Kira kusan biyar tayi mata bata d’aga ba yayinda hisham ya cigaba da wayarsa da
nuzlah yana fad’a mata kalamai masu sanyi da sanya natsuwa wanda hakan yasa nana
hauwa’u ta soma jin wani iri aranta zuciyarta ta dinga tafasa tana mata zafi da
ciwo ,nan da nan yanayinta ya sauya haka ma kwayar idanunta ta cika da ruwan
hawaye sai dai duk yadda taso ta danne amman sai da sheshekar kukanta ya bayyana
"ta fara gajiya da wulakanci da yaya hisham yake mata, wallahi gara ya aro nuzla
din su zauna tare da su taru su kasheta da bakincikinsu ."
runtse idanunta tayi gam tana zubar da hawaye tana sake zurfafa tunaninta " bata
son ta sake masa magana akan nuzla tunda sun rigada sun gama mgn akanta sai dai
duk da hakan bai kamata ta dinga d'aukar wulakanci har haka ba "wani bangare na
zuciyarta ya fad'a mata haka ,ahankali ta girgiza kai sakamakon wankakkiyar
zuciyarta dake bata shawara "kema ya kamata ki sake tuntubar mumy ta amince ya
auri nuzla a wuce gurin ,ai kuwa gara ki tursasa mata ta amince da haka akan
wannan wulakanci da suke miki, dan kuwa da zarar sunyi aure shikenan wasu abubuwa
dole zasu ragu tana kallonsa ya sauke kafafunsa ya mike tsaye ya shige d’ayan
parlour’nsu ."
ahankali ta dinga share hawayenta tana rarrashin kanta "meye dan ya wulakantaki ya
kaskantar dake a karkashinsa fa kike ai wanda ya isa akewa haka dan allah nana
hauwa'u ki sanyawa zuciyarki hakuri ki daina nuna damuwarki daman tare kika gansu
dan haka ki kawar da idanunki akansu sosai ta bawa kanta hakuri kafin daga baya ta
tashi ta nufi hanyar parlour’n daya shiga ta iskesa zaune yana cigaba da waya ta
durkusa a gabansa muryarta a sanyaye ta kira sunansa "yaya hisham !bai amsa ba
illa tsura mata ido da yayi yana kallonta "ban san me yasa ba amman ina jin kamar
nayita kuka ina baka hakuri akan abinda nasan ba laifi nayi bane ."
" ina matukar tausayawa kaina a yanzu yayinda nake jin nadamar aurenka da nayi
arayuwata ". jikinsa yayi sanyi zuciyarsa ta karye da jin abinda ta fad'a sai dai
ya nuna mata tamkar bai ji komai ba ya cigaba da wayar da yake ,ta kai hannunta
taja dogon sajensa mai maseefar kyau da sheki tattare da d'aukar hankali ,da
sauri ya ciza lips dinsa yana fadin "auchhhhh "tare da tsura mata ido sosai yana
kallonta yana jin wani sauyi a gabad'aya ilahirin jikinsa ."Itama din tsura masa
ido tayi tana masa murmushi wanda yafi kuka ciwo tace "dan allah ka bar wayar
nan haka."
Ya cire wayar a kunnesa yana cewa “a kan wani dalili kenan zan bar wayar ? "
adalilin na baka dama ka auro nuzla ka had’amu “. wallahi a shirye nike da
amsarta a matsayin abokiyar zamana ban hanaku aure ba bare hakan yasa ku zabi ku
dinga quntata min ."wallahi wallahi!! da nasan nuzla na sonka da bazanyi wasa da
rayuwata ba ,hakika nayi mata laifi mai girma dana cancanci wannan hukunci daga
gareta amman tayi hakuri ,na rokkeku ku yafe min ?"
nunfashi yaja ya sauke yana katse wayar gabad’aya ya ajiye a gefe ya rungume
hannuwansa a qirji yana kallon kafafunsa dake sanye da safa"ku yafe min kuskuren
shiga rayuwarku da nayi "sarai yaji ta amman ya shareta ya d'auki wayar ya soma
danne danne ." ta kamo hannunsa d'aya cikin nata tana shafa saman tafin hannunsa
ahankali ,dole ya tsaida duk wani abinda yake ya dawo da hankalinsa gareta qirjinta
yabi da kallo babu abinda ta rasa kuma babu abinda nuzla tafita hasalima tafi nuzla
dirin jiki mai kyau .”
Ya tsura mata ido sosai a kallon da yake mata bai san sanda ya zame hular kanta ba
tulin gashinta dake d'aure ya kalla ahankali kuma yasa yatsunsa guda biyu ya zame
ribbon din dake rike da gashin nan take gashin suka baje abayanta bai tsaya wata
wata ba ya fara shafa yalwataccen gashin kanta ."
Naunayen ajiyar zuciya ta sauke tace "ka auro nuzla wallahi zamu zauna lafiya da
'yaruwata idan kuma kana ganin bazaka iya had'ata dani ba ka sakeni ka aurota."sai
lokacin ya d'an ja numfashi yace "bazan iya sakinki ba saboda mumy na matukar
sonki sosai ba kuma zata yarda ba ".
zan fahimtar daita sannan zan bari ta yarda zan fita arayuwarku gabad’aya , da
dai ka dinga wahalar da abinda mumynka take so gara ka raba kanka daita gbdy ka
huta dan .." wani qara ta saki mara sauti tare da yin shiru sakamakon yatsunsa
biyu da yayi amfani dashi ya buge mata baki, ta kama bakinta dake mata zugi tana
shagwabe masa fuska ."Kmr zatai kuka tace " da irin damuwar da kake kunsawa
zuciyata gara ka sallameni ka bawa zuciyarka abinda take ..."shiiiii !mum wil kill
me idan na sakeki ."
“Shikenan haka ni rayuwata zata qare agidan ka ?haka mumy ta tsara ,itama kuma ta
tabbatar da hakan rayuwar zata qare kalamansa yasa ta zare hannunta dake cikin
nashi ta mike tsaye da kyar dan kafafunta sun soma rikewa, ta juya da kyar zata
bar wajen tana cewa " kayi shawara yaya hisham ni zan so rabuwar da kai ka bawa
zuciyarka abinda take so karka ji komai ni zanji da mumy " hannunta ya fixgota da
karfi ta juyi luuuu ta fado jikinsa ."Suka tsurawa juna ido suna exchanging din
numfashi juna .”
ya kai hannusa saman sumar kanta data zubo baya batare da yace uffan ba, numfashi
ta sauke tana cigaba da kallonsa tayi imani bancin nuzla data dawo rayuwarsa da
yanzu ita dashi sun zama abu daya ,bakinta ta kai daidai lip's dinsa ta fara tsotsa
yaso ya hanata amman ya kasa hanata dan yana matukar jin dadi “wani numfashi
yayita saukewa da sauri sauri ."wani irin kissing take masa tun yana iya daurewa
har ya fara mayar mata da martani yayinda koina ajikinsa ya soma rawa tunda yasa
mu ya cafke bakinta yaji komai ya sauya masa karo na biyu kenan da yake rasa gane
kanshi sakamakon kasancewarsu tare ."
sosai yake juya harahensa abakinta jin yana ta'bo wasu wurare ajikinta yasa tayi
qoqarin zare bakinta ya riketa gam aranshi yake cewa "karki min haka please ki
cigaba da kasancewa dani sake qoqarin zarewa tayi tare da yunkurin mikewa taji
hannunsa abayanta ya rike kugunta gam "zan tashi !"ta fad'a kwayar idanunta cikin
nashi ."na rikeki ne ? ya fad’a yana lumshe idanunshi ta kai hannunta saman
hannunsa dake rike daita, numfashi ya sauke da karfi sannan ya zare hannunsa yana
sake lumshe idanun ta mike tsaye da kyar tare da juyawa zata bar parlour’n ."
Ya gyara zama yana dan bud'e idanunshi sosai yana kallon yadda take juya
mazaunanta ,tafiyarta ma kawai abun burgewa ne uwa uba bare akai ga lafiyayyun
nonuwa bombom tamkar wanda aka dasa mata su ahankali yake jin kamar yana murzasu
anya kuwa bazan hakura da matata na bar nuzla ba ?"
yayiwa kanshi tambayar yana kallon yadda gabansa ya mike sambal ,sosai
kwakwaluwarsa ta shiga tunani yayi imani ko mumynsa zata bari ya auri nuzla ba
yanzu ba to kuma shi haka zai yita zama yana cutar da kanshi abanza , gashi baya
neman mata bare yace yana da gurin zuwa ya rage zafi ."
Da misalin Karfe takwas na dare ATA na zaune yana amsa waya mb ,maryam ta
qaraso inda yake tana cewa “yaya Adam sannu da hutawa "yayi mata banza ya cigaba
da wayarsa "na kawo abincinka nan ne ?" yayi mata banza "bari na zubo maka abinci
still banza yayi mata, taje ta zuba masa ta kawo gabansa ta ajiye "ga abinci dan
Allah kaci ko kad'an ne "ke dole ne sai naci abincinki ko daman ina cin abincinki
ne ?"ta girgiza masa kai"to maza ki tattara ki bar nan dashi bana bukata "haba yaya
tun da na tare a gidan nan baka cin komai dana girka ba "meye zanyi da wani
mugun abincinki .?"
"Allah kaci kaji zakaji dadinsa ya kwabe fuska Kmr yaga wani mugun abu "maggie
zanci naji dadi ?numfashi ta sauke sannan tace "ka ci kaji idan bai maka ba sai ka
barshi na sake dafa maka wani .”
shiru yayi dan ya soma gajiya da magana "bud'e bakinka na baka to "Oh my god
sweetheart me yasa kika had'ani da maseefa ?me yasa kika hadani yarinyar da zata
kasheni da damuwa ? Nace bana bukata sai kace dole “ ya fad'a yana dafe
goshinsa ."
cikin rawar murya tace "me nayi da zan kasheka da damuwa ?"ni bance zaka kasheni da
damuwa ba sai kai ?"wai dan girman allah me nayi maka ne da ka tsani ne haka ka
tsani duk wani abu daya dangan ceni ?ya tsaya cak yana kallonta a dage."dan girman
allah ka daina tsanata ka barni naji da damuwata domin zuciyata tana cikin tsaka
mai wuya ".nan take ransa ya qara 'baci zuciyarsa ta soma tafarfasa sakamakon jin
maganganunta wasu marasa Kan gado bai san lokacin daya ya soma mgn cikin zafin
zuciya ba "ni zaki fad'awa kina cikin tsaka me wuya ?tayi shiru tana zubar da
hawayen bakinciki "
"Dole na fad'a maka domin kai kafi kowa cancatar na fad'awa dan Allah ka bar
zuciyata haka nan ta huta , ka kalleni da kyau ya Adam kallo d'aya zaka min ka
fahimci bana cikin kwanciyar hankali da walwala tun daga ranar da aka sheida min
sakon mami akan aurenmu ban sake samun isashen bacci da natsuwa ba "me yasa
haka ?"me yasa na rasa duk wata natsuwata da kwanciyar hankalina ?"
Wani kaskance kallo yayi mata mai firgitarwa wanda yasa tayi shiru ta kasa cigaba
da maganar ta qara shiga tashin hankali mai tsanani shiru ne ya ratsa parlour'n
bata sake cewa komai ba kamar yadda shima bai sake cewa komai ba har tsawon minti
biyar suna zaune kafin daga baya ya motsa labbansa muryarsa a tsarke yace "karki
yi kuskuren kamuwa da soyayyata domin muddin kikayi haka hakika kin d'aukarwa
zuciyarki wahala “dan kuwa mummunar ciwo ne zai kamaki a karshe ki rasa rayuwarki
gabad'aya ,gara ki cigaba da rayuwarki haka batare dani ba domin ni a kowani lokaci
zan iya rabuwa dake saboda nayi matukar tsanarki ."na tsaneki ina sake fad'a miki
na tsanakeki ".yana gama fad'ar haka ya mike tsaye ya barta ya haye sama cikin
sauri sauri yake taka step ."
kuka maryam ta fashewa dashi tana cewa "ya allah idan wani laifi nayi ma yaya
adam yasa hankalinsa bai kaina ya allah kasanyaya zuciyarsa ,allah ka sani ina
tsananin son mijina ta yadda bazan iya rayuwa idan babu shi ba ,allah ka sanyaya
zuciyarsa akaina ,allah ka juyo min da hankalinsa gareni ka bamu zaman lafiya tana
kuka wayarta na ringing wanda kuma tasan nana hauwa'u ce amman ta kasa d'auka domin
dai kota dauka daga mata hankali zatayi kawai da kyar ta mike ta nufi dakinta ta
kwanta lamo tana neman mafuta akan zamansu .”
Sosai zuciyarta da kwalkwaluwarta suka shiga tunani “Ya kamata yaya Adam ya
dandani zafin so ko dan yasan martaba da kimar son da take masa,” to me ya kamata
nayi “? ta tambayi kanta “dan dole akwai bukatar na tashi tsaye na kwatarwa kaina
yanci a wajensa shiru tayi “tana son mijinta bazata iya rabuwa dashi ba ,dan ko da
wasa bazata iya furta masa ya saketa ba sannan bazata iya ta’ba bashi damar ya
had’ata da kowace mace ba taya kenan zai d’andani zafin so bare yasan
darajanta ."?”
Zumbur ta mike zaune “dawa ya kamata nayi wannan shawara “?nan take kwalkwaluwarta
ta bata amsa da “sister mana ita kad’ai ce zata baza baki shawarar yadda zaki yi
ta mike ta isa inda ta ajiye wayarta ta soma kirata alokacin tana zaune a
parlour’n tare da yaya hisham tana shirin mikewa domin ta shiga dakinta ta amsa
wayar yaya hisham ya zame ya kwanta akan cinyarta yana d’auka remut dole tasa wayar
a silet dan karta damesa ta cusa hannunta cikin sumar kanshi tana jin sanyi
aranta dan batayi tunanin zai kwanta a saman cinyarta ba duk tunaninta barin gidan
zaayi yaje gurin nuzla .”
Ahankali ta cigaba da shafa sumar kanshi ta d’an kai bakinta daidai kunnensa sai da
ta sakar masa murmushinta sannan tace “abinci fa ?wani zazzafan numfashi ya sauke
yana qara narkewa akan cinyoyinta masu laushi da kyar ya fixgo magana “zanci sai na
gama kallon new’s “yayinda maryam sai faman kira take baa dagawa “oh my goodness
wai me yasa sister bata daukar waya ne ?ita kanta nana hauwa’u tana son ta d’auka
amman bata son ta damu mijinta kuma bata son yaji abinda zata fad’a sai dai
hankalinta ya rabu gida biyu wani yana tare da mijinta wani kuma na wajen maryam
bini sai ta kalli screen din wayar taga kira na cigaba da shigowa a karshe dai yaya
hisham yace “lafiya ?”
A firgice nana hauwa ta kallesa “kina kallona karya na fad’a ?tasan gsky ya fad’a
amman meye na sake fad’a mata ?ta sake duba wayar zata mayar ta ajiye ya karba ya
d’aga tare da sakata a hands free nan take muryar maryam ta bayyana cikin fashewa
da kuka “sister ina kika shiga ne tun d’azu nake kiranki ina cikin damuwa “wallahi
zuciyata kamar ta fashe ki bani shaawara ya zanyi da yaya Adam wallahi idan aka
cigaba ahaka komai zai iya faruwa dani “.
“Sister !”nana hauwa ta kira sunanta “ina jinki sister ina bukatar ki bani shawara
sister yaya zanyi da yaya Adam ya zaayi ya dan dani zafi so ?ina son yaji zafi da
ciwo kamar yadda nake ji ,sonshi yayi min yawa “
murmushi nana hauwa tayi “wannan kuma ai abinda muka dade dasan ne kece daman kika
kasa yarda da hakan “maryam bata san sanda hawaye ya zubo mata ba tace “amman
kisan cewa yayi kar na kuskura na kamu da soyayyarsa domin muddin mayi haka na
d'aukarwa zuciyata wahala “dan kuwa mummunar ciwo ne zai kamani a karshe na rasa
rayuwata gabad'aya ,gara na cigaba da rayuwata haka batare dashi ba domin ni a
kowani lokaci zai iya rabuwa dani saboda yayi matukar tsanata ."
Yaya hisham yayi saurin runtse idanunshi yaji zafin kalmar ahankali yaji zuciyarsa
na yi masa zafi kamar zata fito waje tausayin maryam ya kamashi
Yayinda nana hauwa tace “subhallah gsky yaya Adam bai kyauta ba sam abinda yake
baya kyautawa amman ki bari zamuyi waya zuwa gobe yanzu bani kadai bace “tana gama
fadar haka ta katse wayar gbdy “kinga irin muguntarsa ba wallahil azim adam mugu ne
sam sam zuciyarsa babu imani bare tausayi babu imani acikin zuciyarsa “yana gama
fad’ar haka yaja tsaki ya mike tsaye ya shige d’akinsa .”
Nana hauwa tabi bayansa da kallo tasan yayanta bai da kirki amman me zasu iya yi
akai ?”yayyunta ma baya jin maganarsu bare ita da ko kusa da inda yake bata isa
taje ba matsawar bashi ne ya bukata ba .”tana zaune yaya hisham ya fito da key din
motarsa ya nufi kofar fita “ta mike da sauri tana cewa “ina zuwa kuma ?fita zanyi
baka ci abinci ba fa?ya juyo ya tsaya tare da tsura mata ido kawai yana qare mata
kallo batare da yace mata komai ba kafin daga baya yasa kai ya fice daga
parlour’n ya barta tsaye cikin tashin hankali dan tasan wajen nuzla zashi zama tayi
tare da zabga tagumi .”
*******
Tashin hankalin da ba'a sa masa rana wayewar gari yau din nan subaia suka tashi
da mutuwar mahaifinta sosai suka shiga tashin hankali ita da kannenta wanda baki
bazai fad'a ba tabbas rayuwarsu zata sake shiga cikin matsala babba yanzu saura
abinda ya rage masu mahaifiyarsu ce itama kuma ba wani isashen lafiya gareta ba
lallai suna cikin tsaka mai wuya basu da mataimaki sai allah shiyasa sunyi kuka
kamar me maryama taje ta kuma ta tausaya mata matuka dan tana tausayin kanta
amman idan ta tuna rayuwar subai'a sai taga gara ita akanta from rich to poor is
not easy .”
a bayan can mahaifinsu mai arziki ne sai dai bai yiwa kanshi tanadin komai ba har
zuwa lokacin da yayi accident ya samu matsala a bayanshi ."alokacin da yake tsaka
da jinya sai yayi tunanin da zaman da yake na rashin sanin ranar warkewarsa mai zai
hana bazai hada kwssamominsa da abokansa guda biyu ba tunda shi bazai iya komai
ba su kuma daman ba wani samu suke ba kusan a karkashinsa suke samu alhj sani da
alhj dan umma ,tofa tun daga wannan lokacin daya hadasu komai ya sauya agareshi
domin kuwa babu abinda ya biyo baya sai danasani dan kuwa tunda suka fara samun
kudi suka juya masa baya basuyi tunanin su taimaka masa ba.”
tun suna masa naci har yazo ya gagaresu sai rufin asiri allah mahaifinsu na cikin
wannan halin mahaifiyarsa ta kamu da hawan jini ga diebites daman tana dashi ,
shekaru biyar yayi yana jinyar sai yau rai yayi halinsa aunty tazo da ummah zaune
su subai da kanneta suke wajan gaisuwa amman da ka kalli fusk'okinsu kasan suna
cikin rud'u da tashin hankali ."sai dai fatan samu sausauci daga Allah.”
Ranar asabar da misalin karfe tara na safiya bayan an shirya komai na bangaren umma
tsaf yayinda aunty salma tayi duk wani shiri domin janye zuciyar yusif ta hanyar
malaminta ya koma kan soyayyar daya daga cikin yayanta , kausar data gama gaisawa
da umma ta fito neman maryama tana kwance acikin kalubalin rayuwa da yake zuwan
mata lokaci lokaci ita gbdy ma data sanin girmanta take domin gara tana yarinya
radadin rashin mahaifi ne kawai Ke damunta da kuma cin zarafin yan gidansu amman
bata taba kwana da abinda Ke daga mata hankali har ya hanata runtsawa ba ."
Da gudu kausar ta fado kanta tana cewa masoyiya I miss you a lot duk da halin qunci
da take ciki bai hanata nuna mata itama tayi farinciki da zuwanta ba "wallahi
gidanmu kullum zanceki muke kowa mamaki yake wai yaya yusif yaga mace Kuma yana
sonta har kuma ya kasa samun sukuni saboda ita tayi shiru kawai domin neman take ta
daurawa zuciyarta damuwa acikin kahon zuciyarta domin dai ita tuni ta rufe babinsa
da komai rayuwarta kawai take "dan Allah masoyiya ki tashi ki shirya yana parlour'n
umma nasan ke kadai yake jira ."
Maganarta ta bata mamaki to idan haka ne ina batun baba gali da yace yusif din ya
amince da auren shikura abbanau ya yarda da batun da baba yaje masa dashi maryama
batayi nauyin baki ba kamar yadda ta saba tace “ai ina ganin Ke akwai abinda
bakisani ba kausar ta kalleta cikin rashin fahimta tace "kamar me fa ?bayan
tafiyarku baba yace sunyi magana da abbanku an maida wa yusif shukura amatsayina
“kausar ta zaro ido tace "saboda ana hauka Ke waya ya fad'a miki wannna" baba !"
Sakina da shikura kuwa duk wani abinda ya Kamata aunty salma tayi masu wanda zasu
jewa yusif dashi dan hK suka shirya cikin hadaddiyar kwaliya mai daukar hankali
suka dauki abinda aka tanada domin shi suka nufi bangaren umma yana zaune jin
tafiya yasashi fad'a da murmushinsa har wani mikewa yayi amman ganin sabanin
abinda zuciyrsa Ke mararin gani ya dauke idanunshi daga kallonsu sukai sallama
cikin siririyar murya tare da durkusawa suka ajiye mishi farati gabanshi suka zauna
"ina kwana ya kuma hanya ?”ya dan kallesu "sannna ya tsaida kallonsa akan sakina
yana cewa "kece sakina ?"
"Eh nice tayi mgnr tana sunkuyar da kanta "sannuku da kokari atare suka sakar
masa wani kayataccen murmushi "me mukayi na Godiya batare da ya kalleta ba yace “ya
cancanta na gode tunda kunyi aikin da baku ya kamata kuyi ba maryama ta baku wahala
domin wannan aikinta ne tazo gareni da abinda zan saka abakina idan ma da hali ta
ciyar dani” gbdy jikinsu yayi sanyi ta gyara zama "ai ya cancata muyi maka haka ya
dan gyara zama sannna ya fuskancesu da wani iyayi da suke masa "akan me kenan ?
sukai shiru hankalinsu ya soma tashi "tabbas wannan mutumin mai wuyar shaani ne
idan da hali ma suce masa dan wulakanci, akace daya daga cikinmu zata iya maye
gurbin maryama a wajenka ko baa fad’a maka bane .”
Mmn sudais
💗💗💗💗💗💗
MAR'ADAMS
💖💖💖💖
💗💗💗💗💗💗
*AYSHA A BAGUDO*
WATTPAD @HAUESH
AREWABOOKS USERNAME
AYSHAABAGUDO
bismillahirrahmanirrahim
Wannan littafin na kudi ne mai bukatar karantashi byn na kammalashi zai biya
1000 ta wannan account number din 1438775094 Aishat abdullahi access idan an tura
sai a turawa wannan 09136918331 alert domin tabbatar da an tura domin sauraron
littafaina a tuntubi chaneel dina (Hausa bakwai ) a YouTube.
Page 9
"Yusif ya d'an yi dariya kad'an sannan yace "saboda kuma kawai a garin mahaukata
ake sai ku maye gurbinta? " maye gurbin maryama ko mace' yar kasar england ce
maryama tafi gabanta awajena ." Jikin a sa'bule suka d'an yi shiru daga bisani
shukura tace "amma baka san cewar akwai wanda yake son maryama ba har ma ana
shirye shiryen kawo kudin auren ta?"wani mugun harara yusif ya buga mata yana
d'aga kafad'unsa alamun ko ajikinshi ."
Ta sake bud'e baki zatai magana a fusace yace,"Ku dan Allah ban son sakarci da
iskanci banza ku ta shi kuje ku sanar da maryama dominta kawai na zo gidan nan ba
dan wasu 'yan iska ba ,ta yi sauri tazo ta samar da nutsuwa acikin raina ita
kad'ai zuciyata Ke muradin son gani baku marasa kamun kai ba"
sakina da shikura sukai shiru suna kallonsa tare da jinjina girman wulakancinsa,
yayinda zuciyar shukura ke qara lissafo mata abinda zata sake fad'a masa amman
ta kasa domin tsoron amsar da yusif din zai bata "lallai wannan ba wanda zasu zo
suyiwa wargi bane, dole sai mahaifiyarsu ta sake shiri akanshi atare suka tashi
jikin babu kwari suka fice daga d'akin cike da 'bacin rai ."
Aunty salma na zaune tana tunanin ya yusif zai kar'bi ya'yanta sai gasu sun shigo
mata rai 'bace ajiyar zuciya ta sauke sannan ta mike tsaye da sauri cike da
fargaba duk da dai bata da já akan aikin malaminta tsayawa tayi tana kallonsu
d'aya bayan d'aya kafin daga baya tace "yana ga kun dawo min jiki a sanyaye .?"
"wallahi mama wannan mutumin mugun d'an wulakanci ne na bugawa a jarida nan shukura
ta zayyane wa aunty salma komai daya faru cikin 'bacin rai sakina tace ,"ni dai
gsky mama ki hakura ki barwa maryama yusif ta aura tunda ya nuna ita din dai yake
so bashi da abinda zai yi damu ita kuma shukura sai ta auri malam yahuza " .bayan
aunty salma ta gama jin abinda ya faru tas da abinda sakina ta fad'a tace "bazaa
hakura abar mata shi ba wannan auren muddin ina raye sai anyisa da d'aya daga
cikinku ."
"to gsky mama ni dai banda ni sai dai ki aura masa shikura taje can su qarata dan
bazan iya da wulakancinsa ba "na gode sosai yar'uwa dan dama zuciyata tana cikin
d'ard'ar ne kar shirin mama yayi tasiri akanki gashi daman dani yafi dacewa tun
dana d'aura kwayar idanuna akanshi na kamu da matsanancin qaunarsa "inji cewar
shukura ".
"yauwa shukurata nasan bazaki ta'ba bani kunya ba daman kuma kamaninmu d'aya "haka
ne kuma dole halinku yazo d'aya ba" sakina ta fad'a acikin ranta sannan fili tace
"yar wahala sai kije kiyita fama amman kisani bazaki ta'ba daraja acikin idanunshi
ba karshe ma ki qarasa rayuwarki a wahala "tana gama fadar haka tasa kai ta shige
d'akinsu ta barsu tana jin babu dadi aranta duk da ahalin yanzu babu wani shakuwa
da soyayya a tsakaninta da maryama amman a wasu lokutan tana jin babu dadin abinda
mahaifiyarta take mata ."
"Kece yar wahala daga nace ina son shi sai Kiyi min mummunar fata in sha allahu
akanki zai qare "aunty salma taja hannun shukura zuwa cikin d'akinta tana cewa
"manta da sakina muyi abinda Ke gabanmu "ta saki hannunta ta qarasa gaban wasu
kwanuka
ta bud'e d'aya daga ciki ta d'auko tandun kwalli ta mikawa shukura tana cewa "ungo
nan shukurata maza ki shafa wannan kwallin à idanunki" shukura ta kar'ba ta soma
qoqarin shafawa yayinda aunty salma ta juya da sauri ta sake d'auko wani qaramin
gwan gwani wanda Ke d'auke da wani bakin magani ta sake dawowa inda shukura take
tsaye ta miko mata hannunta d'aya tana cewa "bani kwalli ki bani tafin hannunki
idan yasan wata ai bai san wata ba zai san dani yake ".
Cike da farinciki shukura ta mika mata tandun kwallin sannan ta mika mata tafin
hannunta kamar yadda ta buqata cikin sauri ta zuba mata bakin maganin tana cewa
"ki fad'i sunansa sau uku sannan ki fad'i duk abinda kike son yayi miki idan kin
isa gabansa ina mai tabbatar miki bazai sake miki mutsu akan komai ba sai akan
abinda kika fad'a masa zai yi aiki dashi kuma zai bi umarninki ."
nan da nan shukura tayi abinda aunty salma ta umarceta"ki lashe kije zaki ga irin
tarbar da zai miki sannan zaki ga irin tarbar da zai yiwa maryama zabinsa ,matsawar
kika ga tarban da yayi miki bai miki ba ko ya had'a da tozarci ko cin fuska karki
'bata ranta ki dawo kawai amman kuma wallahi wallahi sai nayi masa abinda sai ya
wulaqanta akan soyayyarki sai ya dawo yana kuka akanki, ke sai yayi sambatu akanki
sai ya fifitaki akan uwar data kawo shi duniya ".
"yauwa mamana shiyasa nake mugun sonki allah dai ya bar min mamana ."maza kije
garesa cike da Kamala da mutuntaka da kamewa ki shirya duk wasu kalamai masu sanyi
da sanyaya zuciya da zakiyi amfani dashi allah ya bamu sa'a wani irin numfashi
shukura ta sauke tare da rungume aunty salma ajikinta tana furta "ameen !sannan
ta saketa ta juya da sauri ta bar d'akin ta nufi d'akin da yusif yake ."
ahankali ta shiga d'akin bakinta d'auke da sallama yana nan zaune kamar yadda suka
fita suka barshi sai dai idanunshi a runtse suke suna kallon saman d'akin sallamar
daya ji anyi ne yasashi bud'e idanu tare da sauke idanuwanshi abakin kofar d'akin
suka sauka akan shukura dake tsaye tana kallonsa fuskarta cike da fara'a do cikin
ido suke kallon juna ."
Wasu abubuwa ya dinga ganin suna fitowa daga cikin kwayar idanunta suna shiga nashi
nan da nan ya gyara zamansa sosai yana cigaba da kallonta cikin wani irin farinciki
mara misaltuwa tamkar lokacin ya fara ganinta arayuwarsa cike da tsananin farinciki
yace "ya kika tsaya qaraso gareni zuciyata Ke take muradin son gani "cike da
karairaya shukura ta dinga taku har ta qaraso ta zauna kusa dashi ya zuba mata ido
kawai yana sakar mata tsadadden murmushinsa cikin shukin qaunarta daya ji daga sama
"yaya yusif !"
Ta kira sunansa cikin wata irin murya idanuwanshi kawai ya zuba mata batare da
yace mata komai ba " akace daya daga cikinmu zata maye maka gurbin maryama a
wajenka me ka gani ."?murmushi yayi kawai "gabanta ya shiga fad'uwa amman data
tuna irin tarban da yayi mata a yanzu sai taji wani sabon gwarin gwiwa ya shigeta
"ina son na maye gurbin maryama acikin zuciyarka me zaka iya cewa ?"ai wannan ba
komai bane na amince dake dan ma kin fita dacewa dani ".
ta lumshe idanunta kana tace "amman kace domin maryama kawai kazo gidan nan ba dan
wasu yan iska ba ?tayi masa tambayar tana mai kafesa da idanunta yayi shiru yana
kallonta qirjinsa na wani irin bugawa da karfi "maryama kad'ai zuciyarka ke
muradin son gani bamu marasa kamun kai ba ?ya kai hannusa ya riko hannunta gam
cikin nashi yana matsewa "yaushe na fad'i haka ?ni babu wacce zuciyata ke muradin
gani sai ke murmushi tayi kawai aranta tace "aiki yayi tasiri kanan "ta qara damke
hannunsa dake cikin nashi "baka ci komai da'aka kawo maka ba".
"na koshi domin ganinki ma kawai ya kosar dani "ya fad'a a daidai lokacin da kausar
ta shigo hannunta rike dana maryam ."wani irin bugu zuciyar kausar yayi da karfi
sakamakon ganin yanayinsu dan ita maryama daman ta rigada ta cire samunsa acikin
ranta ganinsu haka ma bai d'aga mata hankali ba ."
cikin wani salon jan hankali shukura ta tsura masa ido tana kallon kwayar
idanunshi tana jin wani irin shaukin sonshi na ratsata yayinda maryama ta zame
hannun ta cikin na kausar ta samu waje ta jingina bayanta da bangon d'akin Tare da
sunkuyar da kanta kasa tana kallon zara zaran yatsun kafafunta dan bata son ganinsu
bancin darajan kausar ma da ko hanyar d'akin bazata biyo ba ."
cike da tashin hankali kausar tace "yaya meye haka kuma ?"mai nayi kausar ?shima
ya tambayeta yana jin kamar ana soka masa allura a gabad'aya ilahirin jikinsa
"jikin maryama ya qara yin sanyi rauninta ya soma bayyana idanunta suka fara
ciccikowa da ruwan hawaye "shikenan shima an gama dashi "ta fad'a acikin zuciyarta
"dan Allah malama ki sakar masa hannu"kausar ta fad'a tana zabga mata harara
shukura tayi murmushin mugunta tana zare hannunta cikin nashi tsaki kausar taja
sannan ta soma zayyane masa duk abinda maryama ta fad'a ".
Amman da mamakinta sai ji tayi yace "sai me idan ta fad'a miki haka ?ta sake
kallonsa a matukar tsorace tana cewa "yaya me kake nufi da fad'ar haka ?ina nufin
yanzu shukura nike so kuma ita zan aura "ya salam yaushe wannan alamarin ya faru ?
amman ko akan hanyarmu ta zuwa nan babu wannan tsarin a zuciyarka ? maganar
maryama kake tayi babu tsarin auren wata shukura arayuwarka "to yanzu na canza
raayina ita nake so kuma ita zan aura " a kan me ma zan auri wannan yarinyar? ya
fad'a yana nuna maryama da babban yatsan hannunsa ."
"kausar ta rikice ta gigice ta waiga ta kalli maryama dake tsaye shiru tana ciza
lips dinta na kasa "haba yaya me yasa zakayi haka ?me yasa zaka sa'ba alkwarin da
kayiwa mumy ?me yasa ka furtawa maryama cewar kana sonta zaka aureta yanzu kuma
kazo da wata magana da hankali bazai d'auka ba "why why !!? yaya dan allah karkayi
haka,ka dawo haiyacinka karka yiwa maryama haka tayi maganar cike da tashin hankali
idanunta na kawo ruwan hawaye ."
"Duk yanzu na daina jin komai akanta sai dai ko a cikin masu mana aiki a gidanmu
zan bawa wani shawarar ya auri wannan yarinya,amman yanzu sai shukura itace zabina
a halin yanzu ma na kagauta na d'auketa daga wannan gidan dan ta fi karfin
zamansa ita din ta dabance acikin zuciyata Ina kallonta ina jin farinciki araina
"
hawaye dake makale acikin idanunta maryama suka zubo akan kuncin tayi sauri tasa
hannunta ta goge yayinda zuciyar shukura tayi mata sanyi ta qara tabbatarwa kanta
aikinsu yayi tasiri akanshi ta d'auko ruwan lemu ta tsiyaya a cup ta mikawa yusif
tana cewa "ungo sha kaji sanyi aranka "yasa hannu ya kar'ba yana sakar mata
murmushi cikin tsananin tashin hankali kausar tace "karka sa'ba alkwarin daka
d'auka ,da maryama kawai kafi dacewa ba da wata shukura ba ka bud'e idanunka da
kyau please ."
cikin wata irin murya mai sanyi da tausasawa maryama tace "kausar karki d'aga
hankalinki dan baya cikin hankalinsa da natsuwarsa hasalima bazai ta'ba fahimtarki
ba a halin yanzu ,kiyiwa danuwanki addua dani da shukura duk abu d'aya ne bazan
ta'ba bakinciki dan yusif ya canza ni da shukura ba fatana allah ya basu zaman
lafiya tana cikin fad'ar haka taji an fasa kuka abayanta mai kukan tana fadin"
lahaula wala kuwwata inna lillahi wa inna ilahi rajiun wannan wani irin massefa ne
haka ?
Duk suka juya umma suka gani tsaye cikin matsanancin tashin hankali "Shukura me
maryama tayi miki kike shiga rayuwarta ?amman Kisani allah baya bacci kuma zai saka
mata da kyakkyawan sakayya Ke kuma zaki ga muguwar sakayya dake da uwarki "idanu
kawai yusif ya zuba mata ya kasa cewa komai "kiyi mata na malam yahuza ta hakura ta
bar miki shi yanzu kuma yusif din kike so ?".
"umma gashi nan ki tambayesa bani nace ina sonshi ba shine da kanshi ya canza dani
" yi min shiru munafukar allah daga Ke har uwarki zaku girba abinda kuka shauka ,da
izinin allah sai maryama ta samu wanda yafi yusif komai kausar ta bukaci umma tayi
mata qarin bayani akan mlm yahuza batare da 'bata lokaci ba ta zayyane mata
komai ."
"uhmm lallai maryam kina cikin tashin hankali allah ya fitar dake kawai zan iya
cewa sannan ta cire wayarta daga cikin fost dinta ta kar6i mukullin mota daga
hannun yusif ta fice waje tana neman layin mumy yusif ya cigaba da yin shiru
maryama ta juya jiki a sanyaye ta bar d'akin tana goge hawaye haka zalika umma
kasa cigaba da tsayuwa tayi zuciyarta na tafarfasa ta shige d'akanta tana kuka ."
yaya sadam dake tsaye yana waya ya hango fitowar maryama tana tafiya tana goge
hawaye ya bita da kallo Kamar ya tsaidaita yaji damuwarta sai kuma ya rabu daita da
zumar zai nemeta daga baya ya cigaba da wayar da yake cikin haka kiran umma ya
shigo wayarsa daman what's app call yake ."ya katse kiran domin ya d'auki kiran
ummah kiran ya katse ya lalubo qaramar wayarsa yayi mamakin ganin missed call
dinta dayawa ashe a silet yake "
ya kirata dan baya son ya shiga sai ya gama wayar da yake ,tana d'auka yaji
muryarta can qasa tana kiran sunansa ya amsa yana tambayarta "lafiya ummah naji
muryarki haka ?tace sadam kana ina ne ?ina cikin gida " tace ka shigo yanzu yanzu
"okay! kawai ya fad'a ya soma tafiya cikin sauri ya shigo d'akinta."ya garasa
inda take zaune yana cewa "lafiya umma meke damunki kamar ma kinyi kuka ?."
wani sabon kukan ta fashe masa dashi tana zayyane masa abinda ya faru yace "ikon
allah anya kuwa lafiya ?ina fa lafiya sadam kai ma kasan ba lafiya ba ,"yanzu dai
sai a kira abba aji me zai ce ,ai wad'an nan mutanen abun nasu babu imani ai bazasu
bar iyayensa ma haka ba duk abinda zasuyi dan su juyar da hankularsu zasuyi ."
jikin yaya sadam yayi sanyi ya kasa cigaba da magana "wallahi da ina da inda zan
kai maryama ta cigaba da rayuwarta da nayi dan ina son taji dadi, maryama tasha
wahala a hannun mutanen gidan nan sam sam basa son ganin cigabanta .""Kiyi hakuri
umma komai zai wace babu abinda yafi karfin addua maryama malama ce nasan zatayi
addua ."ban ta'ba shiga tashin hankali irin na yau ba domin har ga allah naso auren
maryama da yusif amman da izinin allah bazasu ci bulus ba duk abinda sukai mata
bazai tafi a banza ba sai allah yayi mana maganinsa ."
bayan fitarsu maryama yusif ya tattara hankalinsa kacokan akan shukura ita kuma
sai faman zuba masa surutu take ,acikin zuciyarsa baya jin dadin hirarta amman kuma
zahiri abun ba haka bane murmushi kawai yake sakar mata yana biye mata ."karfe biyu
daidai suka fito tare da shukura sai ga baba gali ya shigo ."yana ganin yusif tare
da shukura ya washe hakora yana cewa "a'a yusif ashe dai kazo?yusif ya gaishesa ,
baba gali ya amsa yana tmbyrsa "ina ita maryama take dana ganka da shukura ?yusif
ya d'an tsotsa keyarsa yace "yanzu ta wuce tana kuka wai dan nace shukurace
zabina ita zan aura "shukura kuma yusif ?yayi mgnr Kmr bai san komai ba "kwarai
kuwa baba ita zan aura dan haka da zarar na koma gida zan sheidawa dady da mumy
agaugauta azo a nemar min aurenta ta zama mallakina ".
"Ikon Allah haka kuma abun ya kasance ?kai kuwa yusif me yasa zakayi haka?" idan
wani abu tayi maka sai ka sanar ayi mata magana bawai ka canzata da shukura ba ya
fad'a haka a fili amman a bad'ani murna yayi yace abu yayi kyau aikin salama yayi
tasiri daman yasan zata iya fiyye da hakan muddin akan biyan buqatarta ne "babu
laifin da ta min kawai dai bana sonta ne yanzu shukura zan aura "to to shikenan
allah yayi maka albarka Allah yasa ayi damu ."
Yasuf ya amsa da "ameen !ya tura hannunsa cikin aljihu ya ciro bandir din yan
dubu ya mika wa baba gali "ga wannan baba "kai yusif har da wata hidima ai da ka
barshi ni murnar auren shukura ma da zakayi ya wadatar dani sukai sallama da baba
gali ya wucesu yana murna yasuf ya kira kausar tana dauka yace "Ke kina ina ne ?ina
tare da maryama ne " ta bashi amsa da haka "to ni zan wuce idan kin shirya ki fito
mu wuce idan kuma na wuce ne na barki to ?ok minti biyu kawai na baki tare da
maryama suka fito tana kwantar mata da hankali "
kausar kenan karki wani damu dani fa idan da sabo maryama ta rigada ta saba kawai
Kiyi wa dan'uwanki addua in sha allahu nima zan tayaku yi masa addua ki gaishe min
da mum kice ina matukar qaunarta "tana gama fad'ar haka ta juya ta soma taku a
natse kausar ta bita da kallo hawaye na zubo mata ."tunda maryama ta juya hawaye
ke turereniyar zubo mata qirjinta banda bugawa babu abinda yake ta kasa shiga
bangarensu ta wuce bayan d'akinsu tana kuka tun daga kasan zuciyarta " ko kallon
shukura kausar batayi ba ta fice daga gidan cike da tausayin maryama suka wuce ."
"Kinga bari na kira fati na sheida mata ta soma shirinta "ya fad'a yana lalubo
wayarsa "wani shiri kuma gareta ?aunty salma ta tambayesa "ai muktar dinta ke
mutuwar son maryama tun kwanaki dana je gidanta take sheida min nace ta d'an
jinkirta muga me zai faru kinga yanzu dama ta samu",lallai kam dama ta samu daman
shine daidai da aurenta" aunty salma ta fad'a tana kwashewa da wata mahaukaciyar
dariya zaa qare auren dan giya " kai salama baki da dad'i wallahi bakaji dadin da
naji ba ai nan duniya bana qaunar maryama yarinyar kamar aljana ga kyau ga shiga
rai suje su karata da muktar, shi din ma bazata auresa ba sai ya'yana sun bar gidan
nan ."
Cike da murna da farinciki baba gali ya kira aunty fati ya sheida mata komai ai
kuwa tayi murna dan muktar din ma ya dameta kullum bashi da magana sai na maryama
hatta shaye shayen da yake yace zai daina muddin zaa bashi aurenta" da kyar maryama
taja kafafunta ta shigo parlour'nsu tana mai danne damuwarta sai dai kallo daya
zaka mata ka fahimci tana d'an cikin damuwa aunty ta dubeta tace "Kuna fita aunty
fati ta kira waya wai kizo gobe da safe tana son ganinki "to !kawai maryama ta
fad'a ta shige d'akinta dan bata son tayi doguwar hirar da har zai sã mahaifiyarta
ta fahimci wani abu duk da tasan dan dole tasani amman ba da wuri haka ba "safa da
marwa ta shiga yi acikin d'akin tare da cure hannuwanta waje d'aya" tsawon shekaru
aunty salma na bibiyar rayuwarta ."
"laifin me tayi mata ? me ta tare mata? idan wani laifi tayi mata ta fad'a mata ta
nemi yafiyarta ta barta ta huta "? wasu hawaye masu ciwo suka gangaro mata a yanzu
ba kanta kad'ai take tausayawa ba har da mahaifiyar yusif da yaruwarsa dan ita
tsakaninsu dasu aunty salma da baba gali da ya'yanta allah ya isa ne bazata ta'ba
yafe masu ba ,domin cirewa kanta damuwa Kan kujerar zanenta ta nufa ta zauna ta
zaro farar takarda ta ajiye agabanta ta d'auki pencil ta tura cikin bakinta ta fara
tunanin me zata zana ?".
Babu abinda yazo cikin kwakwaluwarta sai fuskar kausar murmushi mai hade da damuwa
ya bayyana akan fuskarta "kausar zan zana domin dai nasan shikenan ni da ita kuma
sai wani ikon allah ."ahankali ta soma bada shape din fuskarta tunda ta zauna bata
tashi ba sallah laasar né kawa ya tashita koda ta idar ma Kan aikinta ta koma ta
cigaba ranar a d'akin maryama ta qarasa niyyinta da misalin karfe bakwai aunty ta
shigo d'akin ta isketa tana gabatar da sallar magrib ."
Ta qarasa gaban table din kayan zanenta nan idanunta yaci karo da hoton kausar har
da kalar kayan data zo dashi yau din nan aunty ta saki murmushin jin dadi tare
da cewa "lallai princess an fad'a soyayya ko da yake yarinyar tana qaunarki ta
qarasa mgnr adaidai lokacin da maryama ta sallame ta mike jiki a sanyaye take
kallon aunty dan wallahi sai take jin kamar bata kyauta mata ba tunda ta tabbatar
kota fada mata kuka kawai zatayi tayi hakuri sannan ta kwantar mata da hankali "
"kinyi shiru kina kallo meke damunki ?girgiza mata kai tayi alamun babu komai
"amman tun bayan tafiyarsu kausar na lura kike cikin damuwa idan wani abu ne ki
sheida min mana ?ajiyar zuciya ta sauke da karfi tace "babu komai "to muje kici
abinci ta kamo hannunta suka fito tana cewa "gsky zanen kausar yayi kyau idan
tagani zataji dadi sosai tare da aunty suka ci abinci bata wani ci abincin kirki ba
tace ta koshi ta sha ruwa ta mike ta shiga bayi ta dauro alwala ta koma d'akinta
sallar ishai ta gabatar byn ta idar ta mike tana nade daddumar sallah ."
Ta ajiye a inda yake ta tsaya shiru acikin d'akinta tana jin wani irin faduwar
gaba ta qarasa ta kakkabe wajen kwanciyarta sannan ta kwanta rigingine ta hade
hannuwanta duka a qirji tana tunanin rayuwa ganin zata damu zuciyarta ne kawai a
banza ta sauke ajiyar zuciya ta soma karanta suratul mulk ahankali bayan ta gama
karantawa ta shafe jikinta da addua ta kwanta, ahankali bacci ya dauketa cikin
baccinta tayi mafarkin umma tace a daura aurenta da yaya sadam har ma ya amince da
auren kiran sallah asuba ne ya tasheta daga mafarkinta ta mike ahankali ta zauna ta
zuro kafafunta kasa tare da dafe goshinsa ."
Tayi shiru tana tunanin mafarkinta addua tayi Allah ya zaba mata abinda yafi zama
alkhairi arayuwarta da kyar ta yunkura ta mike tsaye ta fito ta shiga bayi ta
dauro alwala ta dawo daki tayi sallar asuba duk ta rasa meke mata dadi duk da tasan
mafarki ne amman sai taji abun ya tsaya mata arai cike da raunin zuciyata ta koma
ta kwanta ahankali bacci ya kwasheta aunty ce ta shigo ta tasheta tana cewa "bazaki
gidan aunty fati bane kinfa san halinta babu hakuri sai ta d'auki abun wani iri
azo ana damun rayuwarki “ numfashi ta sauke kawai tare da mikewa zaune tana dafe
goshinta "ko baki jin dadi ne dan tunda kika koma kika kwanta bacci bayan sallahr
asuba to baki da lafiya tayi mika tace "kaina ke d'an min ciwo sai dai kuma .."sai
tayi shiru ta kasa mgn "sai dai kuma me ?"
"Wallahi umma mafarki nayi wai umma tace a daura aurena da yaya sadam kuma har ya
amince ?aunty tayi dariya tana cewa "kai princess wani irin aure kuma bayan ga
maganar yusif ? ta kalli aunty tana jin fad’uwar gaba mai tsanani tace “aunty
ki bar maganar yusif muyi maganar mafarkina gsky banji dadin mafarkin nan ba "
to ai mafarki ne mafi yawon lokuta mafarki baya zama gasky tashi ki sha magani kije
tun karfe tara aunty fati take kiran waya "to ni me zan mata ne ?tayi magana Kmr
zatayi kuka "ni wallahi bana son zuwa koina idan kaga sun nemeka to aikin wahala ne
ga wannan d’an nata mai shegen maseefar kallon tsiya kamar zai cinye mutun ".
"To ko na fad'a mata bakijin dadi bazaki samu damar zuwa ba ta kira kaulat ko
Islam suje idan wani aiki zaa mata sai suyi mata ?maryama tayi shiru can tace
"yanzu rashin zuwan nawa zai zama tashin hankali azo ayita kananan magana "shiyasa
nake son kije idan ma aiki ne kika ga zai miki yawa Kiyi iya wanda zaki iya ki dawo
,nifa ba aikin bane damuwata kamar matsefaffen kallon da yaya muktar yakewa mutane
".
"Babu ruwanki da kallonsa kiyi abinda ya kaiki maza tashi ki tafi dan ki samu ki
dawo da wuri “numfashi ta sauke” gsky aunty bazanje yanzu ba “ya fad’a tana wasa
da yatsun hannunta “sai yaushe zaki?maryama tayi shiru ta kasa mgn “da dai kin
daure tunda kinga baki da lokaci sai asabar da ladidi tsaki maryama taja kana tace
“wallahi ban san dalili ba hakan nan najin fad’uwar gaba kuma dai yau bana son zuwa
koina “aunty ta numfasa tace “to shikenan Kiyi zamanki muje kiyi wanka ki karya ki
sha maganin ciwon kai ta mike ta fito wanka tayi ta shirya ta karya aunty ta bata
magani ta sha tayi kwanciyarta akan kujera .”
Ahankali ta rufe idanunta lokaci d’aya kwakwalu warta ta bud’e tunani ya kusantota
yaki barinta ta huta duk da bata son tayi tunani akan matsalarta amman haka tunani
ya mamayeta , ahankali ta dinga tunanin maganganun yusif ,me yasa zaki damu kanki
maryama already kin rigada kin yarda kin rasa yusif har abada kamata yayi kin haka
rami ki binne komai ya zama tahiri arayuwarki” zanyi haka zan cire komai araina
kuma zan dage da addua har na samu nasara arayuwata ahankali tabi shawarar
zuciyarta ta haka rami mai zurfi aciki zuciyarta ta binne duk wata matsalarta .”
tun daga wannan ranar maryama ta cire tunani da damuwar komai acikin ranta ta toshe
kunnenta duk abinda ke faruwa aciki gidan tana ji kuma tana gani amman ta share
sannna taki bari mahaifiyarta tasan halin da’ake ciki yayinda kullum sai aunty ta
sheida mata sakon kiran aunty fati har sanda sati ta cika aunty ta matsa mata
lallai taje taji dalilin kiran da take mata “Allah aunty bana son zuwa duk sanda
kika fad’a min sakonta gabana faduwa yake “kiyi hakuri ki daure kije bana son tazo
gidan nan “ta fad’a muryarta a raunane ganin yanayin aunty yasa ta riko hannunta
“shikenan aunty zani bari na sauya kaya naje yanzu na dawo .”
“Yauwa princess maza tashi kije Allah ya tsare min Ke “Ameen !ta furta a tsanake ta
fito ahankali take taku har fito titin unguwarsu ta mike zuwa captor road tana
gama garasawa bakin titi ta samu adaidai mai zuwa unguwarsu aunty fati tafiya
kad'an suka yi ta sauka pencilima ta mikawa mai adaidaita kudi ta ta tsallako
hannunta na hagu inda zai shigar daita amawo ."a natse ta shiga gidan kai tsaye
bangaren aunty fati ta nufa bakinta dauke da sallama ta shiga parlour'n inda ta
iske muktar da aunty fati zaune ."
Rike da remut tana qoqarin canza tasha a tare suka kallo kofar tare da amsa sallama
.”
tun daga kasa muktar ya dauki kallon maryama ransa nayi masa dadi wani irin yanayi
ya tsinci kanshi ciki mai wuyar misaltuwa yana jin yadda soyayyarta ke fixgarsa
yayinda maryama ta had'e fuska sosai tmkr taga wani mugun abu ta qarasa ta
tsugunna har kasa ta gaishe da aunty fati ,aunty fati ta amsa mata fuskarta a d'an
sake wanda hakan ya dan bawa maryama mamaki domin tunda suke daita kyara da
hantara tattare da zagi né a tsakaninsu ."
Maryama ta dauke kanta tare da mikewa tsaye ta zauna tana jiran taji dalilin
nemanta da aunty fati take "ke maryama baki ga muktar bane da bazaki iya bud'e ki
gaishesa ba ko shi kike jira ya gaisheki ?
"murmushi ya saki yana cewa"Kinsan ‘yan boko ba dai girman kai ba " wani kallon
takaici maryama tayi masa daga sama har kasa wanda yasa ma kasa cigaba da magana
illa ya zuba mata kwala kwalan idanusnhi masu firgitarwa ."sama da awa daya tana
zaune tana wasa da yatsun hannunta sannan aunty fati ta gyara zama ta kira
sunanta .”
"maryama !
muryarta a raunane ta amsa da “na’am !"na kiraki né domin na samu labari wannan
yaron yusif ya canzaki da shukura yanzu ita zai aura shine muktar yace abashi ke
tunda kowa gudnki yake kinga kenan shi zai taimaka ya aureki sai yanzu na na gane
dashi kika dace ba da sauran mazan da suke zuwa neman aurenki suna guduwa , d'ago
idanunta tayi ta zubawa aunty fati tana kallonta gabanta na dukan tara tara sannan
ta waiga ta kalli inda muktar din yake yana kallonta kamar tsohon maye ."
"Karki dauka ya rasa wacce zai aura ne yasa zai aureki aa tausayi kika bashi domin
yaji babu dadi aransa , yanzu me kika gani zaki auresa ko kuwa zaki tsaya jiran
masu kudin da basamu zakiyi ba ?ta tambayeta tana gyara zamanta tare da tsareta da
idanunta "parlour'n ya dauki shiru na kusan mintuna goma batare da maryama tace uhm
ba bare uhmm illa nazari maganar aunty fati da take da kuma tunani amsar da zata
bata domin dai a halin yanzu wannan shine labari mafi muni daya kusanto rayuwarta
muktar fa ? "ke nake sauraro !?"
Murayarta can kasa ta soma magana a tsanake "a zahirin gasky ni ina da wanda nake
só kuma wanda a shirye yake da aurena idan da hali zaa iya bashi kaulat ko
Islam ,ko kuma sakina amman ni dai gsky ayi min hakuri akwai wanda muka tsaida
magana dashi ."ta tsinci kanta da fad’ar haka ba dan akwai din ba sai dan tsiratar
da rayuwata daga shiga maseefa”waye shi kuma a ina yake ?"maryama tayi shiru ta
kasa magana hankalinta idan yayi dubu tô a tashe yake tayi datasani zuwa gidan
amman tasan ko bata zo wannna maseefar sai ta biyota har gida "
“ke banson iskanci banza bayan nasan babu kowa a kasa shine zaki ce kina da wanda
zaki aura tô ke nake son ya aura ,oh a zuwan kinfi karfin aurensa shine kika
lissafo min daidai shi ko ?"ko d'aya aunty a dai bashi cikinsu shine zai samar da
kwanciyar hankali "bata son wata fitina ta kuma lura kamar fitinar ce take
bibiyarta arayuwarta, ran a aunty fati a matukar bace tace "d'an ma Kinsamu zai
taimaka miki maza tashi ki bani waje na sallameki sannan ki fara shirin aurensa
dan dolenki ki auresa"
Jiki a sanyaye maryama ta mike hankalinta a matukar tashe bazata ki dan shaye
shaye ba dan mahaifinta ma har ya bar duniya yana sha babu komai acikin rayuwarsu
sai matsala ita me kai ta saka rayuwarta cikin ha'ula'i ?kuma tasan idan ba
tsanarta da aunty fati tayi ba babu yadda zaa yi tace ta auri d’anta domin ko ita
take da diya kamarta tayi imani bazata dauketa ta bawa muktar aure ba mutumin da
idan yayi shaye shayensa har kwata yake fadawa haka maryama ta koma gida tana cika
tana batsewa duk ranta a dagule ."
Aunty ce ta fito daga kitchen tace "lafiya kuwa naga har kin dawo yanzu ?hawaye
maryama ta share tace" aunty laifin me nayi da allah ya qaddaroni cikin wannan
dangin ?basa sona basa qaunar cigabanna idan akwai wacce suka tsana a duniya tô
nice suna jin kamr su kasheni wallahi suzo su kasheni su huta da muguwar tsanar da
suka min na rasa me nayi masu arayuwar nan da suka tsane ni."aunty ta zauna kusa
daita jikinta na rawa tace "me ya faru maryama ?"na gaji da wannan rayuwar aunty
fati so take ta kasheni dan Allah ku barta ta kasheni ni yanzu nafi bukatar mutuwa
da rayuwata akan dai ta hadani da muktar .”ta qarasa maganar tana kuka .”
“kwantar da hankalinki kiyi min bayani da kyau ban fahimceki ba ta hadaki da muktar
kamar ya ?"
"Wai ya aureni !"numafashi aunty ta sauke cikin rarrashi tace "haba maryama ki
daina daga hankalinki tunda ga maganar yusif nasan baba gali zai yi mata bayanin
komai maryama ta fashe da wani sabon kuka dan ta ta’bo mata wani ciwo ne data
binne "babu wannna auren bilkisu .”muryar umma suka jiyo daga bakin kofa aunty ta
juya da sauri qirjinta na bugawa fiyye da kaida ummah ta gyada mata kai "haka né
abinda kikaji na fada shima an canza masa tunani har ma dana iyayensa ahankali ta
tako ta dafa kafandan aunty dake kallonta a tsorace cikin tsananin tashin
hankali ."
“Ummah ban gane ba me kike qoqarin fad’a min ?“abinda kika ji shi na fad’a miki
balkisu yusif ya koma wajen shukura “inna lillahi wa inna ilahi rajiun shi kawai
tayita fad’a tana maimatawa nan da nan yanayinta ya sauya ta zauna shiru taji duk
wani kuzari na jikinta yayi kasa tsawon mintuna talatin sannan ta bud’e bakinta da
kyar tace “shima yusif din ya koma wajensu "Ki kwantar da hankalinki babu abinda
allah bazai iya ba kuma in sha allahu allah zai kai maryama matakin da ba'a só
allah yasa hakan shine mafi zama alkhairi arayuwarta ummah ta zauna ta dinga tausar
aunty da maryama tana bata baki har aunty ta saki ranta sai dai hawaye yaki tsayawa
umma ta qara da tabbatar masu duk runtse maryama bazata auri muktar ba “
Maryama ta rungume ummah ajiknta “na gode umma dan allah karki bari a aura min shi
wallahi na hakura da auren ma har abada “bazaki hakura da aure ba akan wani dalili
domin duk dan sunah baya gudun aure yadda akayi aure aka haifeki in sha allahu kema
zakiyi aure har ma da ya’ya da jikoki ummah ta fad’a tana shafa bayanta suna cikin
wannan hali habib ya shigo aunty tayi sauri ta goge hawayenta tana daidaita
natsuwarta ganinsu haka ya fahimci akwai damuwa dan haka da hanzari ya qaraso ya
riko hannun aunty cikin nashi yana tmbyarta “lafiya na ganku haka ?babu komai
aunty ta basu amsa “ya babu komai ?ya kalli ummah fuskasa dauke da tambaya .”
“Me yasa zaku boye masa yana da kyau ya sani ko babu komai zai taya yaruwarsa addua
nan ummah ta fad’a masa komai “shiyasa nace ta hakura da batun wani aure ,bafa
dole sai mutun yayi aure zai shiga aljanna ba “kul kar na sake jin ka fad’a haka
zatayi aure musa aranmu dukkaninsu babu mijin aurenta acikinsu mu godewa allah da
yasa har tana masu sonta baa barta haka ba babu abinda zai zo da bazai wuce ba wata
sai labari ahankali ummah ta shawo kansu suka shiga wata hirar ,”
******
Kwanakin dari kenan da auren su maryam wanda yayi daidai da kwanakin sabain da
tarewar maryam a gidan ata acikin lokacin babu wani abu da yayi sauki acikin zaman
auren mai dadi a tsakanin maryam da ata duk abinda maryam zatayi domin ta cire
kiyayyarta a zuciyar ata tayi amman ko a jikinsa domin dai yaki sakewa
daita ."shiyasa damuwarta ta qaru zamansu babu wani shaawa dan ata yaki rungumar
marym sai ma kyma da nuna ko in kula ."
Sosai motocin jami'an tsaro guda hud'u dake gaba da bayan motar da ata ke zaune
aciki ke falfala gudu akan titi kamar suna gasar tsare baka jin komai sai jiniya
mai tsanani domin a kauce abasu hanya sosai motocin dake Kan titi suka dinga komawa
gefe suna basu hanya wanda adaidai wannan lokacin maryam na can tsaye acikin
kitchen tana kwashe abinci tana zubawa a kuloli ."
Bayan ta gama ta jerasu akan table duk abinda take cikin hanzari take yi kar oga
ata ya shigo bata gama ba duk da ba abincinta yake ci ba sai maakatan gidan ke
ciki kuma idan tayi lattin ganawa yaci ubanta ,qarar jiniya taji alamar dawowarsa
dan zaro ido tayi tare da daga kai ta kalli agogon dake manne a parlour'n karfe
takwas da minti ashirin cikin sauri ta haye sama ta shiga dakinta wanda ya sha
gyara gwanin burgewa. ta cire kayan jikinta ta daura towel sannan ta nufi bayi ."
Cikin jin isa ya turo kofar parlour'n tare da shigowa babu kowa a parlour'n jakar
dake hannunsa ya ajiye akan kujera da wayoyinsa sannan ya nufi sama yayinda zuwa
wannan lokacin maryam ta fito tana tsaye a gaban madubi tana shafa lip's dinta byn
ta gama ta tsaya tana tunanin kayan da zata saka can zuciyarta ta bata umarnin ta
saka marasa nauyi tun sanda ta tare a gidan tsawon sati tara kenan atamfa da
dogayen riguna take sakawa ta sanya kaya marasa nauyi masu yanayi dana bacci yana
tsaye a dakin yaji an turo kofa bai juyo ba ."
cike da faraa ta tsaya a gabansa tana cewa "oyoyo baby sannu da zuwa "wani kallo
yayi mata a dage yana sake tamke fuska tmkr yaga wani mugun abu cike da sanyin jiki
ta kallesa ganin yadda yayi mata kallon kaskanci "leave my side “ya fad'a yana
nuna mata kofar fita yayi maganr cikin bacin rai bata wani damu ba tunda idan da
sabo ta saba da halinsa "ga abinci "bana ci kina tunanin zanci abinncikin ne ko
me ?”kayi hakuri please kaci ko kadan ne na sha wahala sosai kafin na gama bai ce
mata komai ba ya juya ya bar parlour'n.”
Wani bakinciki ta dinga ji acikin ranta "oh ni maryam me zan yiwa wannan bawa naka
na canzashi?gani bata da abinda zatayi yasa taja kafafunta ta koma dakinta ."ta
fad'a kan katifa wasu hawayen bakinciki na zuraro mata nasihar sister ce ta fado
mata "maryam kinsan yadda akayi auren nan hakuri zakiyi da Adam idan kina son kici
riba ,auren da kayi dan soyayya ma hakuri kake yi bare wanda iyaye suka had'a zaman
aure dan hakuri ,gidan aure makaranta ce mai girma ba zaka gane hakan ba sai ka
shiga, akwai darussa kala dabam dabam sai kin zauna acikinsa zaki fahimta."wasu
hawaye suka qara tsiyayo mata yanzu haka zata qare rayuwarta cikin hakuri "tunda
kina son shi dole zakiyi hakuri dashi ."zuciyarta ta bata amsa da hakan .”
Mmn sudais
💗💗💗💗💗💗
MAR'ADAMS
💖💖💖💖
💗💗💗💗💗💗
*AYSHA A BAGUDO*
WATTPAD @HAUESH
AREWABOOKS USERNAME
AYSHAABAGUDO
bismillahirrahmanirrahim
Wannan littafin na kudi ne mai bukatar karantashi byn na kammalashi zai biya
1000 ta wannan account number din 1438775094 Aishat abdullahi access idan an tura
sai a turawa wannan 09136918331 alert domin tabbatar da an tura domin sauraron
littafaina a tuntubi chaneel dina (Hausa bakwai ) a YouTube.
Page 10
Ahankali ta yunkura ta mike tsaye kamar wata mahaukaciya ta soma zariya acikin
d'akin tana sambatu "yanzu me zan masa na kawowa kaina kwanciya hankalin acikin
gidan nan ?tayiwa kanta tambayar tana mai qara shiga tashin hankali "babu abinda
zaki iyawa wannan mai shegen taurin kan da zaki burgesa ,komai zaki masa a banza
ne a wajensa "tayi shiru na minti biyar tana tunani kafin ahankali ta qarasa inda
wayarta take ajiye, ta kai hannu ta d'auka tana tunanin kiran d'aya daga cikin
yan'uwansa wani tunani tayi sai kuma ta fasa kiran domin dai tasan kowa a cikinsu
abu d'aya yake fad'a mata shine hakuri hakuri !! kuma yanzu da zata kirasu hakurin
dai zasu bata ."
"bana son wannan hakurin gashi kuma hakurin dole zanyi tausayin kanta ya
kamata tana mai jin kamar duk ita ta jefa rayuwarta cikin matsala a dalilin
zunzuruntun qaunar da take masa da taki auren tun farko data zauna da rayuwarta
lafiya ."yanzu me zanyi ?ta sake tambayar kanta tana cure hannuwanta waje d'aya
"idan da hali ki sake zuwa wajensa ki kwantar da kai tunda kece a kasansa "da sauri
ta girgiza kai alamun shawarar bata yi mata ba "wallahi da zan cire kulafucinsa
nayi hakuri na bar rayuwarshi da komai zai zo min da sauki "ta sake bawa kanta
wannan shawara "amman ina bazata iya ba dan tana da kulafucinsa tana mutuwar son
shi kamar yadda yake mugun kinta murmushin takaici maryam tayi tana cewa "Allah
kasani ina wa adam wani irin so mai girma, allah ka nuna min ranar da zai soni
kamar yadda nake sonshi dan zan só faruwar haka."
"burina a koda yaushe mu kasance a matsayin miji da mata kamar sauran ma'aurata dan
haka maryam karki gaji da halin mijinki kije ga mijinki baki san abinda allah zai
yi ba wata rana sai labari ga kuma alqawarin da kika d'aukarwa mahaifiyarsa kuma
mami ta yarda dake shiyasa ma ta baki amanarsa
da wannan shawar ta fito daga cikin d'akin cike da sanyi jiki ."bayansa ta hango
yana taka step ahankali yayinda hannuwansa duka ke cikin aljihun wandonsa kunnensa
manne iPod ."kai tsaye bayansa tabi yo tana kallon yadda yake taka step yana wani
rangaji." alamun taku yaji abayansa ya waiwaya ya kalleta sannan ya juya ya
cigaba da taku ,yana gama sauka ya samu waje ya zauna akan d'aya daga cikin
kujerun parlour'n ya d'aura kafarsa d'aya akan d'aya yana cigaba da wayarsa "karka
qara min damuwa ammar akan wanda nake ciki, ina ruwa da wata yarinya ta gama bautar
qasanta mana ina ruwana ."
"idan zanyi aure dole sai ita zan aura ?" kaga dan allah malam mu bar maganar nan
ta isheni haka
yes of course ni na furta zan qara aure amman ba lallai sai wannan yarinyar
ba .""Inna lillahi wa inna ilaihi rajiun maryam ta furta a kasan zuciyarta qirjinta
na dukan uku uku sakamakon jin maganarsa ,ta tsaya nesa kad'an dashi tana kallon
yadda yake motsa bakinsa tare da sauraron maganarsa .shiru ATA yayi can yace
"ammar ba lallai tayi min ba ka dai san halina ba duk abinda yayiwa mutane yake
min ba ina da test "maryam ta runtse idanunta qirjinta ya cigaba da beating very
fast amman kuma ta d'an ji sausauci jin abinda ya fad'a dan haka ta taka ta shige
kitchen tana mamakin yaya ammar ."
"In da wani ne ya fad'a mata zai kasance cikin masu bawa mijinta goyon bayan ya
qara aure zata musa sai gashi taji da kunnenta sosai taji ciwon abun aranta ta
had'o masa shayi irin wanda tasan yana so ta qaraso inda yake zaune jikinta a
sanyaye ta mika "ga shayi !".ya d'ago tsumammun idanunshi ya zuba mata batare daya
kar'ba ba ya cigaba da wayarsa "kasan Allah da nayi niyyar naga yarinyar nan ko sau
d'aya ne amman jin yadda kake wani zuzutata naji bazan iya ganinta ba ." wani
naunayen ajiyar zuciya maryam ta sauke najin dadin abinda ya fad'a dadinta dashi
akwai ra'ayi kuma ra'ayinsa nayi mata dan ba duk abinda mutane ke so yake masa ba
"ga shayi ka sha " ta sake furtawa a raunane kwayar idanunsa ya sake d'agowa ya
zuba mata wanda yasa ta sake shiga tashin hankali "nasan kana da d'abiar shan
shayi a duk lokacin da ka dawo daga aiki ".
wani dogon tsaki yaja yana d'auke kwayar idanunshi akanta "abinda ya kamata tayi
tun a farko shine dan shirme irin nata ya dawo karshe" ya sake jan tsaki ."
Daga can bangaren ammar kuwa cewa yayi "haba ATA kaji da madam mana ,dan allah
kayi qoqarin kabi mahaifiyarka shine kawai zai samar maka kwanciyar hankali da
natsuwa "na sani ammar ina iyakacin qoqarina the girl always doing nonsense wai
abinda ya kamata ayi da farko dan hauka irin nata shine ya dawo karshe "haka zaka
d'aure kayi hakuri kuma da zaka d'aure ka .."enough ammar ! ya fad'a tare da amsar
qaramin cup din hanunta ya ajiye akan table ya mike ya nufi kofar fita ya barta
a wajen tsaye bayanshi tabi da kallo tana furta "oh ni maryam naga takaina."
Haka taja kafafunta ta koma d'aki duk yadda taso kin kiran kowa acikin yan'wansa
amman zuciyarta ta gaza hakurin haka sai data kira nana hauwa'u "tana dauka ta
fashe mata da kuka tana cewa "sister me na tsarewa yaya ammar da yake son yaya
Adam ya qara aure?" "aure kuma ?wallahi da kunnena naji suna hirar inda allah ya
taimakeni yayanki yana da raayi yaki yarda da maganarsa "to ki godewa allah da bai
yi raayin qarawa ba dan koni bazan so akawo miki wata matar gidanki a halin da'ake
ciki ba ciwo zaa qara miki akan ciwo "."Sister wai taya zaayi na shawo Kan
yayanki ne ?ina ji ajikina hakurina ya kusan qarewa acikin gidan nan "na sani
sister kina hakuri sosai da yaya Adam amman ki qara akan wanda kike yi sannan karki
gaji dashi ki cigaba da bashi duk wata kulawa da mata ke bawa mijinta idan babu
mutuwa akwai rabuwa wata rana zai ga amfaniniki sai abu na gaba " ki dage da addua
abinda na fahimci kina sakaci dashi kenan sister wallahi idan kika rike allah zai
isar miki ,dogaro da allah shi ke yaye wa mutun damuwa sosai nana hauwa'u ta ajiye
damuwarta ta dinga kwantar mata da hankali ."
******
Maryama na zaune a d'akinta tana nike kayanta yayinda kunneta Ke makale da hearpis
tana waya da ammar "tayi murmushi ai kam da zamu samu zamu ji dadi sosai dan ance
samun aiki a Z&A akwai matukar wahala amman tunda kana nan nasan bani da wata
damuwa ,Allah kuwa zuwa lokacin ma mun qare nysc dinmu allah dai yasa muna da rabo
, daga can bangaren ammar yace "wai waye wanda yayi muku hanyar samun nysc dinku a
Z&A ?"ta sake fad'ad'a fuskarta da murmushi sannan tace "wani tsohon saurayina
"kai dan allah?wallahi kuwa malamin islamiyyarmu ne mutumin kirki ai ina ganin da
allah ya qaddaro aure a tsakaninmu da yanzu ana daf da bikinmu amman yanzu babu
wannan maganar ".me ya faru da babu maganar "long story ne sir "tana rufe bakinta
tajiyo muryar aunty fati tana cewa "ina maryama !"
mikewa aunty tayi da sauri tare da kallonta ganin ta shigo mata babu ko sallama
kamar wata zararriya " ina maryama take ?" jiki a sanyaye maryama ta kai dubanta
ga kofar d'akin ,sannan a tsanake cigaba da waya da oga ammar har ta qarasa ninke
riga kwaya d'ayan dake hannunta ta had'a da sauran kayayyakin da take nikewa
muryarta a sanyaye tayi masa sallama ta mike ta ajiye kayan a ma'ajiyarsu sannan
ta fito parlour'n tana jin mummunar fad'uwar gaba wanda adaidai wannan lokacin
sautin muryar aunty ya shiga kunnenta "maryama ta .."tana d'akinta "yauwa hakan
ma yayi kyau dana sameta a gida ,ta sheida miki yadda mukayi daita ?".
numfashi Aunty ta sauke tace "akan me kenan?Karya kike mara mutunci kice baki san
komai ba dan nayi imani babu abinda take boye miki idan kuma baki sani ba bari ni
na fad'a miki da kaina akan aurenta da muktar ne nasan kina sane da zamansa karki
ce min a'a kiga tashin hankali yanzu ."
nan da nan zuciyar maryama ta jagule taji kamar ta d'ora hannu aka tasa ihu ko taji
saukin zafin da zuciyarta take mata ."aunty tayi shiru tana kallon Aunty fati a
tsanake kafin ahankali tace " idan wannnan maganr ne ta fad'a min "amman .."ya isa
!tunda ta fad'a miki ya kuke ciki ?akan me kenan aunty fati ? wani kallon raini
aunty fati tayiwa Aunty sannan tace "kan batun saka ranar aurensu mana dan na
matsu na matsu naga maryama a gidan muktar".aunty muktar yaron kirki ne ,sannan
bashi da wata makusa amamn maryama ta nuna min bata da ra'ayinsa mafi alkhairi
abar maganar allah ya had'a kowa da rabonsa na alkhairin ".Karya kike mara mutunci
ga dukkanin alamun na fahimci
daga gareki zaa samu matsala " ta fad'a tana zare mata ido "ai wannan matar bata
da kai bata san mai sonta ba yaro ya had'u yana da aikinsa mai kyau ,ita yartaki
ba yar kowan kowa ba dilalin kashi zaki ce bata da ra'ayinshi "inji cewar aunty
hasana data shigo ."
aunty ta kalleta wani iri ,cikin jin haushi tace "idan dai haka ne me yasa ke
bazaki bashi d'aya daga cikin ya'yanki ba ?"ki bashi Islam ko kaulat mana ."
"Oh haka ma zaki ce ?kwarai kuwa na fad'a tunda auren zumunci kuke só had'awa kunga
zumunci zai fi maku dad'i ,ina dalili zaku saka min yarinya gaba dame zata ji duk
mutanen kirki kun kuresu zaku wani had'ata da muktar ".amman yanzu kika gama cewa
muktar yaron kirki ne ?ai bazan ta'ba aibanta d'an wani ba tunda inda nawa " oh
kice dai kina gudun yarki ta auri dan shashaye?aunty hassana tayi mata tmbyr tana
murmushin mugunta "aunty tayi shiru kawai tana kallonta zuciyarta na tafarfasa."
"ke yanzu har kin guji mai hali irin nashi ?"kinga ni bana son kananan magana aure
ne dai maryama bazata auri muktar ba tun da bata son shi "wallahi baki isa ba
karewa ubanta ma menene ."?inji cewar aunty fati hankalin maryama yayi matukar
tashi jikinta rawa tace "aunty fati please mana dan allah duk abun bai kai haka ba
bana son ana tashin mahaifina ta wannan han.."bata qarasa ba ta qara bud'e murya
"wai dan giya ne da shaye shaye bakya son ana fad'a kome ?"maryama ta sunkuyar da
kanta kasa tarasa meke mata dadi "wannan wani irin dangi ne gareta?" hakika aunty
bata masu adalci ba data zabar masu uba acikin wannan zuri'ar ."
Cikin wani zare ido da maseefa aunty fati tace "kaf dangin ubansa babu mai shaye
shaye bare giya sai acikin dagina kinga kuwa ubanki ya gada, aunty ta runtse
idanunta tana jin wani irin zafi acikin ranta "wallahi aunty fati wannan yarinyar
muguwar yar bakinciki ce kuma ba kowa take wa bakinciki ba sai wannan tsinanniyar
uwaratata takewa domin ubanki kwalbar giya biyu aka bashi ta ishesa ya miqa ki ga
duk uban dayazo neman aurenki ." aunty ta sake runtse idanunta tana datasani
maganarta data tasan magangun da zasu gasa mata kenan da babu abinda zai kaita yin
magna ."aunty fati ta kalli maryama a wulaqance tace "idan kika kuskura kika kawo
matsalar akan auren nan ni da kaina zan kawo wanda zai tura miki ciki kuyi auren
dole dashi".
Maryama tayi raurau da idanu "aunty hassana tace "ni kuma wallahi kinji na rantse
muddin kika ki auren muktar sai dai ku tattara ku bar gidan nan amman aurensa
babu fashi sai anyisa kuma acikin satin nan . "to ni yanzu idan ma auren ma
za'ayi me muka ajiye da zaayi acikin satin nan ?uwarki zaki yiwa wannan tmbyr bani
ba aure ne dai sai kin auresa kuma ni babu gudumuwar da zan bayar mara kunyar
banza zan fad'awa dangin ubansa suzo a saka rana aiki banza kawai suna gama
fad'ar haka suka juya suka fice daga parlour'n."shiru maryama tayi cikin tsnanin
zullumi da juyayin maganr yayar mahaifinta " wallahi duk aunty ce tajawo masu
wannan wulakanci da tozarcin "ta tsani dangin mahaifinta ta tsanin akidarsu "why
aunty me yasa kika cutar damu haka ?me yasa kika auri mahaifinmu tayi maganr a
fili ."
"shiru aunty tayi ta kasa cewa komai yayinda hawaye suka cika kwarnin idanunta
aunty kuka maryama kuka "abinda mahaifiyarsu tafi karfi yau shi yafi karfinta
adalilin biyewa son zuciyarta "
yayar mahaifinta zata aurar daita ga lalataccen d'anta.",ina ma aunty zata koma
zuwa ga dinginta ina ma zatai hakan ko sau daya né, tasan yan'
uwanta zasu yafe mata su karbeta kuma bazasu ta'ba barin taji kunya ba zasu tsaya
mata suyi mata komai hawayen da take kokarin boye né suka samu nasarar zubawa tayi
saurin saka hannunta ta goge tana kokarin maida sauran dake kokarin zubowa ."
A tsakar gidan su Aunty fati sukai cikibis da ummah aunty fati tace "yauwa ga aunty
nan ma daman wajenki zan shiga yanzu "ina jinki me zaki shigo yi? tmbyr ya dan
bawa aunty mamaki amman dai ta danne tace "muje daga ciki mu zauna muyi mgnr ai
kamar zaifi ?A'a muyi anan "nan aunty fati ta zayyane mata komai tana dasa aya
umma tace "a'a fati babu mai kamar maryama yayi shaawar bawa muktar aure "meye
illarsa aunty ?tayi mgnr tana zaro mata ido itama ummah cikin zaro ido tace "illoli
dayawa, na rasa meke damunku ?ta qarasa mgnr da karfi tare da yarfar da hannu ."
"Aikuwa tunda har muktar yace yana sonta ko sama da kasa zasu hade sai anyi auren
sai duk abinda zai faru ya faru "sama da kasa bazasu hade ba haka zalika babu
abinda zai faru aure ne dai bazaa yi shi muddin kika ga anyi wannan auren to
maryama ce da kanta taji tana so amman wallahi babu wanda ya isa yayi mata auren
dole hayaniyarsu ce ta fito da aunty salma da aunty wani irin asirtaccen murmushi
aunty salma tayi tare da karkacewa tana kallonsu .""Bata fada miki akwai wanda suke
maganar aure dashi ba ?"ta fad'a amman wannan maganar karya ce babu kowa saboda duk
abinda ke faruwa acikin gidan ina sane dashi, dan haka karya ne babu wanda yake
sonta idan kuma har akwai ya fito mugansa "
tana gama fad'ar haka umma ta juya zuwa bangaren ta, duk suka bi bayanta da kallo".
Bayn kamar minti biyu ummah ta fito hannuta rike dana sadam a d'an rikice aunty
salma ta maida kallonta sosai garesu "ba kowa bane illa sadam shine wanda suke
soyayya da maryama."aunty ta tsura ma ummah ido idanunta na kawo ruwan
hawaye."aunty salma zaro idanu tayi tana girgiza kanta bata so saka bakinta cikin
maganarsu ba amman ya zama dole tace wani abu dan haka tace "umma yaushe suka
fara so.."bata bari ta qarasa ba tace " bakiyi tsammanin faruwar hakan ba ko ? to
haka rayuwa take salma sadam shine wanda zai auri maryama da izinin allah "ba
aunty da Aunty salma da sauran mutanen dake tsaye ba shi kanshi sadam ya shiga
rudani da tashin hankalin jin abinda mahaifiyarsa ta fad'a "taya ummansa zata masa
haka ?" yaushe suka yi haka daita ."?yayi wa kanshi tambayar ajere yana had'a
zufa .
"Gsky wannan had'in yanzu ne ,wallahi a yanzu aka shiryasa ta kalli sadam "da
gaske kuna soyayya da maryama ?kasa amsawa yayi dan gbdy ya gama daburcewa
kwakwaluwarsa ta toshe kansa ya cunkusheya rasa me zai fad'a mata yayi dan duk
abinda aunty salma ta fad'a haka ne a yanzu aka shirya komai kai shi sai da suka
fito yasan dalilin da yasa mahaifiyarsa ta fito dashi "kun gani ba ai bazai iya
cewa komai ba dan wannan had'in shirin yanzu ne sam sam babu maganar a kasa "Ke
salma bana son makirci da shashanci banza d'anki ko d'ana ?"
"d'anki ne amman wannan had'in yan.." babu ruwanki had'in yanzu ko akwai maganar
a kasa naki ido ne idan kuma kikace zaki bi dare kibi dubu akan maganar nan zaki
mutu ."
"Kai sadam kalleni nan ya d'ago kwayar idanunshi da kyar ya kalli Aunty fati
"karka boye min komai sadam kasan matsayinka a wajena ina sonka fiyye da ya'yan
cikina nan kuma jikin ummah ya fara yin sanyi ,"nan ji duk abinda mahaifiyarka ta
fad'a amman ina son naji gskyar magana daga bakinka ,da gaske ne sadam kana son
auren maryama"? ya runtse idanunshi gam yana jin wani sabon tashin hankali na
ta'ba zuciyarsa da kwalkwaluwarsa sai data sake tmbyrsa sannan ya bude idanunshi ya
kalli mahaifiyarsa dake tsaye cikin tashin hankali tana dubansa ,a yanayin yadda
take kallonsa bazai iya kunyatata a bayyanan nasi ba".
"kai nake sauraro sadam wallahi da gaske zan iya bar maka maryama na nema muktar
wata matukar kana sonta " jikin ummah ya sake yin dan tasan akwai soyayya a
tsakaninsu ,"kace wani abu "da gaske ne aunty ?ya fad'a cikin wata irin murya mai
cike da tsananin tashin hankali "aunty salma ta zaro ido tana cewa "kai wallahi
aunty fati karya ne , babu wata soyayya a tsananinsu "kinga salma magana ta qare
sadam nawa ne koda karya ne tunda ya amsa da bakinsa bani da ja domin soyayyar sa
dabam ce acikin zuciyata "shiru aunty salma tayi dan ta dade dasanin son da take wa
mahaifinsa ne ya juye kanshi .dariyar mugunta aunty salma tayi ta juya ta koma
bangarenta abun bai mata dadi ba dan bata son maryama ta riga ya'yanta aure amman
zata yi iya yinta taga ya'yanta sun rigata aure ita da take da suruki kamar yusuf
me zai dameta da wani sadam gashi ga dukkanin alamun dole akayi wa sadam din zai
aureta."
aunty fati tace" sadam d'ana ina maka fatan alkhairi suna gama fadar haka suka bar
wajen zuwa bangaren aunty hassana suna shiga aunty hassana tace "yanzu ke kin yarda
da wannan tsarin"?nasan karya ne dole akayi masa amman tunda ta zabi haka ki zuba
ido Kiyi kallon abinda zai biyo baya da wannan maganar suka kawo karshen zance suka
shiga wata ."maryama na zaune cikin halin tashin hankali umma ta shigo parlour'n
tana ganin ummah ta mike ta rungumeta tana kuka "ummah me nayiwa su aunty
fati ?"me zanyi su soni ?wallahi banason muktar ki taimakeni ummah kar a d'aura
auren nan laifin me nayi masu ummah ?ina ta bawa zuciyata hakurin rayuwa dasu,
amman kullum burinsu suga bayana ."ta karashe mgnr tana kuka."
"ki qara hakuri da kowa da komai akan wanda kikeyi maryama rayuwarki qaddara ce
zuwa yanzu ya kamata ace kin saba da qaddararki karta dinga baki tsoro "wallahi
ummah jarabawa bata bani tsoro saboda na maida alamarina zuwa ga allah "yauwa
abinda nake son ji kenan kowa ce rayuwata cike take da lullubali da qaddara kuma
sai allah yana sonka yake jarabaka domin yaga karfin imaninka idan kuma akace haka
dole sai ka shirya, jarabawa ko ta class ce yaya kike jinta bare jarabawa daga
allah? fatana allah ya bamu ikon cinye jarabawa ."ta fad'a tana shafa bayanta tana
jin fad'uwar gaba ."tana Tunanin yadda zata shigo mata da zance sadam taji sautin
muryar maryama tana cewa "ni dai ummah kisa abar maganar muktar ke kad'ai ce nake
da yakinin zata min wannan gatan ."
ummah ta zareta ajikinta ta kamo fuskar maryama da hannuwanta duka tana kallon
fuskarta tace "babu wani muktar da zaki aura na yanke shawarar zaki auri yayanki
sadam, maryama ta zaro idanu tana duban umma cike da matsanamcin mamaki "yaya
sadam kuma ummah ?"a matukar rikice ummah tace "Eh ko baki sonshi."ahankali ta
shiga girgiza mata kai domin dai tasan ko giya ta sha bazata iya furta hakan
gareta ba ,bare kuma tasan
tayi hakan ne dan yantota daga hannunsu aunty fati ."ai ko bata son yaya sadam ta
karba kuma ta amince sai dai fargaban yadda yaya sadam din zai karbeta muryarta a
raunane tace "ummah kina tunanin yaya sadam din zai amince ?
"ya ma amince maryama "kuka ta fashe dashi mai karfi "shikenan mafarkinta ya
tabbata"ya allah kabani kwarin gwiwar cinye jarabawar da duk zaka min
"alhamdulillah alhamdulillah shine kawai abinda umma taji yana fitowa daga bakinta
"allah ne abun godiya maryama babu abinda zai biyo bayan wannan auren sai alkhari,
karshen wahalarki yazo ta fad'a tana sake rungumeta ajikinta " aunty ta qaraso ta
zauna kasa kusa da kafafuwan ummah "ban san da wace irin kalmar godiya zanyi amfani
dashi wajen gode miki ba amman zan zabi wannan kalmar allah yay miki sakamakon da
gidan aljana "na gode na gode !!sai kuka ya kufce mata daga maryama har Aunty suka
saka ummah tsakiya suna mata kuka ."
koda habib ya dawo yaji hukuncin ummah abun yayi masa dadi sosai dan gara sadam
sau million akan wani muktar fatan alkhairi yayi yana tmbyr aunty maryama .""Tana
d'aki !" ta fad'a atakaice tana sauke numfashi a daki ya iske maryama kwance akan
katifa tayi kuka har idanunta sun kunbura tana tunanin yadda qaddarori suka yita
zuwa mata daki daki akan aurenta a she tana tare da mijinta bata sani ba "ya zauna
kusa daita yana kiran sunanta "heartbeat ".ta sauke numfashi tana dubansa da
kunburarrun idanunta "bakiji dadin hukuncinsu umma ba ko ?ta langwabar da kanta
kawai batare da tace komai ba "heartbeat idan da wani aka baki zance Aa amman yaya
sadam dabam ne karki ce aa bazaki samu kamarsa ba "
"kai ma ka amince dashi ?sosai kuwa dan mutumin kirki ne kuma yana duk wasu
quality's da zaa so shi ta sakar masa murmushi wanda ya bayyana wushiriyarta sama
da kasa tana gyara kwanciyarta
ta jingina bayanta da abun gado ta janyo pillow ta rungume tana jin wani nauyi a
qirjinta"bana jin son yaya sadam ko kad'an acikin raina amman bani option zan rayu
dashi muddin rai "yayi shiru kawai yana kallonta cike da tausayawa dan bai san me
zai sake cewa ba ,domin farincikinta farincikinsa ne haka zalika damuwarta
damuwarsa ne zai sake magana ta katsesa ta hanyar cewa "karka ce komai after dad
tunda har ka amince daman kai kawai nake jira naji raayinka tana gama fadar haka
ta sauko "muje parlour'n muci abinci ta riko hannunsa binta kawai yake jikinsa a
sanyaye ."
*******
Tun bayan da ummah ta furta maganar aureta da yaya sadam habib bai zauna ba ya
shiga buga bugan neman aiki karfi daga wannan kamfani zuwa wannan duk kuma saboda
ita da mahaifiyarsu ne daman da karatu da kwallon kafa ya dogara dan yana d'an
samu a buga kwallon kafa amman ba wani samu sosai ba dan kudin ba wani kudin azo
agani bane amman babu laifi yana toshe masu wata kafar dan hatta mashin din da
yake dashi yanzu da dan kudin da yake samu ya siya ."matslar dai ba koda yaushe
ake samu ba sai a dauki alokaci baa daukesa ba shiyasa yaga gara ya had'a da aikin
kamfani ranar da'akayi dashi za'a d'aukesa a ranar ya samu damar buga kwallon
kafa zuwa ogun state kenan ya samu promotion daga jahar lagos zuwa wata jahar .
"
Adaidai wannan lokacin maryama ta kammala bautar kasa tare da kawarta subai'a babu
inda take zuwa tana zaune a gida abinda tafi tsana kenan zaman gida sam a yanzu
bata son zaman gidansu gashi dai tana samun kulawa gata sangarta só qauna soyayya
tarairaya daga mahaifiyarta haka ma habib sai ummah wacce sanadiyyar sadam yasa
yanzu motsin kad'an tana bibiyar me take ciki komai ta samu ita zata bawa amman
zaman gidan baya mata dadi saboda zuciyarta ta rasa abu d'aya wato mai d'ebewa
zuciyarta kewa dan gabad'aya tunda akayi maganar aurensu da yaya sadam ta rasa gane
kanta dashi karon kashi sadam din sai ma taga ya rage bata kulawar daya saba bata
ada can baya ."
****
A hankali ATA ya shiga office dinsa babban ma'akacinsa mai tantance ma'aikata na
kamfaninsa Z&A na biye dashi abaya ,ya zauna a mazauninsa yana kallonsa batare da
yace komai ba "good morning sir ? ya gaishesa cike da girmamawa "uhm ! yayi gyara
murya kawai alamun yana jinsa yana maida hankalinsa Kan system "uhm amm sir ko
zan iya magana yanzu "uhm ! ya fad'a a takaice "adadin mutane kimanin dubu dari uku
ne suke bukatar aiki a karkahainmu ,sir wannan shekara ko zaa hada da masu
degree ? Ko kuma daga master zuwa sama ne zaa dauka ."?" ka ma da kake maganar daga
wani mataki ka fara aiki ?"sorry sir ya fad'a a tsorace "duk mutumin da aka
tabbatar takurdunsa sunyi kyau ayi masa interview idan ya cancata a d'aukesa ."
"sai abu na gaba kada a Kuskure akarba' kwabo duk wani mutun domin samar masa
aiki a duba cancanta yana gama magana ya dauke idanunshi akan system zuwa wani
bangare dabam yana cewa fatan" ka fahimta "yes sir sai kuma game da compaing dake
kasar togo sun kira suna bukatar almustapha "me zance masu?" kai komai bazakayi da
tunanin kanka ba sai ka tmby ? "am sorry sir"ya juya da sauri ya bar office din ."
Ranar monday tun asuba da maryama ta tashi tayi sallah bata koma ta kwanta ba ta
soma shirin zuwa wajen interview duk abinda tasan zaa buqata ta had'asu waje d'aya
acikin jakarta hatta kayan da zata saka ta fito dashi sannan ta shiga wanka karfe
bakwa daidai ta gama shirinta ta fito parlour'n ta hango aunty tsaye a kitchen ta
qarasa ta rungumeta ta baya "good morning mumy "ta kai hannunta ta shafa gefen
fuskarta morning my princess har kin fito ?yes !ta fad'a tana duba agogon dake
daure da tsintsiyar hannunta "muje ki karya kafin ki fita "aunty da kin bar
breakfast din nan Kiyi min addua kawai" bakince akwai wanda zai tsaya maku ba ?
aunty ta fad'a tana fitowa daga kitchen maryama ta biyo bayanta tana cewa "akwai
but bashi zai mana interview ba amman dai ina ji ajikina zamu samu nida subai'a "to
Allah yasa a dace "Ameen !ta fad'a a lokacin da wayarta ta d'auki qara ta ciro ta
duba tana cewa "aunty subai'a ce ."
Tayi sauri ta d'auka tana "cewa hello suby okay gani nan fitowa mgnr second biyu
sukai ta katse kiran tana cewa "aunty ni zan wuce subai'a har ta fito "kema yanzu
zaki wuce ta kai cup din tea bakinta ta kurbi kad'an ta kai bread bakinta a haka ta
shanye cup din tea tace "na gode sosai Allah bar min Ke mamana ina sonki ta kai
mata kiss a kumatunta ta nufi kofar fita da sauri tana cewa aunty "bye ye sai na
dawo "bye ta d'aga mata hannu tana kallon bayanta kai tsaye bangaren ummah ta shiga
da sallamarta yaya sadam ta gani zaune Jiki a sanyaye ta gaishesa "yaya sadam ina
kwana?"ya dago idanunshi ya kalleta sannan ya amsa da" lafiya !"
ta nufi hanyar dakin ummah sai ga umma ta fito"maryama har kin fito ?na fito umma
to Allah yasa a dace tace Ameen " ina zata ?ya tambaya batare daya kallesu ba
"interview ! ummah ta bashi amsa da haka "aiki zatayi kenan ?" to meye amfanin
karatunta idan batayi aiki ba ya dan yi shiru can yace "nifa gsky bana da wannan
raayin yana gama fad'ar haka ya mike yana cewa " ni na wuce tsaya ka sauke min ita
"bai ce komai ba ya fita maryama tabishi da kallon mamaki dan bata ta'ba tunanin
zata samu matsala dashi akan aiki ba ganin shima dan boko ne ita kam akan aikinta
zata iya hakura da auren dan
sam aure baya ranta a yanzu mutuntakan umma ne ta duba da tausayin mahaifiyarta
bawai son aure take ba ,ganin yadda yanayinta ya canza yasa ummah tace "karki
wani damu zakiyi aikinki "amman ummah alamunsa ya nuna baya so "gsky ne sadam bai
son amman zai yarda kinji wahalar karatunki bazai tafi a banza ba ,yana ma daga
cikin abinda yasa ban bari an daura maku aure ba nafi son ki shiga da aikinki".
kanta kawai ta gyada mata "maza bishi ya saukeki ."
Mmn sudais
💗💗💗💗💗💗
MAR'ADAMS
💖💖💖💖
💗💗💗💗💗💗
*AYSHA A BAGUDO*
WATTPAD @HAUESH
AREWABOOKS USERNAME
AYSHAABAGUDO
bismillahirrahmanirrahim
Wannan littafin na kudi ne mai bukatar karantashi byn na kammalashi zai biya 1000
ta wannan account number din 1438775094 Aishat abdullahi access idan an tura sai a
turawa wannan 09136918331 alert domin tabbatar da an tura domin sauraron littafaina
a tuntubi chaneel dina (Hausa bakwai ) a YouTube.
Page 11
Jiki a sanyaye maryama take taku gabad’aya kuzarin jikinta yayi kasa ,”aiki zatayi
kenan nifa bana ra’ayi ? maganarsa ta shiga yawo acikin kwakwaluwa da zuciyarta ,
tana tafiya tana tunanin maganarsa , a qalla yaya sadam ya kusan minti shabiyar
zaune acikin motarsa yana jiranta , ya dubi agogo a karo kusan na shabiyar yaja
qaramin tsaki a lokacin da wayarsa ta soma ringing ya kai hannu ya d’auka ya duba
yaga sunan ummanshi ke yawo akan screen din wayar. numfashi ya sauke sannan ya
d’auka cike da girmamawa “sadam !”ta kira sunansa ya amsa da “na’am “ina son kaso
maryama tun daga qasan zuciyarka ,sannan zaka iya zama madadi ko ka cike gurbin
abubuwan da maryama ta rasa a rayuwarta na shekaru baya.”
“ina jin ciwon da qunci abubuwan da sukai ta faruwa daita amman ina fatan kai ne
zaka wanke min wannan quncin ya dawo farinciki na har abada “naji ummah in sha
Allahu zan yi iyakar qoqarin na kawo miki wannan farinciki “dan allah sadam ka son
maryama “ yayi murmushi kawai yana sosai keyarsa yayinda idanunshi ke kallon hanyar
da maryama zata bullo .”ahankali yaga tahowarta a natse take yin komai nata kamar
bata son taka kasa koma yace tausayin kasar take “nayi magana ba kace komai ba ?
“duk abinda ummanah take so ya zama dole naso “ya fad’a yana sake tsaida idanunshi
akanta “
“na gode maka allah yayiwa rayuwarka albarka yadda kayi min biyayya kai ma allah ya
baka ya’yan da zasu maka biyayya “Ameen ya hayyu ya qayyum “
qirjin maryama na tsananin fad’uwa ta qaraso bakin titin unguwarsu har ta tsaya
jikin motarsa bai iya d’auke kwayar idanunshi akanta ba ,jikinta a matukar sanyaye
ta bud’e gaban motar yaya sadam ta shiga yayinda zuciyarta Ke bugawa da karfin
gaske ta zauna tare da rafka tagumi cikin rashin sanin madafa madadin taji yaja
motar sun wuce sai taji yayi sallama ya ajiye wayar hannunsa ya kunna music yana
bin wakar ahankali .”
Kanta taji ya sara mata ganin bashi da niyyar tafiya ga lokaci na wucewa ya sata
kallonsa kamar mai shirin yin kuka tace “yaya sadam !”tamkar ba magana take yi masa
ba haka ya cigaba da bin wakarsa babu alamun damuwa ko nadama a fuskarsa hannu ta
mika hakan yasa sukayi daf da juna wanda da zata qara matsar da hannunta zata iya
yin masauki a jikinsa, a natse ta kashe wakar ta sake kallonsa tace “i am talking
to you yaya sadam “.“me kike son na yi ?ya fad’a a sanyaye “kayi hakuri dan allah
idan wani laifi nayi maka lokacin na tafiya gashi naga baka da niyyar tafiya wannan
aikin shine rayuwata bana son rasashi .”
ya d’an matsota yana cewa “ni dana zauna jiranki tsawon mintuna shabiyar bani da
aikin yi ne ?”ko bani da wajen zuwa ne?” ko kuma aikina bashi da mahimanci
ne ?”yayi mata tambayar ajere yana sake kunna wakarsa .”sake kashe wakar tayi ta
kallesa a marairaice sannan tace “am sorry duk maganarka ce ta rikitani har yasa
kuzarina yayi kasa wallahi da kyar na kawo kaina bakin titin nan shiru yayi yana
kallonta fuskarsa a d’aure tmkr wanda bai ta’ba dariya ba “ka d’an saki fuska nan
dan fushi baya maka kyau “ ta furta cikin wani irin salo da sautin murya mai sanyi
huci bakinta da numfashinta duka na dukan wuyansa wanda sanadiyyar hakan ya
haddasawa tsigar jikinsa mikewa ya kuma qara bugawar da zuciyarsa take .”
ajiyar zuciya ya sauke yana jin wani iri a ilahirin jikinsa “saboda nace bana
ra’ayin aiki ?”wallahi duk shi ya sanyayyar min da jiki da dai zaka amince zanyi
farinciki da hakan “bai sake cewa uffan ba ya kunna motar ya soma tafiya kamar wasu
kurame haka suka cigaba da tafiya .”qarfe tara saura wasu mintuna suka isa bakin
tafkeken get din Z&A yaja ya tsaya batare daya kashe motar ba cikin siririyar
muryarta tace “yaya sadam na gode sosai allah ya kai lafiya “ ta fad’a tana qoqarin
fitowa daga cikin motar adaidai lokacin da hancin motar ammar ta sanyo kai “Ameen
ki kula da kanki “I will !ta fad’a tana sakar masa murmushi duk da bawani sonshi
take ji ba amman taji dadi sosai kuma zata iya rayuwa dashi muddin rai .ammar yana
kallo sukayi bankwana “
da sanyi jiki ta shige cikin sadam ya cigaba da tsayuwa yana kallon bayanta har
ta ,bace masa sannan ya lumshe idanunshi lokaci d’aya kuma ya bud’e “oh my goodness
god “ya furta a can qasan zuciyarsa ta yadda idan ba bakinsa ka kalla da kyau ba
bazaka fahimci abinda yace ba .”murmushi ya kwace masa a saman fuska wa zai same
kamar maryam yace bai so ?”sai dai wani dalili na dabam ya haifar da hakan ,sam ya
manta a inda yake sai da yaji mutane ana masa hon a she fa motoci ya tare duk suna
tsaye suna jiransa murmushi yayi sannan ya kama gabansa yayinda maryama tuni ta
shige cikin ma’aikata bata ma san lokacin da yaya sadam ya wuce ba .”
tana shiga sauran abokan aikinta suka qaraso suna mata magana suna shirin shiga
inda zaa wa masu neman aiki interview amman ita maryama hankalinta bai garesu yana
kan neman inda subia ta shige ,tunda tasan a tun lokacin da sukai waya daita ya
cancanci ace tana wajen koma anyi mata interview an gama .”taja ta tsaya tana cewa”
kuje zanzo na sameku daga baya “.ta bud’e jakarta ta ciro qaramar wayarta ta shiga
neman layin subai’a ,ganin an bud’ewa ammar mota ya fito yana nufota yasa ta sauke
wayar daga kunnenta tare da kashewa gabad’aya “ya iso har inda take tsaye yana gama
qarasowa wayar hannunta ya amsa ya rike ta kallesa tana murmushi sannan tace “barka
da safiya ?
“Barka !
“me ya tsayar dake da sai yanzu kika qaraso ?ya tmbyeta yana duba screen din
wayarta sunan wacce ya gani ne yasa ya mika mata wayar “wallahi wanda zan aura ne
ya ‘bata min lokaci “ tayi maganar cikin salon jan hankalin duk wanda yake tare
daita, ammar kasa magana yayi kafin daga baya da kyar cikin fad’a yace “wato har
zaki iya fad’a min wanda zaki aura ne ya ‘bata miki lokaci ? tayi shiru tana wasa
da yatsun hannunta dan batayi tsamanin zai ji haushi maganarta ba ganin babu komai
a tsakaninsu sai mutunci da girmamawa “amman ki sani wannan ba mutuncinki bane ko
nace zaki zubda mutuncin family d’inku ne .”
“Ai shima family dinmu ne da mahaifinsa da mahaifina the same mother the same
father wani irin kallo yayi mata mai cike da tunhuma,itama kallonsa tayi numfashi
ya fesar yace “shi kuma mijin da nayi miki fa ya zanyi dashi ?tayi murmushi tana
cewa “allah sir ka daina min haka wallahi kana d’aga min hankali ,kai kanka kasan
kafi karfina bare wanda kake fad’a wannan sai dai na qara dagewa da aikin ibada
wata killa na samu irinsa a aljanna yayi murmushi yace muje “.
Ahankali suke takawa yayinda mutane suke gaishesa wasu ya amsa wasu kuma ya d’aga
masu hannu “kefa ko anyi miki interview ko ba’ayi miki ba dole zaki yi aiki damu
“sure tunda inda kai ba ,ai sunanki na can tuntuni kinga office dinki can ta kalli
inda ya nuna mata “woow gsky naji dadi sosai “kinga ga office dinki ga na mijinki
in sha allahu “tayi murmushi kawai tana cewa “subai’a fa ?nifa nafi son naji kana
magana kana had’awa daita zai yi magana kenan, wayarsa ta d’auki qara sauti ,ya
soma qoqarin d’auka bata tsaya jiransa ba ta cigaba da tafiya dan daman da kyar
take iya jirawa dashi da sauri ta qarasa tana shiga aka kira sunanta .”
Sai da tayi addu’a sannan ta shiga office din ta gaishe da mutumin data gani zaune
mai suna wale yana duba wasu fararen takardu,ya d’ago ya kalleta a natse sannan ya
sake kiran sunanta “maryama hussein !”tace yes sir ! sai daya bata izinin zama
sannan ta zauna a natse tana wasa da yatsun hannunta wanda ya zame mata jiki ,ya
d’an saci kallonta yana mamakin matsayin da aka bata ,domin kujera ne da suka dade
suna neman wanda zai maye gurbinsa , sai dai lokacin daya fara auno mata tambayoyi
akan kasuwanci da kuma matsayin da zata taka ya ajiye mamakinsa a gefe domin kuwa
ta cancanci ta hau matsayin kuma irinta mai kamfanin ya dade yana nema .”
bata wani jima ba ta fito har da award aka bata sakamakon aikin da tayi dasu
daman kuma sun ajiye ne domin rana irin ta yau “congratulations sauran abokan
aikinta suka shiga yi mata tana amsa masu da “thank you tare da rungumar mata daga
cikinsu duk wannan farinciki da take ciki bai kawo mata natsuwa ba saboda rashin
ganin subai’a da batayi ba ta ciro wayarta ta soma nemanta tana tafiya ahankali har
ta fito haraban ma’aikatan subai’a ta d’auka tana kuka hankalin maryama ya sake
tashi sosai ciki tsanani tashin hankali tace “subai’a kina ne na shigo har an
d’aukeni aiki banganki ba ? tana shirin sake yin magana ta hangota a bayan wata
bishi tana qoqarin fitowa .”
Da sauri maryama ta qaraso ta tsaya tana qare mata kallo tsab hawayenta yasa
zuciyar maryama tsananin bugawa “me Ke faru dake subai’a ?kukan me kike yi ?muryata
cike da kuka tace “na rasa aikin nan ,da yawa wad’an da suka d’auka alfarma ne
yanzu bansan ta yaya zamu cigaba da rayuwa ba daman da allah da aikin nan na dogara
gashi ban samu ba muddin sai da wata alfarma zan samu aikin nasan har abada bazan
samu ba .”ta riko hannunta maryama tana cigaba da kuka ta soma rokonta “dan girman
allah maryama karki barni haka ki taimakeni ki bar min aikin nan nasan zaki samu
wanda yafishi gabad’aya idanun subai’a sun rufe har sai da maryama ta kira sunanta
sannan ta tsaigaita kukanta “ki kwantar da hankalinki ki bar kuka nan haka” amman
ta yaya babu sunanki bayan ..”sai kuma tayi shiru ta janyo hannuta zuwa ciki “zo
muje .”
maryama na gaba subai’a na bayanta har suka qarasa bakin office din james ta nemi
izinin ganinsa aka bata damar shiga ,wanda ta samu wannan damar ne saboda ammar
domin yadda yake mata yasa mutane dayawa d’aukar sonta yake maryama ta shiga tare
da subai’a dake kuka har lokacin .”bayan ta gaishesa cike da ladabi tace “dan allah
ina neman wata alfarma agareka ya kalleta dan shima ta burgesa yadda ma’akatan suka
dinga yaba kwazonta tun kafin tazo kuma zuwanta wale ya sake tabbatar masa iri
irinsu basu dayawa a duniya dan tunda ya sheida masa ya kira mai gidansa seun ya
sheida masa muryarta a matukar sanyaye ta soma magana kamar zatayi kuka “dan allah
sir wannan yaruwa tawa nake son ta maye gurbina ma’ana acire sunana a saka
nata .”ya kalleta a tsanake domin yasan yadda ake shan wahalar neman aiki yanzu da
kudinka ma baka samu “.
“Saboda allah zakayi karka tsaya tunanin komai ni inda aikin da zanyi domin tallafa
rayuwata for now ,ita kuma bata dashi da wannan aiki Kawai ta dogara ga mahaifinta
ya rasu ko da yake nima marainiya ce amman dai tafini bukatan aikin nan saboda tana
da kanne dayawa da mahaifiya mara lafiya dake karkashin kulawarta itace komai nasu
“da wannan maganar ta karyar da zuciyar James ya kalli subai’a cike da tausayawa
yace “sorry oo !”zan iya miki wannan alfarma sai dai bazata maye gurbin kujerarki
ba “tayi shiru tana tunani abinda zata ce kafin tayi magana ya cigaba” kujerarki ke
kad’ai ake bukata sakamakon oga ammar sunanki ya bayar gashi yanzu kinzo da wata
magana “karka ji komai a saka a duk inda zaa sakata nidai burina ta samu aikin ni
zuwa gaba in sha allahu zanyi aiki daku amman a yanzu burina subai’a ta samu
aiki .”
Mr James ya saka sunan Subai’a ya cire sunan maryama “ suka fito zuwa gindin wata
bishiya maryama na cewa subai’a “congratulations na tayaki murna kawata yanzu kin
zama cikakkiyar maaikaciya ta fad’a tana murmushi subai’a ta rungumeta cike da
farinciki “na gode na gode maryama allah ya saka miki da mafifincinsa nayi imani
zaki samu aikin da yafi wannan da kika bar min tana kuka tana gode mata” haba subai
ki daina kuka kawai dan na sadaukar miki da aikina kike wannan godiya da kuka
haka ?” ta goge mata hawaye tana cewa ni na zan bar ki na wuce gida nasan akwai
abubuwan da zaku yi kafin ku wuce ina miki fatan alkhairi allah yasa ki fara aiki a
saa ta juya a hankali ta soma taku subai’a tabi bayanta da kallo hakika bazata
ta’ba manta alkhairinta gareta ba .”
Da wuri maryama ta dawo gida koda ta shigo kai tsaye bangaren ummah ta shiga ta
sheida mata amman ta isketa a dakinta tana bacci dan haka ta fito ta shiga
bangarensu ta zauna a parlour’n tana sauke numfashi tare da dafe goshinta ko
cikakken minti biyar batayi ba ,Aunty ta fito da mamaki take kallonta “lafiya naga
har kin dawo ?lafiya aunty nan ta zayyane mata komai sosai ran aunty ya baci kamar
ta rufeta da duka musaman data lura ko ajikin maryama dan babu alamun damuwa atare
daita “me yasa zaki bada aikinki bayan Kinsan muma muna fama da kanmu ? “aunty kiyi
hakuri kin sani ni zan iya cigaba da aikin zanena kafin na samun wani aikin ita
fa ?bata da wani sanar hannu da zatayi kuma rokona tayita tana kuka saboda bata da
hanyar da zata kula da kannenta da mahaifiyarta fatana allah yasa ya zame min
alkhairi ta qarasa mgnr muryarta na rawa alamun kuka “.
Aunty ta samu waje ta zauna kusa da ita tana cewa “shikenan allah yasa ki samu wani
wanda yafi shi muryarta a raunane tace “Ameen ko da ummah da habib suka ji suma
abun bai masu dadi ba amman babu yadda suka iya tunda ta bayar sai hakuri da fatan
alkhairi .”washegari tana zaune a parlour’n su tare da aunty kiran ammar ya shigo
ta tashi ta koma dakinta sannan ta d’auka tana dauka ya rufeta da fad’a “kin kyauta
saboda shakuwa da qaunar da nake miki yasa na tsaya lallai Ke zaa bawa wannan
matsayin saboda ina son shakuwa mai karfi ta shiga tsakaninki da Adam amman kika
zuba min qasa a ido ,ina ganin idan shakuwa ta shiga tsakaninki dashi zai taimaka
kwarai wajen janyo hankalin gareki shine kika bar wata .”
sanyayyen murmushi tayi kamar tana gabansa “to amman ai na fad’a maka akwai wanda
zan aura .”“wanda zaki aura din banza ,wallahi ko ba dan Adam ba nan gaba kadan
zaki fara gano illar abinda kika aikatawa kanki ,kuma duk abinda ya faru babu
ruwana ke kar ma ki sake nemana ko da yake ma tafiya zan yi gobe kuma zan dauki
lokaci ban dawo kasar ba “allah ya kaika lafiya “Ameen amman babu ruwana dake
wallahi ko a hanya kika gani kika min magana sai bata miki rai “a ina ma zan ganka
dole sai ma’aikata kuma babu abinda zai kaini tunda bana aiki a karkashinku tayi
mgnr aranta alokacin ya katse kiran .”
ranar yau din jinsa maryama tayi dabam wani irin damuwa ta tsinci kanta ciki ita
kanta tana jin mai yasa tayi abinda tayi kowa ya kalli fuskarta zai ga canji laifin
kanta ta gani me yasa ma ta bar wayarta a kunne bata kashe ba da wata killa bai
qara mata damuwa akan wanda take ciki ba tayi shiru yayinda a cikin zuciyarta
takewa kanta fatan alkhairi .”awanni sukai ta zuwa suna wucewa amman maryama bata
daina jin damuwa dan haka fito ta nufi bangaren ummah tana shiga ta isketa tana
tsinke ewedu “sannu da aiki ummah!Yauwa maryama ya zaman gida ?gamu dai yanzu zamu
fara ummah tayi murmushi “zaki samu wani aiki nan kusa ta zauna kusa daita ta
d’auki gayen ewedu ta fara tsinkewa “gobe nan ma zan fara nema ssi ku tayani da
addua,in sha allahu alkhairi zamu ji .”
Ahankali sukai ta hirarsu daga nan umma ta sako mata maganar sadam “maryama kin dai
san komai daga Ke har sadam baku kawowa zuciyarku zaku zama abu d’aya ba sai gashi
allah yayi ikonsa dan haka ki saki jikinki dashi karki tsaya sai yajaki ajiki ai
kin fahimceni ina ganin nan da wata biyu masu zuwa zaa daura maku aure” maryama
tayi shiru ba dan bazata aikata abinda take butaka ba bata da option dole zata
jashi ajiki tuni ma ta sadaukar da rayuwarta garesa ko ba dan shi umma ta wuce
komai gareta nan ta garasa yininta tare sukai komai a kitchen har karfe shida da
rabi ta buga ta fito parlour’n inda ta iske yaya sadam zaune shiru a falon da
alamun yayi zurfi cikin tunani maryama ta qaraso idanunta akanshi kallon minti goma
tayi masa sannan tace “meke damunka yaya sadam kayi shiru haka ? “
Ya sauke numfashi tare da sauke kwayar idanunshi akanta a natse ta samu waje ta
zauna kusa dashi tana cewa “ya wurin aikin naka ? babu komai aiki kuma alhamd wasu
abubuwa né suka sha min kai amman in sha allahu zan shawo kan komai na gode sosai
da kulawarki “no karka damu yaya sadam , sukai shiru na kusan minti goma sannan ya
kira sunanta “.marayam! ta tsura masa ido kawai tana kallonsa “ya batun aikin da
kika fita nema ?”naje na samu amman na bawar qawata subai’a aikin “why ?!ya
tamvayeta yana dubanta. “saboda tafini bukata aikin itace komai na gidansu gashi
mamanta bata da lafiya ga rashin mahaifi da sukai yaya sadam wallahi ina tausaya
mata “gsky abar tausayi ce kin kyauta sosai da kika bar mata .”
taso yayi mata fatan samun wani aikin amman taji yayi mata shiru “yaya sadam a
fahimtata naga baka son auren mace mai aiki ya kalleta kawai “nasan kana da
dalilinka kin haka amman ka yarda dani zan kare maka mutuncin aurenka wallahi bazan
maka wasa da aurenka ba ,nima fa nasan ciwon kaina bayan hakinka dake kaina akwai
hakin allah dan allah ka bari nayi ayyukana “zan duba !ya fad’a atakaice tare da
mikewa tsaye “na gode sosai “.
******
Cikin sauri ata ya shigo office dinsa mataimakinsa na biye dashi ya zauna a
mazauninsa yana kallonsa batare da yace komai ba “good morning sir “morning! Ya
amsa atakaice yana maida hankalinsa Kan system “uhm amma sir ko zan iya magana
yanzu “uhm ! Ya fad’a a takaice daman
akan yarinyar nan dana baka labari tana da kwarewa sosai akan lissafi duk wani
lissafi na kamfanina nan tasan kansa ta hada komai daake bukata takardunta sunyi
kyau sosai kuma anyi mata interview komai nata daidai ,amman abun mamaki tace bata
bukatar aiki damu wai a dauki wata amadadinta .”ATA ya dago kyawawan idanunshi a
natse yana furta “ what ? She rejected our job duk yadda aiki yake wahala a kasar
nan? .”
Ya kankantar da idanunshi tare da yin shiru yana tunanin abinda zai sa wani mutun
biladam mai jini ajiki yayi rejecting din aiki a maakatarshi ya hade rai sosai cike
da takaici a fuskarsa sannan Ya koma ya zauna sosai akan kujera yana jujjuyawa a
hankali yana cigaba da tunanin Ya furzar da iska mai zafi yana tsotsa keyarsa “ina
ganin wannnan yarinyar tana da damuwa a brain dinta ,kai kwata kwata ma
dakikiya ,for god sake ni me ye damuwata yanzu ? me yasa zaka kawo min wannan
banzar maganr ?meye damuwata daita dan taki amsar aiki inda ga mutane can bila
adadin suna nema ?ya qarasa mgnr cike da jin haushi yana ja tsaki “ noncess !Ya
furta yana dungule hannunsa .
“Am very sorry sir daman dan ka bukaci mai ilimin lissafi ne shiyasa har muka
bukaceta amman dai tace zuwa nan gaba zata iya kasancewa damu “I don’t care kawai
make sure bata samu aiki a koina ba a duk fadin garin nan, kai har karshen
rayuwarta duk inda kuma aka dauketa aiki let me know .”
“an gama sir …ring din wayarsa yasa seun yayi shiru tare da daukar wayar ya mika
masa cike da girmamawa Ya amsa ya manna a kunnensa tare da mikewa Ya qarasa jikin
window office dinsa yana kallon haraban ma’aikatan yana amsa wayar ransa duk abace
“daga can bangaren nana hauwa’u ta gaishesa “ ina kwana yaya ?”lafiya ya kike auta?
“lafiya ! daman na kira na fad’a maka zan biya na d’auki maryam muje gaishe da mami
“okay ! ya fad’a tare da katse kiran .”ya cigaba tsayuwa yana jin zafi aransa .”
Nana hauwa’u tayi shiru kafin daga baya ta mike tsaye ta kammala shirinta ta fito
ta shiga mota kai tsaye hanyar gidansa ta dauka daman sunyi waya da maryam din
itace ma tace ta kirasa ta fad’a masa a bakin kofar gidan ta tsaya ta kirata bayan
ta fito ta shiga gaban mota suka dauki hanya suna tafiya suna hira maryam tace
“sister ya zamanku da yaya hisham kuwa naji kwana biyu bakya magana akanshi “na
gaji sister na kawo ido na zuba masu duk wanda yayi da kyau zai gani ina sauke duk
abinda ya rataya a wuyansa na zamantakewa aure hakinsa ne ban tauye masa ba idan ya
nema zan bashi ,idan bai nema ba huta roro zama haka maryam ta sauke numfashi tace
“duk da haka dai ai naki da sauki tunda yana cin abincinki “eh to da sauki gsky
Kinsan daman shi ba mai daukar abu da zafi bane kamar yaya bane .
“Ni dai gsky babu wani sauki a zamanmu dashi muddin yana gida bani da kwanciyar
hankali sausaucin da nake samu dukkaninmu kuna kokari dani ,kuma na gode sosai da
kulawarku ‘yanuwa allah ya bar zumunci amman ina jin tsoron ranar da zai hadu da
wacce yake so yace zai qara aure ina rokon allah kafin zuwan ranar allah ya kasheni
dan nasan bakincikin da zan qunsa yafi wanda nake qunsa yanzu “ babu wannna ranar
for now mami fa tace muddin yana son qara aure sai ya kwantar miki da hankali shi
kuma Kinsan halinsa da wahala ya kwantar da kai “kina ganin har yarinyar mafarkinsa
in da zasu had’u mami bazata yarda ya aureta ba ?”yadda idan mutun ya mutu baya
dawowa haka labarin wannan mafarkin nasa yake.”
Maryam tayi shiru tana tunani nana hauwa’u ta dafata tana cewa “don’t worry siater
komai zai daidaita kinji “ naji amman rayuwarta abar tausayi ce baya son ganina
baya son ko jin muryata idan ya ganni ko yaji muryata Kmr ya matu mgn kadan nayi
yace na cika surutu ni yanzu dan allah ina da magana ?tai mata tmby tana dubanta
girgiza mata kai nana hauwa’u tayi “wallahi bancin na bar gidansa mami zata shiga
damuwa wallahi dana gudu,” ki gudu kije ina? kar ma ki soma muna tare babu inda
zaki maryam ta girgiza kai tana jin zafi aranta sister wallahi baki san abinda nake
hadiya bane .”idan kika tafi babu ni babu ke har abada zumunci mayi a lahira maryam
tayi saurin goge hawyenn daya soma bin gefen idonta tare da cewa “ nima wasa nake
babu inda zani muna tare mutu ka raba tafiyar mintuna ta kawosu bakin get din
estate dinsu sukai hon masu tsaron get suka bud’e masu suka shigo sukai parking .”
atare suka nufi gidan mami suka kunna kai ciki tare da sallama a parlour’n suka
iske Aunty shahida ,da Aunty khadija ,har ma da Aunty zabiba zaune sai mami da
mamaki maryam ta bude baki cikin tsananin farinciki da gudunta ta kwaso bata zube
gaban kowa ba sai a gaban aunty shahida ta ruqunqumeta tsam ajikinta tana cewa
“wayyo allah babbar yaya naji dadinku daman sister kinsan suna nan ne ?ko daya
yadda kika gansu yanzu nima haka nagansu ta zame jikinta ta durkusa gabanta “ina
yini babbar yaya aunty shahida ta shafa fuskarta “ya kike maryam “lafiya lau .” ta
isa gaban mami ta durkusa ta gaisheta cike da farinciki da girmamawa cike da kulawa
mami ta amsa tana kallonta a tsanake “ dan tun washegarin tarewarta sai yau ta sake
daura kwayar idanuna akanta “wallahi Allah mami jiya kasa bacci nayi saboda zan zo
na ganki sai kuma gashi naga yan’uwana gabad’aya .”allah sarki maryam nima nayi
kewarku sosai .”
Tayi murmushi mami ta cigaba da kallonta “tunda sister ta fad’a min zamu zo tare
nake murna sai naga gari kaman da gangan yaqi wayewa don kada inxo na ganki” to
gaki ga maminki kinganta cikin koshin lafiya “wallahi gashi na ganki kuma naji dadi
sosai ai ni ina ganin ma na dawo kenan bazan koma wannan gidan mai kama da
makabarta ba sai na kwana biyu “.nana hauwa’u ta zungurinta kan tayi shiru amma ina
maryam bata fuskantarta ba mami ta miqe tsam ta basu waje dan tasan dole zasu
tautauna a tsakaninsu .” mami na fita nana hauwa’u ta zubawa maryam duka a cinya
wallahi ki rufa min asiri baki isa ki kwana a gidan nan ba yadda na dauko ki haka
zan maidake gidanki “.
wajen da nana hauwa’u ta daketa take sosawa tana dariya tace “wallahi babu inda
zani “kamar zaki iya bayan kina tsananin sonshi ? “kai nana hauwa’u ban da sharri
wa ya fad’a miki son 'ya'yan take?inji zabiba ta fad’a tana murmushi nana hauwa’u
tace “ai ni tuni na san da wannan ga tanan kuma idan ta isa ta karyata ,sister ban
da sharri fa auren daaka samu na amince da kyar zaki zo kice ina son shi nana
hauwa’u ta sake qara mata wani dukan maryam tace “babu komai wallahi koda da zafi
ni banji zafin ba, dan bakya laifi ko kin kashe dan masu gida wani dan masu
gida ?”yayanki ! dariya suka bushe da ita gabad’aya su Aunty zabiba tace "Kefa
sabon iskancin mai lasisi kikaje kika koyo a gidan yaya “barta dole tayi iskanci da
alamun taga gadon baccinsa shima yaya naga ya canza kwana biyu da alamun ya
angwance inji cewar zabiba “.
wallahi ku daina fad’ar haka kar sautsayi ya shigo dashi mu shiga uku “ku dai shiga
uku amman mu ai yayensa ne dole ya daga mana kafa dariya maryam ta saki har da tafa
hannu “wannan kanin naku ai mami kawai yake d’agawa kafa hira suke sosai yayinda
maakatan gidan suka cika gabansu da kayan marmarin da abinci da abun sha aunty
khadija ta dubi auta “da alamun kin samu lafiya “alhamdulillah Aunty khadija
rayuwar aure is not easy amman haka zamuyita hakuri har allah ya kawo mana sauki
Ameen “ kefa maryam yaya zaman naku da uban shegu ?uhm ta numfashi “to da sauki
zance amman ni matsalata mai girma ce kuma ban san ranar da zan fita ciki ba” ta
qarasa maganar kamar zatayi kuka .”
Gabad’aya suka zuba mata ido cike da tausayawa “ita fa siater matsalarta mai sauki
ce ba kamar ni ba da ko muryata baya son ji baya cin abincina kona girka sai dai
masu gadin gida suci bani da kwanciyar hankali matukar yana gida , sister kuwa
nuzla ce matsalarta amman ni zanyi maganinta “ki rabu daita huce haushi take akan
hisham shi kuma rashin ganewa ne idan ba haka ba ko sauraranta ma yayi “inji cewar
aunty khadija “allah ya kyauta daga nan Suka cigaba da hirar matsalolin rayuwa wani
suyi dariya wani suyi jimami cikin haka aunty abida ta shigo daman ita tana yawon
shigowa ko dan taji halin da ata yake ciki a wajen mami diyana da rukkaya suka
shigo su kuma nana hauwa’u ce ta kirasu kusan duk yammatan gidan suka shigo aka
sake bud’e habin hira banda nuzla har karfe shida ta buga suna tare ana hira .”
Ahankali motocin ata suka shigo haraban estate dinsu sakamakon kiransa da mami tayi
suna gama daidaita tsayuwar motocin ya fito kamar ance ya kalli kofar gidan baba
babba hisham ya gani tsaye tare da nuzla ya zuba mata ido kamar zai mata
numfashi .”shiru yayi yana mamakin karfin halinsa ko bai ji kunyar kowa ba ai ya
duba mami bare tsakaninsa dashi” ahankali nuzla ta kalli inda yake kallo d’aya tayi
masa ta d’auke idanunta tana jin farinciki dan yanzu bata jinsa aranta haka ne ma
yasa take son dandanawa jininsa wahala kuma har ga allah tana son ta auri hisham
yanzu dan hishsm miji ne bancin yana kawo mata uzurinsa akan mahaifiyarsa da yanzu
ta dade da kasamcewa a gidansa .”
daya daga cikin masu tsaron bakin get din ya dagawa hannu ya taho da sauri ya tsaya
a gabansa cike da girmamawa “daman hisham na zuwa wajen nuzla ne ?Eh !ranka ya dade
kusan kullum yana zuwa shiru yayi kafin daga bisani yace “okay zaka iya tafiya “ya
juya ya koma bakin aikinsa shi kuma ya nufi kofar gidan mami yana kiran mb ,yayan
mami suna shirin mikewa su kama gabansu har nana hauwa’u dan ita maryam mami tace
ta zauna ATA zai zo sai su wuce tare suka ga mutun ya shigo kamar wanda aka jehoshi
yana huci “gabad’aya suka mike tsaye suna kallonsa .”bai ce masu komai ba ya samu
waje ya zauna akan kujera yayinda kannensa suka gaishesa amman yaki magana ya soma
waya da yaya Ibrahim .”
Hankalin mami ya tashi ta qaraso garesa ta dafa shi tana tambayarsa “lafiya adamcy
naga ka shigo wani iri ?still shiru yayi yaki magana ganin haka aunty
shahida ,aunty khadija da zabiba har da nana hauwa’u sukai ma mami sallama zasu
wuce muryarsa a kausashe ya soma magana cikin tsananin fushi “auta kar naga kin
fita daga gidan nan kin dawo gida kenan .”gabad’aya suka dawo cikin tsananin tashin
hankali suna dubansa “akan wani dalili kenan adamcy ?aunty shahida ta tambayesa
“yayi shiru yana huci tamkar zaki “ka barta ta koma gidanta tayi zaman aure tunda
suna zaune lafiya da mijinta “inji wa yace miki haka ?ya fad’a a zafafe yana fesar
da hucin numfashi “zaku iya wucewa amman ita babu inda zata mami kam shiru tayi ta
kasa magana “mami kice wani abu mana kinyi shiru kina kallonsa “aunty khadija ta
fad’a tana dubanta “zaku iya wucewa zanyi magana dashi “
Suna shirin fita mb ya shigo dole tasa suka tsaya kallo d’aya yayiwa abokinsa ya
fahimci akwai damuwa ya qaraso kusa dashi ya zauna yana cewa “yaakayi friend ! kace
nazo yanzu yana qoqarin bud’e bakinsa yaya Ibrahim ya shigo “ya fesar da numfashi
sannan ya soma mgn “mb daka shigo yanzu kaga hisham tare da nuzla ko baka gani
ba ?“na gansu amman.” dakata mb “an tabbatar min kullum yake zuwa wajenta kuma
nasan yana yin hakan ne saboda ne “.juya can ka kalli auta da kyau “haka aka kai
masa ita ?yau zaa yita ta qare gidan nan laifin mai tayi masu ?idan laifi ne ,ni ne
nan nayi saboda naki amincewa da soyayyar nuzla kuma nasan shine sila da dalilin
son a kuntatawa auta tunda ni babu abinda zaa iya min ,dan haka yau zan kashe
wannan aure .”mami ta sauke numfashi sannan ta mike ta bar wajen.”dan tasan halin
d’anta wani irin murdaden mutun ne mai wuyar shaani ”
Yan’uwansa ma numfasawa sukayi domin wannan karon fad’an gasky yake da son kwatarwa
kanwarsa ‘yanci amman sunyi mamaki wannan shine karo na biyu da ya nuna kulawarsa
akan nana hauwa’u amman duk da haka bazasu bari ya kashe mata aure ba .”maryam ta
kallesa taga yadda hankalinsa ya tashi akan yaruwarsa ya manta irin azabar da yake
gana mata ,ya manta cewar itama diyar wani ce yake quntata mata hawaye ya cika
idanunta tausayin kanta ya kamata ta kalli nana hauwa’u taga itama hawaye take ta
kalli ata cikin sa’a idanunsu ya tsarke cikin juna tayi kamar zata girgiza masa kai
amman wata katuwar hararar daya zabga mata mai had’e da kallon banza yasa ta d’auke
idanunta akanshi ,tana mai share hawayenta da hannu ta qaraso kusa daita nana
hauwa’u ta riko hannunta zuwa gefe “sister kinji hukunci yayanki dan allah karki
yarda ya kashe miki aure saboda ya hisham mutumin kirki ne nuzla ce matsalarki .”
“bani da zabi sister bazan iya ce masa a’a ba duk abinda yake son ya zarta akaina
na amince ni mai biyayya ce a garesa ,maryam ta rungumeta ajikinta “bakya son yaya
hisham ne ?”to bazan ce bana jinsa araina ba , amman idan yayana yace na koma
gidansa zanyi idan yace a’a babu inda zani “wallahi sister kina son mijinki “ta
fad’a tana zare jikinta a nata ta tsura mata ido tana kallonta hawaye ne kawai yake
fita daga cikin idanunta qirjinta har wani sama da kasa yake “ta riko hannunta tana
cewa “ shi bai rike nashi auren ba zai kashe auren wasu muje ki fad’awa mami kina
son mijinki nana hauwa’u taki binta ta zare hannunta ta rakube gefe tana share
hawayenta dole tasa maryam ta dawo ta tsaya kusa daita tana share mata hawaye .”
mb ya kira layin hisham cikin kankanin lokaci sai gashi ya shigo yayi mamakin
ganin mutane cike ya tsaya yana kallonsu d’aya bayan d’aya sai dai bai ga matarsa
acikinsu ba , wani mugun kallo ata yayi masa sannan ya qaraso gabansa ya tsaya tare
da jin kai ya zuba hannuwansa duka cikin aljihunsa “baka son auta shiyasa ka zabi
ka dinga quntata mata ta wannan hanyar ko ?hisham yayi shiru yana mai sunkuyar da
kanshi kasa dan jin kunya “kasani nasani kowa yasani ban bada goyon bayan auren nan
ba dan har yanzu bana son aurenku daita “cool down ata mb ya fad’a yana dafashi ya
buge masa hannu yana qoqarin cukumar wuyan hisham yaya ibrahim ya shiga tsakaninsu
“dan girman allah ka matsa “ babu inda zani ka samu waje ka zauna ayi magana ta
natsuwa “idan har kaga na zauna to ya miko min takardar sakinta dan bazata qara
zaman aure daahi ba har abada ya saketa yaje ya auri wacce yake so .”
Mmn sudais
💗💗💗💗💗💗
MAR'ADAMS
💖💖💖💖
💗💗💗💗💗💗
*AYSHA A BAGUDO*
WATTPAD @HAUESH
AREWABOOKS USERNAME
AYSHAABAGUDO
bismillahirrahmanirrahim
Wannan littafin na kudi ne mai bukatar karantashi byn na kammalashi zai biya 1000
ta wannan account number din 1438775094 Aishat abdullahi access idan an tura sai a
turawa wannan 09136918331 alert domin tabbatar da an tura domin sauraron littafaina
a tuntubi chaneel dina (Hausa bakwai ) a YouTube.
Page 12
Jin abinda ATA ya fad'a yasa maryam duk ta rud'e sai zufa take fitarwa hankalinta
yayi matukar tashi gbdy ta nemi natsuwarta ta rasa domin tasan halinsa tunda ya
furta zai raba auren lallai zai aikata hakan "ta fashe da wani irin kuka mai
karfi , haka ma nana hauwa'u kuka take sosai , yadda maryam ta rud'e haka matan
dake tsaye a wajen suka rud'e gashi babu damar yin magana .mazan kuwa sai faman
bashi hakuri suke yana fixgewa mb ya fuskancesa sosai yana cewa "haba ATA ka
kwantar da hankalinka abi komai ahankali "kasan allah muddin ina raye sai na kashe
wannnan banzar auren ."
qanqame maryam nana hauwa'u tayi ajikinta suna mai fashewa da wani kuka cike da
tashin hankali maryam ta soma magana muryarta na rawa "sister ke kad'ai ce zaki
kawo karshen wannan matsalar "nana hauwa'u ta zare jikinta ta tsura mata
ido ,idanunta na sake cika da ruwan hawaye . saboda babu mai fad'a ma yaya adam
yaji sai ke a yanzu idan kika nuna masa kina matukar son mijinki shikenan magana ta
qare dan dole zai hakura ya barku "nana hauwa'u ta girgiza mata kai "dan allah
sister karki bari ya rabaku yaya hisham mutumin kirki ne ki tashi kiyi wani abu ta
karashe mgnr tana kuka numfashi nana hauwa'u ta sauke tana share hawaye "bazan iya
ba sister duk abinda yayana ya zaba min shine daidai ."haba sister haba sister !!
karkice haka mana kiyi hakuri kiyi wani abu mana ta qarashe maganar tare da qoqarin
mikar daita tsaye "
da kyar nana hauwa'u ta mike tsaye bisa kafafunta ta soma tafiya jikinta na rawa
rawa taku biyar tayi ta tsaya cak ta kasa cigaba da tafiya hawaye na sake wanke
fuskarta yayinda ata da hisham suka tsurawa juna ido kowannensu zuciyarsa na zafi
cike da tashin ahankali ." hisham ya janye kwayar idanunshi cikin nashi ya tsurawa
nana hauwa'u yana mai shafa kanshi abu d'aya zuwa biyu ne suka tsarga masa a tsayen
da yake a gabansa ,abu na farko farinciki yadda Adam yaji zafi da ciwo acikin
zuciyarsa ,abu na biyu kuma mahaukaciyar soyayyar nana hauwa'u da yaji yana bin
jinin jikinsa tare da huda duk wani tsoka dake sansar jikinsa ,cikin wani irin
sauri zuciyarsa ta dinga tsalle tana bugawa da matsanancin karfi kamar zata fito
daga cikin qirjinsa hannuwansa duka ya miko mata alamun tazo garesa dan bazai iya
rabuwa daita ba ."
ta kalli yayanta dake tsaye rike da kugunsa, ta waiga ta kalli yan'uwanta sannan
ta kalli hisham da har lokacin yake miko mata hannunwansa gabad'aya nana hauwa'u ta
nemi natsuwarta ta rasa ji take kamar zuciyarta zata buga sakamakon fad'uwar gaban
data risketa ,haka ne ma yasa jikinta ya cigaba da rawa gashi yaya hisham yaki
d'auke kwayar idanunshi akanta wanda yayi sanadiyyar da suka fad'a kogin tunani
hankalinsu ya bar duniyar da suke ciki ya lula dasu can wata duniyar . "friend kayi
hakuri ka kwantar da hankalinka hisham bazai ta'ba cutar da auta ba ,sannan
hukuncin da d'auka akanshi daidai ne ko yanzu ka taka rawa aciki rayuwar aurensu
wannan zai zama kashedi ne mai karfi kayiwa hisham".
"shi kansa bai san yana son matarsa ba sai yau haka zalika itama auta tana son
mijinta ka duba ka gani yanayin da suke ciki na damuwa a yanzu "ATA ya sauke
hannunsa dake rike da kungunsa ya juyo yana kallon mb a kallon da yake masa ya
fahimci ransa ya kai kololuwar tashi da maganar da yayi masa ahankali ya kalli inda
hisham yake tsaye yana mikowa nana hauwa'u hannu ranshi ya qara 'baci cikin
tsananin fushi yace "wallahi wallahi idan kika kuskura kika isa garesa sai na
balballa ki "Jin sautinn muryarsa yasa nana hauwa'u tai saurin dawowa haiyacinta
tana mai sunkuyar da kanta kasa ."
A rud'e maryam tace "me yasa yaya adam "! ta matso gabansa ta tsaya tana dubansa
hawaye na sauka daga idanunta "me yasa zaka kashe mata aure alhalin tana son
mijinta ?ya kamata kayi masa uzuri saboda kai kanka kasan yaya hisham mutumin kirki
ne wallahi bazai ta'ba cutar da sister ba duk duniya a halin yanzu sister bata da
kamarsa idan ka tsaya domin kwatar mata 'yancinta nifa ?"nida kake min fiyye da
abinda yake mata fa"? sai da gaban kowa dake wajen ya bada wani sauti bugu mai
karfi
Wani mugun kallo yayi mata da tsumammun idanunshi yana nuna da yatsan hannunsa
"wacece ke da ina magana zaki saka min baki ?ya fad'a tare da d'auketa da wani
gigitaccen mari yana sake nuna ta how dare you ?".
" duk nan babu wanda ya isa bare ke din banza da ko kwatan matsayi kowa anan baki
kai ba ." abinda nake miki ina yi ne dan bana sonki ,suma kuma da kika ga zan
rabasu dan nasan basa son juna sukai aure, bana goyon bayan auren da ba'a so, dan
bana son a aura min matar da bana só kamar yadda adabaibayeni dake "yayi maganar da
karfi jikin maryam yana rawa ta fad'a jikin aunty shahida tana wani irin kuka mai
ta'ba zuciya ."gabad'aya parlour'n yayi shiru tamkar babu wasu halittu acikinsa,
babu wanda bai tausayawa maryam ba illa aunty abida wacce taji dadi aranta kuma
hankalinta ya kwanta ta qara tabbatarwa kanta sultana ce macen da zatai wining din
heart dinsa dan haka ta washe baki cikin jin dadi tace tana ".
"kema maryam da karanbani kike keda kika san matar cushe bata daraja ,me ya kaiki
saka masa baki a maganarsa ?."you're very stupid kema nace ki saka min baki a
maganata ne ?"ko ina ruwanki ? kai tsayuwar me ma kikewa mutane anan ?da mijinki
nake da issue ba dake ba oya leave "ya nuna mata kofar fita cikin kuka tace "ah ah
ni ai yar'uwarka ce dole ina da ikon da zanyi magana kuma ma ai anan ka sameni ba
daga sama na shigo ba ,magana kuma dole nayi wallahi wannan kam ba irin matarka
bace sam baku dace ba ka jira matarka na nan zuwa amman kam sam ba mata bace "
abida i saiid out of this hall kuma ko da wasa karki sake shiga hurumina idan ba
haka ba zan baki mamaki .yaya ibrahim ya kama hannun matarsa yayi hanyar waje daita
amman aunty abida ta turje tana cewa "ka sakar min hannu babu inda zani da kyar ya
samu ya fitar daita ya dawo ."
"Me ye laifinta adamcy ai gsky maryam ta fad'a maka "wato laifi tudu ka take naka
ka hango na wani ya kalli Aunty shahida da kyau yace "ina mata abinda nake mata ne
saboda bana sonta kuma da ina da dama zan iya rabuwa daita har abada ,haka zalika
shine dalilin da yasa zan kashe auren auta domin zukatan kowa ya huta, yaje ya auri
wacce yake so itama ta samu wanda take so yake sonta ya qarasa mgnr gumi na karyo
masa sannan ya kalli nana hauwa'u "Ke maza ki koma d'aki "da mugun sauri ta juya
tayi hanyar d'akin tana jin wani irin fad'uwar gaba mai tsanani hisham ya kallesa
kawai batare da yayi magana ba duk da maganar yake son yi amman idan yace zai yi
komai zai qara rikicewa ne shurunsa ne yafi zama alkhairi ."
A rikice mami ta fito alamun tashin hankali aunty khadija na biye daita ."ta tsaida
nana hauwa'u aunty khadija ce taje ta fad'a mata abinda yayiwa maryam tana gama
qarasowa ta dakawa ata tsawa tace "me maryam tayi maka ka mareta "?yayi shiru yana
sake tamke fuska sosai "adamcy kaji tsoron allah, kaji tsoron ranar da hakin maryam
zai kamaka idan baka sota ba'ace ka qaunaceta ba amman me yasa zaka dinga tozarta
min ita agaban mutane wallahi duk namiji mai wulakanta matarsa agaban mutane yayi
asarar rayuwa dan haka ka bata hakuri yanzu yanzu ."
"What !?
ya furta a razane zai sake bud'e bakinsa yaji mami ta d'aukesa da mari "you're
very stupid too hakurin ne bazaka bata ba "sweetheart marina kikayi akan wannna
yarinyar ?na mareka kai ma baka duba darajata ba bare hisham ya duba darajata har
ya ragawa diyar cikina "hisham ya sunkuyar da kanshi kasa yana mai tsananin jin
kunyarta "yanzu sweetheart akan na mari wannan duwaf din yasa kika mareni?"eh
akanta na mareka idan ka sake ce mata duwaf zan maka double dinsa idan bakaji
kunyata ba bazan ji kunyarka ba bare na raga maka maryam ta rike hannu mami dan ta
fahimci qara masa wani marin zatayi "dan allah mami ki rufa min asiri kiyi hakuri
karki masa komai ."
a fusace yake kallon maryam fuskarsa a tsuke itama din shi take kallo nan da nan
jikinta ya dauki rawa ."ido cikin ido suke kallon juna a karo na farko kenan a
rayuwarsu duk da suna kallon juna amman ba kamar haka ba kallon nadama take masa
yayinda shi kuma yake mata kallon zaki gane kurenki da sauri ta janye kwayar
idanunta saboda wani irin mugun kallon da taga yanayi mata yana fesar da iska mai
zafi daga bakinsa."hisham !"mami ta kira sunansa ya d'ago a natse yana dubanta cike
da girmamawa "ban hanaka qara auren duk wacce kake so ba amman bazan d'auki tozarci
da wulakanci ba karka wulakanta min yarinya idan kasan wulakanta min yarinya zakayi
na had'aka da allah ka sauwake mata kamar yadda d'anuwanta ya bukata ".
"kiyi hakuri Mami "ba maganar hakuri bane hisham bazan yarda yarinyata tayi zaman
rashin yanci a gidan aurenta ba" hisham ya sauke boyayyen ajiyar zuciya domin gani
yayi kamar son kai garesu menene ata baya yiwa maryam? irin cin kashin da yake mata
shi ko kwatansa ba yayiwa nana hauwa'u amman shine dan son kai irin nasu zasuji
haushi har su buqaci raba auresu "idan kasan baka bukatarta arayuwarka kaje ka aiko
min da takardarta "muryarsa a sanyaye sannan cike da girmamawa yace "mami Kiyi
hakuri ina son aurena ! "to kayi magana da yayanta tana gama fad'ar haka ta juya ta
zata koma d'akinta." taji qara fashewar glas tass !
Ta tsaya cak tare da juyowa ata ta gani tsaye jini na bin hannunsa ,ya rasa meke
masa dadi bakinciki goma da ashirin ga marin da mami tayi masa ga damar da ta bawa
hisham yasa zuciya ta dibesa ya bugi show glass din dake gefensa shine nan take
jini ya soma bin hannunsa aiko maryam ta rikice "na shiga uku mami yajiwa kanshi
ciwo ita kanta mami cikin tashin hankali da kidema take kallonsa ranta ya baci
matuka da abinda yayiwa kanshi amman ta danne zuciyarta daga taimaka masa ta maida
idanunta ga maryam dake kyarma cikin alamun rashin damuwa tace "meye damuwarki
dashi ?cikin yin qasa da murya maryam ta kalleta "jini ne fa mami ."ina ruwanki oya
wuce muje d'aki taja hannunta suna tafiya maryam na kallon bayanta ."
Shi kuwa ATA zuciyarsa banda tuttukin bakinciki babu abinda take Mb ,yaya ibrahim
yan'uwasa har ma da hisham hakuri suke bashi ganin yadda jinin ke tsiyayya a
sakamakon jininsa dake gudu fiyye da kaida amman ko motsi bai yi ba ,da kyar suka
kamoshi suka zaunar dashi akan kujerar dinnig d'aya byn d'aya mutanen dake tsaye
suka fita a parlour'n ya saura iyasu kawai nana hauwa'u ta yage bakin mayafinta ta
durkusa gabansa idanunta cike da kwalla bai d'ago ya kalleta ba ,tana qoqarin kamo
hannunsa cikin zarewar ido da maseefa ya janye hannunsa ." cikin tsarkewar murya
tace "please yaya karka ce a'a wallahi zan iya had'iyar zuciya na mutu idan wani
abu ya sameka bazamu iya jurar rashinka ba muna sonka fiyye da tunaninka ,bazamu so
mu rasa d'an'uwa kamarka ba ."
runtse idanu shi yayi kawai jikinta na rawa ta sake riko hannunsa dake tsiyayar
jini wannan karon bai dakatar daita ba ta daure tana cewa "bari a kira doctor"
still bai ce uhm bare uhm ba sai dai wata irin zufa ke tsatsafo masa akan goshinsa
da ilahirin jikinsa ya kamo lip's dinsa na qasa yana cizawa da karfi ya bud'e
tsumammun idanunshi da suka gama canza kala tsabar zuciya ,hanunsa dake daure ya
tsurawa ido suka dan ja baya kad'an dan ya samu dasataccen iska ." yana zaune yana
cikin tsananin damuwa maryam ta fito da sanyi jiki ta kallesa zaune shiru har
tsawon minti uku kafin ahankali ta dinga takowa har ta qaraso garesa ta tsaya taga
alamun an daure masa hannu ."
ajiyar zuciya ta sauke kana ta daura tafin hannunta akan goshinsa tare da goge masa
zufar dake tsatsafo masa duk da sanyin ac dake ratsa parlour'n idanunshi ya sake
runtse wa yana jin qarin ciwo akan wanda yake ji cikin kulawa tace "sannu yaya bai
amsa ba sai ji da yayi kamar ya tashi ya rufeta da matseyacin duka, ganin bai ce
komai ba ta juya da sauri ta nufi dining area ta zuba ruwa a glass cup ta nufo
inda yake zaune yana huci tamkar zaki da sauri aunty shahida ta rikota tana girgiza
mata kai alamun ta barshi hakan sai dai itama kanta ta girgiza mata tana kokarin
fixgewa daga rikon datai mata ta qaraso inda yake jikinta na kyarma ta mika masa
cup din ruwa cikin tsanani tashin hankali ta furta" ruwa ..! "
ya dago fuskarsa a hade cike da fushi da zafin zuciya ya amshi glass cup din
hannunta ya buga akan tayis yana huci tare da cewa "Congratulations maryam kinyi
nasarar kinyi nasarar !! sace min zuciyar mahaifiyata ba? Cike da tsoro ta qame a
gabansa hawaye na turereniyar zuba daga idanunta tana girgiza masa kai ya mike
tsaye yana nuna ta "wannan kad'ai Ya sake ninka wutar kiyayyarki acikin zuciyata ,
bana sonki kuma bazan ta'ba sonki a matsayin mata acikin gidan nan ,bazaki ta'ba
zama suruka acikin gidan ba dan ban amince dake a matsayin matata ba "yana gama
fadar haka ya ciro waya daga cikin aljihun wandonsa ya soma kira wata number yana
tafiya yana waya "kuna da daki a girls house dinku okay ka duba min ina bukatar
d'aki ganin nan zuwa ".
Yana tafiya suna biye dashi babu irin kiran da Aunty shahida batayi masa da yaya
Ibrhim mb har da hisham ba amman ina ATA bai waigo ba ya ma dade da yin nisa dan
tuni ya shiga motarsa atare gbdynsu suka sauke ajiyar zuciya suna sauke numfashi su
aunty shahida suka riko hannun maryam suka shigo parlour'n suka bar su yaya ibrahim
tsaye a waje suna tautaunawa ."suka zaunar da maryam wacce ta gama rikicewa tare da
zuba masa ido "dan girman allah waye ya fadawa mami ya mareni ?sukai shiru "wallahi
ko waye bai kyauta min ba saboda kunga abinda aka jawo min, kunga bala'i da aka
had'a min allah ne kadai zai kwace a hannunsa ta qarashe mgnr tana zubar da
hawaye."
"kiyi hakuri maryam na d'auka hakan da mami tayi zai kawo miki mafuta né
arayuwarki " maryam ta matso ruwan hawaye tace "dan allah karku bari mami tasan ya
tafi guest house dan damuwar zata sake mata yawa mu bar shi a tsakanin mu ta qarasa
mgnr tana sheshekar kuka dan tasan yau allah ne kawai zai kiyayesa daga koma wa
shan giya sigari kam ma baa magana tasan dole sai ya sha aiyar zuciya suka sauke
gabad'ayasu babu wanda zai fad'a basu sani ba bayan shigar mami ta dawo parlour'n
kuma taji duk abinda ya faru sam batayi nadamar abinda abinda ta aika masa ba duk
da tasan a yanzu adamcy yayi girma da ya kama ta ace ya wuce ta kai hannunta
jikinsa amman bazata iya d'aga masa kafa akan maryam ba "su aunty shahida suka qasa
komawa gidajensu kuma basa jin zasu koma din har sai sun san halin da danuwansu
yake ciki suna zaune jugun jugun ."
bayan awa d'aya suka soma neman layinsa sai dai babu abinda computer Ke fad'a masu
sai swichoff .maryam ta zamo daga Kan kujerar kushin din da take zaune zuwa kasa ta
dafe kanta tana ganin itace silar faruwar komai da bata tsoma bakinta ba da duk
hakan bata faru ba "me yasa na saka bakina ta furta a fili tana fashewa da wani
sabon kuka cike da kulawa aunty khadija tace "lahaula wala kuwata illa billa babu
tsumi babu dabara maryam dole hakan zata faru "ahankali ta kalleta da idanunta da
suka yi jazir alamun tarin tashin hankalin tace "bazaku tafi gida ba ?"bazamu iya
tafiya ba dole mami tana bukatar mu "."zaku iya wucewa suka tsinkayi muryar mami
cikin rashin nuna damuwarta ."
ahankali ta cigaba da motsa lip's dinta "kuci abinci ku wuce gbdy na sallameku suka
girgiza mata kai "ni ba uwar banza bace yadda bazan dauki haka daga matar dana ba
haka bazan barku ku kwana batare da kun sanarwa mazajenku ba da kwarin gwaiwar mami
suka wuce gida ya saura daga maryam sai nana hauwa'u da mami .mami tasa aka kawo
masu abinci ita kuma ta maida hankalinta ga tv kamar abun bai dameta ba , kasa ci
sukayi ta waigo ta kallesu a natse "ku ci abinci mana!" suka girgiza mata kai
alamun basa ci' ko akawo maku abinci mara nauyi ?da kyar nana hauwa'u ta fixgo
magana "ni dai bazan iya ci komai ba amman ban san ko sister ba mami kam tasan
maryam bazata ci ba dan haka ta mike ahankali tana cewa "sai da safenku "yanzu mami
bacci zakiyi ?to me zanyi maryam ?Zan kashe kaina akan adamcy ne ."kuma kuje ku
kwanta ku hutar da ranku dan shi bai ma san kun damu da halin da yake ci ba ta juya
ta fara tafiya ."
daren ranar daga maryam har nana hauwa'u babu wanda runtsa damuwar nana hauwa'u ta
hade mata biyu na halin da danuwanta yake ciki da kuma kewar mijinta dan tasan da
yanzu suna can makale da junansu duk yadda yake nuna mata bai sonta amman basu
ta'ba raba wajen bacci ba kuma kwana yake yana wasa da jikinta ganin baccin yaki
zuwan mata sai juyi take ta juya gefenta inda maryam take kwance yadda ta barta
haka take ta mike ta shiga bayi ta dauro alwala ta soma gabatar da sallam ganin
haka yasa maryam ma ta yunkura da kyar ta tashi itama taje ta fara jera
nafilfili ."
washegari tun karfe takwas yayan mami suka wa gidan diran makiya dan kwana suka yi
kiran layukansa amman baya shiga ita dai mami bata ce masu komai ba ta cigaba da
tsabgar gabata ."kwana biyu ATA bai dawo gidan ba kuma gbdy sun sa an bincika
gidajensa bai je can ba hatta office bai zuwa gashi babu wanda yasan girls house
din da yaje gbdy yanuwana sun shiga damuwa maryam kam kallo daya zaka mata ka
fahimci yadda ta fita haiyacinta Har mamakinta suka dinga yi gabad'ayasu sun gane
tana mutuwar sondanuwansu "zabiba ta matso kusa daita "ki rage son nan maryam zai
miki illa ta kalleta kawai tana sauke numfashi "ki yawaita addua sai komai yazo
miki da sauki babu wanda bai kira layinsa ba amman yaki daga wayar har da wasu
layuka da dabam sun kirasa da zarar yaji muryarsu zai katse kira tun suna boyewa
har dai sai da mutanen gidan fahimtar sun nemesa an rasa ne dan duk sunfita
haiyacinsu ."
Ganin da mami tayi ya'yanta sun fita haiyacinsu yasa ta dauki wayarta ta soma neman
layinsa kira daya tai masa ya dauka alokacin ana bude masa bayan mota zai shiga
"barka da... "bana bukatar gaisuwarka
"Kana ina? ta katseshi da fad'arhaka ?ina wani wuri !"tô ka dawo gida yanzu yanzu
muddin baka son ka hadu da mummunar tashin hankali arayuwarka ".tana gama fadar hk
ta katse kiran dole ya bada umarni a dauki hanyar zuwa gida dashi yana shigowa gbdy
yan'uwansa sukayo kansa banda mrym dake rakube cikin farinciki dawowarsa "big
sister aunty shahida ta zauna kusa dashi tana shafa gefen fuskasa tana kamo
hannunsa me ciwo "hope kana Lfy ?yayi mata banza hannun suka tsurawa ido nad'e da
bandages "dan allah adamcy ka dinga hakuri wannan maganar bai kai ace ka bar gida
ka tare a guest house ba, "dan rani wayo kawai wallahi wannan ba mutuncinka bane
tô ita mrym meye nata laifin "?
"Oh My god ! taya yarinya na had'ani da mahaifiyata zakice meye laifinta wallahi
tana damun rayuwata sweetheart kuma na damuna akanta, kuma kullum mgn d'aya ya
zanyi ne? dame zanji ne? bana sonta amman kun matsa sai dana aureta dole , kuna son
na mutu ne ?duk yayi masu tmbyr a matukar rud'e gbdy suka girgiza masa kai alamun
a'a ita kam mrym hawaye ne ke zuba a idanunta tana jin ciwon yadda yake iya furta
kalmar bai sonta a gaban kowa "ka dubi allah ka duba lamarin maryam " what ! ni kun
duba lamarina da zan duba nata ?ihu nake kamar mahaukaci amman bani da mai
fahimtata acikinku bare ku taimaka min ."
"Samu natsuwa adamcy ,yanzu me kake so?" mafarkina nake so !"muddin ana son wata
taji dadina sai dai a nemo min ita, idan ba haka ba wallahi wallahi kowa bazai ji
dadina ba acikin gidan nan , yadda zuciya take quna a kullum haka take son kowa
yaji radadin da take ji, kun kasa samo min ita ,kun kasa yi min komai akai ,kun
kasa fahimtata kun kasa min uzuri kullum maganar mrym marym !! ku dai burinku
yarinyar taji dadin rayuwar aure ni kuma ko oho Inpossible wallahi bazai yuwu ba
sai dai mu taru muyi rayuwar qunci gbdy ."
suka zuba masa ido kawai suna kallonsa cike da tausayawa "matuqar kuna son
farincikina ku nemomin mafarkina ya qarashe mgnr yana huci sannan ya mike."
" ina kuma zaka "ina bukatar na kasance ni kadai daga haka bai qara cewa komai ba
kai tsaye step ya haye mrym ta juya tana kallon bayansa zuciyarta na bugawa da
sauri sauri gbdy suka qaraso suka zagayeta "karfa ki yarda ki saka damuwa aranki
muna sonki mahaifiyarmu tana tare dake me ye abun damuwa ?kai ta girgiza "yan'uwana
bazaku gane yadda nake ji araina ba ,aunty zuciyata kamar ta fashe idan naji yana
magana akan mafarkinsa da furta bai sona, idan ya zama dole ne sai ya furta ni ya
dinga fad'a min ni kad'ai ciwo bazai dame ni haka ba wai har a gaban aunty
abida ,rukkaya ,diyana ."
In fact ya nunawa duniya ni din bakowa bace garesa hatta zumuncin dake tsakaninmu
yayi watsi dashi ."
"Kiyi hakuri komai zai zama labari wata rana "babu komai allah ya nuna min wannan
ranar bari naje na kai masa wani abu yaci ta barsu tsaye ta nufi kitchen bayanta
suka bi da kallo suna jinina girman hakurinta dan ko su bazasu iya daukar
wulakancin nmj haka ba ,amman tunda ita haka allah yayita da hakuri sai su tayata
da addaur allah ya qara mata hakuri ."tana qoqarin had'a masa abinci wayarta ta
soma ringing ta duba taga mahaifiyarta ce dan haka tasa wayar a handsfree muryarta
a sanyaye ta gaisheta "umma ina yini ?lafiya kalau maryam ya kike da wannan mugun
mijin naki ?yana nan yana halin nasa ko ?"duk lafiya muke dagani har shi amman dan
allah ummah kiyi hakuri ki daina kiransa da mugu yaya adam nada kirki fa kawai dan
bai sona ne ."
"Wannan shine dalilin da yasa bana son shi yanzu bai son jinina me zanyi dashi "tô
ai shi só halitta ne umma amman ina sa rai wata rana zai duba lamarina da izinin
allah ki tayani da addua,addua kam muna yi dan tun daakayi auren naku ban zauna ba
wajen neman miki taimakon samun 'yanci a gidan miji ,yanzu haka ma ga wani taimakon
nasa an amso miki daga zuru zan turo miki ta jirgi kije ki karbo da kanki acikin
abinsa zaki zuba masa idan allah ya taimaka yaci wallahi sai dai wani ba wannan
adamun ba sai yadda kikayi dashi maryam tayi sauri ta cire wayar a speaker tana
waiga bayanta dan datasan mgnr da zai cigaba da fitowa bakin mahaifiyarta kenan
bazata saka wayar a speaker ba."
Ta sauke numfashi sannan ta maida wayar kunnenta ta rage murya sosai ta cigaba da
magana "gsky ummah bana son nayiwa yaya adam wani abu tukun ya soni nafi son ya
soni dan kanshi "tô shikenan zanyi amfani dashi tayi discounting kira tare da soke
wayar acikinta ta kawo karshen maganar né da fad'ar haka dan ita bazatayi masa
amfani da komai ba , taji ma da tarin zunubin dake kanta ta hada masa abinci akan
qarami tray ta fito ta nufi hanyar d'akinsa bynta suka sake bi da kallo cike da
tausayawa a hankali ta tura kofar d'akin ta shiga yana zaune a kasan d'akin ya
tokare hannunsa yana kallon sama . yana jin motsin shigowa d'akin ya kalli kofar
ganinta yasashi jan tsaki yana kwar da idanunshi gefe ta karaso ta tsugunna kusa
dashi jikinta da murya na rawa ta d'an saci kallon hannunsa mai ciwo sannan tace
"ga ...ga abinci!
" bai ce komai ba ya kamo lip's dinsa na kasa yana cizawa da karfi "kayi hakuri da
abinda ya faru wallahi bani da masaniyar faruwar komai da kuma nasan hkn zata faru
wallahi bazan bari ba bazan ma sa bakina ba daman nayi haka né dan "ya waigo a
fusace ya kalleta a kaskance hakan yasa ta kasa cigaba da magana zuciyarta na
bugawa ganin bai yi magana ba yasa ta sake bude baki zatai mgn ya d'aga mata hannun
tare da tsareta da idanunshi wanda hkn ya haddasawa zuciyarta shiga rudani da
bugawa da sauri "kin kamu da sona ko ?tai shiru tana duban cikin kwayar idanunshi
karo na biyu kenan daya furta mata haka sai dai ta kasa bashi amsa tmbyrsa ."
"kina sona kuma shine dalilin da yasa kika dawo abar tausayi haka ba ? nan ma shiru
tai masa dan batasan me zata fad'a masa ba "nonsense girl kawai wallahi kin cuci
zuciyarki ke yanzu kinga dacewar mu da zaki kamu da sona ?tai saurin girgiza masa
kai "ba.." bana só.."you are very stupid shut up iam talking you talking sai na
kasheki da mugun duka taja bakinta tayi shiru tana sauke numfashi."
Ya mike tsaye yana dubanta kamar zai had'eyeta da idanunshi "itama da sauri ta mike
jikinta na kyar "ni zaki kalla kice baki so ?ta sake girgiza masa kai ."
"better kin taimaki kanki da kanki ,kingan ni nan har abada bazan ta'ba ganganci
barin ki zauna acikin nan ba "ya nuna daidai saitin zuciyarsa da d'an yatsansa ."
" zan baki shawara kiyi gaugauwan cire sona aranki kamar yadda na ta'ba fad'a miki
adam mallakin mafarkinsa ne idan ban sameta ba mallakin wata ce dabam amman bake ba
"tunda ya soma magana tske jin tashin hankali mara misaltuwa" me yasa zakace haka
yaya adam? daga ranar da ka zama miji agareni daga ranar na sanyaka acikin abinda
yafi zuciyata da gangar jikina ,zuciyata ta haukace akan sonka ina jin ciwon
kiyayyar ka gareni amman na kan kawar dashi domin na samu damar dasa soyayyata
acikin zuciyarka ta hanyar maka biyayya "enough...! bana son jin maganar soyayya
daga bakinki ai tunda kina iya shiga tsakanina da mahaifiyata kin kad'e a wajena
domin wannan son wa ni kadai ya dace ban dake amman gashi an kasashi gida biyu "ya
fad'a ya fusace ."
"ban kwace maka soyayyarka ba mami tana sonka fiyye da komai kuma matsayinka na nan
acikin zuciyarta ,bazata ta'ba canzaka da wata ba, watan ma ni ai ban isa na taka
matsayinka a zuciyarta ba kuma duk wannan kulawar da kake ganin tayi karfi yanzu
saboda kai ne saboda ..."please let me be alone ya fad'a yana juya mata baya cike
da jarumta ya zuba hannuwansa duka cikin aljihunsa "out of this room now ya nuna
mata hanyar fita ."shiru tai ta kasa motsa jikinta ."ganin hk yayi tunanin bar mata
d'akin ya nufi hanyar fita ta biyosa da sauri tana cewa "d'an allah kayi hakuri
kaci wani abu sai daya bari ta fita daga d'akin gbdy ya dawo da baya ya rufe kofar.
cike da muryar kuka tace" ka yafe min banyi maka laifin komai ba wallahi ban
had'aka da mahaifiyarka ba ni kaina bansan hakan zata faru ba wallahi dana san
wanda zai fad'a mata alokacin dana hana bai ce uhmm ba bare uhmm ya bar jikin kofar
yana jan tsaki tare da furta "nonsense!wani sabon kuka ta rushe dashi"maza masu
sanyin halima baka barinsu haka ,bare miji irin naki dole sai kin tashi tsaye wajen
mallakesa sannan zaki samu 'yanci agidan aurenki "maganar mahaifiyarta na karshe
kenan a wayar da sukai yi d'azu nan take taji ta yarda kuma zuciyarta ta amince
zatayi amfani da maganin da mahaifiyarta zata aiko mata domin samarwa kanta
kwanciyar hankali a gidan mijinta "ahankali taji an dafata ta waigo idanunta cike
da ruwan hawaye "Mami ce !
"Mami dan allah ki fad'a masa cewar bani na hadashi dake ba, dan allah mami ki bari
ya fahimce hakan " naunayen ajiyar zuciya ta sauke " na rasa me yasa adamcy yake
son caza miki kwakwaluwa mami ta fada hk a fili "ita kuwa mrym kuka kawai take tana
rokon mami ta fahimtar dashi "kukan ya isa haka zan fahimtar dashi duk da ba
rarrashi ya kawo wajensa ba amman zan kwantar da kai saboda ke "yauwa mami na gode
sosai dan allah ki lalla'bashi kar kiyi masa fad'a ta fad'a tare da share hawayenta
"mrym ki daina yawon kuka ki dinga dauriya mijinki ba mutun bane mai damuwa da
kukan mutun ko sanin mahamancin hk, jajurcewarki ita zatasa kiyi nasara akansa ta
runtse idanunta wasu hawaye masu zafi zuka zubo mata ".
"nace kukan ya isa haka "tô mami kice ya bude kofar yaci abincin nasan tunda ya bar
gidan bai ci komai ba amman sam sam yaki saurarata"kije for now nasan halin d'ana
kema kuma idan da sabo ya kamata ace kin saba da halinsa bazai ce miki komai ba
sannan bazai ci komai ba, ki bari zan fada masa komai zan fahimtar dashi baki da
laifi kuma zan lalla'ba miki bazan masa fad'a ba ki kwantar da hankalinki naunayen
ajiyar zuciya ta sauke sannan ta fara janjikinta ta bar wurin mami tai knocking
tana kiran sunansa da kyar ya bud'e mata kofa.
Ahankali ta tura kofar ta shiga ta tsaya abayansa bai juyo ba tasan yayi haka
saboda fushin da yake daita ."
Numfashi ta sauke tare da d'aura hannunta ta dafa kafad'ansa tana kiran sunansa
"adamcy nah !kmr jira yake ya juyo ya zuba mata tsumammun idanunshi yanayinsa kmr
zai yi kuka itama mami ganinsa haka ya karyar da zuciyarta domin ya zube ya fita
haiyacinsa acikin kwanki hud'u kawai idanunshi duk sun rikid'e sun canza kala
alamun shan sigari hannunsa mai ciwo ta kamo tana kallo nan take yanayinta ya sauya
idanunta suka fara kawo ruwa .ganin haka ya rungumeta ajikinsa qirjinsa na bugawa
da wani irin karfi sai da mami taji tsoron yanayin bugun zuciyarsa . ta zaresa
ajikinta tana kallonsa hawaye ta gani a fuskarsa hankalin mami ya qara tashi wannan
shine karo na biyu da taga d'anta na kuka a tun tasowarsa lallai adamcy baya son
mrym ".
"kiyi hakuri sweetheart ina 'bata miki rai hakika ban rike amanar da dad ya bani ba
ki yafe min zuciyata ta kasa son mrym ki bani damar na auro wata please." nasani
nasan baka sonta amman ina sa rai zaka sota wata rana ,ni ban hanaka qara aure ba
ko kawo zabinka ba amman sai naga irin adalcinka ina son kasan mutunci maryam kasan
daraja maryam ka bata kimarta da darajarta ta matarka ,ka bata matsayin mata acikin
zuciyarka, ka yarda daita wannan shine burina kafin ka shigo da wata matar
gidanka."adamcy maryam na da kirki tana da biyayya da hakuri ban maka zaben tumun
dare ba na zaba maka abinda zaka yi alfahari ne ko bayan raina zaka yi alfahari
daita fatana ka rike matarka amana na yafe maka na yafe maka na kuma janye fushina
akanka allah yayi maka albarka allah ya azurtaku da samu zuria masu albarka ".
Shiru yayi yaki amsawa da ameen "ina son maryam sosai Adamcy kai ma kuma ina son ka
koyi sonta .."ya qara tsura mata idanunsa da sukai jazur "zaka min wannan alfarmar?
zaka koyi sonta ?shiru yayi ya kasa furta komai "kayi shiru Adamcy ya kamata kace
min wani abu ko zuciyata zata samu salama ta fad'a tana d'aura hannunta akan sumar
kanshi yayinda hawaye ya cika idanunta ta rasa wani irin baqar zuciya garesa tun
yana yaro take fama dashi idan ya tsani abu ya tsana kenan idan yace yana son abu
shima haka ne, tasan da wahala ya so maryam kamar yadda take bukata. ta cire
hannunta dake Kan sumar kansa ta tsurawa yatsun hannunsa ido hawayenta ne suka
dinga diga akan nashi tafin hannun da sauri ya dago kansa ya sanya kwayar idanunshi
cikin nata yana furta "why sweetheart me yasa zaki min haka ."?
Hawaye ta cigaba da zuba aiko ya rude "wayyo allah na shiga uku ,mami ki taimakeni
karki cigaba da zubar da hawayen nan idan dai ba so kike wani mummunar bala'i ya
sameni ba "ya qarasa maganar cikin rawar jiki numfashi ta sauke ta janyo hannunsa
mara ciwo ta zaunar dashi sannan ta zauna gefensa tana cewa "babu abinda zai sameka
zakayi albarka da izinin allah domin kai ne komai arayuwata babu abinda zai sameka
zan daina kuka amman kai ma kayiwa maryam adalci ka duba irin kulawar da take bani
irin kulawar da take bawa yanuwanka da kowa naka ni mahaifiyarka ce na fi kowa
sanin abinda ya dace da rayuwarka ka sake da maryam zata kula da rayuwarka dan
dukkanin alamunta sun nuna tana sonka yanzu ,ganewa bakwa yi amman kun fi samun
kwanciyar hankali a wajen matar dake sonku ,matan da kuke so kuma wahala suke
baku ."shiru ATA yayi yana nazarin maganarta ."
" kasan me yasa na had'a aurenka da maryam ?ya girgiza mata kai yana daura kansa a
saman cinyarta ya natsu sosai ya bata dukkanin natsuwarsa "na had'a aurenku ne
saboda ko byn raina maryam zata maye maka gurbina zata baka kulawar da uwa ce kawai
zata baka, zata jurewa duk wani shagwa'ba da jin kanka,uwa uba hakuri
gareta ,zatayi hakuri da duk wani iskancinka dan haka ina mai umartarka ka dauketa
a matsayin mata zakaji dadin rayuwar aure daita". ta qarasa maganar tana shafa
sumar kansa ya dago a hankali ya sake zuba mata idanunshi kamar zatai kuka "please
sweetheart karki min haka karki bani umarni ,zanyi kokari na koyawa zuciyata sonta
ta yadda zata bata matsayin mata amman ki bani lokaci ."
ta numfasa taso ya fadi abinda yafi haka amman a hakan ma ta gode "na gode allah
yayi maka albarka ta mike tsaye bari na turo maka maryam ta zuba maka abinci kasa
ma cikinka ,kanshi kawai ya gyada mata tana barin d'akin ya sauke wani wahalallen
numfashi yana tunanin maganganunta "ta ina zai fara bawa maryam matsayi mata ?"
"matsayin mata da take nufi fa tana nufin wani abu ya shiga tsakaninsu kenan ?ya
mike tsaye cike da sanyi jiki "tabbas abinda take nufi kenan idan dai haka ne ta
ina zai fara ?a hankali ya shiga zariya acikin dakin yana ciza lip's dinsa at the
same time yana hura hancinsa ."
byn kmr minti biyar mami ta dawo d'akin hannunta rike da mrym tana bata umarni
"maryam zuba masa abinci" ta fad'a tare da samun wuri ta zauna kusa dashi tana
dubansu adamcy nah bari mrym ta zuba maka abinci kaci ka d'an kwanta ka huta kafin
zuwa anjima ka d'auki matarka ku wuce gida kaji masoyina ."kallonta kawai yayi yana
mai tausaya mata " maryam ta zuba masa abinci ta janyo qaramin table gabansa ta
ajiye masa tana satar kallonsa aranta tace "rigimamme kawai da baya son zaman
lafiya ."
yayi shiru kawai yana kallon abincin kafin ahankali ya fara tsakura babu laifi ya
d'an ci kad'an ya ajiye spoon alamun ya koshi mami ta tsiyaya masa ruwa a glass cup
ta bashi ya sha sannan ta mike idan ka tashi ka d'auki matarka ku wuce gida kanshi
ya gyada mata batare da yace uffan ba , ta juya har tayi taku biyu taja ta tsaya
"batun hisham kayi hakuri kabar auta ta koma d'akinta zai yi magana tace "alfamar
na nemar masa a bashi dama ta biyu stil bai yi magana ba ta fito ta bar maryam tana
tattara wajen ."da yamma mami ta kira hisham yazo ya d'auki matarsa bayan tayi masu
nasiha mai ratsa jiki ." haka ma maryam tabi mijinta suka wuce. gidan ya saura daga
mami sai yayanta wad'an da suke shirin tafiya ."
Akan hanyar su nana hauwa'u ta koma gida tafiya ce sukai tamkar kurame hassalima
bata kalli inda yaya hisham yake ba ta juyar da kanta gefe tana kallon tsirarrun
motoci dake wucewa akan titi saukar hannunsa taji akan nata wani irin yarrrr taji a
gbdy ilahirin jikinta, sai dai bata juyo ta kallesa ba ta cigaba da kallon titi
"auta !" ya kira sunanta yaushe rabon da ya kirata da wannan sunan ?sai daya sake
kiranta sannan ta juyo da kyar ta zuba masa idanunta ya kwantar da murya sosai
"kiyi hakuri da abubuwan da suka faru a tsakaninmu shiru tayi Kmr bazata yi magana
ba sannan ta motsa labbanta tace "babu komai ,komai ya wuce ,"Kinsan ko wanene ba
haka halina yake ba ."
"Nasani shiyasa nayita mamaki wai yaya hisham mai tausayi da kulawa ne nake rayuwa
dashi cikin fargaba da nadamar da tsoron kasancewata dashi yadda baka son auren nan
haka nana hauwa'u bata só ,alfarma tayi ta sadaukar da farincikinta, na dauka yadda
nayi zai sa na kasance masoyiyarka tare da tunanin zaka fi kowa jin dadi da sona
amman sai naga sa'banin haka wallahi nayi mamaki yaya hisham ban ta'ba tunanin haka
daga gareka ba". ta qarasa mgnr cikin rawar murya ya kamo hannunta ya tsarke cikin
nashi" yana murzawa ahankali yana jin canjin yanayi a sansar jikinsa ,yayinda
soyayyarta ke sake huda zuciyarsa "kiyi hakuri hisham zai dawo miki fiyye da yadda
kika san shi a baya ,bazan sake yunkurin cutar dake ba ."wani sanyi dadi taji yana
bin jinin jikinta ahankali ta dinga jin gurbin daya fara samu a zuciyarta yana
qaruwa ."
Washegari ATA na barin gida aka kira maryam sakonta ya iso take ta shirya ta fita
batare da neman izininsa ba ta karbo magani cike da farinciki ta dawo gida ta kira
mahaifiyarta ta sheida mata ta kar'bi sakon ,yini ranar cikin farinciki da murna
maryam tayisa da yamma ATA ya dawo gida cike da kulawa ta tarbesa da abinci ,bai
kalli inda ita da abincinta yake ba ya haye samansa wanka yayi ya sauya kaya ya bar
gidan gbdy .hankalinta a tashe ta kira mahaifiyarta tayi mata bayani "umma ki
tambaya ko zan iya zuba masa cikin abun shansa dan baya cin abinci sai coffe da
ruwan gidan kawai yake sha?to shikenan sai najiki ."
*****
Bangaren maryama kuwa zaman gida ya soma damunta yayinda subai'a tuni ta fara aiki
da kamfanin Z&A dan haka ta fara neman aiki sai dai duk inda taje ba'a daukarta
aiki tun abun baya damunta yazo ya fara damunta tayi tunanin tayi chart din ammar
ko zai taimaka mata dan haka ta shiga what's app dinta tayi masa sallama ya bude
amman bai bata amsa ba. ta sake aika masa still ya bude amman babu amsa dan haka
tayi tunanin kiransa WhatsApp call bai dauka ba sai ma sakonsa ta gani "lafiya !?
kiran me kike min ?"Jikina na rawa ta soma typing "dan allah oga ammar kayi hakuri
akan abinda nayi, yanzu nasan nayi kuskure mai girma "ta tura masa."
jin kad'an sai ga amsarsa ta shigo " bakiyi kuskure ba tukun sai anan gaba karki
manta don't ever call me again or chart me "inna lillahi wa innna ilahi rajiun
allah ka gani taimako nayi allah karka barni da iyawata kabi bayana akan dukkanin
lamurana ."
tun daga wannan rana maryam bata kuma wani sukuni ko walwala ba ,har mamakin kanta
takeyi dan bata d'auka abun zai dawo ya dameta ba kullum cikin damuwa take da neman
aiki bata wani cin abincin kirki gashi kowa ya gane halin da take ciki a gida sai
dai kowa ya tambayeta sai tace bata da lfy ne aunty salma kam kirikiri take mata
dariya tare da cewa "an gama boko anyi bautar qasa babu riba dole a zaman gida tare
damu ."
azumi da nafilflii kullum cikinsu take domin allah ya kawo mata mafuta da samu
aikin, abun duniya ya ishi Aunty dan yar magana da take ma yanzu ta rage Ta sake
dawowa shiru shiru ga rashin aiki ga aurenta da yaya sadam na matsowa ranar monday
ta shirya zata neman aiki aunty tace kar taje koina "me yasa Aunty ?"bazan iya kije
ki dawo baki samu ba ki kwanta rashin lafiya nafi bukatar lafiyarki akan aiki ida
ma zaki iya muje Asibiti a duba min lafiyarki dan wannna ramar ta isheni" muryarta
a sanyaye tace "nifa lfy ta kalau "ina wani lafiya ana ?Kiyi hakuri aunty ki barni
naje ."
"Ni baki min laifin komai ba "to amman ai fushi kike dani Kiyi min addua ko zan
samu aiki "kullum ina miki addaua amman dai yanzu kinsan kiyi wasa da damarki ta
barwa subai'a aikinki ?nasani Kiyi min addua allah ya sake aramin wata damar "allah
yasa a dace sai kin dawo allah ya tsare" jiki a sanyaye tace "ameen!"sannan ta fita
yau din ma dai kamar ko yaushe bata samu tayi kukanta har idanunta suka kunbura
damuwarta ta qaru wunin ranar cikin tsananin damuwa tayisa . yadda take cikin
damuwa haka zuciyar ATA ta kasa samun sukuni duk inda ya motsa sai yaji zuciyarsa
na luguden bugu da tunaninta duk inda ya motsa yana jinta a jikinsa da
zuciyarsa ,wunin yau din wutar soyayyarta sai qaru yake a cikin zuciyarsa ya sauke
naunayen ajiyar zuciya ya yunkura ya mike tsaye daga zaunen da yake yana gyara
zaman yar saman suit dinsa ."
Dakin dake manne acikin office dinsa ya shiga ya tsaya hannunsa d'aya rike da
kugunsa yana qarewa makeken zanenta kallo "to ban zata daidai bane ko ya ?ya
tambayi kansa yana zurfafa tunaninsa "amman kuma wannan fuskar nake gani acikin
mafarkina "me zai hana kasa a nemo maka kwararrun masu zane su zana maka ita kaga
nasu kwarewar ko akwai abinda zai bambamta da naka ?nan take ya amince da shawarar
zuciyarsa ya fito yana kiran yaronsa seun cikin kankani lokaci ya shigo cike da
girmamawa "yayi masa bayanin abinda yake bukata "amman sir me zai hana ka gwada
masu zanen kamfaninka AGC mana "nasan dasu na buqaci wasu dabam ,kaje kayi abinda
nasaka "okay sir ya juya da sauri ."yadda yake cikin damuwar rashinta haka itama ta
kasance cikin damuwar maseefar rashin aikinta dake bibiyar rayuwata kukan data yini
yi ne yasa kafin shida na yamman ranar jikinta yayi zafi tamkar garwashin wuta
aunty ce tsaye akanta tana shafe jikinta da jikakke
towel byn ta bata magani tasha ."
Mmn sudais
💗💗💗💗💗💗
MAR'ADAMS
💖💖💖💖
💗💗💗💗💗💗
*AYSHA A BAGUDO*
WATTPAD @HAUESH
AREWABOOKS USERNAME
AYSHAABAGUDO
bismillahirrahmanirrahim
Wannan littafin na kudi ne mai bukatar karantashi byn na kammalashi zai biya 1000
ta wannan account number din 1438775094 Aishat abdullahi access idan an tura sai a
turawa wannan 09136918331 alert domin tabbatar da an tura domin sauraron littafaina
a tuntubi chaneel dina (Hausa bakwai ) a YouTube.
Page 13
amatukar galabaice ATA ya qaraso gida zuciyarsa na hasko masa fuskar zanen
mafarkinsa " mai yasa na qasa mantawa dake ?yayiwa kansa tmbyr yana shafa sumar
kansa, gbdy yau din tunaninta ya hanani sukuni ya fad’a a fili yana fesar da
numfashi mai zafi daga bakinsa ,qirjinsa kuwa banda bugawa da karfi babu abinda
yake, ahankali ya shiga zagaye d’akin hankalinsa na sake tashi ,a tsakiyar d’akin
ya tsaya rike da kugunsa yana ciza lip’s dinsa na qasa “mai yasa bazan manta daita
na cigaba da rayuwata ba ?”ya wurgawa 'kwal'kwaluwarsa tmby " ban san me yasa nake
ji araina kina cikin wannan duniyar ba yaja qaramin tsaki “what's wrong with my
brain ?I have to stop all this nonsense.”ya fad’a yana cigaba da d’aga kafafuwansa.
bayan kamar minti biyar ya tsaya cak yana sake kamo lips dinshi na kasa yana cizawa
ahankali ahankali ya d’auki lokaci mai tsawo yana shawagi acikin d’akin sannan ya
cire kayan jikinsa ya shiga wanka ya fito ya sanya kayan marasa nauyi riga yellow
mai hannun hamles da farin wondo iya gwiwa , ya samu waje ya zauna a bakin gado
zuciyarsa na sake hasko masa fuskar zanensa.”
“ idan tunaninta ya sakashi gaba jin zuciyarsa yake kamar zata buga hakan yasa
yaki sauka parlour ‘n gidan kamar yadda ya saba a duk sanda ya dawo .”tsaki yaketa
já yana qarawa domin tunaninta na damun kwakwaluwarsa,idan a son ranshi ne baya son
yana damun zuciyarsa da kowa i irin tunani yana nan zaune a bakin gado yayinda
kafarsa daya ke kasan tayis d’ayan kuma ya tankwashe tare da dafe gaban goshinsa
dake sara masa kad’an kad’an gefe guda kuma yana jin damuwar da ciwon abinda
dakikiyar yarinyar nan tayi ,shi tunda yake babu wanda ya samu aiki da kamfaninsa
yayi rejecting dinsa sai ita ,ai kuwa zata ga wahala ganin idanunta yana zaune
maryam ta turo kofar d’akin ahankali ta shigo bakinta d’auke da sallama bai amsa
mata ba haka zalika bai d’ago ya kalli inda take ba .”
kusan minti biyar tana tsaye tana qare masa kallo sannan yaji sautin muryarta a
sanyaye “baby sannu da zuwa !”ta fad’a ahankali tamkar wacce mako shinta Ke ciwo
“ya d’ago a natse ya kalleta sanye take cikin kananan kaya wondo da riga maron
colour mai ratsen fari ajiki yayinda jikinta ke fitar da kamshi hannunta rike da
wani had’ad’den tray. bai amsa mata ba ,ya d’auke kwayar idanunshi akanta zuwa wani
bangaren yana jan tsaki dan ya tsani sunan baby din da take kiransa dashi ,bugu da
qari bazai iya jurar cigaba da kallonta ba, dan babu macen data isa ya tsaya yana
kallonta .” sa’banin ita daya rigada ya saba da kallo irin nata indai tana kusa
dashi to fa dukkanin idanunta da natsuwarta suna kanshi ne “ bata damuwa da duk
irin wulakancin da yake mata hassalima ya fahimci dadin kallonsa take ji dan ya
santa farin sani babu yadda zaayi tana tsaye haka agabansa idanuwanta ba akanshi
suke ba .”
daga sannu da zuwan da tai masa bata sake ce masa uffan ba ta ajiye tray hannunta
ta soma hidimar zuba masa abinci bayan ta gama zuba masa ta sake motsa bakinta
“baby ga abinci “!still bai ce mata komai ba sai ma haushi da ta sake bashi ta
cigaba da kallonsa dan kallonsa ba qaramin jefata cikin nishadi yake ba ,kamar ta
bud’e baki ta tambayesa meke damunsa dan ta fahimci yanayinsa na yau ya canza fiyye
da sauran lokutan daya saba kasancewa cikin miskilanci amman ta qasa tmbyrsa sbd
gudun abinda zai je yazo .taga ya sake kallonta amman sai ta qasa d’auke idanuwanta
akanshi duk da ta fahimci shi hakan yake buqata daga gareta .”madadin ta d’auke
kwayar idanunta kamar yadda yake buqata sai ta durkusa gabansa ta d’auki glass cup
ta had’a masa coffe ta mika masa “baby ga coffe ka sha nasan zaka fi buqatarsa “.
a matukar zuciye ya kar’bi cup din hannunta ya saita ta dashi zai kwata mata ruwan
zafi tayi saurin zaro ido tare da yin gefe ,glass cup din ya samu bangon d’akin,
nan take ya tarwatse a qasa , ya mike a fusace sauran kad’an ya taka wani bangaren
na glass cup din dan har kafarsa ta sauka akan kwalba maryam ta saki qara mai sauti
dole ya d’aga kafarsa Ya koma ya zauna tana dafe goshinsa .ahankali ta juya ta fita
da sauri bata jima ba ta dawo ta durkusa ta tattara dukkan wajen ta mike tana
dubansa “dan girman allah ka dinga bin komai ahankali kada kajiwa kanka ciwo “ ta
furta cikin wata irin murya mai sanyi da tausasawa “muga kafarka allah yasa bakaji
ciwo ba yaji tana fad’a “ya salam wannan wata irin mayya yarinya ce haka? ita sam
bata damuwa da wulakancinsa ,har sai zuwa yaushe ne wuya zai sa ta gudu ta fita
cikin rayuwarsa?”yana son ta gaji dan kanta ,yana son hakurinta ya qare ta gudu da
kafafunta ba sai ya sallameta ba amman da alamun shine zai gudu ya barta .”
“bai ankara ba yaji ta kamo qafarsa data fi tunanin ita ce ta kusan taka kwalba ta
sanya tafin hannunta karkashin tafin qafarsa ta soma murzawa ahankali
“Alhamdulillah babu abinda ya sameka kamar wanda ya farka daga wani mummunar
mafarki ya fixge qafarsa da mugun sauri yana huci. numfashi ta sauke ta mike tsaye
idanunta na kanshi miniti biyu tsakani ta juya adaidai lokacin da wayarsa ta soma
ringing ta d’an rage tafiyarta ya kai hannu ya d’auka ya manna a kunnensa “yaakayi
ammar ?ya fad’a yana furzar da numfashi ,dan girman allah bana ce ka rabani da
maganar yarinyar nan ba? na rantse da girman allah zamu samu matsala da kai mutuqar
baka rabu dani ba ,makaho ne ko me ?maryam ta kasa cigaba da tafiya ta tsaya cak
zuciyarta na karkarwa “eh haka né nasa a nemo min kwararun masu zane “ban gane na
fara ganinta kafin na anemo masu zane ba ?”dan allah share yarinyar nan kwata kwata
banason ganinta “wace yarinya ce wannan da yaya ammar ya damesa daita ?tayiwa kanta
tmbyr yanayinta na canzawa lallai akwai buqatar taga wannan yarinyar .”
ahankali suka cigaba da tautauna can yace “dolen dolalo muna nan a yadda muke taki
zuciya ta gudu ,wallahi ban soma jin komai akanta ba kuma bana fatan na so wannan
yarinyar “ wannan magar da yayi ce tayi sauri dawo daita daga d’an tunanin da
kwakwaluwarta ta tafi na wuncin gadi .jiki a sanyaye ta cigaba da sauraronsa “kai
fa na fahimci baka son kaga ina cikin kwanciyar hankali ,wannan ba matsalata bace
dan ni har yanzu ban maidaita matsayin mata ba ita ..”tun kafin ya qarasa ta fice
da sauri idanunta na kawo ruwan hawaye bata san me suka cigaba da tautauna ba
“amman kalma d’aya zuwa biyu suka fi tsaya mata a kahon zuciya “bai sonta da kuma
tayin auren da yaya ammar yake masa “anya kuwa bazata kai qarar yaya ammar wajen
mami ba ta taka masa burki ?akan wani dalili zai dinga tursasa mata miji alhalin
tana iyakar qoqarin taga ta shawo kansa sun zauna lfy?amman kuma da tayi tunanin
hakan zai iya janyo mata gagarumin matsala da shi ta fasa gara ta nemi yaya ammar
din tayi magana dashi .”
Bayan awa d’aya da wasu mintuna ta sake dawo d’akin ahankali ta qaraso ta tsaya
nesa kad’an dashi ta d’auki kallonsa gabad’aya yanayinsa ya koma na damuwa ,ta
kalli abinci data kawo masa ga dukkanin alamun bai ci ba ,amman dai ta bud’e taga
bai ci din ba kamar yadda tayi zato har yayi sanyi “me yasa bazaka barwa allah
komai ba ?ka sani duk duniya nan idan suna son zamammu ma’aurata ida allah bai
hukunto hakan a tsakaninmu ba bazai kasance ba ,haka duk kinka da auren nan idan
allah yaso mutuwa ce zata raba mu .idan kuma allah yayi iya rabon zama ne
atsakaninmu dole za rabamu karka manta yadda baka son auren nan amman allah ya
qaddara sai da akayi .”
Tai shiru tana dubansa sam bashi da alamun zai kalli inda take bare yace wani
abu ,tunani rayuwarsa kawai yake ta ina zai cigaba da zama daita bai ta’ba jin
komai akanta ba ,shikenan mafarkinsa ya kasance karya ne kamar yadda aka sha fad’a
masa dan da gaskiya ne yadda yake qoqarin neman princess daya sameta “nasan na
dameka da magana kayi hakuri sannan dan allah kaci abinci .”shiru ne stil ya biyo
baya bata ji komai aranta ba dan wannan yana cikin halinsa rashin son magana ta
numfasa tana cigaba da kallonsa idanunta cike da ruwan hawaye .“dan allah kayi
hakuri kaci wani abu ,rashin cin abincinka zai iya haifar maka da mummunar damuwa
kuma bashi bane mafuta agaremu dan allah kaci wani abu tayi mgnr muryarta can kasa
sannan cike da rawa .”
sai lokacin ya cire hannuwansa dake sarke cikin juna ya d’an kalleta ,gabad’aya ta
dawo kalar tausayi amman ko kad’an bai ji wannan tausayin ba acikin ransa .”har
sanda ta cigaba da magana “nasan baka yarda da wannan aure ba ,sannan baka sona
amman at least dan allah ka boye wannan rashin qaunar da kake min a idanun mutane,
idan ya zama dole sai ka nuna ka nuna shi atsakaninmu ,saboda samun kwanciyar
hankalin mami ,aunty shahida da sauran yan’uwana bana son na gansu cikin damu “.“I
can’t do it and I can’t accept this marriage ban tsara rayuwata dake ba gbdy bakya
cikin tsarin rayuwata.” ya katseta ta hanyar fad’ar haka “why sweetheart ?” me yasa
kike son tursasa zuciyata?shiru tayi tare da runtse idanuwanta hawayen dake boye
cikin kwarnin idanunta suka samu nasara zubowa,ba tayi yunkurin sake cewa komai ba
ta bude kular abinci ta zuma masa wani ta mika masa “ya adam eat your food zan juri
komai amman bazan iya jurar rashin cin abincinka ba .”
kin amsar plet din hannunta yayi dan baya ji zai sauko haka cikin sauki ya rungume
aurenta never yatsan hannunsa ya kai ya nuna mata bakin kofar fita “please leave i
don’t want to see your face “ya furta a tsawace “ya Allah ta furta a fili tana
sauke naunayen ajiyar zuciya sannan ta cigaba da kallonsa fuskar nan nashi a d’aure
kamar koda yaushe,”amman yaya ..”I said leave …”ya sake nuna mata hanyar fita daga
d’akin maryam kam gbdy ta rikice ta rasa abinda zatai jiki a sanyaye ta mike har
tayi taku biyu tajiyo sautin muryarsa a kasalance tankar bashi ya gama rashin mutun
ci ba “ki d’auke wannan banzar abincin naki !” lumshe idanunta tayi tana mai
had’eye kololun bakincikin daya tokare mata qirji ta dawo ta durkusa ta d’auki tray
ta fito ta shiga d’akinta .”
Kwanaki biyu kenan aunty ta rasa gane kan maryama haka umma da habib har ma da
sadam sosai suka d’aga hankalinsu dan haka ranar monday tun da safe umma ta shigo
bangarensu tace ta shirya suje asibiti maryam ta kalleta a marairaice tace
“lafiyarta kalau fa !umma tace “ke dai ki shirya muje a duba min lafiyarki
hankalina yaki kwanciya, dan wannan rashin lafiyar bata rashin samun aiki bane
kawai akwai abinda ke damunki “.maryama ta mike da kyar ta shirya cikin doguwar
riga milk colour tayi Roling din kanta da mayafin doguwar rigar ta sanyawa
qafafunta takalmi flat.” ita dai aunty idanu ta zuba masu har suka fice maryama
naja qafafuwa umma da yaya sadam da habib na biye daita har bakin titi suka rakosu
sai da suka shigarsu mota sannan suka dawo gida zaman jiransu ”.
Kai tsaye asibitin mayfear dake oke koto suka nufa umma tayiwa likita bayani yadda
maryama take ji sannan likita ya bukaci ta basu guri fitar ummah yasa likita
tambayarta yadda take ji “kasala nake ji sai qirjina dake min nauyi ga ciwon kai
mai tsatsanani sannan zuciyata na min ciwo likita ya gwaggwadata sannan yace “kina
yawon tunani ko ?tayi shiru tana nazarin maganarsa can tace “eh to bazaa rasa ba
“.tunanin me kikeyi da qarancin shekarunki haka ?muryarta a raunane tace “ba
komai ! ya kalleta na second biyu sannan ya d’auke kanshi yana rubuce rubuce tare
da cewa “karya ne kina tunani domin tunani ne ke kawo duk abinda kika lissafa”
shiru tayi ta rasa mai za tace likita ya dage lallai sai yaji damuwarta .”
numfashi ta sauke mai karfi tace “kawai d’an damuwar rashin samun aiki ne nan tayi
masa bayani kad’an acikin damuwarta likita yace “to shikenan ki daina yawon tunani
kisa allah a gaba ya rubuta mata magunguna suka koma gida da addua da rarrashin
ummah da aunty tare da yaya sadam dan yanzu kullum yana tare daita yana bata kulawa
har mamakinsa take kafin ya fita office zai shigo ya dubata haka idan ya dawo zai
shigo daga shi har mahaifiyarsa suna bata kulawa wanda hakan yasa maryama ta dawo
daidai ta cire zance samun aikinta aranta ta maida hankalinta akan zane .”ranar
wata lahadi tana zaune a bangaren ummah suna hira suka jiyo sallamar subai’a
ahankali ta d’ago idanuwanta ta saukesu akan kofar shigowa tana kallon subai’a
tsaye, sanye cikin wasu hadaddun kaya riga da siket tayi rolling kanta da mayafi
baki kafafunta sanye cikin baby shoe masu shegen kyau hannunta rike da leda kana
kallonta zaka fahimci rayuwa ya sauya mata daman kuma idan Z&A suka d’aukeka aiki
suna baka kudi masu yawa ka fara kimtsa kanka bare ita matsayin da take tasan zata
samu da d’an yauwa .”
hakan nan taji wani abu ya tsarga mata da sauri tayi qoqarin kawar dashi acikin
zuciyarta dake bugawa da karfi ta sakar mata murmushi wanda suka bayyana wushiyarta
sama da qasa .”ummah ma ta saki fuska tana “cewa subai ce a gidanmu yau .”?marhabun
lale da zuwa “cike da farinciki subai’a ta qaraso ciki ta durkusa har kasa gaban
ummah tana cewa “nice ummah ina yini ?lafiya kalau subai ya mamanki da kannenki ya
aiki kuma ?alhamdullahi mun godewa ta mike tsaye ta zauna kusa da maryama da
idanunta ke kanta har lokacin ga wani murmushi da yaki daukewa akan fuskarta .subai
ta kamo hannunta cikin nata “daga wajen aunty nake tace kina nan ya kike ya kwana
biyu ?lafiya qalau subai’a nayi kewarki sosai ,wallahi nima kina raina kullum da
tunaninki nake kwana nake tashi amman yanayin aikin dana iske a office babu
sauki .”
maryama tayi murmushi tana cewa “wallahi subai’a idan na ganki cikin farinciki sai
naji dadi a raina ”na gode kawata ina alfahari dake ta kalli ummah “umma ki tayani
godiya a wajen kawata ta sadaukar min da aikinta “allah ya taimaka ai yiwa kai ne
subai’a allah ya bata wanda yafi wannan amman maryamah ta nunawa duniya cewa ita
mai qaunarki ce ummah ta furta tana dubanta .”Sosai kuwa ai bazan ta’ba mantawa
daita arayuwata ba allah ya bar mana zumunci mu har ya’ya na haifi mace ta haifi
nmj mu had’asu aure ummah tai murmushi “to allah yasa muna da rai da lafiya maryama
ta mintsine cinyar subai’a tana cewa “dan son kai kece zaki haifi nmj ni kuma mace
salon ki dinga kwacewa d’ana yan kudadensa subai’a ta sosa inda maryama ta
mintsineta tana dariya “to shikenan ni na yarda zan haifi nmj ai duk ya’yana né
atare suka rungume juna cike da farinciki .”
bayan su natsa maryama ta mike ta kawo mata ruwa da abinci tare da janyo ledar
data shigo dashi tana cewa “kawata me kika kawo min né ?subai’a tace “bud’e kigani”
ta bud’e mayuka ne set da turaruka masu yawa har da pad aciki ta saki murmushin jin
dadi“tun kafin maryama tayi mgn tace” duk naki ne kawata .maryama ta dan zaro ido
“kai subai’a na kuwa go ..”no maryama kin wuce haka a wajena me ma nayi miki da
zaki gode min ?maryama ta mikawa umma ledar ta duba itama godiya tayi kuma yabawa
subai’a sosai .”ahankali subai’a take cin abinci suna hira da maryama a qalla sun
d’auki minti talatin zaune cikin parlour’n umma sannan subai’a ta kalli maryama a
karo na sau babu adadi “kawata kinsan karfin zuwanah yau din nan kuwa ?maryama ta
girgiza mata kai alamun a’a.”
“mr ATA mai kamfaninmu yana buqatar kwararrun masu zane a kamfaninsa na AGC shine
nace nazo na fad’a miki ko zaki shiga tsawu masu neman aiki akarkashinsa?”why not ?
me nake jira ?to ai kuwa sai shirya zuwa da samfurin zanenki kiyi sumit ta haka ne
zaa tantance sosai tayi mata qarin bayanin yadda tsarin yake “kai gsky kawata naji
dadin wannan labarin da kika zo min dashi na gode sosai,dan allah ki daina ai babu
wannan tsakaninmu “na ma yi tunanin ko mr ammar ya fad’a miki ,wallahi ko d’aya bai
fad’a min ba ai fushi yake dani .”fushi kuma ?”akan me zai yi fushi da yar gaban
goshinsa ?
“manta dashi kedai thank you so much I really appreciate “ko akan kin bar min
aiki ?kai nasan ma saboda shine yake fushi dake ,”nace ki manta dashi muyi wata
hirar yadda maryama ta tsinci kanta cikin farinciki haka ma ummah har murnata taso
tafi ta maryama sosai ta sake sakankancewa da subai’a lallai itama kawar arziki ce
daman sai hali yazo d’aya ake kawance ummah ta tashi ta shiga ciki domin ta basu
waje .”hira ce ta barke sosai atsakaninsu sosai maryama taji dadin zuwan subai’a
sunyi hira mai mahimanci da subai’a dan bata boye mata komai ba akan aurenta da
yaya sadam aiko tayi murna tare da mata fatan alkhairi” sai laasar sannan subai’a
ta mike tayi masu sallama ta kama hanyar zuwa gida.”
Zaune maryama take a d’akinta tayi nisa a zanen samfurin da zata gabatar a A.G.C ta
jiyo sautin muryar aunty tana kiran sunanta “Ina zuwa aunty “ sai dai shiru bata
mike ba ta cigaba da zanenta aunty ta shigo d’aki ta mika mata cup din tea” na gode
my world best kamr Kinsan ina bukata “ don’t worry my life is for my princess.
aunty ban san irin son da nake miki ba wallahi ina jin kamar na fasa auren nan na
cigaba da zama dake .”thank you so much my princess nima zanyi kewarki sukai shiru
na wani lokaci yayinda maryama ta cigaba da zane .”
“ maryama !”
da sauri ta d’ago daga abinda take ta tattara hankalinta dan duk sanda mahaifiyarta
ta kirata da wannan sunan abu ne mai mahimanci zata fad’a mata “nan kusa zakiyi
aure my princess Kinsan rayuwar gidan aure ba kamar rayuwar gidan iyaye bane ina
son ki sawa ranki cewar lallai sai sadam ya yarda zakiyi aiki sannan ki amince da
aurensa da zuciya d’aya sannan ki sonshi har cikin zuciyarki .”
Maryama tayi shiru tana cigaba da kallon mahaifiyarta .”me zai hana ki hakura ki
ajiye aikin ki rungume rayuwar aurenki “wani dogon naunayen ajiyar zuciya ta sauke
“aunty kina son aurena da yaya sadam kusan duk kinfi sonshi akan sauran wad’an da
suka nemi aurena a baya ?”sosai kuwa my princess ina son ki auresa , mahaifiyarsa
ta taimaka min arayuwa ,mahaifiyarsa mutunce da kirkinta ya wuce misali ,bancin
allah da ita da yanzu ban san makotana acikin gidan ba ,ta tsaya min ta tsayawa
ya’yana ta yanto min ya’yana daga bauta nasan bakisan dalilin da yasa aunty salma
da hassana suka daina bautar dake ba ?itace silar wannan ta kwatar min ‘yancinki
wallahi ko yanzu na mutu nasan ruhina zai samu salama tunda gabadaya kulawarki zata
koma qarqashinta .” ta qarasa maganar hawaye na cika idanunta .”
shiru sukai gbdy babu wanda yace uffan daga aunty har marayama kafin daga bisani
maryama tace “ amman aunty taya zan bar aikina dana rayu dashi idan ma na hakura da
aikin office aikin zane fa ?ban san ya zanyi ba bayan rayuwar nan babu tabbas “
amman shikenan aunty karki damu zanyi komai akanki haka qaddara rayuwata tazo yaya
sadam yazo cikin rayuwata ba dan ina sonshi ba na sasadaukar da rayuwata zan auresa
yanzu kuma ya zo ya rusa min komai nawa ,gbdy yayi distroyen rayuwata matukar bai
barni nayi aikina ba “ta ajiye pencil din zanenta tasa hannunta tai tagumi tana
kuka.”kuka take sosai har da sheshekan nan da nan hankalin aunty ya tashi “ki daina
kuka please!” me zanyi aunty ?”me zanyi daya wuce kuka tund bazan iya ja da
dukkanin umarninki ba “.
******
Zaune ATA yake a parlour’nsa tare da abokansa kuma yan’uwansa shawul,mb da salim
hira suke amman shi jifa jifa yake sanya masu baki “qarar takun takalmin maryam ne
ya janyo hankalinsu wani hill ne mai shegen tsini tasa wanda ya qara mata tsawo
daman kuma haka gabad’aya takalmanta suke bata da silipas sai na yawo acikin gida
da bayi sarai ATA yaga tahowarta ta qasan idanunshi itama ta lura da hakan amman
kuma sai take ganin kamar ba gaske bane , dan yadda yayi din bazaka ta’ba cewa ya
kalleta ba .a natse ta qarasa saukowa fuskarta a sake ta gaishe dasu “sannuku da
zuwa ina yininku ko ina kwana zance dan ban duba lokaci ba na sauko ?lallai yar
mami kinji dadin aure to ina yini muke “inji cewar mb shawul yace “wannan mijin
naki ne zai yarda azo masa gida da safe ai wallahi da sai ya tafattakemu.”
gabad’ayasu suka dariya ta d’an saci kallonsa taga ko kallonsu bai yi ba danne
danne kawai yake a wayarsa tace “a’a karku yiwa mijina sharri babu wani
fatattakarku da zai yi ta fad’a sannan ta samu waje ta zauna kusa dashi sukayi
mugun daf da juna da zata qara taku guda zata iya masauki a faffad’an qirjinsa
shawul ya kalli salim yace “lallai yarinyar nan wuyanki yayi kauri har kin soma
shigar masa ?.”
“ba dole ba miji ai ba wasa ba” zaro idanu sukai duk hirar da suke ATA yana jinsu
amman bai ce uhm ba bare uhm uhm sai ma wani kololon bakinciki daya tokare qirjinsa
yadda ta wani saki baki “yaya bello bari naje na shirya maku dining na dawo “ta
yunkura ta mike ta soma taku su kuma suka cigaba da kallon ATA mb yace “dan allah
dan annabi abokina ka sausautawa yarinyar nan haka “me nayi mata ?ya tamnayesa
batare daya kallesa ba ,bansani ba !kai ka iya wulakanta ya’yan wasu amman baka son
ayiwa taka ai wallahi hisham yayi min daidai da yake cin kaniyar auta “au kaniyarta
yake ci har yanzu kenan ?ya fad’a tare da kallonsa a fusace “shiru mb yayi “tmbyrka
nake kayi shiru kabani amsa kafin naje na samesa yanzu “to sarkin zuciya kwantar da
hankalinka maganar da né numfashi ya sauke “ko ma nene tunda ka furta akwai kamshin
gsky dole na ziyarci gidan “.
“Inna lillahi wa inna ilaihi rajiun “dan girman allah kayi hakuri kayi zamanka tare
da matarka ba sai kaje ka d’aga masu hankali ba ,yayi maganar kamar zai fashe masa
da kuka ganin yadda ya koma kamar ba soja ba yasa ATA yace “nonsense !kai wallahi
ko kasuwanci bai kamaceka ba bare aikin soja ni ban san yaakayi aka daukeka aikin
soja ba ,mutun kamar mace.” gbdy suka sa dariya shi kuwa ATA bai dara ba “ya zanyi
ai dole na kwatar da kai nasan halinka ne , haukanka bashi da magani yanzu sai ka
tashi hankalin kowa “suna nan zaune maryam ta dawo tana cewa “kona kawo abincin nan
ne ?yaya salim yace kawo kawai uwargida sarautan mata the only first lady Adam
tariq” nan da nan annurin fuskarta ya sake bayyana yayinda annurin fuskar ATA ya
d’auke qaramin tsaki yaja yana maida hankalinsa kan wayarsa ya cigaba da danne
danne.”
Cikin kankanin lokaci ta cika masu gabansu da abinci da kayan fruit kala dabam
dabam haka lemuka yadda take zuba kamshi haka girkinta ke zuba gamshi ta dan suguna
ta fara zuba masu mb yace “had’a min da abokina mun kwana biyu bamuci abinci tare
ba aiko murna ya kamata dan tasan da wahala bai ci ba,dole mb zai tursasa yaci ko
babu yawa ,ta godewa allah data barbade abincin kafin ta kawo gabansu abinda ake so
wanda daakayi aikin dominsa yaci ko yaya ne shikenan bukata ta biya .”maryam ta
goge gun da abincin ya taba zuciyarta fess sai sannu suke mata amman shi ATA sam
bai kula da ita ba ,ta juya domin dauko hadin salad shawul ya kalli abinci ya
hadiye miyo yana cewa "kai mutumina,irin wannan liyafa haka,gsky kana cin dadi
allah yayi da rabona ne shi yasa muka zo"kanka ake ji sarkin kwadayi,yi inji cewar
salim.”
Ta dawo a natse ta zuba masu hadin salad fuakarta dauke da mayalwacin murmushi sai
dai ta qagu ta kammala ta bar gun, tun dagowar farko ta lura da yadda ATA yake
faman zabga mata harara da sauri ta bar gurin ta samu waje ta zauna akan d’aya daga
cikin kujerun dining .da kyar da rarrashi mb yasa ATA ya fara qoqarin cin abinci
tana zaune rike da wayarta amman hankalinta kacokan yana wajensu tana Allah Allah
yaci ko loma daya ne tana kallo ya kai spoon bakinsa wani boyayayyen ajiyar zuciya
take qoqarin saukewa sai dai kafin ta sauke taga ya furzar da abinci yana kallon
inda take zaune .”
a fusace ya soma zuba mata ruwan bala’i “zaki kashe mutane ? ai daman nasan babu
komai acikin girkinki sai hauka haka ake girki .”?cool down ATA me ya samu abincin
nan ?bana son rainin hankali kai yanzu zakace bakaji abinda ya samu abincin nan
ba ?”uhm dan yaji ne kad’an amman wannan ai norma ne bazai sa kar aci ba. tsaki
yaja ya fara danne danne wayarsa text ya turawa auta cikin kankani tayi masa reply
dinsa dan hk batare da bata lokaci ba ya soma neman layin mahaifiyar maryam tare da
saka wayar a speaker dan wannna karon uwarta zai kira ba mahaifiyarsa ba, yadda
mahaifiyarsa ke biye mata tana d’and’anan bakinciki haka uwarta zataji yau .”
"hello Adam ya kake ? " muryar mahaifiyar maryam ya bayyana” inna ilaihi wa inna
ilahi rajiun maryam ta furta ba ita ba hatta su mb sun shiga tashin hankali mai
tsanani nan take mb ya girgiza masa kai alamun kar yace komai dan ya fahimci rashin
mutunci yake son yi amman ina ATA yayi kamar bai gansa ba " ammm yarinyar nan taki
aure aka kawo ta gidan nan ko kisan kai ?"a matukar razane maryam take kallonshi
tare da d’aura hannuwanta bisa kai cike da tashin hankali ta juya sai kuma ta dawo
ta tsaya ta maida kanta qasa yayinda tunin idonta suka canza kala sakamakon qwallar
data soma dan taruwa mata.” rashin mutuncinsa ya tashi daga kanta ya koma Kan
mahaifiyarta kenan ?”fatanta allah yasa kar mahaifiyarta ta biye masa .”
cikin faduwar gaba umma tace”Adam ina da baki yanzu amman me ya faru me maryam din
tayi haka ? ta tambayesa tana hadeye damuwarta " wannan shashar yar taki ce zata
kasheni da yan’uwana da yaji mai mugun azabar zafi ga maggie daman can baki koya
mata yadda ake girki bane kuka turota gidanmu tayi mana babakere har aka samu damar
makala min ita gashi zata kasheni ?ajiyar zuciya ummah ta saki "kasan yadda ka bani
tsoro kuwa ?yayi mata banza yana hura hanci “wallahi na d’auka wani gagarumin laifi
tayi da yayi kamanceceniya da kisan kai a she just akan yaji yayi yawa ne kake
wannan hauka?”
“what !?
eh !hauka mana menene aciki dan yaji yayi yawa cikin abinci ?nan da nan jikin
maryam ya kama rawa bata san sanda ta qaraso kusa dashi ba tana cewa “umma dan
Allah! ke rufe min baki anan idan Ke zaki dauki iskancinsa dan kina son zama dashi
ni ba son shi nake ba kuma ba qaunar zamanku dashi nake ba bare na
lallabashi ,tunda aka haifesa ya girma yake cin yaci a gidan uwarsa bai yi complain
ba sai yanzu ?ko sau nawa muke cin abinci uwarsa mai mugun yaji kamar zaa bawa
mutun maita bare nasan duk zabga yajinki cikin abinci bazaki taba kai uwarsa ba
“.wani irin mugun kallo ATA yayi wa maryama yana qoqarin damko wuyanta .”
Mmn sudais
💗💗💗💗💗💗
MAR'ADAMS
💖💖💖💖
💗💗💗💗💗💗
*AYSHA A BAGUDO*
WATTPAD @HAUESH
AREWABOOKS USERNAME
AYSHAABAGUDO
bismillahirrahmanirrahim
Wannan littafin na kudi ne mai bukatar karantashi byn na kammalashi zai biya
1000 ta wannan account number din 1438775094 Aishat abdullahi access idan an tura
sai a turawa wannan 09136918331 alert domin tabbatar da an tura domin sauraron
littafaina a tuntubi chaneel dina (Hausa bakwai ) a YouTube.
Page 14
Da sauri maryam taja baya hankalinta na sake tashi yayinda MB yay sauri ya shiga
tsakaninsu yana shafa qirjinsa alamun ya kwantar da hankalinsa inda sautin muryar
umma ya cigaba da fitowa cikin munanan kalamai masu zafi “yaji da maggie ne
kawai suka yi yawa cikin abinci ka wani d’aga wa mutane hankali , tana sane zata
aikata hakan ne ?” babu wanda ya wuce ya samu irin wannan problem din a girki ,zai
iya faruwa akaina ,zai iya faruwa akan uwarka hakazalika zai iya faruwa akan
kowace mace “.rawar da jikin maryam yake ya qaru taji qafafuwanta suna barazanar
kasa d’aukarta lokaci guda taji zuciyarta na barazanar tarwatsewa “shikenan umma ta
kasheta da ranta dan tasan yau mai kwatarta a hannun yaya Adam sai allah.”
shawul da salim mikewa sukai suna dubansu cikin tsananin kad’uwa da tashin hankali
zasu iya cewa yanayin da suka ga ATA a yanzu basu ta’ba ganinsa cikin irin yanayin
ba “enought is enough Adam maryam ba baiwa bace ta fad’a a tsawace sannan ta
cigaba da magana “inda ya kamata a d’aukar mata masu aiki bilaadadin suyi mata
hidimar gidan amman ita ta hakura ta kwantar da kai tana bauta maka bayan ta gama
bauta wa uwarka shine zaka zo ka saka min yarinya a gaba ?”to wallahi kaji na
rantse bazan d’auka ba, rashin mutuncinka ya tashin akan maryama ya dawo kaina
wallahi adam I can’t take it any more duk kuma abinda ya samu yarinyata bazan duba
sanayya dake tsakaninmu ba kotu ce zata rabamu da kai idan kuma kana ganin babu
abinda zai faru dan girman allah ka gwada idan kace kai surukin zamani ne to ka
had’u da surukar zamani kuma daidai da kai .”
“Inna lillahi wa inna ilaihi rajiun “shikenan umma kin sake sakani cikin tsaka mai
wuya “me zai miki ?kima kwantar da hánkalinki babu abinda zai miki “umma …!”ta kira
sunanta a rud’e tare da wani irin kuka mai karfi dake fitowa daga qarqashin
zuciyarta so take ta cigaba da magana amman kukan da take ya hanata ,bata ta’ba
tsintar kanta cikin tashin hankali irin na yau ba, wani dogon tsaki ATA yaja sannan
yay discounting din kiran alokacin da umma take qoqarin son cigaba da magana ya
yiwa MB alamar ya matsa daga gabansa domin ya isa ga maryam “dan girman allah karka
mata komai "oh my god MB ka matsa daga gabana nayi ma yarinyar nan abinda uwarta
zata kai ni gaba da kotun koli ".
“ ka natsu muyi magana first “no way !” ya fad’a a fusace tare da d’aga hannusa
salim da shawul har da mb suka matsosa tare da rikesa suna bashi hakuri wanda dole
tasa ya kasa aiwatar da nufinsa yayi shiru kawai sai dai ilahirin jikinsa rawa
yake”yayinda maryam ke kallonsa ,banda kuka babu abinda take tana bashi hakuri
amman wani sabon tashin hankali take hangowa a tattare dashi a matukar rikice ta
kallesu “dan girman allah ku kira mami ita kad’ai ce zata..” wani mugun kallo ya
d’auketa dashi da idanunshi wad’an da gbdy sun canza kala “adam ! wai me yasa baka
iya control din fushinka ne ?! ATA bai iya cewa komai ba sai ma zuba masa rinannun
idanunshi da yayi yana dubansa .layin mami salim ya soma kira domin dai shi
kanshi ya tabbatar ita kad’ai ce zata iya sauko dashi daga fushinsa yayinda MB
yayiwa maryam alamu da idanunshi cewar ta bar gurin .”
babu musu maryam tabi umarnin MB da sauri ta haye sama jikinta na rawa ta shiga
d’akinta ta d’auki wayarta ta soma kiran layin mahaifiyarta tana d’auka tasa mata
kuka .”haba umma haba ummah!! “mai yasa zakiyi min haka ?wallahi idan kinyi haka ne
dan ki kwatar min ‘yanci to kisani kin sake jefa rayuwata cikin mummunar bala’i ne
“daga can bangaren umma ta fusata “kenan tashin hankalin mijinki kike jin tsoro
akan abinda yayi min ?maryam tayi shiru tana goge hawaye “gif haka ATA ya zauna
saman kujera yana qoqarin runtse idanunshi cikin murya mai cike da tashin hankali
yake furta “muddin ban canzawa yarinyar nan kamani ba to shege ne cikin uwata da
ubana “kayi hakuri dan allah itama fa kamar mahaifiyarka ce karka manta danganta
dake tsakaninku ko babu maryam atsakaninku ita din matar kanin mahaifiyarkace “.
“amman ai kunji irin maganganun ta gareni da kuma mahaifiyata ?munji amman kai ma
ai abinda kayi bai dace ba ,bai kamata ka kirata kana fad’a mata son ranka ba “ya
d’ago kwayar idanunshi yana duban MB wanda shima tashin hankali ya nuna a fuskarsa
lokaci guda ATA ya cigaba da fad’in “but MB how dare her talk to me like that “?
mahaifiyata fa ?yanzu sweetheart ta cancanci haka “?ya mike tsaye yana girgiza kai
yana duban MB da salim dake rike da waya da karfi ya shiga jijiga MB “MB
Mahaifiyata fa ?! “zagin ma ya wuce kaina har mahaifiyata she could have kill me
akan cin mutuncin uwata da tayi.” yadda yake maganar zaka fahimci yana cikin
tsananin damuwa .”
kamo kafad’unsa MB yayi ya zaunar dashi a saman kujera yana qoqarin calming dinsa
“plse ATA try to calm down d’ago idanunshi yayi wad’an da gabad’aya a rikice suke,
kau da kai gefe ATA yayi yana sake tariyo abubuwa da ummah ta fad’a masa lokacin
guda ya dunkule hannuwansa yana murzasu waje d’aya .”shawul ya qaraso ya kamo
hannun ATA yana dubansa cike da tausayawa dan gsky shima bai yi sa’ar samun
suruka ba ,sam sam bai yi exepeting haka daga mahaifiyar maryam ba ,yadda yake
kallon maryam ya d’auka mahaifiyarta zata fita saukin kai a she abun ba haka
bane . ATA huci mai zafi ya furzar sannan ya mike ya isa jikin window ya zuba
hannuwansa duka cikin aljihun wondonsa cikin rashin sanin abinda zai yi.”
suna tsaye cirko cirko mami ta shigo cikin tsananin tashin hankali tana kiran
sunansa “where’s adamcy ?
”Kasa juyowa yayi sai dai jin muryarta ya soma qoqarin saisaita kanshi ,MB ya
numfasa wanda har lokacin yana tsaye ya tsurawa waje d’aya rinannun idanunshi,
dafashi yayi yana fad’in “try to calm down ga mami tazo karkayi abinda zai ‘bata
mata rai “duk kuna nan zaune aka dinga ciwa mahaifiyata mutunci babu wanda ya taka
mata burki ,kodan dan ba mahaifiyarka aka zaga ba ?” MB yayi shiru yana dubansa
daman kuma haka yake duk sanda ransa ya ‘baci he can talk nonsense. ya sake dafashi
yana qoqarin cigaba da magana “ don’t ever ask me to calm down again .” yayi
maganar jijiyoyin goshinsa na sake fitowa sosai gumi na kuma tsatsafo masa kafin
ATA ya sake cewa wani abu mami tace “wai meke faruwa ne ?!.
“salim tunda ka kirani jikina ke rawa haka ma zuciyata bugawa take fiyye da kaida
ina maryam take tukun ?shiru sukai gabad’ayasu “kunyi min shiru ,ku fad’a min
abinda Ke faruwa “mami ki zauna first zan miki bayanin komai “inji cewar salim
“ina maryam take ina son nasan halin da take ciki kafin komai ?“maryam tana
lafiya babu abinda ya sameta tana sama ya fad’a yana kamota ya zaunar daita akan
kujera yayinda MB ya janyo hannun ATA ya zaunar dashi bai d’ago kanshi ba
sakamakon zafin da zuciyarsa keyi masa tunda yake babu wanda ya taba ciwa
mahaifiyarsa mutunci sai yau .”
“Ku sanar dani abinda Ke faruwa tun kafin zuciyata ta tsaya ta daina aiki
gabad’aya “MB ya bud’e baki zai yi magana kenan ATA ya d’ago tare d’aga masa hannu
ya janyo wayarsa ya shiga recond dan tunda ya fahimci rashin mutunci ummah zatai
ya danna record ya kunna ya tura wayar gaban mami nan take sai ga muryarta ta
bayyana ,mami tai shiru tana sauraro tare da runtse idanunta abun ya girgizata
matuqa ,kuma yayi mata zafi duk da tasan halin d’anta he can talk rubbish and
nonsense idan rashin ya’baci amman ai ita bata cancaci haka a wajen madina ba”
mami ta numfasa irin nasu na manya tana dubansu, sannan ta soma magana a natse “duk
me ya kawo wannan tashin hankali haka ?”duk sukai shiru “ lallai akwai abinda ya
faru bancin haka ina da yakin madina bazata aikata haka ba ?gabad’ayansu suka tsaya
suna duban mami suna duban ATA “magana nake daku kuna jina kun yi min shiru kuna
dubansa ?MB ne yayi karfin halin fad’a mata komai daya faru “tabbas mami abinci
yayi yaji da maggie amman ban so yadda adam yayi react ba.”
“ yanzu sweetheart baki ji zafin abinda tayi ba ?to ko naji zafi adamcy ya zanyi ?
wa yaja min cin mutunci da akayi min ? da bakayi ma madina rashin kunya ba
bazatayi min haka ba dan bata isa ba ,nafi karfin ta fad’a min haka .”ta karshen
maganar cike da jin zafi dan da zaa bud’e zuciyarta bakinkirin zaa gani tsabar
ciwon da taji amman babu yadda zatayi dan kuka shi ke jawowa uwarsa jifa “ATA bai
ce uffan ba har ta gama maganganunta sai dubanta da rinannun idanunsa yake “yanzu
nasan zakace zaka huce akan maryam “?ta tambayesa tana tsaresa da ido wanda ko
motsi mai kyau ya kasa sai ma damke hannunwan sa da yayi ,mami ta gyara zamanta
tana karantar d’anta tasan halinsa tasan abinda zai yi da wanda bazai yi ba
“tunaninka a yanzu yadda zaka huce akan maryam kakeyi ko?still shiru yayi ya kasa
cewa komai dan ya ma rasa mai zai ce amman tabbas tunaninsa kenan ,mami ta dubi MB
ta kuma dubi salim da shawul “ku sheida muddin adamcy ya ta’ba lafiyar maryam ban
yafe masa ba “ta fad’a tana dubansu d’aya bayan d’aya nan taga yanayin ATA ya
sauya tamkar wanda aka cirewa laka ajiki sai dai zuciyarsa tayi bakinkirin jin
abinda mami ta fad’a.”
ahankali mami ta yunkura ta mike ta nufi hanyar step bata tsaya akoina ba sai
abakin kofar d’akin maryam ta tsaya sai dai hakan nan zuciyarta ta dinga rawa rawa
har ta kai hannu zatai knocking sai kuma ta sauke hannunta tana nazarin
zuciyarta .”ahankali ta tura kofar d’akin ta shiga maryam na tsaye ta juyawa kofar
d’akin baya tana sheshekan kuka “inda acan bangaren ummah take cewa “wallahi
maryam wannan miji naki ya zame miki damuwa arayuwarki amman bamu da yadda zamuyi
tunda allah ya jarabeki da mutuwar sonshi amman idan muna son muyi nasara akanshi
dole sai munyi abinda zamu rabashi da tunaninsa dole ya zama abokin rayuwarki ya
shiga jikinki ki shiga nashi ku zama abu d’aya “mai zanyi ummah da zan samu wannan
matsayi a zuciyarsa ?”ya kusanceki shine cikar burina a yanzu bayan ya kusanceki
ina fatan kuma ya zama “d’a “zan so faruwar hakan “amman ummah ta yaya hakan zai
faru a tsananimu ?Kai nifa gsky ummah na gaji na
gaji !! da yin amfani da magungunan da kike aiko min dashi dan baya ci komai daga
gareni “wallahi kuwa duk wannan bala’i da yayi bana tunani ya had’iye abin…“.
“Maryam !” mami ta kira sunanta a matukar firgice ta juyo ganin mami tsaye tayi
saurin sauke wayar a kunnenta tare da kashewa tana dubanta jikinta na kyarma kafin
ahankali tace “a’a mami har kin zo ?sannu da zuwa mami ga waje ki zauna ,tayi
mgnr a rud’e cikin rawar jiki ,mami tai mata duban natsuwa sannan tace “ban jima
da zuwa ba daman kin san zan zo ne ?ta gyad’a mata kai alamun eh !“ai nice ma nace
yaya salim ya kiraki ta fad’a tana duban mami mami tayi shiru itama maryam tayi
shiru cikin rasa abinda zatace dan hankalinta yayi matukar tashi adduarta d’aya
allah yasa bataji maganarta ba.
cikin zafin nama mami tace “ya kikayi shiru haka ?ta girgiza mata kai tana cewa
“babu komai “dawa kike waya “? muryarta cike da tashin hankali tace
“ummah!”okay !”amman ya’akayi maryam kika bari yaji da maggie yayi yawa acikin
abinci?naunauyen ajiyar zuciya ta sauke dan ba abinda tayi tsamanin zai fito daga
bakinta kenan ba duk tunaninta mami taji maganarta cikin rawar murya tace”wallahi
mami bada niyya bane sautsayi ne kawai sai gani nayi ya kira umma yana fad’ar
maganganu marasa dadi .”
Mami ta numfasa kana tace “kiyi hakuri maryam nasan adamcy baya kyautawa kuma bai
kyautawa ummanki ba kuma naji dadin abinda tayi masa allah yasa ya zame masa darasi
kuma nayi masa gargadi mai karfi akanki dan haka ki kwantar da hankalinki babu
abinda zai faru kinji diyata mami ta riko hannunta ta zaunar daita a saman kujera
tana cewa “kema ki dinga kula most especially akan girki .
“ba tun yau nake fad’a miki ba ,ba’a són maggie da yaji na zarcewa abinci ,a
wannnan rayuwar da muke ciki idan nmj na tsananin son mace ko bata iya girki ba ya
Kan yi hakuri yayi rayuwa daita a yadda take amman Idan tana da matsalar girki ko
tsaftacce muhalli da jikinta kuma akayi sa’ar babu so tsakaninsu to shi yafi komai
rashin kwanciyar hankali dan kuskure kad’an zatayi zai zame masu damuwa .“ina
sonki da adamcy shiyasa nake yawon jan hankalinki ,ki dinga kula daidai girkin da
zakiyi daidai maggie da yajin da zakiyi amfani dashi ,karki lura da yanayin girkin
da’ake nunawa a social media kice zakiyi amfani dashi a’a suma suna duba yanayin
yawon girki ne ,dan haka ki dinga duba yanayin yawon miyarki ko qanqantarsa , ki
dinga kula kinji allah ya baku zaman lafiya .”
Zuciyar maryam tayi fari qal farinciki biyu suka hade mata fahimtar mami bataji
komai ba da kuma tabbatar mata dole ATA yayi hakuri ya barta batare da yayi mata
komai ba ,ta mike tsaye tare da riko hannu maryam suka fito zuwa parlour’n kasa
“nayi closing case din nan kuma har abada banason naji an sake ta dashi ATA ya
gyara zama yana mai shan mur sosai ,kafin ya soma girgiza kafarsa d’aya cikin
tsananin bacin rai yana duban mami “zanyi maka gargadi na karshe adamcy for the
last time karka sake kiran madina da magana irin makamanciyar wannan dan ba
abokiyar wasanka bace, uwarka ce duk abinda zai faru a tsakaninka da maryam ka
barshi a tsakaninku .”tana gama fadar haka tace “ni zan koma gida allah yayi maku
albarka gaba d’ayansu har maryam suka fito yiwa mami rakiya amman banda ATA dake
zaune cikin tsananin ‘bacin ran bai samu damar cin uban maryam ba “.
Maryam taja mami kusa da motar data kawota tana cewa “mami na gode sosai bancin
inada ke da bansan ya rayuwata zata kasance acikin gidan nan ba na gode na gode !!
allah ya shirya miki zuriarki Allah kuma ya jikan iyaye “nima na gode maryam allah
yayi maku albarka mami ta d’an yi shiru can kuma ta numfasa sannan ta fuskanceta
da kyau “maryam kamar koda yaushe ga d’ana adam ,a kullum shi masa albarka nake,
duk da abinda nake masa akanki ba wai banason shi bane a’a kema kinsani adamcy
raina ne ,ina matukar sonshi fiyye da komai ban had’a shi da komai ba ,duk
abinda ya shiga raina ya kan shiga ransa ya zauna daram ,sai dai a waje d’aya
muka samu sa’banin ra’ayi shine aurenki dashi wanda yaki ya kar’ba uzurin da nazo
masa dashi nasan yadda yake jin radadi zama dake amman nasan da sannu zaki zama
jinin jikinsa “ki cigaba da hakuri da adamcy kinji ,ta gyada mata kai tana wasa da
yatsun hannunta “ki kular min dashi karki manta adamcy amana ne agareki sai kinyi
hakuri dashi kafin kiyi nasara akanshi “cikin rawar murya tace “in sha allahu mami
zan kular miki dashi ta qarasa maganar cike da tausayawa mami .”
“Anya kuwa tayiwa mami adalci da take son biyewa mahaifiyarta ?”tayiwa zuciyarta
tambaya nan take gur’bataccen zuciyarta tace “adalcin kenan kina tsananin sonshi
ita kanta mami tana son faruwar haka kuma zata fi kowa jin dadi idan zamanku ya
daidaita dashi “sai na kuma zuwa wanda ina fatan ziyarar da zata kawoni ba sulhu
bace alkhairi ce ta fad’a tana shiga mota maryam ta rike murfin motar tana ce mata
“bye mami !”bye maryam take care of adamcy ki rike min amana “jiki a sanyaye ta
gyada mata kai daga nan sukai sallama har dasu mb wad’an da basu koma ciki ba
kowannensu ya kama gabansa.” tamkar mara laka ajiki ta shigo tana dubansa a tsanake
yanayinsa gabad’aya ya sauya daga zafi zuwa sanyi ta wucesa hankalinta kwance dan
tasan babu abinda zai faru ta haye sama tana jujjuya masa jiki amman shi ko kallo
bata ishesa ba dan bai ga abinda zai burgesa ajikinta ba bare ya kalla.”
Tana shiga d’akin ummah ta fara kira “bangaren ummah tmbyrta tayi” wacece tazo
“mami ce !”ta bata amsa” yanzu yaake ciki ?komai ya daidaita kinsan halinsa zuma ne
sai ancisa da wuta ake zaman lafiya “ai zagewa zakiyi ki dinga cin ubansa ,maryam
ta zaro ido waje tana dafe qirjinta tare da cewa “ummah ki rufa min asiri wallahi
bazan iya ba “to shikenan daman idan lalla’bawa yaki bud’e wuta shine
mafuta ,banda yaya adam bazai d’auka ba idan baso kike ya nakasa miki ni ba” karki
damu nan kusa zai gane shi din ba kowa bane, wallahi duk wannan zafin ran da
zuciyar zaki nemasa ki rasa akwai maganin da zan aiko miki akarkashin gadon
baccinsa zaki saka masa da zarar ya Kwanta sai dai ya tashi da muguwar soyayyarki
,zai manta soyayyar kowa sai taki dan a cewar malamin har uwarsa sai kin tuna masa
wacece ita agaresa ,amman malamin yace matukar aka sakashi akarkashin gadonsa yayi
kwana uku bai kwanta ba aikinsa ya karye ,ai kina samun damar shiga d’akinsa?wannan
ba damuwa bane dan bai fiyye rufe d’akinsa ba yanzu haka d’akinsa a bud’e yake
yanzu yaushe za’a turo ?gobe da dafe “nan suka cigaba da tautaunawa.”
Shiru ATA ya cigaba da yi zaune he’s thinking of what his going do to her dan
zuwa mami bazai sa na barki haka ba ko ban ta’ba lafiyar jikinki ba tunda anyi min
iyaka zan yi punish naki cikin ruwan sanyi I can never leave you at all saboda duk
wannan abun da sweetheart take ,so take ta kawar da tsorona acikin zuciyarki and I
will never let it happen “what’s your gain in this ? kwakwaluwarsa ta aikawa
zuciyarsa tambayar “my gain is that I don’t want her to be happy at all bana son
taji dadi wannan shine ribata a zamana daita kullum so nake naganta cikin damuwa a
qarshe ta tattara ta bar rayuwata “this is very bad adamcy zuciyarsa ta sake fad’a
masa haka ahankali ya girgiza kai yace “a’a it’s not mikewa yayi a natse cike da
kwarin gwiwa ya nufi step da sauri sauri yake takawa ya shiga d’akinsa ya sauya
kaya ya d’auki duk abinda yake bukata ya sauko ya rufe kitchen ya zare key tare da
fitowa zuwa haraban gidan yana bawa masu tsaronsa umarni cire wutar gidan ,sannan
ya kulle kofar shiga ciki sannan ya bawa masu tsaron get umarnin kar abar duk wanda
yazo ya shiga ,ya shiga mota suka bar gidan .”
Maryam na zaune tana waya taji wuta ta d’auke amman son jiki ya hanata tashi ta
cigaba da waya bayan sun gama waya ta shiga social media sannu ahankali idanuwanta
suka fara mata yaji alamun bacci ,ta ajiye wayar a gefenta ta kwanta nan da nan
bacci ya d’auketa, ba ita ta tashi ba sai karfe shida da kyar ta yunkura ta mike
ta shiga bayi ta d’auro alwala tana mamakin daukewar wutar gidan alhalin yana gida
tunda tazo wutar gidan na d’aukewa ake kunna dizu .jiki a kasalance ta fito ta
gabatar da sallah laasar byn ta idar ta mike ta fito kai tsaye kofar d’akinsa ta
nufa ta murd’a tajita a kulle shiru tayi kafin ahankali tayo hanyar step ta sauko
qasa bata gansa ba tayi tunanin fita yayi dan haka ta soma tattara kayan abincin da
sukai amfani dashi sai dai tana isa bakin kofar kitchen taji gam kofar a rufe
handling ta kalla taga babu key ajiki .
Mamaki ya kamata nan take kuma taji tashin hankali mai tsanani yana shigarta
kwakwaluwata ta fara hasko masa wasu abubuwa “kar dai yaya adam cire wutan gidan
yayi ?babu shakka cire wa yayi tun da gashi ya kulle mata kitchen jiki a sanyaye ta
dawo rike da kula ta ajiye akan table ta zauna jagwab akan kujera tana dafe
goshinta “what’s all this ?ta furta tana zaune har bakwai tayi lokacin duhu ya
shigo sosai ,ta yunkura da kyar ta mike ta nufi kofar fita da niyyar bawa masu
tsaron gidan umarnin su kunna mata wutan gidan tana murd’a kofar tajita gam nan
wani sabon mamaki da tashin hankali ya ziyarci ilahirin jikinta “mai haka yake nufi
?tayiwa kanta tmbyr “ki koma d’aki ki jira har sanda zai dawo “nan take ta amince
ta koma d’akinta ta d’auki waya lokacin sauran kad’an cajinta ya qare a 10 percent
yake ,ta ajiye wayar akan sallayya ta sakê shiga bayi ta d’auro alwala tayi sallah
magrib byn ta idar ta d’auki wayarta what’s ta shiga tana duba sakonin qawayenta
dana yan’uwa.”
Tana nan zaune har takwas tayi ta mike ta gabatar da sallah ishai, byn ta idar ne
ta d’auki wayarta taga battery low tayi tunanin kiran nana hauwa’u number na soma
ringin wayar ta matu gabad’aya“inna lillahi .”ta furta a fili tare da mikewa ta
kullo kofar d’akinta ta dawo jikin window d’akinta bata hango masu tsaron gidan
ba kasancewar window d’akinta ta baya yake ,labule ta d’an zuge ta bar net awa
d’aya tazo ta wuce shiru bai dawo ba wata awa d’aya tazo ta sake wucewa goma da
wasu mintuna amman shiru babu alamunsa sam bata ji tsoron komai ba ta cigaba da
zama ita kad’ai yunwa data soma ji ne ta fahimci lokaci ya tafi .ta bud’e kofarta
wani mugun duhu tagani ko tafin hannunta bata iya gani ta fito tana shafa bango.”
Ahankali ta dinga tafiya daf da zata sauko daga step ta tuntsura ta fad’i akan
goshinta wani azababben zafi ya ziyarceta ta dafe goshinta tana runtse ido tana
jin kamar tayi kuka ,rarrafawa ta cigaba dayi har ta samu ta gano inda center
table din yake da hannuwanta duka take lalube allah ya taimaketa hannunta ya sauka
akan plet din abincin data zuba masu bata tsaya neman na kula ba ta d’auka ta
soma ci ,abinci yayi sanyi sosai amman bata da zabin da wuce taci ,tas ta lashe ta
koma laluben ruwa da kyar ta gano ruwan roba ta kafa abakinta bata cire ba sai data
shanye tasss sannan ta ajiye roban tana sauke numfashi ta soma qoqarin komawa sama
wannan karon da kyar ta gano hanyar step dan ta kusan minti shabiyar tana
shawagi.hankali ta hau saman katifarta ta kwanta abunta , matsalarta a yanzu
wayarta da babu caji dan ita idan tana da caji a waya bata da damuwar komai nan da
nan bacci ya dauketa sakamakon babu abin yi.”
Washegari ma haka ta yini babu wuta babu ATA tayi tunanin zai dawo gida da daddare
amman kamar jiya har karfe d’aya na dare idanunta biyu acikin duhu bai dawo ba
gabad’aya hankalinta ya tashi damuwa ta saukar mata na rashin wuta da kuma rashin
miji ita dama kulleta kawai yayi ya bar mata wuta ,ranar ma haka ta kwana cikin
duhu dan abinci yunwa tasa taci abincin jiya ruwa ne dai ta koma shan na bayi dan
ta shanye wanda yake Kan table ,ahaka tayi kwana biyu wanda zuwa lokaci bata iya
cigaba da cin sauran abincin, ruwa kawai take sha tayi kuka har idanunta suka
kunbura “da wannan punishment din ai gara dukan mutuwa yayi mata ,tayi datasanin
zuwa mami domin kuwa shine ya jefata cikin halin da take ciki yanzu ,dan da yayi
mata duka bazai mata punishment ba .”
Da misalin karfe tara na dare nana hauwa’u na kwance akan cinyar yaya hishsm
jikinta sanye da wasu hadaddun kayan bacci iya gwiwa wadan da suka d’an bayyana
surar jiknta yayinda gashin kanta ke kwance wanda ya sha gyara sai sheki yake ga
wani sihirtaccen kashi dake tashi a gabadaya sansar jikinta ,ta kamo yatsun
hannunsa na dama guda biyu ta zira cikin bakinta tana tsotsa ahankali inda kasala
ta dinga saukar masa ,gabad’aya ya d’auke hankalinsa akan kallon da yake ya maida
kanta, ya dinga jin kamar tana tsira masa allura ne a gabad’aya ilahirin
jikinsa ,numfashi kawai yake janyowa yana saukewa da sauri sauri .ya lumshe
idanunshi adaidai lokacin da wayarsa ta soma ringing ya bud’e idanunshi da kyar ya
d’auki wayar ya duba sunan wacce ya gani ne yasa shi ajiye wayar ya cigaba da
kar’ba sirrintaccen sakon nana hauwa’u kira ne ya cigaba da shigowa babu kaukautawa
da zarar ya duba yaga mai kiran zai ajiye .”
Ahankali ya kai hannu yana shafa fuskarta bayan kamar minti talatin wani kiran ya
sake shigowa ya kai hannu ya d’agata ya saka mata qaramin pillow yana cewa “bari na
amsa kiran nan idan ba haka ba bazaa barni na huta ba .”bata iya kwanciya ba tabi
bayansa da kallo alokacin da tuni ya d’auki wayar yana cewa “ina gida mai yasa
bakya son zaman lafiya ne ?iyakar abinda kunnuwanta suka jiyo mata kenan ko baa
fad’a mata ba tasan da wacce yake waya ,tashi tayi ta zauna tare da rafka tagumi
cikin zullumi da rashin sanin madafa tunaninta abu d’aya ne a yanzu tana tsananin
qaunar mijinta musaman a yanzu da take hango tarin soyayyarta mai tsanani acikin
kwayar idanunshi sai dai batasan me zatayi ta raba mijinta da nuzla ba ,bata da
tsarin yi mata mugunta ko rashin mutunci kawai burinta ta bar rayuwarta data
mijinta cikin sauki itama ta ji dadi rayuwar aure ahankali ta koma ta kwanta tana
jin damuwa da kishi mai tsanani tasa tafin hannunta ta rufe fuskarta dan kar ya
dawo ya fahimci halin data shiga .”
mintuna goma ya dauka ya dawo ya tayar daita zaune yana gyara mata gashinta daya
baje kallonsa tayi tare da sakar masa kasalallen murmushi ya shafi gefen fuskarta
tare da bude baki yace “yaya ?lumshe masa ido tayi cikin laushin murya tmkr babu
abinda ke damunta tace “babu komai ! tsura mata ido yayi yana son gano wani abu
atattare daita amman ya kasa fahimtar komai saboda murmushin dake kwance a
fuskarta, ya zauna kusa daita amman gabad’aya attention dinsa na kanta suka cigaba
da kallo wani kiran ne ya sake shigowa kamar d’azu kasa d’aga wayar yayi nan take
ta fahimci saboda ita ne baya son ya d’auka dan haka tun kafin ya tayar daita
ajikinsa ta yunkura ta mike zata bar wajen dan bashi damar amsa wayarsa ya riko
laulausan tafin hanunta yayi mata masauki akan cinyarsa yana kallonta ta kai
hannunta tana shafa sajen fuskarsa batare datace masa komai ba.”
riko hannunta dake gefen fuskarsa yayi tare da shafo gashinta har zuwa fuskarta ya
zarce saman dukiyar fulaninta ya soma shafawa yana kallonta cikin wani irin yanayi
da kyar ya bude baki “ina zaki tafi ki barni bayan…” “you have something to do ta
katseshi ta hanyar fad’ar haka girgiza mata kai yayi “babu wani abu mai
mahimanciki yanzu .”tayi murmushin maganarsa tare da kai hannunta ta cigaba da
shafa fuskarsa zuwa qirjinsa bata sake cewa komai ba.sake tsareta da ido yayi “ina
son smile din nan naki duk nacin mutun idan kina yinsa bazai ta’ba fahimtar
damuwarki ba ,yana cikin abinda yasa kika kwacewa nuzla hisham dinta da soyayyarta
“kallonsa tayi gabanta na fad’uwa saboda sunan daya ambata ta sunkuyar da kanta
tare da shigewa jikinsa “soyayyar nuzla dabance acikin zuciyarka kuma tayi tasirin
da babu wata mace a duniya data isa ta kwace mata .”
“shiru yayi kafin daga baya ya kai bakinsa daidai kunneta sai daya sauke mata hucin
numfashin bakinsa “wani irin yanayi ta tsinci kanta ciki dan gabad’aya tsigar
jikinta sun mike “ki yarda dani auta hakurinki ,biyayyarki ,kawar da kanki akan
komai tuni sun fara sani jin kunyarki ta yadda bazan iya daukar wayar kowa ce irin
mace agabanki ba “hakika sai yanzu nake farinciki da zabin momy nah kuma tun baaje
koina ba na fara alfahari da hkan a halin yanzu zuciyar hisham taki ce sai yadda
kikayi dashi . ta d’ago kanta da sauri ta tsura masa fararen idanunta “ki yarda
dani auta bazan qara cutar dake ba a yanzu ni masoyinki ne na gskiya ina da yakinin
nafi kowa sonki “.
a hankali ta kwatar da kanta a qirjinsa tana balle botiran gaban rigarsa ta soma
shafa wuyansa zuwa qirjinsa adaidai Kan nipples dinsa ta tsaida hannunta cak wani
irin wahallen numfashi ya sauke da karfi yana mai qara kwatar da murya sosai “ina
sonki fiye da soyayya kowa da yake miki acikin duniyar nan a yanzu kece rayuwata
“dan allah yaya hisham kana sani jin kunya jin kalmar so daga bakinka “ya janyota
sosai jikinsa suna fuskantar juna “kalli cikin idona auta babu abinda zaki gani
face tarin soyayyarki kema kuma nasan kina sona “
Tayi shiru taki cewa komai ta sake shigewa jikinsa ta kwanta luf ta cigaba da
shafasa “karki cutar damu auta “ta d’an saci kallonsa cikin salon jan hankali “ya
lumshe mata ido yana cewa “yes dan nasan kema kina sona kuma kina jin the same
abinda nake ji akanki “ya zakayi da soyayyar nuzla ?itace damuwarki ba ?ya
tambayeta yana shafo turming dinta “.
“Shiru tayi kawai ta kasa mgn “shafa lafaffen cikinta ya cigaba da yi yana shige
mata yana lumshe ido “kinyi shiru auta nuzla ce damuwarki ko ? tabbas nuzlah
damuwa ce agareni amman dan allah karka cutar da zuciyarta domin yanzu kowa yasan
tana sonka “ki manta da maganar nuzla “bai kamata ba .ya bude idanunshi da kyar ya
tsura mata “ka aurota kawai tazo muyi rayuwa tare tayi maganar gabanta na faduwa”ki
fara bani ragamar rayuwarki naja tukun kafin ki shigo da maganar wata ya qarasa
maganar yana matseta ajikinsa “uhm halin maza sai su sam sam canzawarsu bai da
wahala amman duk runtsi bazata zurma ba ,sannan bazata ta’ba yarda dashi ba domin
dai nmj idan yana da mata biyu bakinsa biyu né haka mata d’aya da budurwa a waje
abinda zai fada agabanki dabam hakazalika idan yaje wajenta .”
muryarsa can kasan makoshi wanda sai kayi da gaske zaka iya fahimtar abinda yake
fad’a “kina da jiki mai taushi “yayi mgnr yana yawo da hannusa sansar jikinta yana
shafa qirjinta zuwa kasan mararta ,sai daya d’auki minti shabiyar yana shafata
sannan ya kamo hannuwanta duka bai tsaya akoina ba sai akan jijiyarsa “ta’ba nan
kiji ya “wani wahallen numfashi ta sauki jikinta na sake tsuma dan gbdy ilahirin
jikinta ya shiga wani shauki na dabam wanda bata ta’ba tsintar kanta ciki ba”kinji
yadda gabana ya tashi “Inna lillahi ta furta a fili tana mai jin tsananin kunya
“ko abaya da zaran zaki kasance dani haka gabana yake tashi tayi yunkurin zare
hannunta ya sake damke hannunta da jijiyarsa “a yanzu ina jin kamar an hallacci
ruhina da soyayyarki ne wallahi ki yarda dani ban san ina sonki ba auta sai da ATA
ya nemi rabani dake.”
idanunta suka sauya zuwa ruwan hawaye ya kalleta yana girgiza mata kai “ko zatona
ba gsky bane auta bata son hisham ?hawayen dake makale acikin idanunta suka zubo
ahankali ya kamo fuskarta ya hade da nashi yana shakar numfashinta yana lashe
hawayen dake gangarowa Kan kuncinta “karki min kuka na cancanci rashin so daga
gareki iya haka ma ya isa ba sai kin yi min asarar hawayenki ba .”yana gama fadar
haka ya d’agota daga jikinsa ya zaunar daita ya mike tare da wayarsa ya shige
d’akinsa bayansa tabi da kallo tana jin yadda soyayyarsa ke fixgarta yana sake bin
jinin jikinta .”
Kasa cigaba da zama tayi ta mike da kyar dan gabad’aya yanayin jikinta ya sauya
akwance ta iskeshi ya takure jikinsa waje d’aya ta rungumesa ta baya bai juyo ba
amman yana jin yadda take sake shigewa jikinsa tana manne masa tare da shafo wasu
wurare a sansar jikinsa kusan mintuna talatin suna kwance yaji ta kira sunanshi
“yaya hisham !”ta furta cikin wani irin salo da sautin murya hucin bakinta da
numfashinta na dukan wuyansa wanda ya haddasawa tsigar jikinsa mikewa “juya min
baya daidai yake da bugawar zuciyata “still shiru yayi mata “wad’an nan idanuwan
nawa bazasu iya runtsawa ba a daren nan matukar ka cigaba da juya min ba ta qarasa
maganar tana shafa qirjinsa zuwa nipples dinsa ahankali ya juyo gabad’aya wanda
sauran kad’an su had’e ya tsura mata narkakkun idanunshi “fushi kayi dani ko ?
numfashi kawai ya sauke yana cigaba da kallonta matso shi ta sake yi tana shafa
gefen fuskarsa muryarta a matukar sanyaye “ka fi kowa sanin ni masoyiyarka ce ina
son ..”fixgota yayi gabad’aya ajikinsa cikin wani irin salo ya hade bakinsu ya soma
sucking lips dinta yana tura harshensa cikin bakinta wani iri kissing yake mata
tun tana jurewa har ta fara mayar masa da martani
Mmn sudais
💗💗💗💗💗💗
MAR'ADAMS
💖💖💖💖
💗💗💗💗💗💗
*AYSHA A BAGUDO*
WATTPAD @HAUESH
AREWABOOKS USERNAME
AYSHAABAGUDO
bismillahirrahmanirrahim
Wannan littafin na kudi ne mai bukatar karantashi byn na kammalashi zai biya
1000 ta wannan account number din 1438775094 Aishat abdullahi access idan an tura
sai a turawa wannan 09136918331 alert domin tabbatar da an tura domin sauraron
littafaina a tuntubi chaneel dina (Hausa bakwai ) a YouTube.
Page 15
A qalla sun d’auke sama da mintuna shabiyar suna makale da juna suna sucking din
bakin juna sannan yaya hisham ya zare bakinsa cikin nata ya tsura mata idanunshi
da suka canza ,numfashi nana hauwa’u ta sauke sannan tayi qasa da idanunta tana
kallon qirjinsa ,shi kuwa cigaba da kallonta yayi yana jin kamar ana fixgar
zuciyarsa ne akanta ,bai ta’ba tunanin soyayyarta zata masa bazata haka ba ,babu
abinda zai cewa momynsa sai godiya dan shi a tunaninsa son rai momynsa tayi masa
dan karta ji kunyar jama’ar da suka zo mata biki yasa ta had’asu aure ,a she ita
tasan dalilin da yasa tayi masa haka ashe gata tayi masa bai sani ba dan gashi
tun ba’aje koina ba yana alfahari da zabinta dan baya jin zai yi wautan rabuwa
daita. “
“wato duk wanda yayiwa iyayensa biyayya akan aure ko akasin haka zai had’u da
nasarori da kuma jin dadin rayuwar duniya ,idan kuma kayi buris da zabinsu ko
umarninsu kanka zaka yiwa illa mai girma , dan kuwa zuciyarka bazata ta’ba zaman
lafiya ba sannan bazata daina cunkushewa da bakinciki ba kullum acikin damuwa
rayuwarka zata qare wanda hakan alama ce dake nuna mahimanci da kimar tare da
darajan iyaye ga ya’yansu .“ina ma adam zai yi hakuri da yanayin rayuwar daya
tsinci kanshi akan maryam ?” I know t’s not easy for you adam kayi saurin amince
wa da aure irin haka ,amman at least biyayyar iyaye zata iya samu jin dadin
rayuwar aure da rayuwar duniya gabad’aya ,“allah sarki momy nah na gode miki ,kuma
ina neman afuwarki bisa fushin danayita sakaki ,hakika dana yi Kuskuren kin bin
umarninki da yanzu rayuwata tana cikin qunci irin na Adam domin bazan ta’ba jin
dadin rayuwata ba har abada .”
wani sanyayayen murmushi ne ya bayyana akan fuskarsa alokacin da sautin muryar nana
hauwa’u ya ratsa zuciya da kunnuwansa “ka yarda dani yaya hisham ina sonka”
“nasani!” nasan kina sona auta kamar yadda nima a halin yanzu nake jinki ajikina
ta yadda bazan iya cigaba da rayuwa babu ke ba sonki yayi min kamun bazata I love
you” .cikin rawar jiki ta sake shigewa jikinsa tana shafo wasu bangare
ajikinsa ,ahankali ya lumshe idanunshi jin tsayayyun dukiyar fulaninta sun
tokaresa qirjinsa batare da ‘bata lokaci ba ya kai hannu ya ciresu yana kallon
tantsa tantsan nonuwanta cikin wani irin gigicewa ya cigaba da bi bakinsu da kallo
jajur dasu tamkar yadda skin dinta yake ,wani ajiyar zuciya ya sauke mai karfe
yana lumshe idanunshi kafin ahankali ya bud’e idanunshi fess akansu yana sake jin
wani irin yanayi a gabad’aya ilahirin jikinsa yayinda gabad’aya tsigar jikinsa suka
tashi babu abinda yake muradi a halin da yake ciki kamar ya kai hannunsa garesa ko
kuma ya tsotsa .”
yadda yanayinsa ya canza ya dawo tamkar bugage haka yanayin nana hauwa’u ya dawo
idanunta sun qanqance saboda wutar shaawarsa dake rurawa a zuciyarta daman momynsa
tasa an aiko mata da magunguna na qarin ni’ima tasha ta tsumu sosai dan gbdy
gabanta ya cika da ruwan ni’ima haka zalika Kan nonuwanta sun cika sun cure waje
d’aya alamun suna buqata a tsotsa ko a murja . kayan bacin dake jikinta ya fara
cirewa yana wuli dashi sai daya rabata da komai na jikinta sannna yayi mata runfa
da qirjinsa yana kallonta gbdy yaga yanayinta ya sauya duk da kasancewarta ba mai
qarancin shekaru ba amman sai daya fahimci akwai alamun tsoro atattare daita wanda
ke nuna alamun rashin sabo ,dan haka iya albarkatun qirjinta da sansar jikinta
kawai yayita sarrafawa sai dai yayi wasa da jikinta sosai sannan ya barta ya
janyota jikinsa ya rungumeta .”
sosai ta shige jikinsa tana shakar kamshin turarensa kafin ahankali ta fara lumshe
ido alamar bacci take ji d’agata yayi yana qarewa yanayinta kallo sannan ya zuro
kafafuwansa makale daita suka nufi bathroom yace “sunyi wanka tare amman tsananin
kunya ta hana nana hauwa’u amincewa sai ma juya masa baya tayi tare da kamkame
jikinta waje d’aya,yin duniya yayi suyi wanka tare amman taki ba dan bazata iya ba
sai dan kunyarsa da take ji .”ta qasan idanunta take kallonsa har ya fara wanka .”
bata ankara ba taji ya fixgota ya had’eta da jikinsa ya kai bakinsa daidai kunnenta
sannan ya riko hannunta d’aya yana massaging cikin nashi “kunyata kike ji ko
me ?”yayi mata tmbyr yana manne mata ajiki . ai kuwa nan take ta sake jin wata
sabuwar kunyarsa da shaawarsa ta lullu’beta nan da nan tsumar da jikinta keyi ya
qaru sakamakon gabansa da take ji ajikinta dan sosai ya shige mata .”
ahankali ruwa ya dinga sauka ajikinsu ya wanketa tass shima yace lallai sai tayi
masa wanka idan ba haka ba sai dai su kwana haka babu yadda ta iya dolenta tayi
masa tana yi tana jin kunya dan ta kasa dubansa suka fito ya mayar mata da kayan
baccinta shima ya saka kayan baccinsa sannan suka kwanta ya shafesu da addua ya
janyo bargo mai taushi ya lullubesu ya riko hannunta yana massaging yana jin sonta
sosai suna makale da juna bacci ya d’aukesu .”
*****
Zaune ATA yake a office dinsa ya hard’e hannuwansa duka a qirji yayinda idanunsa
na kan d’aya daga cikin wayoyinsa dake ringing sunan sweetheart daya gani ne yasa
yayinsa ya dawo haka, har wayar ta gama ringin dinta bai dauka ba yana tunanin mai
zai fad’a mata idan ya d’auka yau tsawon kwana hud’u kenan bai kirata ba sannan
bai je inda take ba bugu da qari ya garqame yar lelenta a gida bai sani ba ko ta
ziyarci gidan ne yasa ta lalubo sa , koma menene jikinsa ya rigada ya bashi akanta
ne ta kirasa “. ahankali yayi baya kad’an da kujerar da yake zaune idanunshi har
lokacin na kallon wayar fuskarsa babu annurin kirki shiru har kusan minti biyar
wani kiran ya sake shigowa ya sauke hannuwansa duka daga qirjinsa inda kyakkwar
zuciyarsa ta shiga gargadinsa “ATA mahaifiya ce fa wacce baka da kamarta a duk
fad’in duniyar nan ,bakasan a halin da take ciki ba yana da kyau ka d,auka kaji
muryarta “ lumshe tsumammun idanunshi yayi yana saisaita zuciyarsa tare da saukowa
akan mummunar fushin daya d’auka daita , ya danna koren maddanin ya saka wayar a
speaker “sweetheart ina yini …!”?
“dakata adamcy bana bukatar wata gaisuwarka” shiru yayi kawai yana kallon wayar
gabansa yayinda yaji kanshi ya fara sara masa “ni zaka share haka adamcy ”? bai
ce komai ba illa ya cigaba da kallon inda wayar ke ajiye “yanzu har nice na koma
haka ina kiranka kana kin d’auka ? still shiru yayi tun d’azu nake kiranka miss
calls bakwai nayi maka amman bakayi peaking ba sai yanzu saboda ka gama raina
mahaifiyar datayi sanadiyar zuwanka duniya.”
“Amm sweetheart.. !
“Bana buqatar wata doguwar magana da kai” lafiya maryam take tun jiya nake kiran
layin wayarta bai shiga ba haka zalika mahaifiyarta ta kirani bata sameta ba ?
muryarsa a dake yace “lafiya take !”
”lafiya fa ?” amman maryam da wahala ka kirata baka sameta ba haka na bincikata a
WhatsApp ya nuna kwanaki hud’u kenan bata hau ba “.
“lafiya kalau take sweetheart “shiru mami tayi haka nan take jin wani iri ajikinta
“shikenan karfe nawa zaka koma gida ?”uhm kamar biyar haka ya bata amsa yana shafa
kwantaccen sumar kanshi “zan kira ka karfe shida daidai kuma idan har kayi
Kuskuren kin d’auka zaka ga fushina adamcy.” tana gama fadar hk ta katse wayar , ya
kife kanshi a saman table ckin fushi yace” gsky ban so komawa gidan nan yanzu ba
sai na tabbatar data narke ta zama kwarangwal sannan na koma nayi mata shaka d’aya
na aikata barzahu kafin taga mutuwata ni zan fara ganin nata “duk mai yayi zafi
haka ATA? Zuciyarsa ta aikawa kwakwaluwarsa tambayar “duk laifin sweetheart ce
sanin kanta ne baza’ayi rayuwar aure mai dadi acikin wannan had’in ba amman ta nace
lallai sai anyi. matsawar bata rasa d’aya cikin shi da yarinyar nan ba hankalinta
bazai kwanta ba ,bazata bar rayuwarsa ta sarara ba, shiyasa shine zai fara kashe
maryam din in yaso idan tagansa garqame a prison hankalinta zai kwanta.”
yini ranar cikin tsananin fushi yayi ayyukansa karfe hud’u da rabi direbansa da
jami’an tsaronsa suka d’aukosa zuwa gida karfe shida saura motocinsa suka shigo
haraban gidan lokacin maryam na kwance babu yadda take cikin kuwa banda turirin
zafin yunwa babu abinda yake mata .”
Cike da mutuwar jiki ya shigo parlour’n inda ya isketa takure kwance rike da
cikinta. kallo daya yayi
mata yasan tana cikin damuwa da tashin hankali dan gabad’aya yanayinta ya canza
idanunta sun rikid’e sun canza kala zuwa na yunwa, sannan da alamun ma kuka take
atakaice a yadda yake son ganinta a haka ya ganta tayi zuru zuru ta dawo abar
tausayi sai dai sam zuciyarsa babu digon tausayi ko nadamar abinda ya aikata mata
bare tausayinta yayi tasiri a zuciyarsa, sai ma tarin qiyayyarta da yake ji .
Abinda sweetheart dinsa ta kasa gane kenan tursasa zuciyarsa akan yarinyar yasa
wutar qiyayyarta ke sake mamayesa kullum .”
zuba masa ido kawai tayi hawaye na gangarowa akan kuncinta “ki d’auke wad’an nan
banzayen idanun naki akaina ai tunda kika nacewa aurena ni ne zanyi sanadin
mutuwarki dan tun tuni naji rashin alkhairi akan aurenki ,kinga idan kin mutu ni
kuma na tsinci kaina a prison hankalin ke da sweetheart zai kwanta amman tabbas ina
ji ajikina idan baki kasheni ba ni zan kasheki ya fad’a yana nuna ta da d’an
yatsansa.”
Batace komai ba illa kanta data dukar qasa kamar yadda ya bukata tana sauraron
bakaken maganga nusa akanta ,yayinda jikinta Ke karkarwa saboda tsananin yunwar da
take ji “yadda bana son auren nan ko sau d’aya ki fito kema kice bakya so amman
kinki furtawa sai ma nuna alamun son zama dani wanda hakan babu abinda zai janyo
miki sai bala’i da tashin hankali ,”wallahi wallahi kinji na rantse dana zauna dake
har qarshen rayuwata gara na kasheki na qarar da sauran rayuwata a prison.”
cike da tarin damuwa ta d’ago idanunta duk sun cika da kwalla tasan tunda ya
rantse tabbas zai aikata abinda ya fad’a indai bata bar rayuwarsa ba “wallahi
sweetheart bata min adalci ba kuma ta cutar dani domin tayi min abinda yasa na qasa
mata biyayya , maryam ta sake kallonsa cike da mamaki “wallahi sweetheart bata min
adalci ba kuma ta cutar dani ta maimaita abinda ya fad’a afili “yes haka nace shima
ki kwashe ki fad’a mata dan kin iya munafurci har kingaji ,ko da yake ai siffar
munafukai gareki ,ahankali muryarta ta fito “yaya adam kayi hakuri dan allah karka
bata ranka bazan fad’a mata komai ba tana kaiwa nan sai wasu hawaye “.
“Dan allah malama bana són munafurci ki daidaita natsuwarki ga waya kuyi magana
daita da sauri ta goge hawayenta da hannuwanta duka tana shafa qirjinta dan dawo da
natsuwarta sannan ta mika masa hannunta wai kallon banza yayi mata yasa wayar a
speaker yana rike da wayar” hello tajiyo sautin muryar mami zuciyarta cike da rauni
tace “hello mami ina yini “yauwa maryam lafiya qalau daman dake nake son magana
lafiya naji muryarki haka ?ta kalli inda ATA yake ,mugun kallon daya dauketa dashi
ne yasa ta dauke kwayar idanunta akanshi , ta kalli cikin wayar “lafiya qalau mami
“to mai ya samu wayarki an kiraki bai shiga ?maryam tayi shiru tana jin rauni
atare daita “mahaifiyarki tun shekaranjiya take neman layinki ni kuma tun jiya
nake kiranki haka ma auta idan akwai damuwa ki fad’a min”.
ta waiga ta kalli ATA dake binta da mugayen idanunshi “adamcy na wajen ne ?”uhm !
ta bata amsa atakaice,okay kina jina zan miki tmby idan gsky ne kice “eh! idan
karya ne a’a !“Tun daga ranar da abun nan ya faru a tsakaninki da adamcy ya kwana
a gidan ?“muryarta na rawa tace “eh !mami tayi shiru can tace mikawa adamcy wayar
“ai wayar tana hannunsa “mami ta furta “aa ! cike da tsananin mamaki mami tace
“wayar ma bazaka iya bata ba kamar wata mugun abu ?aransa yace”ai ta zarce haka
acikin zuciyata amman a fili cewa yayi “ina jinki sweetheart “muje what’sapp tana
gama fadar haka ta katse kiran ta kirasa vedio call ido cikin ido suke kallon juna
tace “ina maryam take ?”
ya haska mata fuskarta dake kode alamun wahala “maryam natsu ki fad’a min gsky
babu abinda zai iya miki me ya sameki duk naga kin dawo wani iri haka “me kuwa zai
sameta ?” wai sweetheart mai yasa bakya son zaman lafiya ne ? kin tmbyi yarinyar
tace babu komai ,kina son lallai sai ta kirkiro karya ta fad’a miki akaina “Ke
dan ubanki meke damunki ? ya fad’a a tsawace ”maryam tayi saurin girgiza kai tana
cewa “mami babu komai ! adamcy karka nemi ka raina min hankali maryam fad’a min
gsky gani nan zuwa yanzu “a’a mami dan girman allah karki zo wallahi babu abinda
yake min kawai dai kwana biyu bana jin dadi ne “wato adamcy dai ka raina ni da
gsky “.
“me kuma nayi sweetheart ?“taya yarinya bata da lafiya har tsawon kwanakin nan
amman kai daka ajiyeta baka sani ba ?“ wa kenan ya ajiyeta sweetheart ? “inna
lillahi! mami ta furta “tô ai maganar gsky ne sweetheart ni ban ajiyeta ba ba kuma
zamana take acikin gidan ba, zamanki take dan Ke kike aurenta bani ba “okay haka ma
zaka fad’a min ? am sorry sweetheart amman kin dade dasani zamanki take acikin
gidan nan “okay har kana sake jaddada min? to wallahi bazaka qara jin dadina ba
haka kawai ka dinga ganawa yarinyar mutane azaba laifi ne dan ta rufa maka asiri ta
aureka ?“.
“wace azaba kuma sweetheart yarinyar da babu abinda Ke hadani daita, ya kalli
maryam Kiyi mata bayani mana kinyi shiru kina kallona da wata munafukar fuskarki ?
maryam kam shiru tayi ta tsaya tana kallon fuska mami ,ya sake mata alamar tayi
magana akaro na biyu a matukar fusace “Ke kina hauka ne ya buga mata tsawa “ ki
bud’e baki mata bayani “Allah babu abinda yake min “ karki sake ki min karya
maryam “wai sweetheart me nene haka ne ?ya kalli maryam yana cewa “wallahi idan
baki bari ta yarda babu komai ba sai na canza miki kamani, ta kalli mami cikin
tsananin tashin hankali tace “mami dan girman allah ki bar maganar nan ni babu
abinda yake min kawai zazzabi dare nake fama dashi kuma walalhi laifina ne ban
fad’a masa ba nasan dana fad’a masa zai kai ni hospital ko ya kira min doctor “tana
gama fadar haka ta juya kafin mami ta sake cewa wani abu .”
mami tayi shiru tana dubansa ta cikin waya “sweetheart kinyi shiru “me zance adamcy
tunda kafi karfina ka rainani ka nuna min ban isa da kai ba duk lokacin da nace ga
abinda zakayi bazakayi ba amman wallahi bazanyi kaffara ba muddin ba cigaba da
zaman lafiya da maryam a cikin gidan nan ba na rantse da girman allah babu ni
babu kai “ki kwantar da hankalinki sweetheart kin ma kusan rasani gabad’aya
“bangane na kusan rasaka gabad’aya ba ?“eh mana na zabi mutuwa akan cigaba da
rayuwa da wannan munafakar yarinyar akowani lokaci zaki bud’e idanunki baki ki
daina ganin adamcynki “bazaka iya aikatawa kanka komai ba kai fa muslimi ne kuma
kasan hukunci haka addininance dan haka ka bar maganar nan bana son na sake jin ka
fad’a kazo gobe akwai maganar da nake son nayi da kai mai mahimanci,amman dan
allah na roki arziki ka bar yarinyar maryam ta samu natsuwa acikin gidan nan “naji
!iya abinda ya fad’a kenan sukai sallama.”
Maryam na shiga dakinta ta rushe da kuka tana cikin kuka wutan gidan ya kama sai
datayi kuka mai isarta sannna ta janyo wayarta ta jona caji ta fito lokacin baya
parlour’n kitchen ta nufa direct aiko taga key makale naunayen ajiyar zuciya ta
sauke tana godewa allah cike da rawar jiki ta kai hannunta tana waigen bayanta babu
alamunsa ta zare key daya ta tura cikin rigar nononta sannan ta murd’a kofar ta
shiga ta bud’e fridge duk abinda Ke ciki da d’an sanyin amman da zai sake d’aukar
time zasu tashi aiki ire iren abincin data saba ci tana ajiyewa a firdge shi ta
dauko tasa a microviw cikin mintunan da basu wuce uku ba yayi zafi jikinta har rawa
yake wajen fito dashi .
a kitchen ta zauna taci nan da nan zufa ya rufe ta da kyar ta mike ta ajiye plet
acikin zink ta sake bud’e frdge ta d’auki vatermilk ta kafa abakinta bata ajiye
kwalbar ba sai data shanye tass sannna ta ciro apple da inibi ta daura akan plet ta
yayyaka kanana ta dawo d’akinta koda ta shigo wayarta ta kunna kanta ta kulle
dakinta ta zauan ta dauki wayarta ta hau what’s app tana duba sakwanin kawayenta
suna ta tambayata “ ina ta shige kwana biyu wasu kuma suce wai dadin aure yasa
yanzu ta rage hawa online ita dai dariya kawai take musu tana fad’a masu yadda tayi
mugu kewarsu bayn ta gama dasu ta kira mahaifiyar ta sun jima suna waya inda take
jaddada mata lallai taje airport gobe ta karbo sakonta tun washegarin ranar da
sukai magana ta aiko .”
Washegar da ATA zai fita bai bada umarnin cire wutan gidan ba sai dai ya zare key
kitchen ya wuce dashi koda ta sauko taga babu key ta fashe da dariya har da tafa
hannu ta koma d’akinta ta d’auki waya ta turawa auta sako akan abinda yayanta yayi
tana dariya nan take nana hauwa’u ta kira suna masa dariya maryam tace “ga keyn
dana sace zanyi amfani dashi wallahi sister wannan yayan naki mugu a duniya babu
kamarsa ,ki dai bi ahankali kar ya gane azabtar min dake kunnenta makale da waya ta
sauko ta bud’e kitchen lafiyayyen breakfast tayi mai kyau tana ci suna waya da
nana hauwa’u bayan gama ta sallami nana hauwa’u ta bar gidan batare da izinin ATA
ba zuwa airport ta karbo sakonta a parlour’n gidan ta tsaya tana bud’e bakar
jakar dake rike a hannunta wata yar qaramar tukunya ta gani ta sauke numfashi tare
da maida tukun yar cikin jakar ta mike ta shige d’akinta tayi masa kyakkyawan ajiya
acikin duro dinta har zata rufe durowar idanunta ya sauka akan littafin addu’oin
da mami ta bata lokacin da zata tare ,ta dauka tana dubawa ko sau d’aya batayi
tunanin ta duba tayi amfani da wasu abubuwa daga ciki ba ta zauna rike da littafin
tana qoqarin dubawa wayarta ta fara ringing dan haka ta ajiye ta d’auki wayarta
kiran mahaifiyarta ne .”
Har karfe goma shadaya na dare maryam na zaune tana jiran dawowar ATA sai dai
shiru bai dawo gida ba, karfe shabiyu daidai ya shigo tana jin motsin shigowar
motocinsa ta zabura ta mike tare da adduar neman saa jikin labulenta ta qarasa
cikin sauri taga yana tafiya har sanda ya nufi kofar shigowa ta saki labalen tana
cewa “ya Allah ka bani sa’a akan maganin nan bakin kofar d’akinta ta dawo ta labe
tana kallonsa ya bud’e kofar dakinsa ya shiga batare daya zare key ba wanda ga
dukkanin alamu ya manta ne sadaf sadaf ta bud’e kofar d’akinta ta fito ta tura
kofar d’akinsa ta leka baya nan sai kayansa ta hango akan katifa alamun ya shiga
wanka ta janyo kofar ta rufe ahankali sannan cike da tsoro ta cire key d’aya acikin
key’n dakinsa tayi wuf ta fad’a d’akinta ta kulle tana dafe qirjinta da hannuwanta
duka tare da furta.”
“allah na gode maka da kabani wannan saar gobe da safe yana fice wa daga gidan zan
shiga nayi abinda zanyi “kai maryam mai yasa zaki dogara da irin wadan nan
abubuwan wannan fa shirka ne qarara zaki aikata domin tukun yar tsaf ce ummah ta
aiko miki dashi rayuwar nan fa babu tabbas babu yadda allah bazai yi ikonsa ba
qaddara kuma tana fadawa bawa daidai yadda allah ya hukunto masa amman addua itace
mafuta cikin ,rayuwar aurenki da Adam qaddara ce ki cigaba da hakuri zama dashi
haka sarewa ta kalli mukulli hannunta kafin ahankali ta kira wayar mahaifiyarta ta
koma can karshen dakin tana dauka “tace umma abin nan kuwa zan iya sakawa yaya Adam
shi ? bana son abinda zanyi na cutar dashi ,sannnan hakan nan wannan aikin yake
bani tsoro tun da kika fad’a min zai iya mance har mami tsoro ya shigeni ,rayuwar
mami babu Adam akwai damuwa bugu da qari ta damqa min amanarsa idan na cutar mata
dashi allah bazai barni ba “.
“ina so mana umma ina son nayi rayuwa mai dadi dashi domin hakan yana da mahimanci
ga rayuwata ko sau daya ya soni ya furta ya kuma kula da rayuwata bangaren ummu
kuwa cewa tayi “tunda kina son faruwar haka ki manta da wata uwarsa Ke Kinsan irin
nata mulkin datayi lokacin mahaifinsa ?tayi mulki kuma har yanzu tana kai haka
kawai take juya kowa son ranta ?dan haka kiyiwa kanki adalci ki cire wannan
tausayin Kiyi abinda ke gabanki domin raba zuciyarki da nauyi “wallahi ummah ina
jin zafi har acikin raina ace sai nayi asiri yaya Adam zai soni “ta qarashe maganar
tana zubda kwalla mai zafi bata jin zata iya daukar wannan nauyi “dole kiyi tunda
soyayyar da kike masa da biyyya tare da hakurinki bai yi miki amfanin komai
ba ,ke bari na fad’a miki wani abu ko Adam nason aurenku dole sai kin tashi tsaye
akanshi dan irin masu taurin kansu sai da asiri ake samun kansu Kiyi qoqari kawai
ki saka tukun yar nan da zarar ya kwanta aiki ya fara kenan sai dai wani Adam din
bashi ba zai fad’a wata duniyar ta dabam lokacin da zai dawo kin tara masa yaya
masu yawa “.tana gama fad’ar hk ta katse kiran .”
Yana fitowa daga wanka cikin sauri sauri ya soma shiri dan tafiya ce ta samesa zuwa
kasar ingila karfe daya da wasu yan mintuna jirginsa zai tashi bai sheidawa kowa
ba har mami ya fito da wata yar qaramar jaka ya kama hanya ya fice ya bar gidan
washegari maryam bayan ta gama gyara gida ta bud’e dakinsa ,tana kallon dakin , da
mamallakinsa na nan bata isa ta tsaya cikinsa cikin natsuwa ba gaban mirrow dinsa
ta qarasa ta tsaya tana duban frame din hotonsa cikin hadadden suit baki idanunshi
manne da farin glass ,tana kallonsa tana jin yadda zuciyarta Ke sake narkewa akan
son shi wata irin soyayyarsa Ke ratsata bata ta’ba son wani halitta kamar yadda
take son shi ba .
ta kai hannunta ta dauki freme din ta rungume ajikinta tana mai lumshe
idanunta“akanka na aikata manya manya laifi masu muni da tsayawa arai me yasa
bazaka sauko ka karbeni ba ?“wallahi ina sonka da sonka na rayu tun tsawon rayuwata
soyayyarka bata misaltuwa yaya adam, a baya nayi babba kuskure a yanzu kuma zan
sake tafka wani kuskure akan Kuskuren baya ka sausauta min zuciyata bazata cigaba
da bugawa ba idan har babu kai ka soni batare da na aikata wani laifi ga
mahaliccina ba “
“Sorry maryam adam fa yayi nisa a qiyayyar ki bazai ta’ba sonki ba karki mata
kalamansa na shekaranjiya
“ai tunda kika nacewa aurena ni ne zanyi sanadin mutuwarki dan tun tuni naji rashin
alkhairi akan aurenki kinga idan kin mutu ni kuma na tsinci kaina a prison hankalin
ke da sweetheart zai kwanta amman tabbas ina ji ajikina idan baki kasheni ba ni zan
kasheki .”
“Tabbas zai iya komai dan kawar dake a duniya saboda tsananin kiyayarsa gareki
kiyayyarsa tun fil azal ce wato tun ran gini tun ran zane karki cutar da kanki
gara Kiyi amfani da komai ya zama mallakinki na har abada ,amman kuma duk daren
dadewa asiri zai karye maryam ga laifin asiri ga hakin mami akanki ko ba dade
hakinta zai bibiyi rayuwarki ranar nadamarki na zuwa kuma alokacin nadamar bazata
yi miki amfani ba jikinta yayi sanyi tana zubar da hawaye tana makale da hotonsa
“maryam ki bar wannan tunani a yanzu yadda yaya adam zai soki shine mafuta agareki
,ki dauko tukun yar ki saka ki kama gabanki jiki a sanyaye ta ajiye freme din
hannuta taje ta d’auko tukun yar ta daga katifa tasa sannan ta gyara masa d’aki
tsaf ta fito ta kulle ta zare key ta koma dakinta ta shiga yanat gizo .”
Maryam batasan da tafiyarsa ba ta dai zuba ido taga dawowarsa mami kam tun a
daren jiya taji batun tafiyarsa ,ranta yayi matukar baci sakamakon rashin fad’a
mata da bai yi ba amman kuma hakan bai hanata yi masa addua da fatan alkhairi
arayuwarsa ba , bangaren maryam kuwa hankalinta yayi matukar tashi ganin bai dawo
ba har washegari batayi tunanin tafiya yayi ba ta d’auka yaji yayi mata kamar yadda
ya saba ,hankalinta a tashe ta kira mahaifiyarta ta sheida mata halin da’ake ciki
“ki kwantar da hankalinki tabbas kaidarsa kwanaki uku ne zai tashi aiki amman akwai
mafuta dan zaa iya yin wani sabon aiki “ irinsa umma? Eh mana irinsa zaayi “
wannan maganar ya kwantar da hankalin maryam ta cigaba da tsabgoginta tunda tana da
wuta kuma tana da keyn kitchen a hannunta burinta ya dawo ya bud’e d’akinsa ya
kwana akan gadon .”
Washegarin ranar da ya cika kwanaki bakwai nana hauwa’u ta kirata ta fad’a mata
qawarsu safiya ta haihu har jibi suna dan haka jibi su hadu a gidan safiy daga
suka hira inda nana hauwa’u Ke tmbyata ko yayanta ya dawo ?bai dawo ba har
yanzu ,sister kina ganin bancin na sace keyn kitchen ba niyyar kasheni yaya adam
yayi ba kamar yadda ya fad’a “? nana hauwa’u tayi murmushi “bazai ta’ba kashe
common sauro ba bare mutun wannan duk fad’a yake kuma tunda akwai waya a hannunki
kuma akwai wuta a gidan duk zai zo da sauki ba kamar kwanaki ba koni da kaina zan
dinga zuwa ina kawo miki abinci sun jima suna hira a tsakaninsu .”
Ranar da ya cika kwanaki goma cif sai gashi ya duro gidan tmkr mashi alokacin
maryam na tsaye gaban madubi tana ta shek'a kwalliyar zuwa suna kamar wacce zata
canja fuska, ta shafa wannan ta goga wancen ta dangwala wancen, ta d'auki lokaci me
tsawo kafin ta gama,dan kwallinta ta d'auka ta d'aura, ta dauko takalmi hil tasa
saida ta k'are ma kanta kallo ita kanta tasan tayi kyau dan ita bata ganin illar
rashin tsawonta tunda akwai hil kuma duk tsadarsu tana siya sai dai idan bai mata
ba
tana murmushi ta d'auko mayafinta da jaka ta fito da zumar zuwa gidan suna a
hanakali take taku kwas kwas saitin takalminta kenan tana gama saukowa qasa kawai
taga mutun zaune a parlour’n yana cire takalma ,a natse ya dago yana duban step
sakamakon qarar takaliminta mai mugun tsini kallo d’aya yayi mata gabad’aya yaga ta
canza shi da yake jiran ya ganta ta qanjame tsabar yunwa amman yaga tayi fresh .”
baki ya saki yake kallonta kafin ahankali ya kai dubansa ga kofar kitchen nan ya
hango key kwaya d’aya,wani irin tsoro ne ya shigeta nan take jikinta ya kama rawa
wani irin numfashi ya sauke ya dawo da kallonsa gareta tun daga qasa ya sake daukar
kallonta kafin ahankali muryarsa a can qasan makoshi yace "ke ina zaki?”yau ne
sunan wata k'awarmu da ta haihu shine zamuje tare da sister yana qarasa cire
takalminsa ,ya mike tamkar zaki ya fara nufota yana cewa “a ina kika samo extra key
na kitchen?ganin yana nufota cikin wata irin tafiya mai daga hankali qirjinsa har
wani dagawa yake duk wani taku da yayi sai zuciyarta ta buga da karfi .”
bai fi sauran taku daya ya qaraso gareta ba kawai ATA yaga tayi wuli da jakar
hannunta ta saka wata razananniyar qara ta zube qasa tare da dafe kanta tana
jujjuya shi cikin rashin jin tsoro ATA ya qaraso gabanta ya kai hannu da niyyar
sauke mata mari yaji ta daka masa tsawa cikin wata irin kaukausar murya tana fadin
“kar ka kuskura ka taba mana godiyarmu.”cak ya tsaya yana kallonta cike da mamaki
“hahhhh tashiga babbaka dariya cikin wata irin murya mai cike da ban tsoro
tashiga fad’in “wannan ba maryam bace daka saba duka kana wulakantawa nine aljanu
gagare wato kai kullum tunaninka dukanta da wulakanta mana godiyarmu ,ka dauka bata
da gata ne, ita din fa matarka ce ba baiwarka bace ,tana magana tana nufosa, ATA
ya dan ja baya kadan yana qare mata kallo tsab “ daga yanzu idan ka sake kai
hannunka jikinta ko wulakantata hukuncinka agareni shine kisa.” ATA ya kankance
idanunshi yana qare ma fuskarta kallo da abinda Ke fitowa bakinta da kuma yadda
idanunta suka juye kamar gaske kamar kuma wasa tana matsoshi yana ja da baya.”
bakasan karfin aljanin gagare bane shiyasa kake abinda kake yi wallahi duk ranar da
ka sake bata mata rai na rantse bazan duba cewar matarka bace sai datse maka
numfashi kafin ka kashe mana godiyarmu mune zamuyi ajalinka.”
Mmn sudais
💗💗💗💗💗💗
MAR'ADAMS
💖💖💖💖
💗💗💗💗💗💗
*AYSHA A BAGUDO*
WATTPAD @HAUESH
AREWABOOKS USERNAME
AYSHAABAGUDO
bismillahirrahmanirrahim
Wannan littafin na kudi ne mai bukatar karantashi byn na kammalashi zai biya
1000 ta wannan account number din 1438775094 Aishat abdullahi access idan an tura
sai a turawa wannan 09136918331 alert domin tabbatar da an tura domin sauraron
littafaina a tuntubi chaneel dina (Hausa bakwai ) a YouTube.
Page 16
Daga inda yake tsaye yake qare mata kallon tsab yayinda gaba d'aya yanayin jikinta
ya sauya exactly kamar yadda masu aljanu suke react, maryam tana fidda ido ta sake
kallon ATA that's lookin at her wani iri, gashi nan dai kamar ya tsorata da
yanayin ta kamar kuma bai tsorata ba ,amman zatayi komai dan ta tsorata shi ,shi
kuwa he's thinking of gaskiya ne ko karyar aljanu zata masa. tana kallonsa ya
sake d'an ja baya kad'an adaidai lokacin da wayarsa ta soma ringing iPod dinsa dake
manne da kunnensa ya ta'ba taji ya soma magana can kasan makoshi ta yadda bazata
iya jin me yake fad'a ba ,shirun da taji yayi ya cigaba da kallonta ya bata damar
sake nufosa bai fi sauran taku d'aya ta isa garesa ba ,sai ji tayi ya buga mata
wata razananniyar tsawa wacce tasa gabad'aya gidan ya amsa sautinsa ."
a zafafe yace "ke maryam meye haka ?wani irin hauka ne haka ? hahahaha ta cigaba da
babbaka dariya cikin wata irin murya tace "sau nawa zamu fad'a maka wannan ba
maryam bace god'i..." wani gigitaccen mari ya zuba mata wanda yasa nan take ta
durkushe qasa dafe da kuncinta dan sai da taji ganinta da jinta tare da
numfashinta ya d'auke na wani lokaci ,kafin ahankali numfashinta ya dawo ta saki
wani marayan kuka mai cike da ban tausayi tana cewa "me nayi maka ? "ke ni zaki
yiwa wannan iskancin da rashin hankali? ?ni zakiyiwa karyar aljanu ?gaban maryam
ya bada rasss ya shiga bugawa da sauri sauri "kin manta ko waye tsaye a gabanki ?ko
kinga alamun zuciyar tawa tana cike da tsoro ? ko nayi miki kama da matsoraci ?yayi
mata tambayar a here tare da kai hannu ya damki wuyan rigarta ya kifa mata wani
gigitaccen mari ."
ta saki qara mai sauti tana qoqarin kwatar wuyanta daga hannunsa amman ta kasa dan
baqaramin damka yayi ma wuyanta ba yana huci tamkar zaki "wallahi idan hauka kike
ji na fiki hauka "ya fad'a yana zaro mata idanu kamar zasu fad'o qasa kuka ta
fashe dashi har da majina "ki sani ba aljanu ba ko haukacewa zakiyi babu ruwana
kuma hakan bazai ta'ba girgiza zuciyata ba ."wani kuka ta sake saki tana rokonsa"
dan allah kayi hakuri ka sakar min wuya numfashina. wai ma me nayi maka ne "?
wata tsawa ya buga mata tare da sakinta da karfi sauran kad'an bayanta ya bugi
center table din dake parlour'n tayi taga taga ta tsaya bisa qafafuwanta tana shafa
wuyanta yayinda jikinta ke wani irin kyarma. ta tsura masa ido tana kallonsa
hawaye na turereniyar zubowa "wannan fa zalinci ne daga shigowarka ka hau marina da
shake min wuta tayi maganar cike da matsanancin tsoro sai dai jarumtar data aro ta
sanyawa jikinta bai sa ya gane tsoronta ba ."
"Laifin me nayi maka ?ta sake tambayarsa yayi shiru yana kallonta a wulakance
maryam ta share hawayenta ta cigaba da magana "ban maka laifin komai ba ,idan kuma
key daka gani ne ,nice na cire domin bazan zauna yunwa ta kasheni ba , yau kwanaki
goma kenan rabonka da gidan nan ,da kai a tunaninka haka zan zauna nayi rayuwa
tattare da yunwa ? "me kake so dani yaya adam? gaskiya wallahi na gaji na gaji!!
da wannan zalinci, ka tozartani ni daga ni sai kai ,ka tozartani agaban kowa ga
azabtarwa ga horon yunwa "Enough is enough yaya adam da wannan tozarci da wulakanci
biyayya fa ba hauka bane ..."ai bakin maryam tsayawa yayi cak sakamakon ganin "ATA
ya nufota gadan gadan cikin tsananin fushi kamar mayunwanci zaki idanunshi sun
kad'a sunyi jajur a matukar zuciye ya cigaba da magana yana hararta "shut dare kuma
ki natsu ki saurare ni da kyau karki kuskura ki sake magana batare da izinina ba ".
Idan akwai abinda yafi shiru maryam tayi agurin rawar da jikinta yake kuwa sai ya
baka mamaki "wato Ke gaki yar iska wuyanki ya isa yanka ni zaki dinga fad'awa
magana son ranki ?"ba wai na fad'a maka maga..."I said shut up ki shiga hankalinki
har yau baa haifi d'a ko 'yar da ina magana yana magana ba, ba'a min haka sai dai
ni nayi kuma kinsan da zaman haka ni senior man ne you understand ba'a min haka
koda kuwa ana min ke baki isa kiyi min ba saboda baki da wannan darajar da wannan
matsayin a wajena .dan haka to be your first and last da zaki fad'a irin wad'an
nan maganganun saboda bazan barki ba idan kin sake" shiru maryam tayi cike da
tsoronsa wanda a yanzu ta fahimci girman tsoronsa da take ji ne yake sawa yake
mata wasu abubuwan ta runtse idanunta hawayen ciki suka sake wanke fuskarta tana
jin kamar ta kashe kanta ta huta saboda muguwar tsanar da yayi mata ta rasa me ta
tsare masa a rayuwa daya tsaneta haka ?."hawaye maryam ta share wasu na sake zubowa
."
Bai barta taji da bakincikin da yayi mata dabaibayi dashi ba ya sake qara mata
wata damuwar cikin wata irin murya yace "wato ni zaki tsorata da ace banyi saurin
d'aukar mataki akanki ba shikenan haka zakiyi wasa da hankalin mutane wai ke mai
aljanu yanzu ina aljanun suke ? tayi shiru tana dubansa "ina son ganinsu ido da ido
kuma a yanzu ,idan basu fito a zahiri ba sai naci ubanki ."iya firgita maryam ta
firgita jin abinda yake fitowa daga bakinsa kuma yadda yake kallonta sarai ta
fahimci ya gane aljanun karya tayi . Idanunta gbdy sun yi ja har fitsari ta saki
batare datasani ba ."ja da baya ta soma tana karkarwa da kyar take fad'in "kayi
hakuri nifa bansan me nayi ba "wani kallo ya d'auketa dashi "kenan baki san Kiyi
karyar aljanu ba yanzu sai dana zuba miki maruka kika dawo haiyacinki ?jikinta da
bakinta na rawa tace "wallahi allah bansan nayi karyar aljanu ba" wani kallo yayi
mata mai had'e da harara "na rantse maka da Allah ban san nayi ba "shiiiii ! ya
furta a kasalance."
Nan take tasa hannu ta rufe bakinta idanuta sunyi zuru zuru kamar yace "arr ta
zunduma a guje "kafeta yayi da ido yayinda zuciyarsa ke tafasa yace "woww gsky
wannan yarinyar kin qaro iskanci mai upgrade ya kai hannu zai damko hannunta tayi
saurin zamewa tana ja baya da sauri dan tasan bazai mata da kyau ba muddin ta shiga
hannunsa duk ta rud'e sai hawaye take tana fitar da zufa "tsaki yaketa yi yana
kallonta dan dole sai ya gano gaskiyar data boye ,yayinda duk jikin maryam kyar
yake tana yarfe masa hannu duk kwaliyar data 'bata tsawon lokacin akanta ruwan
hawaye ya wanketa cikin kuka tace "gabad'aya ban fahimci inda maganarta ta dosa ba
"ni dai nasan na sauko naga kana cire takalmanka ka tashi ka nufoni bayan haka ni
bansan komai akan maganar aljanu ba ."
juyawa yayi yaje ya kulle kofar shigowa sannan ya dawo ya tsaya yace "banason jin
komai kawai aljanun nake buqatar gani kuma a yanzu maryam ta durkushe qasa "ta ina
zan fara yaya dan girman allah kayi hakuri ka bar zuciyata haka karka qara min wani
sabon tashin hankali akan wanda nike ciki "you are very stupid I mean ina son ki
sake wannan acting din aljanu kuma a yanzu" maryam na kuka tana rokonsa "okay tunda
baza kiyi ba kiyi frog jump kuma zanyi bincike mai karfi idan na gano baki da
aljanu na karya kikayi kin mutu "okay naji amman na manta yaake frog jump ." wani
mari ya kai mata yace "bismillah start !maryam ta kama kunne kawai "kina hauka ne
frog jump nace kiyi kuma wannan shine karoki na farko da karshe da zaki sake
acting aljanu acikin gidan nan ko da kuwa da gaske kina dashi ki fad'a masu mijin
da'aka masa dole ya aurenki yafi su hauka ."
"Allah yaya adam ka yarda dani ban san nayi maka haka ba ,zata cigaba da rantse
rantse ya dakatar daita yace "karki qara kiran sunana idan ba haka ba zan mugun
baki mamaki ,kuma dan allah naji kin sanarwa sweetheart ko wani a gida abinda nake
miki kad'an ne wanda zan miki sai yafi shi ,maryam na kuka tana frog jump sai daya
balain bata wahala jikinta rawa ko ina na mata ciwo sannan yace "leave this place?
aikuwa da mugun sauri ta suri jakarta tayi sama ta shige d'akinta tare da kulle
kofar, ta shiga sheshekar kuka har da rike kai tana "wayyo allah na shiga ukuna
wannan wace irin maseefa ce ? "wallahi na gaji ta jima tana kuka tukun tayi shiru
ta zuba tagumi tana tunani mafuta dan zuwa yanzu ya dace tasan inda Ke mata ciwo
tayi shiru tana tunani " kuma fa da fari yaya adam yaji tsoro acting dinta wannan
marin da yayi mata ne bai kyauta mata ba if not da tayi galaba akansa yama
akayi ya gane ba aljanun gaske bane ?"
"oh my god wallahi yadda ya tsorata da farko abun yayi mata dadi ,ta d'an saki
dariya ta nufi gado ta jingina tana shafa kuncinta daya d'an tashi tana ciza lip's
dinta "da'ace allah ya taimaketa da wata killa shikenan ta dan samu sausauci daga
garesa, ya allah ka kawo min mafuta duk yadda ta dauko shirinta sai ya wargaza ga
tukunyar maganin ma haka ya gama kwanakisa sai jiya ta shiga ta ciro daga
karkashin gadonsa yanzu kuma tayi iskan karya ya gane anya kuwa yaya adam mutun ne
kamar sauran mutane ?wai sai yaga aljani ido da ido ko idan yaga aljani zai tsaya
."?ina ma tana da aljanun gaske su gyara masa zama, mugu kawai bancin son da take
maka wallahi da tuni ta tattara ta gudu ta barsa . tana zaune wayarta ta soma
ringing ko baa fad'a mata ba tasan sister ce tana dauka tace "sister kinji shiru ko
?ai babu maganar fita nan ta koro mata komai nan take nana hauwa'u tashiga
kyalkyata dariya har da rike ciki "haba sister ina fad'a miki wahalar dana sha
amamn zaki bige da min dariya haka ."
bangaren nana hauwa'u tace "wallahi sister na tausaya miki kawai karyar aljanu ne
ya bani dariya ai yaya adam sam bashi da tsoro lokacin yana bording school shike
zane masu aljanu da kin fad'a min zakiyi karyar aljanu wallahi bazan goyi bayan
Kiyi ba dan bazaki ga duro ba wahala zaki sha kawai a banza .kuma fa wallahi komai
ya tafi min daidai gigitaccen marin da yayi min ne ya 'bata komai "karki sake
ganganci nan allah ya rabamu da lamarin aljanu ,ameen yace zai yi bincike dan Allah
ko ya kiraki kice da gaske ne ina dasu "kai bazan daura miki wannan lalurar
ba .Kiyiwa girman allah ki rufa min asiri idan ba haka ba na tattara na gudu tun
dare bai min ba ."nana hauwa'u ta sake kyalkyalewa da dariya tana cewa "dan girman
allah ki rage tsoransa kema fa ya kamata ki kai masa ziyara "ziyara kamar wani irin
ziyara kenan kike nufi ?."
"haba maryam yanzu sai na tsaya na koya miki "menene amfanin social media din da
kike yi ?group's gareki fa sunfi ashirin da wani abu sannan ina karatun novels din
da kike? uhm maryam ta sauke numfashi da ajiyar zuciya tana cewa " nifa wallahi
yayanki tsorata yake, ko nayi niyya yi wani abu sai tsoransa ya shigeni na
fasa .da dabara zaki dinga shige masa kawai Kiyi qoqarin kisan weekpoint dinsa
bazai ki ba "sister nasan duk wani week point din nmj ,kunnuwansa nipples dinsa
sumar kanshi uwa uba jijiyarsu amman yayanki baya yarda na ra'bi inda yake bai ma
son ya bud'e idanu ya gani bare a kusa dashi ai shiyasa nake fad'a miki yaya hisham
mutumin kirki ne ,wallahi sister kin samu miji a yadda kuke gudanar da rayuwarku
yanzu bana jin zai auri nuzla .ke babu ruwanki da sheidar nmj na fad'a miki duk nmj
dake da mata da buduruwa a waje baki biyu garesu idan ma zai aureta suje can su
qarata ni dai a kwantar min da hankali abinda zan fad'a miki Kiyi qoqarin ki rage
tsoransa kinji sun jima suna waya kafin sukai sallama ."
Bayan kwana biyu suna cikin waya da nana hauwa'u taji yana buga kofar d'akin da
karfi da sauri tace "sister gashi nan yana buga kofa ina zuwa ,ta ajiye wayar
batare data kashe ba, ta mike tsaye tun kafin ta isa bakin kofar taji yana cewa
"gidan ubanki ne da zaki dinga kulle kofa ?maryam najin abinda ya fad'a tayi
hanzarin ta bud'e masa kofa tana "cewa duk abinda zakayi yaya adam kayi kuma ya
tsaya a iya kaina kawai amman zagin iyaye bazan sake d'auka ba ATA najin abinda ta
fad'a ya gyara tsayuwarsa da kyau abun ya mugun girgizasa ganin yadda yake
kallonta ta juya ta shige cikin d'akin tana cewa "ka zageni kaci zarafina ni naji
na gani zan d'auka amman iyaye please kayi qoqarin ka daina sakosu ."ai ko babu
komai dady mahaifi ne gareka idan bakayi masa addua ba ai kuma bai cancanci zagi
ba ta fad'a tana rungume hannuwanta duka a qirji ."
A wulakance ya d'auki kallonta daga qasa har sama kafin a hankali ya shigo har
cikin d'akin ya tsaya yana kallon yatsun kafafuwansa a hankali ya motsa lip's
dinsa "say what you said again ina son tabbatar da najiki da kyau tayi shiru taki
cewa komai "gidan nan ba gidan ubanki bane ba kuma da kudin ubanki na gidana shi ba
na maimaita abinda na fad'a ina son kema idan kin isa ki maimata abinda kika fad'a
yanzu ." ya fad'a mata haka kai tsaye kamar bashi ba "daman baa sonki ko digon
d'aya baki da matsayi acikin nan ya nuna daidai saitin zuciyarsa da yatsan hannunsa
"baa sonki amman kike qoqarin shigo da wani salo rashin kunya to zaki sha wahala
akan wahala dan ko ina sonki bazan d'auka ba bare babu d'igo sonki acikin nan.ina
dai zaune dake darajan iyaye ,rayuwar mahaifiyata ke rike da aurenki yau ta
fad'i ta mutu kisani aurenki dani ya qare dan rabuwa zanyi dake da huta ."
"yanzu mami na mutuwa zaka rabu dani "?yes of course zaman me zan cigaba da yi dake
zan rabu da kwallon mangaro na huta da kuda ,baki san kin zame min qaya bane ? ta
runtse idanunta she's so much in love with him amman shi kullum tunaninsa yadda
zai rabu daita , "dan allah meye ribar ka yaya adam da baka son yiwa mami
biyayya ?ta tambayesa muryarta cike da rauni "ai duk akanki ne na kasa wannan
biyayyar kinga kuwa bazan ta'ba sonki ba har na koma ga allah" bazakayi mata
biyayya bayan ranta ba "ubanki zanyi ba biyayya bayan rai ba "ya fad'a a zafafe
yana jan tsaki yare da dafe goshinsa can kuma yace "me keyn d'akina yake ajikin
keyn kitchen?tayi shiru tana dubansa a matukar tsorace "me keyn d'akina yake ajikin
keyn kitchen?" ya sake maimaitawa a karo na biyu hankalin maryam ya tashi sosai
ta masa baya da sauri tun kafin ya sauke mata mari ".
"don't let me rept my self wallahi idan baki fad'a min abinda yasa yazo hannunki ba
zan baki mamaki yanzu .maryam ta sake tsorata dan tasan zai iya aikata komai tunda
ya rantse muryarta na rawa "tace daman saboda na dinga gyara maka d'akin ne "na
buqaci haka daga gareki ?"a'a kawai dai ni naga dacewar haka ne shiyasa "tunda nayi
tafiya kina sharewa ?tace "eh ina sharewa "kina sharewa amman kuma naji d'akin yana
warin mushe ya d'ago yana kallonta tsab yana nazarinta "dan allah dan annabi dan
darajan iyayenka karka min komai ta fad'a haka ne saboda kusancin da suka samu
komai zai iya faruwa.tunda ya tsura mata tsumammun idanunshi bai sake cewa uhm bare
uhm uhm ba sai dai kana kallonsa zaka fahimci ya gaji da damuwarta
"Dan girma allah Ke wace irin halitta ce ?duk abinda mutun bai so shi kike yi ni
wallahi na gaji dake dan hannuna ya gaji da ta'ba jikinki."
" wannann tsana tayi yawa zuciyata karon kanta ta gaji da ganin halin da kike ciki
na fahimci qiyayyar yaya mai karfi ce akanki ya kamata mami ta dauki mataki mai
karfi a kansa" yanzu sister me kika ga zanyi domin kawowa kaina sauki "maryam ta
tambayeta "son da kikewa yaya yayi yawa gashi kuma baya samar min da kwanyar
hankali ?"bari dai yau na kira yaya da kaina nayi masa magana ya sausauta miki
maryam wacce idanunta suka cika da ruwan hawaye tayi saurin cewa "a'a sister karki
masa magana "dan me yasa zaki ce aa?"kinsan halinsa yanzu zai dauka kararsa na
kawo tsaki taja tayi discounting din kiran da kukan nana hauwa'u ta kirasa "a
zaune yake yana kallon labarai amman bai sanda ya mike tsaye ba "a'a auta lafiya
kike wannan uban kukan ?"me hisham yayi miki auta?"
Cikin kuka tace "haba yaya me yasa kake wa maryam haka ?au qarata ta kawo miki ko
me ?sam sam bata kawo qararka ba, nan dai tayi masa bayani yadda akayi taji "dogon
tsaki yaja " ke bazaki gane wannan yarinyar muguwa bace sannan makarya ce gata da
siffar munafukai gabad'aya alamunta na rashin gsky ne, nifa ban ta'ba ganin makirar
yarinyar kamarta ba ga taka min dokoki da take "Allah yaya sister nada kirki kuma
tana sonka "kinga auta ajiye maganar so wannan yarinya muguwa ce na fad'a miki
"wallahi yaya zuciyar maryam a wanke take akanka ,haduwar aurenku daita baku kuka
tsara ba allah ne dan yaya adam kayi hakuri da yadda qaddararka tazo ,sannan
sister bazata taka duk wasu dokokinka ba tana da gudun zuciya gashi ita din mai
biyayya ce . Kayi mata sausauci dani ina son naganta cikin farinciki kamar yadda na
kasance a yanzu , bata ragewa ATA komai ba akan canjin rayuwar daya kawo a gidan
aurenta a sanadiyar matakin da yayi qoqarin dauka akan hisham "
"to yaya ya kake tunani idan maryam tana da yaya ?shima zai dauki mataki
kwatankwacin irin wanda ka dauka akaina amman sai ya kasance sister bata dashi
bata da kowa sai allah da kai ,nayi imani yaya a yadda kake son yanuwanka ko wani
kaga yayi mata haka sai inda karfinta ya qare dan allah ka sausata mata sister na
sonka fiyye da soyayyar kowa da zaka bata dama zakaji dadin rayuwa daita" ata ya
kalli tv yana jin haushin maganarta amman dan ya kawo karshen zance yace "naji sai
anjima kafin tace wani abu ya katse wayar yana jan tsaki ko ana soyayya dole tunda
nace bana yi a rabu dani mana bata ga wahala bane da qafafuwanta zata arce na huta
da jaraba idan taki km zan san yadda zan batar daita a nemita a rasa haba wannan
naci da maseefa ya isheni kowa maryam idan aunty sajida ta kira maganar kenan
maryam duk yan'uwansa maryam dai maryam shi ko Oho babu wanda ya damu da damuwarsa
."
Bayan kwana biyu maryam ta d'an samu natsuwa sakamakon baya shiga lamarinta sabgar
gabansa kawai yake sai dai ita tana iyakar qoqarin na bashi duk wata kulawa idan
yana gida kullum kafin ya fita aiki zata kula dashi idan ya dawo ma haka wasu
ayyukan yace bai so wasu kuma miskilanci ya hanashi magana sai dai yayita cika yana
batsewa.
Yadda take kula dashi ita bata isa ya nuna mata kulawa ko tausayawa ba idan kaga
annuri a fuskarsa to baki yayi amman ita ko oho kuma rashin mutuncinsa agaban kowa
yake yi wannnan yanayi yana sakata cikin tsananin damuwa sai ta zauna tayita kuka
saboda tausayawa rayuwarta idan babu mami a raye tayi imani ko bai rabu daita
kamar yadda ya furta ba allah babu mai kwatarta a hannunsa ."
Ranar lahadi tana parlour'n kasa tana wanke bocxer dinsa da singles tana tunanin
karshe ma yazo yace me yasa tayi dan bai san ta cire acikin kayan wankinsa ba mami
ta shigo bakinta dauke da sallama ,maryam bata san ta shigo ba har sai data
maimaita sallamar sannan tayi firgigib ta dawo haiyacinta tana cewa
"waalaikumussalam ta cire hannunta daga cikin boket ta dauraye ta fito tana cewa
"a'a mami sannu da zuwa "mami tayi murmushi tana cewa yauwa maryam ,maryam ta
durkusa har kasa ta gaisheta ina yini mami ?lafiya maryam ya gida ta fad'a tare
da zama tana qare mata kallo tsab "sannu da zuwa ta sake maimaita fad'ar haka tana
murmushi mami ta kalli parlour'n komai tsaf sai kamshi ke tashi kamar yadda
parlour'nta yake "ji yadda parlour'n Ke kamshi kamar yau aka kawoki "maryam tayi
murmushi kawai " ina fatan dai kina lafiya komai lafiya ko ?lafiya kalau mami ta
fad'a hk dan bata son ta sake yin abinda zai sake kawo masu damuwa "karki boye min
komai maryam idan akwai damuwa ko wani abu dake faruwa tsakaninki da mijinki ki
fad'a min domin nafi kowa kusanci dashi da sanin halinsa."
"Wallahi babu komai mami shikenan tunda kika ce haka daman daga gidan auta nake
nace na biyo na duba ki nasan halin da kuke ciki tunda kince lafiya Allah yasa haka
"Allah sarki mami ya kika baro sister ?duk da dai koda yaushe muna tare , idan bama
waya waya to zaki samemu muna chart, bata gama rufe bakinta ba suka jiyo sautin
muryar ATA a can kasan makoshi yana sallama fuskarsa a hade tmkr zaki ganin mami
yasa ya dan saki fuska kad'ai "sweetheart kice a gidan ?."eh nice ta bashi amsa
tana kallon fuskarsa tsam maryam ta tashi daga zaunen da take ta shiga kitchen
domin samawar mami abinda zata ci ."a natse ya zauna yana cewa "sannu da zuwa
sweetheart ina yini ?"lafiya ya aiki ?"alhamdulillah yay shiru yana d'an ciza lip's
dinsa na kasa batare da ya sake cewa komai ba har kusan second biyar mami ta
numfasa tace "wato kai yanzu idan ba nemanka nayi ba bazaka zo inda nike ba yau
kusan kwanaki ashirin kenan babu labarinka kawai rayuwarka kake yi baka tunanin
halin da zan shiga na rashin ganinka "
"Wallahi adamcy ka bani mamaki daka iya tsallake kasar nan baka fad'a min ba haka
zalika ka dawo baka tako kazo inda nike ba duk akan na fad'a maka gsky shine ka
d'auki mummunar fushi dani "babu komai rayuwa ce kuma arziki ganina a raye ne duk
ya janyo haka "kiyi hakuri sweetheart kina raina wato yanayin aiki ne yayi min yawa
a office sai kuma ga tafiyar gaugauwa ta sameni shine dalilin da yasa baki ganin
ba amman ba fushi nake dake ba yau din nan nake son nazo na ganki wallahi kina
raina duk abinda zan yi sai kin fado kuma nasan zakiyi tunanin haka amman aiki ne
"."yayi agogo sarkin aiki amman tun ranar da nazo akan case dinka da mahaifiyar
maryam ka dauki fushi dani ya kalleta kawai "karka wani min wannan kallon
naka ,nasan halinka fa ko da qafa kayi magana wallahi zan fahimceka fushi kayi dan
ban goyi bayanka ba amman kai a ganinka goyon bayanka shine alkairi?"
"at least sweetheart ya kamata kiji haushin kalaman data fad'a akanki sam sam babu
respet dan haka ni har abada bazan ga girmanta ba "ai shikenan ka cigaba allah ya
bada saa ni zan tafi maryam maryam!! ." na'am mami ta fito da sauri daga kitchen
taga mami tsaye "mami ba dai har zaki tafi ba gashi na daura miki abinci ?tafiya
zanyi maryam daman nazo naga lafiyarki ne ta mika farar ledar data zo mata dashi
wanda Ke dauke da kayan snak "ga wannan kin dinga tabawa kina rage kwad'ayi sai
kuma an kwana biyu na gode mami allah ya saka miki da alkhairin allah ya bar mana
Ke amman dan allah mami ki tsaya kici abinci mana "abincin kuma maryam ?Aa bazan
tsaya naci komai ba ni akoshe nike zuwa kawai nayi naga lafiyarki in allah ya yarda
kuma sai an kwana biyu ."to shikenan mami allah ya tsare mana ke ta nufi kofar fita
ATA na biye daita tare da maryam ya bude mata gidan baya ta shiga ta zauna yace
"Allah ya tsare tayi masa banza Kmr bata jisa ba ya rufe murfin mota suna tsaye har
sai da suka ga tashin motar mami sannan suka juyo zuwa cikin gidan ."
suna shiga parlour'n yace "ke me kika fada mata ?wa ni ?Aa ni! ina tmbyrki kina
tmyta ko kinyi hauka ne ?ya fad'a ransa a matukar bace "kamar yaya kake nufi ? ni
fa bance mata komai ba ko kana tunanin zan fad'a mata wani abu ne ?yayi shiru
kawai ya tmbyeta ne sakamakon ganin yanayin fuskar sweetheart din ba kamar yadda
ya saba gani ba "nifa babu abinda na fad'a mata bai tsaya sake jin komai ba ya haye
sama ya barta tsaye tana kallon bayansa yayinda idanunta suka ciko da hawaye ta
daura hannunta duka saman kanta ta fashe da kuka "na shiga uku ta furta a fili
yaushe zan fita cikin wannan damuwar ?."babu rana idan ba rabuwa zakiyi dashi
ba ,zuciyarta ta bata amsa da haka jiki a sanyaye taje ta cigaba da aikinta tana
wanki kwakwaluwarta na tunanin mafuta akan zamanta da mijinta ta dauraye singlet ta
fito zataje ta shanya ya sauko daga shi sai qaramin wondo iya cinyarsa wanda ya
kama jikinsa da kallo tabi sa dashi ,kyau ne dashi har a surar jikinsa, babu
lafiyayyar macen da zata gansa haka bataji shaawarta ta motsa ba,yana tafiya yana
shafa qirjinsa bai kalli inda take ba ya samu waje akan kujera ya zauna nan da
nan tunaninta ya canza zata so ace mijinta ya kusanceta amman taya hakan zai faru
?” ta wacce hanya zata bullo masa domin duk biyayyarta garesa bazai saurareta ba ”
“Komawa tayi d’akin bayan ta gama aiki ta cigaba da tunanin mafuta ,har dare
zuciyarta bata barta ta huta ba ta kasa runtsawa washegari tun da sassafe ta kira
nana hauwa’u” sister na rasa yadda zanyi ki taimakeni sister ,gabdaya kaina ya
kulle na rasa me zanyi ina son yaya adam ya kasanceni amman Kinsan idan nace zan
nemi yaya adam kai tsaye ubana zai ci “shikenan ki kwantar da hankalinki ga shawara
ina wannan grup da nake muke ciki ciwon ya mace da matan so kiyi admn din group’s
din magana zasu iya baki shawarwari “shikenan sister na gode bari nayi masu magana
duk abinda ake ciki zan sanar miki .bayan sun gama waya mata son ta shig ta duba
admn taga tana online dan haka sai ta bita pc tayi mata Slm .”
bayan wani lokaci ummu maryam tayi mata reply da Wslm bayn sun gaisa tace sister
naga kice admn group din matan so naga group din ana gyara aure ne dan allah inada
matsala da mijina dan allah ina son ki bani sharwari “oky babu damuwa ina
sauraronki maryam tayi mata takataccen bayani akan rayuwar aurenta a karshe tace
na kasance mai karfin sha’awa kuma mijina baya kusantata shine nake son dan allah
kibani shawara akan yadda zanyi ya dinga kusantata “okay idan dan wannna ne baki
da matsala dan akwai mafuta muna ta bata shawar yadda zatayi sannan tace muna siyar
da maganin karfin maza idan kina so zaki iya siya akwai wanda ake bayarwa asobo’
akwai wanda ake bayar a coffe ‘ akwai wanda zaki dafa mashi kamar shayi ya sha idan
yana sha ko acikin drinks sannan akwai wanda hanky ne da zarar kin samu damar kin
daura masa akan gabansa zakiyi mamakin yadda zai kusanceki .”
“Amman sis ko akwai wanda zan masa amfani ya kusanceni batare dayasani ba “duk muna
dashi na coffe ne ,yauwa na gode sosai ki tura min account numberki nawa ne kudin ?
nan dai ta fad’a ko nawa zata bayar batare da bata lokaci ba tace ummu maryam ta
tura mata account number dinta maryam ta kira nana hauwa’u bayan ta dauka ta koro
mata komai amman matsalar sister bani da kudi “bangaren nana hauwa’u tace turo min
account number din zan saka mata cikin kankanin lokaci nana hauwa’u ta turo mata
kudi tare da turawa maryam alert domin ta turawa ummu maryam bayan kwana biyu aka
kirata sakonta ya iso cike da farinciki taje ta karbo “da daddare daya dawo daga
aiki yayi wanka ya dawo parlour ya zauna yana kallon news daga shi sai singlet da
qaramin wondo yayinda ita kuma take kitchen ta hada masa coffe acikin qaramin jug
mai rike zafi da cup kwaya daya ta daura akan tray ta fito ta ajiye masa akan table
din gabansa duk da bai cin abincinta amman baya tsallake tayin coffe dinta .”
Ta juya ta haye sama ta sha wanka ta bud’e akwatin kayan lefenta ta duba kayan
bacci mai shegen kyau wanda yake bayyana rabin jikin waje,ta dauka tasa nan take
ta dawo rabi tsirara rabinta waje wanda duk kamun kan nmj idan ya gani sai yaji
wani iri ajikinsa kayan sharara har ana hango kan nipples dinta tasa amercan pent
wanda yar siriyar igiya ce a tsakiyarsa ta feshe ilahirin jikinta da turare mai
shegen kamshi cike da matsanancin tsoro ta sauko ta zauna akan kujerar dake
fuskantarshi tare da daga kafarta har yana hango pent dinta kallo daya yayi mata ya
dauke kanshi tare da juya mata baya yana cewa “Ke ! Ki gyara zamanki tana jinsa
tayi kamar bataji ba sai ma sake budesu tayi tana daddana wayarta ya juyo ahankali
a tunaninsa ta gyara amman sai yaga ta baje tana kallon wayarta “
“Ke wannan irin iskanci ne nace ki gyara zamanki ? Ya fad’a yana siyaya coffe a
cup tare da sake juya baya madadin ta gyara zamanta sai tayi kamar bata jisa ba
bai juyo ba ya kai hannu ya dauki cup din coffe daya zuba ya sha cup biyu kenan
ya sha amman tund ya sha ya rasa tunaninsa cikin kankanki lokaci ya fara jin sauyi
ajikinsa ya dauki cup din daya sha coffe dashi ya duba ciki bai ga komai ba dan
haka ya ajiye ya koma ya jingina bayansa yana kallonta still tana nan a yanayin da
take har ma ta qara bude kafafuwanta cikin wani salo cikin kankanin lokaci ya fara
rasa tunaninsa mikewa yayi amman kasa tsayuwa dan haka ta mike ta rikosa amman
cikin karfin hali irin nasa ya buge mata hannu yana cewa “don’t don’t touch me aiko
ta zame jikinta aranta tace jiki magayi tun baaje koina ba ka fara fita haiyacinka
ya shige d’akinsa ya fad’a kan gado ya kamkame jikinsa waje daya tamkar mai jin
sanyi .”
ahankali ya nemi dukkanin natsuwarsa ya rasa hankalinsa ya fara gushewa jikinsa har
wani irin karkarwa yake babu abinda zai iya tunawa a halin da yake ciki ,shi
kanshi bazai iya tuna waye shi ba ahankali maryam ta tura kofar dakin cikin saa ta
isketa a bude daman adduarta kenan allah yasa bai kulle kofa ba ,tana shiga dakin
cikin sanda ta yaye bargon daya lullluba jikinsa dashi ta shige jikinsa tana sauke
numfashi .ahankali ta fara shafa week point din duk wani lafiyayyen nmj yayi
qoqarin bude idanunshi amman ya kasa yadda take shafasa sai yake jin abun kamar a
mafarki qoqarin bud’e idanunshi yake domin tabbatar da mafarki ne ko kuwa gaske ne
….”to maryam din mami fatan nasara 😂😂😂
Mmn sudais
💗💗💗💗💗💗
MAR'ADAMS
💖💖💖💖
💗💗💗💗💗💗
*AYSHA A BAGUDO*
WATTPAD @HAUESH
AREWABOOKS USERNAME
AYSHAABAGUDO
bismillahirrahmanirrahim
Wannan littafin na kudi ne mai bukatar karantashi byn na kammalashi zai biya
1000 ta wannan account number din 1438775094 Aishat abdullahi access idan an tura
sai a turawa wannan 09136918331 alert domin tabbatar da an tura domin sauraron
littafaina a tuntubi chaneel dina (Hausa bakwai ) a YouTube.
Page 17
ATA ya kasa bud’e idanuwansa sakamakon nauyin da suka masa, yayinda maryam ta sake
manne masa kamar zata tsaga fatar jikinsa suka had’u suka manne wa juna ta shige
jikinsa sosai tana shakar dad’dan kamshin turarensa mai bugar da zuciya wani irin
zazzafan sonshi ke sake shigarta yana bin jinin da tsokar jikinta numfashi ta
sauke da karfin gaske muryarta a raunane tamkar wacce zata yi kuka ta fara magana
“yaya Adam ina tsananin qaunarka ina sonka kada ka rabu dani ,ban kasance marainiya
a duniya ba amman ina jin maraici atare dani akan soyayyarka wallahi idan ka rabu
dani mutuwa zanyi dan bazan juri zama acikin duniyar nan babu kai atare dani ba, ka
so dan Allah soyayyarka na bani wahala .shafa shi take tana magana can kasan
makoshi tana jin wani maganadisu soyayyarsa na huda zuciya dama gangar jikinta.”
yayinda shi kuwa sha’awarsa ta dinga motsawa fiyye da lokutan baya daya saba
tsintar kanshi ciki birkitota yayi ta rufto saman qirjinsa sai da tace “wash !!
saboda rikon da yayi mata sannan idanuwanshi a rufe ya fara tsotsan dukiyar
fulaninta domin dai a idanunshi mafarkinsa yake gani baya ganin wata maryam a
matsayin maryam ,nan take so mai tattare da sha’awarta tattare da sanyi ac ga
kamshin turarenta dana shi dana air freshener sukai had’e suna fixgarsa daga can
karkashin lip’s dinsa ya kira sunanta “my princess! ta yadda maryam baza taji sunan
da ya kira ba, romancing din juna sukai sosai kafin daga bisani ya d’auki hanyarsa
duk yadda maryam Ke jin d’an zafi saboda farkon yinta ne ,haka ta daure ta bashi
had’in kai domin samun cikar burinta iya budurcinta ma kawai daya zamo shine farkon
mutumin daya kar’ba ya isheta qarasa rayuwarta cikin farinciki da salama bare zata
so ya tausaya mata ya sota fiyye da komai dake cikin duniyar nan dan akan shi babu
abinda bazatayi dan ta mallakesa gabad’aya ya zama nata na har abada ba .”
Iya juriya maryam tayi dan sosai ATA ya saki jiki baya ji baya gani yayi
sha’aninsa kuma sosai take jin zafi amman ta toshe bakinta har sai bayan da ya gama
sha’aninsa ya kwanta sharaf a gefenta yana fidda numfashi da ajiyar zuciya yana
shafa nonu wanta ,ahankali ta zame ta sauko kasa da rarrafe ta koma d’akinta ta
fad’a bathroom domin gasa jikinta ta had’a ruwan dumi ta shiga ciki har da qararta
tare da runtse idanunta sai da tayiwa kanta ruwan zafi biyu sannan ta d’an ji dadin
gabanta tayi wanka ta dawo d’aki ta kwanta tare da lullu’be jikinta ta kamkame
jikinta waje d’aya, tayi shiru tare da tsurawa bangon d’akin ido babu abinda take
gani sai hallitar jikinsa tana mata gizo , gani take kamar jijiyarsa take kallo ko
kifta idanu bata yi cikin ranta tace” allah mai halitta yanzu duk girman abun
nan ya iya shigewa jikina ?” gashi baya haiyacinsa bare ya tausaya min runtse
idanunta tayi sai ga hawaye sharar sun biyo kuncinta .”
ta tuna a novel din da take karantawa idan namiji yayi disvirging din mace irin
kulawa da soyayyar da yake nuna mata amman gashi ita ta tashi a zero babu soyayya
babu kulawa hasalima da yana cikin haiyacinsa bazai ta’ba kusantarta ba “to ai Ke
kika jawa kaina tunda kika kai karshen rashin kunya da bai damu dake ba me yasa me
zaki damu dashi ?zuciyarta ta tambayeta girgiza kanta tayi tana sake qamqame
jikinta hawaye na cigaba da gangarowa akan kuncinta da kyar ta samu bacci ya
d’auketa cike da shaukin mijinta. washegari da ciwon jiki mai tsanani ta farka dan
ko iya tashi batayi ba ,daga inda take kwance ta janyo wayarta ta kira layin nana
hauwa’u tana d’auka tace “sister ki taimakeni kizo min da doctor bana da lafiya
jikina ,ke koina ciwo yake min “bata tsaya jin abinda nana hauwa’u zata fad’a ba ta
katse kiran ta sake jan bargo ta lullu’be jikinta ”
Qarfe takwas da mintuna ashirin nana hauwa’u ta shigo parlour’n gidan tare da
doctor aysha saminu babu motsin kowa a parlour’n sai na na’urorin da kuma hasken
qwayayen da basu kashe daren jiya ba kai tsaye saman gidan ta nufa tare da likita a
bakin kofar d’akin ta tsaya tana knocking ahankali, jin shiru ta fara neman layinta
“ki shigo a bud’e kofar take dan haka nana hauwa’u ta tura kofar d’akin suka shiga
tana kwance akan katifa numfashi kawai take saukewa ahankali kamar wacce take da
cutar asthma. da sauri ta qarasa ta hau saman gado ta yaye bargon da ta lullu’be
jikinta dashi ta ta’ba jikinta wani zafi taji ya ratsa tafin hannunta “subhallah
sister sannu numfashi ta sauke tace “yauwa sister ina doctors din dan hankalinta
bai kai ga ganin doctor aysha dake tsaye ba “gata tare muka zo “dan allah kice
doctor aysha ta dubani sister jikina kamar ba nawa ba “nana hauwa’u ta kai bakinta
daidai kunne maryam tayi mata magana cikin rad’a “da alamun buqata tabiya ?bari
sister naji jiki wallahi ban san zan iya dauriyar nan ba “alhamdulillah allah yasa
kwallon yayana ya shige raga “to ameen amman fa ina jin tsoro “ nana hauwa’u ta
d’ago ta dubi doctor aysha tana cewa “dan allah ki duba min sister tare da yi mata
qarin bayani abinda ya faru dan ta samu damar yin aikinta cikin sauki sanann ta
matsa ta bata waje .”
doctor ta dubata taga bataji rauni sosai ba dan haka tayi mata alurai ta rubuta
magani wanda zata sha sannan nana hauwa’u ta sallameta “sister cinyoyina bazan iya
d’agawa ba “sorry tunda anyi miki allura zakiji saukin ciwon ta fad’a tana kai
hannunta jikinta ta soma mammatsa mata “ina yaya yake ?na dai barshi a d’akinsa
bansani ba ko yana nan ko ya fita office ba “qarshen qiyayya ya qare idan ciki ya
shiga shikenan maryam tayi shiru taki cewa komai dan zuwa yanzu tana jin nadamar
abinda ta aikata “allah yasa ciki ya shiga sister”nana hauwa’u ta sake maimaitawa
tana matsa mata kafafunta tana sakin murmushin naunayen ajiyar zuciya maryam ta
sauke “allah yasa idan ya shiga yayi farinciki idan hakan ta kasance zanji dadi
sosa dan wallahi sai yanzu nake jin tashin hankali.” karki wani damu kanki babu
abinda zai faru sai alkhairi Ke dai Kiyi wa kanki kyakkyawan fatan yaya na matuqar
son yara nayi imani kika samu ciki zai ajiye komai ya rungumeki “idan kuma yace
taya hakan ta faru me zance masa ?wallahi tsoronsa nake ji bari na kira mami na
fad’a mata “a’a sister kunya zanji ace amatsayina na diya mace na aikata
hakan ,fyade fa nayi masa ai wannna abun kunya ne a gareni .
“Dan allah karki d’aga hankalinki mu jira lokaci amman ni nasan da gaske zai so
abinda zaki haifa idan allah yasa an samu domin sosai yaya Adam yake son yara tun
maryam na iya bawa nana hauwa’u amsa har tazo tayi shiru sakamakon baccin daya
d’auketa ta lullu’be mata jiki ta fito domin siyo mata magungunan da doctor ta
rubuta .”bangaren ATA kuwa bai farka ba sai karfe goma daidai ya tashi da
matsanancin ciwon kai da ciwon jiki mai tsanani yana tangadi ya tashi ya fad’a
kan kujera safo kwaya d’aya dake dakin ya rike kanshi dake sarawa yana tunanin tare
da son tuna abinda ya faru dashi ,iskancin maryam na jiya ya shiga dawo
masa ,yanayin shigarta da zamanta da kuma coffee din daya sha tsaki yaja ,yayita
qoqarin ya tuna abinda ya faru bayan wannna amman ya qasa tuna komai saboda karfin
maganin ,lumshe tsumammun idanunshi yayi kawai ya yunkura da kyar ya tashi yana
had’a hanya ya daura hannunsa akan handle din kofar shiga bayi sai kuma ya dan
tsaya yana ciza lip’s dinsa “amman dai kamar kayi mafarkinka daka saba jiya?” yes
nayi mafarkin princess dina ya bawa zuciyarsa amsa da haka sannan ya shiga yayi
wanka tsarki ya fito ya tsaya yana kallon d’akin kafin ahankali idanunshi ya sauka
akan bedsheets wanda duk ya baci da spam shiru yayi yana mamakin ganin sha shin
spam wanda bai saba ganin haka ba a duk sanda yayi mafarkinsa , dan qaramin tsaki
yaja sannan ya janye zanin gadon ya nad’e ya ajiye a gefe ya dauki fari bedsheet
ya shimfid’a ya shirya ya fita zuwa office.”
Wunin ranar a gidan nana hauwa’u ta wuni tana kula da maryam sunyi hira mai
mahimanci maryam tace “sister Kiyi min alqawari babu wanda zai san da faruwar
abinda ya faru a tsananina da yayanki “idan ya zama ciki fa ?maryam tayi shiru
cikin tsananin tashin hankali “zan so faruwar hakan amman ina jin tsoro zan so ace
yana cikin haiyacinsa komai ya faru sister wallahi tunanina me zai je yazo yayinda
ciki ya shiga ?kai sister dan allah ki bar wani tunanin abinda zai faru “sai bayan
la’asar sannan nana hauwa’u tayiwa maryam sallama ta koma gida “.
Tsawon kwanaki uku nana hauwa’u na zuwa gidan amman ko sau daya basu had’u da ATA
ba dan tana zuwa Qarfe shabiyu ta wuce bayan laasar a haka har maryam taji sauki
sosai sai dai zuciyarta da gangar jikinta amatukar tsorace suke .”
Yau sati d’aya kenan da faruwar abinda ya faru a tsakaninta da ATA tana zaune a
parlour’n sanye da kayan shan iska sai dai ba irin na ranar nan bane wannan yana
da d’an dama domin wonda da riga ne masu taushi green colour touch of white wonda
iya cinyarta yayinda rigar ta kasance hamles hannunta rike da waya tana chart a
group dinsu na matan so ya shigo ko kallon inda take zaune bai yi ba ya nufi
hanyar sama yana furzar da hucin iska daga bakinsa da sauri ta d’ago daga abinda
take tabi bayansa da kallo tana tuno gamuwarta dashi tana sake jin wani sonshi na
shigarta amman shi ko kad’an bata hango sausauci daga garesa ba har yanzu yana Kan
nashi kudirin na rashin sonta kuma ta tabbatarwa kanta da wahala ya sota din dan
bata hangowa kanta dalili ko abinda zai sanya shi nemanta ba koda zasu shekara dubu
a haka ne , ita yanzu kanta take tausayawa dan duk ranar daya fahimci ya
kusancenta wanda itace silar faruwar haka ta kade .”
Mikewa tayi da sauri tun kafin ya kai ga hawa sama ta sha gabansa tana masa sannu
da zuwa tare da qoqarin amsar jakar hannunsa ,wani kallo ya d’auketa dashi tun daga
sama har qasa sannan yaja tsaki “meye haka ?ya fad’a a tsawace “sannu da zuwa nayi
maka sannan ka kawo jakar na kai maka d’aki wani tsaki yaja “kina da matsala
wallahi wai sau nawa zan nuna miki bana son duk wani abinda zai had’a ni dake ?sau
babu adadi “ ta bashi amsa da haka tana kallon cikin idanunshi “okay tsayawa
matsayinki ne bazakiyi ba kome ?Ko d’aya wannan hakin daya rataya a wuyana ne kaga
dole na sauke kallonta yayi kawai sannan ya cigaba da magana “wad’an nan kayan na
jikinki da wanda kika saka last week kar na qara ganin kin sashi acikin gidan idan
ba haka zaki had’u da damuwa yanzu ma kije ki ciresu bana son ganinsu idan ma kina
sakasu dani ne kinyi aikin banza dan wallahil azim bazaki dauki hankalina ba
saboda bana ganinki a matsayin mace “ yana gama fad’ar haka yabi gefenta ya hau
sama.”
ta biyasa ta shiga d’akinsa alokacin yana tsaye a bakin gado ya soma cire kayan
jikinsa ta cikin madubi ya hangota tsaye still da kayan da yace ta cire tsaki yaja
yayi cilli da kayan daya cire ya shige bathroom fitsari yayi ya fito ya kwanta
flat akan katifa yana sauke numfashi tare da runtse idanunshi dan wani irin ciwo
kanshi Ke masa wanda ya rasa dalili tun last week yake fama dashi ahankali bacci ya
fara fixgarsa , cikin sand’a ta shige bayin ta had’a masa ruwan wanka ta fito
domin had’a masa coffe dinsa na gado baccin minti goma yayi ya mike ya fad’a bayi
yana shirin hada ruwan wanka tsayawa yayi cike da tunani bai yi mamaki ba dan
yasan aikinta ne ,haka take masa a duk sanda ta samu damar shigowa d’akinsa . ya
sanya hannunsa cikin ruwan babu shiri ya shiga dan ruwan yayi masa yadda yake so
dan har wani qamshi yake bai bata lokaci ba ya shige bathtube ya kwanta luf aciki
kamar wani qaramin yaro dumin ruwan na ratsashi ahankali gajiyar jikinsa ke
warwarewa yayinda acan bedrom dinsa maryam tuni ta hau tattara kayan daya cire ta
kai inda yake ajiyewa ta sake gyara masa dakin ta feshe da air freshener .”
Shiru yayi kwance acikin ruwan yana tunanin irin qoqarinta garesa duk duniya a
yanzu bayan sweetheart dinsa tafi kowa sanin abinda yake so sannan tana iyakar
qoqarinta akanshi sai dai bai san dalilin da har yanzu zuciyarsa ta qasa amincewa
daita ba ,zuciyarsa tashiga wasi wasi anya bazai hakura da mafarkinsa ya rungume
qaddararsa ba tunda ya rasa mafarkinsa ?hisham ya hakura ya rungume qaddararsa
suna zaune lafiya ,daidai gwargwado yarinyar tana binsa tana masa biyayya tana jin
tsoronsa wanda abinda yafi buqata kenan ga matar aurensa.”
idanunshi ya daga ya kalli saman bayin “karka kuskura ka karbi wannan yarinyar
yanzu ta yaya zata nuna irin wannan matar a idon duniya matsayin matarka ?mace sam
babu tsari mace kamar ba halitta mutane ba wannan yarinyar kad’an ya rage bata zamo
wada ba .tunani ya dinga yi ya dauki wannan ya duba ya ajiye akanta a qarshe yace
“ no way Adam you can do that sam sam bata cancata ba kwata kwata ma bawan nan
tunani ya kamata ka tsayi ba kai da kake da tafiya agabanka a gobe gara ma ka tafi
ko zuciyarka zata samu natsuwa dan yawon ganin ayyukan alkhairinta gareka zai iya
sauko da zuciyarka kuma abinda bazaka so faruwarsa ba kenan “ wannan tunanin yasa
shi mikewa daga cikin bathtube ba dan ya gama awanni daya saba yi ciki ba ya saba
sabulu ya qarasa wanke jikisa ya daura towel ya fito .”
Abakin madubi ya tsaya da niyyar shafa mai yaji ta shigo ta matso kusa dashi zata
kai hannunta jikinsa yayi saurin matsawa yana mata wani irin kallo yana mai jin
zafi da haushin shishigi irinta bata damu da irin kallon tsanar da yake mata ba ta
sake matsoshi wani mugun tsaki yaja yana sake matsawa tare da jin zafi, zuciyarsa
na sake tsanarta ya qarasa gefen gadonsa wani abu ya danna a gefen gadon take duk
wasu kayan shafe shafensa suka bayyana ya soma dauka daya bayan daya yana amfani
dashi tayi taku uku ta tsaya abayansa har yana jin saukar hucin numfashinta ya juyo
a fusace tayi saurin ja baya hanyar fita ya nuna mata da yatsan hannunsa yana cewa
“wai me yasa baki da zuciya ne ?dole ne ?! nace dole?!! nace banayi banason
ganinki a inda nake ki kama kanki mana ko dole sai mun hada inuwa daya dake ?nasani
ba dole bane amman ni ina qoqarin sauke hakinka dake wuya ne “nace bana so ,In your
life don’t you ever enter this room again idan ba haka ba duk abinda nayi miki kice
kika jawowa kanki leave ya sake nuna mata hanyar fita .”
“Shikenan zan fita amman ga flaks din coffe can na kawo maka nasan zaka buqata “oh
my goodness god “ya furta yana dafe goshinsa murmushi tayi sannan ta fita tana
leka fuskar shi bayan ta fita yaja tsaki sannan ya cigaba da abinda yake byn ya
kammala ya fitar da qananun kaya ya saka sanann ya sanya takalmi silifas wanda ya
dace da kayan jikinsa a nutse yake saukowa qasa, har yanzu parlour’n shiru yake
bata ma cikinsa bai damu ba sai ma dadi yaji da bai tarar daita ,tunanin abinda
zai sakawa cikinsa yake dan tun safe zuwa yanzu bai ci komai ba
hankali ya samu waje ya zauan yana kiran daya daga cikin masu tsaronsa byn ya
dauka yace a turo masa musa domin samo masa abinda zai ci .”cikin kankanin loaci
musa yayi knocking ya bashi izinin ya shigo ya fad’a masa abinda yake so ya ciro
wallet dinsa, fararen sababbin yan dubu dubu guda goma shabiyar ya mika masa ya
juya ya fita da sauri shi kuma ya mike akan kujera ya kwanta ya daura hannunsa daya
akan cikinsa yana shafa lafaffen cikinsa .”
Bai Jima da kwanciya ba musa ya dawo yayi knocking kofar parlour’n yana daga
kwance ya bashi izinin shigowa ya shigo cikin parlour’n hannunsa da fararen ledodi
cike da girmamawa ya sake gaishesa aciki ya amsa tare da mikewa zaune ya amsa
ledodi ya ajiye a saman table din gabansa wallet dinsa ya sake ciro ya ciro kudi ya
mika masa musa yayi Godiya ya fice daga parlour’n .”ahankali ya bude ledodin ya
baje akan table din gabansa ya fara ci sai daya ci ya koshi sannna ya mike ya ya
bar sauran ya haye sama alokacin an fara kiran sallar magrib bayi ya shiga yayi
alwala ya fito ya fita zuwa massalacin dake manne da gidansa bai dawo gidan ba sai
wajen qarfe goma yana shiga d’akinsa system dinsa ya kunna ya zauan akan kujera.”
kusan karfe daya na dare ya kai yana faman aiki akan system wanda maryam duk
tana hankalce dashi dan itama sai zariya take daga d’akinta zuwa parlour’n qasa
cikin wasu hadaddun kayan bacci sosai ATA ya gaji kuma alokacin babu abinda yake
bukata kamar coffe dole tasa ya janyo flaks din da maryam ta ajiye masa da cup ya
tsiyaya ya fara sha yana cigaba da aikinsa kafin ahankali bacci ya fara fixgarsa
ya tattara komai ya ajiye ya kwanta nan da nan wani bacci mai nauyi ya
daukesa .ahankali maryam ta shigo dakin , ta tsaya akansa tana qare masa kallo
tsab ” “ina ma zaka iya bani dama dana bayyana maka irin yadda nake ji akanka
azahiri bani da muni da kake tsanata akanshi ,duk wani abu da mece take dashi na
daukar hankali ina da shi yaya Adam, abu daya ne kawai bani dashi shine tsawo kuma
nima bani nayi kaina haka ba ,haka allah yake son ganina .”
Tana tsaye shiru tana kallon tana zance zuci daya daga cikin wayoyinsa ta dauki
qara da sauri ta durkusa kasa ta kamkame jikinta wuri daya tana rawa jiki, ya
lulobo wayar ya daga da kyar batare daya bude idanunshi ba sakamakon nauyin da
sukai ”hello !!! yaji shiru dan haka ya mayar ya ajiye wayar ya koma ya kwanta da
hannu hagu .”ta sauke naunayen ajiyar zuciya ta mike a hankali tana lika fuskarsa
bacci ya koma dan hk ta soma kokarin dawo gabansa ta zuba masa idanunta tana jin
kamar ta had’iyesa tsabar son da take masa shine farin
Cikinta wallahi da zaa tambayeta dashi da kanta wa tafi so tabbas shi zata za’ba
akan kanta wani kiran ya sake shigowa da wani irin mugun sauri ta hantsila byn
kujerar sofa tana rawar jiki “.okay zuwa gobe kenan eh kazo mu wuce ta nan “iya
abinda taji ya fad’a kenan ya kashe wayoyinsa gbdy ya koma ya kwanta yana sauke
ajiyar zuciya wani bacci mai nauyi ya daukesa cikin sand’a ta fito daga bayan
kujera ta tsya akansa kusan mintuna talatin tana kallonsa kafin ahankali ta kai
hannuta fuskarsa taji gabad’aya yanayin saukar numfashinsa ya canza tayi taku
biyu ta haye gadon ta kwanta abayansa rungumesa tayi tsam ajikinta tare da zagayo
da hannuwanta Kan qirjinsa tana shafa Kan nipples dinsa da hannuwanta duka wani
wahalallen numfashi ya sauke .”
Ahankali ta dinga murza Kan nipples dinsa masu dan girma tana goga masa nonuwanta
ta d’auki sama da minti shabiyar sannan ta zare hannuwanta ajikinsa ta cire rigar
baccin jikinta shima ta cire masa kayan jikinsa ya saura sirara haihuwar mami ta
tsurawa gabansa ido yana da girman gaban sosai tamkar dai yanayin mazan daake
rubutawa a novel ya had’u ta koina ta d’auke idanunta akan jijiyarsa ta kai ga
fuskarsa , pnky lip’s dinsa ta tsaya kallo da wasataccen gashin girasa a natse ta
dawo gabansa ta shige masa tare da lafewa sosai ajikinsa tamkar wata baby cikin
bacci yake jin wani irin shock a ilahirin jikinsa tamkar ana jonashi da wutar
lantarki yayinda sha’awarsa ta soma motsawa bai san sanda yayi mata riko mai kyau
ba ,ahankali maryam tayi shiru tana jin yadda jijiyarsa ke tashi tana harbawa wanda
hakan ya nuna mata alamun yana jin wani abu wasanni ya soma aika mata dashi cikin
kwarewa ita kuma har lokacin tana lafe tana shafa kwantaccen gashin qirjinsa mai
matukar taushi zuwa Kan nipples dinsa yau ma dai kamar wacan ranar sai da tayi
nasara ya kasanceta cikin mayen bacci sakamakon maganin da tayi masa amfani dashi a
coffe taji dadin wannan kasancewar sannan bata ji zafi kamar wannan lokacin ba
baccinsa ya cigaba da yi hankali kwance .”
Ta janyo bargo ta rufa masa tana kallonsa tana jin wani zazzafan qaunarsa mai
tattare da kishinsa nabin jinin jikinta ,bata jin akwai wata mace da zata lamucewa
kasancewa da mijinta duk runtse sai dai bayan ranta amman ita dashi mutuwa ce kawai
zata rabasu “to kuma ai kince kina son ya dandani zafin soyayya taya zai dandana
kenan ?bayan kuma wanda yake dandana akan mafarkinsa “? zuciyarta ta bata amsa da
hakan “wannan ai mafarki ne maryam a zahiri yaga samu yaga rashi “bazan iya ba
bazan iya wannna kasadar ba ,bazan iya barin wata mace koda wasa ta ra’bi inda
mijina yake ba sai dai bayan raina mijina nawa ne ni kad’ai zanyi komai dan ya zamo
mallakina na har abada “tun da asuban farin ta lallaba ta gudu dakinta kafin ya
farka yaganta yaci mata mutunci.”
Shi kuwa bai tashi ba sai karfe goma a gigice ya tashi kamr wacan ranar da ciwon
kai mai tsanani da jiki ya tashi da kyar ya shiga bayi yayi wanka ya dauro alwala
ya fito ya gabatar da sallah byn ya idar ya shiriya sannnan ya soma had’a kayanshi
cikin sauri yana duba agogo qarfe shadaya daidai ya kunna wayoyinsa nan take kiran
mutane ya soma shigowa wayarsa ya sauko parlour’n rike da qaramar jaka alokacin
maryam tana kitchen taga fitowarsa yana amsa waya wanda Ke sake tabbatar mata
tafiya zai yi kamar yadda tayi tunani sakamakon wayarsa ta daren jiya “ta fito da
sauri tana goge hannunta ta kira sunansa”baby ! yana jinta yayi mata banza yana jan
tsaki ganin haka yasa tace “yaya Adam!cak ya tsaya batare daya juyo ba “tafiya
zakayi ne babu sallama ? shiru yayi bai ce komai ba “to shikenan allah ya tsare
allah saukeka lafiya .”
A matukar fusace ya juyo ya kalleta kafin ahankali ya motsa labbansa “yaushe muka
fara haka dake ?ya tambayeta “laifi ne dan nayiwa mijina addua ?hakina ne ka fad’a
min zaka yi tafiya ko ba dan komai ba saboda halin mutuwa ,karka manta idan ka mutu
a yanzu ni din nan dai nice zan maka takaba ,haka zalika idan na mutu kai din ne
dai zai kaini kabari shiyasa yana da kyau ka ajiye komai ka bari muyi zaman aure
kamar sauran maaurata tunda na zame maka dole kai ma ka ..” ai bata kai ga qarashe
maganarta ba ji kake tasss !saukar marin ATA ya zuba mata sai da maryam taji wani
jiri zai qara mata shawul ya rike hannunsa ciki zafin nama sauran kadan maryam ta
fadi kasa .” wani kallo yayiwa shawul din dole tasa ya sakar masa hannu yana cewa
“kayi hakuri mana duk fa abun bai kai ga haka ba …” ina ruwanka !ya fad’a yana
nuna masa kofa fita sannna ya fuskanceta da kyau “sha sha banza sha shar wofi akan
me zaki min addua ance miki ina bukatar adduaki ne ? adduar uwata kadai ya isheni
idan na mutu kika min takaba allah ya isa ban yafe ba Ke kuma idan kin mutu sai dai
Ubanki ya sakaki akabari amman ba dai ni ba banza mara zuciya kawai .”
nan da nan yanayinta ya canza ta zuba masa ido kawai tana kallon yadda yake zuba
ruwan bala’i “matsawar baki daina shiga rayuwata ba kin dinga ganin bacin rai kenan
fiyye da wanda nake miki shawul kam bai wuce ba kamar yadda ATA ya bukata yana ta
bashi hakuri bai yi magana ba ya nufi kofar fita shawul ya cigaba da bata hakuri
murmshi kawia tayi tace “haba yaya shawul babu komai fa kabishi kar ya tafi ya
barka ko kuma ya dawo ya sauke fushinsa akanka abinda ya aikata ba abinda zai
dameni ba kuma bazai sa na canza ba ko a wani yanayi yake zan cigaba da zama dashi
karka damu wata tana zai zama labari “allah ya qara miki hakuri maryam “dan Ke din
salahar mata ce gaskiya kina da kirki da hakuri nima shedane ,tausayi imani Duk
kin hada matar da zaayi alfahari daita ce babu Wanda zai samu mace mai irin
halinki Kuma yaki son ki zama matarsa sai wannna sarkin zuciyar tayi murmushi tare
da cewa “na gode sosai da yabo tare zakuyi tafiyar ne ?eh tare zamu hollond “allah
sarki to dan Allah ka kular min dashi .”karki damu in sha allahu “allah ya tsare
dan Allah idan kun shiga jirgi kayi masa hoto ka turo min ta fad’a tana murmushi
shawul ya juya ya bi bayan ATA yana jinjina girman hakurin maryam da girman
soyayyarta garesa allah ya hada masa komai da komai na duniya amman girman da
nuna isa yasa ya kasa gane salihar macen daya samu .”
Tunda ATA yayi tafiyar nan tashiga damuwa madadin tayi farinciki amman sai sabanin
haka tunanin rayuwar da take a gidan data rashin isashen abinci agidan da kuma ta
kewar mijinta dan yanzu manage rayuwarta kawai take hakan yasa duk tabi ta zabge
ta rame abun duniya duk ya isheta gashi babu wanda zata iya tun kara da wannan
batun mutun daya ce zata iya fadawa itace nana hauwa’u kuma tasan zata nemammanta
mafuta amman dole mami taji idan mami taji kuma dole ATA yaji kuma tasan bazai
barta haka ba sai ya gana mata izaya kala kala wata zuciyar tace ta kira mahaifinta
ta fad’a masa shima dai dole zai fadawa mami dan abun kaskanci ne ace kamar gidan
nan babu abubuwan more rayuwa kusan kullum abu d’aya take ci idan tayi baki duk
kunyar duniya ta isheta wani lokacin nana hauwa’u take kira ta tura mata kudi
saboda baki to kuma ta dinga tambayarta kenan ?”.
bayan sati biyu mami ta sake kawo mata ziyara alokacin maryam tana wanke wanke a
kitchen tana kuka har da shesheka daga bayanta taji sautin muryar mami “Ke me ya
sameki hk ?muryar mami yasa maryam ta juya bayanta da sauri tabbas itace tsaye
nan da nan tashiga goge hawayenta “ina adamcy?ta tambayesa tana qarasowa gareta
tare da kallonta “yayi tafiya zuwa hollond “ kenan bai dawo ba ?maryam ta gyda
mata kai alamun eh nan da nan mami ta shiga cikin kitchen din tana bubbude cabinet
babu komai na abinci sai shimkafa wacce bata wuce kwatan buhu ba “Inna lillahi wa
inna ilaihi rajiun “yanzu haka kike zaune kike rayuwa acikin gidan nan babu kayan
abinci ?”mami ta fad’a tana maseefa “daman an fad’a min to wallahi bazan dauki zama
da yunwa ba ,duk arzikin da allah yayi maka adamcy a iske gidanka haka wallahi
kaji kunya .“mami babu wani problem’s fa ina cin abinci ,karya kike munafukar
allah karesa zakiyi kina cin abinci kalli yadda kika dawo duk kin qare kin
lalace .”
“to mami Kiyi hakuri amman shi yaya bazai san ko akwai kayan abinci ko babu ba
saboda “me bazai sani ba ?ba zamansa kike yi ba .”?shiru tayi tana danne abinda Ke
taso mata mami ta dubeta tana mata kallon tsab batare da tayi magana ba kafin
Ahankali ta cigaba da magana “maryam kina boye min abubuwa amman kuma ina sane da
komai fa hatta kudin cefane adamcy baya baki bare aje kudin kashewa “ to mami
wannan ai ba komai bane idan da kwanciyar hankali duk mai sauki .“lallai maryam son
adamcy ya gama rufe miki ido .maryam tayi murmushi ta riko hannunta tana cewa “dan
allah mami ki kwantar da hankalinki karki masa magana kinsan halinsa yanzu zai
dauki maganar da zafi daman ina jiran idan komai ya qare zan fad’a miki ki aiko min
dashi ,ai bazan bar kaina da yunwa ba ta zaunar da mami akan kujera .”
Mami ta numfasa tare da daura hannunta a saman kanta “duk itace silar komai ,itace
silar jefa rayuwar yar mutane cikin ukuba yanzu ita yaya zatayi da wannan
auren ?”mayye rudeta da sha,awa cikin hada wannan auren ? take zuciyarta ta bata
amsa da
rashin hakuri da maida lamarinki ga Allah ne yasa kika aikata wannan kuskure kin
hada aure dan kawo kwanciyar hankali a zuriarki gashi hakan bata kasance ba sai
zallar damuwa a boye mami take goge hawayen dake bin kuncinta ‚ domin tana
matukar tausayawa maryam da bata hada wannan auren ba maryam da bata kamu da son
danta ba Ahankali maryam ta shanye kukanta sakamakon tunowa datayi akan cinyar mami
take da goge
hawayen idanunta ta mike zaune ta riko hannunta cikin nata “dan girman allah mami
karki masa magana zan miki list din komai ki aiko min dashi “kina ganin rayuwarki
haka shine mafuta ?to ya zanyi mami bani da zabin da wuce zamana acikin gidan nan
“kina son na kashe auren nan maryam ?”
Mmn sudai
💗💗💗💗💗💗
MAR'ADAMS
💖💖💖💖
💗💗💗💗💗💗
*AYSHA A BAGUDO*
WATTPAD @HAUESH
AREWABOOKS USERNAME
AYSHAABAGUDO
bismillahirrahmanirrahim
Wannan littafin na kudi ne mai bukatar karantashi byn na kammalashi zai biya
1000 ta wannan account number din 1438775094 Aishat abdullahi access idan an tura
sai a turawa wannan 09136918331 alert domin tabbatar da an tura domin sauraron
littafaina a tuntubi chaneel dina (Hausa bakwai ) a YouTube.
Dan allah Ina son masu karatu su san wani abu ,bana son yanke wani abu daya
danganci abinda yake cikin labarin nan domin duk abinda aka rubuta akanshi yana da
matukar amfani ga makaramci kuma kowani bangaren yana buqatar a ta'ba shi domin
idan an zo hukunci ,só ina son masu karatu su bani hadin kai domin samun damar
cigaba da rubutu kamar yadda aka bani a kasin haka kuwa babu abinda zai haifar sai
zuwa hutun rubutu ko kuma abun ya koma sai randa naji nishadi nayi typing kuma
kad'an domin ina iyakar qoqarina na ganin na kawo maku komai daki daki kamar yadda
yake aciki amman kamar ku bakwa gani ko kuma nace kamr kunfini hanzarin son ya
had'u da mafarkinsa ko kuma son a gama rubuta labarin nan to wallahi na fiku son
naga na kammala na huta shiyasa tun farko nace arewabooks zan kai wasu daga cikinku
suka nemi alfarma na kawo what'sapp sannnan sunji kuma sun amince ko sau d'aya ne
na dinga basu a wata amman adalci nawa yasa nake baku kullum dan abini a sannu dan
nesa tazo kusa 😉😉."
Page 18
Kan maryam yayi wani irin mugun sarawa da karfin gaske sakamakon jin abinda ya
fito daga bakin mami ,yayinda qirjinta ya dinga bugawa fiye da kaida “kina son na
kashe auren nan maryam ?” kwakwaluwarta ta sake maimaita mata kalmar da take daf da
tarwatsa rayuwarta ahankali ta zame ta zauna a qasa cikin tsananin tahain hankali
mara misaltuwa tayi shiru tana jin yadda magnr mami ke yawo acikin kwakwaluwarta da
zuciyarta, haka ne ma yasa jikinta ya kama rawa gashi mami taki d'auke kwayar
idanunta akanta tana jiran taji abinda zata ce akan hukuncinta . gano yanayin cewar
maryam ta shiga cikin tsananin damuwa yasa mami kiran sunanta .."
“maryam..”!
"ta d'ago kanta da kyar ta zubawa mami idanunta da suka sauya kala tsabar tashin
hankalin data tsinci kanta "kinji abinda na fad'a kuwa ? maryam ta lumshe mata ido
kawai dan bazata iya magana ba a halin da take ciki wanda take jin yafi duk wani
tashin hankali har ma da qiyayyar yaya Adam gareta ."ki bud'e baki kiyi min magana
domin kawo qarshen wannan matsalar ,nice da kaina na had'a auren nan naku ,idan
kina ganin bazaki iya cigaba da zama dashi ba wallahi a bud’e take bazan cigaba da
takura miki ba ko kuma na ji haushinki dan kinyi min qoqari fiyye da
tunanina ,dan zama da adamcy sai mai katoton hakuri zai iya, dashi kuma daman yana
cikin dalilin da yasa zuciyata ta tsallake kowa acikin yan’uwansa da yan’uwana ta
za'beki amatsayin matarsa ,amman yanzu ni kaina na gaji kuma nasan kema kin gaji
maryam hakuri kawai kikeyi .
Ruwan hawaye ya cika idanun maryam “me yasa mami zatayi wannan tunanin ?ita dake
cikin taskon wahala ba tace ta gaji ba me yasa ita zata gaji har da yunkurin rabata
da muradin zuciyarta ?ta yiwa kanta tambayar tana qoqarin danne kukanta “idan dai
har kina ganin babu damuwa maryam zan rabaku kuma a yau domin bazan juri ganinki
cikin wannan tashin hankali ba. kije ki auri wanda zai soki ya kula da rayuwarki
shi kuma ya cigaba da zama haka tunda rayuwar daya za’ba wa kansa kenan ."zuciyarta
maryam kamar zata tarwatse tsabar tashin hankalin data sake tsinci kanta ciki
tayi shiru tana kallon mami tana assessing maganarta fuskarta d'auke da tarin
damuwa tana lissafa idan ace wani ne ya fad'a mata haka da ita kad'ai tasan irin
matakin da zata d'auka akanshi ,amman mami ce babu abinda zata iya "zazzafan
numfashi kawai ta sauke tare da dukar da kanta qasa jikinta na wani irin karkarwa
tana son boyewa mami damuwarta ."
mami ta kai hannu ta d’ago ha'barta tasanya kwayar idanunta cikin nata ido cikin
ido suke kallon juna ruwan hawaye ne taf acikin idanunta "kinyi shiru maryam
banason shirin nan naki ,banason kiji aranki kamar nice silar shiga damuwarki
domin ni karon kaina ina jin haka araina cewar duk nice silar shigarki cikin wannan
tashin hankalin ,kina zaman zamanki lafiya tare da masoyanki masu sonki da qaunarki
na shigo miki da abinda ya zame miki damuwa ,banason ganin tashin hankali shiyasa
nake neman izininki ."wannan buqata ta mami ba abu bane mai sauki ko yuwuwa
agareta "idan zaki d'auki sharawata maryam ki rabu da adamcy ki huta nima zuciyata
ta huta "anya zan iya kuwa mami ?na rabu dashi wanda rabuwa dashi din yana nufin
har abada bayan a yanzu ne ma nake jin bazan iya daidai da kwana d'aya batare dana
yi masa magana ko sanya shi acikin kwayar idanuna .
“Maryam mami tafiki gaskiya rabuwa da yaya Adam shine mafuta agareki amman kuma
tashin hankali ne mai tsanani ga rayuwarki wanda baki san ranar fita acikinsa
ba .ta sake d'agowa taga har lokacin ita mami take kallo tana nazarinta "ki rabu
dashi maryam !mami ta sake bata umarni a karo na biyu "amman mami kina ganin
rabuwar mu itace qarshen komai "?tayi maganar muryarta da jikinta na rawa
"zaman da kuke a tskaninku maryam bashi da wani amfani a yanzu ni kaina ina nadama
had'a wannan auren, na d'auka komai zai samu sauyi a samu cigaba ashe damuwa akan
damuwa kawai za'a haifar. murmushin 'bacin rai ya bayyana akan fuskar maryam kana
ta girgiza kanta "please maryam Kiyi tunani mai kyau kamar yadda nayi bana son ki
bata shekaru cikin wannan halin, still dai shiru maryam tayi wanda hakan yake nuna
alamun shawarar mami bata mata dadi ba “maryam ba kya tausayawa kanki ?ki tausayawa
kanki maryam nasan kina yin komai saboda ni ne na kuma gode da biyayyarki gareni
allah yayi miki albarka ."
Zuciyar maryam wani irin zafi take mata da tuttukin bakinciki tana jin wata irin
tsantsar soyayyarsa na sake ratsata baza ta'ba kuskuren rabuwa da yaya Adam tayiwa
kanta wanan alqawarin suna tare mutuwa ce kawai zata rabusu ,koma yayi qoqarin
rabuwa daita baza barshi ba tagumi ta zuba cikin zullumi da rashin sanin madafa dan
bazata iya aikata abinda mami take buqata ba ,duk magiyar da mami take mata amman
maryam taki bud'e baki tace zata rabu da ATA." sosai mami ta fahimci soyayyar
adamcy din ce mai tsanani ta hana maryam bin umarninta jikin maryam a matuqar
sanyaye ta mike batare data kalli fuskar mami ba tace "mami dan allah ki bar
maganar rabuwar nan haka ,ni abinda nafi buqata daga gareki shine addua ko kad'an
yaya Adam ya soni acikin zuciyarsa tana gama fad'ar tace "bari naje na kawo miki
abun sha har tayi taku biyu ta taya "dan allah mami karki masa magana akaina tana
gama fad'ar haka ta cigaba da d'aga qafafuwanta ."
Mami tabi bayanta da kallo duk ta zube ,duwawukan nan nata duk sun kusan qarewa,
ramar da tayi tasa ta qara kankacewa ,ta fito daga kitchen rike da cup da jug ,kaw
ai taga mutun tsaye kikam tamkar wani jami'in tsaro cikin wani had'ad'den suit ash
colour haka ma takalman dake sanye a qafafuwansa ash ne sai sheki suke ,tsintsiyar
hannunsa makale da agogon rolex ya zuba hannuwansa duka cikin aljihun wondonsa ga
sihirtaccen kamshin turarensa mai tsananin kamshi ,nan da nan kamshi parlour'n ya
canza zuwa na kamshinsa ."suka tsurawa juna ido shi yana kallonta cike da tsantsar
tsana yayinda ita Ke kallonsa cike da tsantsar qauna satinta uku kenan bata sanya
shi acikin kwayar idanunta ba
bata san tayi kewar ganin kyakkyawar fuskarsa ba sai a yanzu da take kallonsa
tsaye agabanta ,kullum kamar qara masa kyau ake sam bazaka ce 40 garesa ba ,ga
kamshin daddan turarensa duk inda ya shiga sai anji wannan mayataccen kamshin
nashi mai tsayawa arai da dagula lissafi,taji kamar tayi wulli da cup din
hannunta taje ta rungume shi ajikinta taji d'umin jikinsa ."
Qaramin tsaki yaja ganin yadda take kallonsa kamar bata ta’ba ganinsa ba arayuwarsa
baya son yawon kallo ya d'auke kwayar idanunshi ya qarasa shigowa sosai ya zauna
kusa da mami ya baje akan kujera yana furta "wash allah nah na gaji “yayinda
maryam ta qaraso tayi masa sannu da zuwa aciki ya amsa mata shima ganin mami zaune
ne ,a natse maryam ta fara hidima da mami "sweetheart a she dana biya ta gida
bazan sameki ba ?"tace uhm bazaka sameni ba amman nasan ko kwanaki nawa kayi zaka
zo ka sameni zaman jiranka kallonta kawai yayi ya d'an ciza lip's dinsa yana
d'aure fuskasa dan ya fahimci kamar akwai wata a qasa . mami ta kalli maryam
dake zaune kusa daita taga ta girgiza mata kai alamun karta masa maganarta take ta
fahimci abinda take nufi numfashi ta sauke inda ATA ya fara jan mami da hira maryam
ta tashi ta dawo gabansa ta tsugunna yayi saurin janye qafafuwansa tmkr yaga mugun
abu numfashi ta sauke ta sake matsowa ta kai hannuwanta ta janyo qafafunsa saurin
runtse idanu yayi yana jin kamar da wuta ta ta’ba shi .”
Ahankali yaji ta soma kwance igiyan takalminsa d’aya kamar ya zare qafarsa ya buga
mata takalmin a fuska amman ya share sakamakon darajan mami dake gurin ,tana gama
cire masa takalman ya janye qafafuwansa ta kwashe takalman ta nufi hanyar step ."y
a bud’e idanunshi ya cigaba da jan mami da magana acikin hirarsu da mami take fad'a
masa kwanakin nan zuciyarta na mata nauyi "wallahi adamcy bana jin dadin zuciyata
jiya fa da kyar na samu na runtsa numfashina kamar zai bar gangar jikina "haba
sweetheart ya zaki min haka?ya kina jin ciwo ajikinki amman ki kasa fad'a min ko
fad'awa aunty shahida "yaushe rabona da kai adamcy ?” duk ya’yana suna zuwa su
duba lafiyar jikina ,amman kai yaushe rabon kazo wajena ?idan dai mai rabawa ta
rabamu ai shikenan kowa ya huta ko da yake kai ne zaka huta idan na mutu amman
sauran zasuji babu dadi "allah ba zai sa naga wannan ranar ba "kema kinsani
sweetheart kina cikin raina da bamu raba gida ba ,babu abinda zai sa kiyi rashin
ganina a duk lokacin da kika só ,dole duk tsananin aikin daya sakani gaba dole zan
dawo gida na kwanta .”
“ wallahi yanayin aiki ne yanzu da kuma d’a nisan da mukayi amman da zaki min
alfarmar rabuwa da auren nan da na huta domin zan dawo gidanki gbdy ta yadda zan
dinga kula da duk wani motsinki "kaji dashi idan zaka kare kanka kayi amman babu
ruwan aure da rashin zuwanka akai akai "to ma meye amfanin auren?me zanyi dashi
tunda bana sauke nauyinsa dake kaina shiru mami tayi tana nazarin maganarsa "to ma
meye amfanin auren?me zanyi dashi tunda bana sauke nauyinsa dake kaina ta sake
maimaita abinda ya fad'a tayi wa maganar falla falla domin fad'a dashi dan ta
fahimci abinda yake nufi idan dai ta fahimta bayan rashin kwanciyar hankalin da
baya bawa maryam har da hakin aurenta baya saukewa kamar tace ya sauwake wa
maryam din kowa ya huta amman maryam din take ji a halin yanzu ,domin dukkanin
alamun sun gama nuna soyayyar adamcy tayi mata kamun kazar kuka "sweetheart Kiyi
hakuri ki yafe min na kasa miki biyayya na kasa son abinda kike mutuwar so "wannan
son ranka ne kake fad'a da nuna baa isa da kai ba "bai sake cewa uffan ba akan
maganar da take sai ma canza magana da yayi zuwa ta lafiyarta "sweetheart ki
shirya next week zamuje India a duba min lafiyarki "a'a ni bana buqatar zuwa koina
anan ma ina samu kulawar shahida tana iyakar qaoqarinta akaina "dan sweetheart ki
amince please ".
“na yafe adamcy abarni anan idan ma mutuwarce na mutu acikin ahlina allah dai ya
bamu saar tafiya tunda yaji inda mami ta dosa ya lalubo wayarsa ya kira musa
yana bashi umarnin yayi order abincin mutun biyu "mami ta kallesa a tsanake tare
da katse masa hanzari ta hanyar cewa "mai yasa za'ayi order abinci bayan ga matarka
a gida ?"shiru yayi yana karkad'a qafa "me ye amfanin haka adamcy ?"allah ya rufa
maka asiri ka nemi ka tonawa kanka "sweetheart ya kike magana haka kamar baki san
shirmen yarinyar nan ba ?"ai cin abincin wannan sakar yarinyar daidai yake da cin
guba ai sai ta kashe mutun da yaji da maggie "yayi mgnr a matuqar fusace yana jan
tsaki kana ya cigaba da bawa musa umarni yana gama wayar ya mike da kyar ya hau
sama ,a bakin kofar d'akinsa yaga ta ajiye masa takalmansa ,ya bud'e dakin sannan
yasa hannu ya kwashe takalman ya shige dakin,wanka ya shiga bai wani d'auki lokaci
ba ya fito bayan ya shirya kansa cikin kananan kaya ya sauko ya zauna alokacin
maryam tana tare da mami tana tmbayarta abinda zata girka mata "ki girka min duk
abinda kike dashi maryam zanci “ata ya zauna adaidai lokacin da maryam ta mike
zata nufi kitchen muryarsa can qasan makoshi yace "ke.."!
Ta tsaya cak a natse tare da juyowa ta fuskancesa "karki dafa mata wannna banzan
abincin naki “
mami na qoqarin bud'e baki musa yayi knocking ya bashi izinin shigowa musa ya
turo kofar parlour'n ya shigo cike da girmama ya gaishe da mami sannan ya rusuna ya
gaishe da ATA ya ajiye ledodin hannunsa ya juya da sauri ya fice ."ATA ya janyo
ledar farko dake gabansa ya bud'e kamshi kifi tilafia ya doki hancin maryam wanda
yaji kayan hadi da arish had'in kabej da sauri ta had'eyi miyo , ya tura takeaway
gaban mami yana cewa "sweetheart bismillah shiru mami tayi taki ci "tana son yi
masa maganar abincin da ya hana maryam girka mata da kuma abincin da babu a gidan
amman tana jiwa maryam tsoron bala'insa dan haka dole itace zata kawo mata komai
na bukata ta ajiye mata batare da saninsa ba "sweetheart eat !ni babu abinda zanci
gida ma zan wuce mami ta fad'a tana haramar mikewa nan take ATA yace"a'a
sweetheart kiyi zamanki babu inda zaki "bangane babu inda zani ba ?"haba
sweetheart ya kike magana hk kamar kina jin haushina ?saboda ke nasa akayi order
abincin nan amman duk kinki ci komai ,nifa ban gane miki ba “idanu ta zuba masa
tana kallonsa ta rasa wani irin mutun ne shi ,babu yadda zatayi magana bai canza
mata magana ba dan haushinsa tana ji amman meye na fitowa ya fad'a mata ?"dan Allah
sweetheart kici komai da nayi miki order "tunda kake dani ka ta'ba ganin naci
abinci order ?"yayi shiru yana furzar iska “da kayi order dan ni nace mka zanci
ne ?"kai kafi kowa sani bana cin abinci waje kuma kai ma akan haka na raineka ina
da tabbacin ko kana cin abincin order sai dai idan baka qasar nan kai ya langwabar
yana dubanta dan gskiya ta fad’a.”
“dan haka kafi kowa sanin bana cin abinci waje kuma kaima haka duk abinda nake so
ina yi da kaina ko nasa kuku su dafa min amman dan ka wulakanta matarka kake wani
aikawa a siyo maka abinci daga waje idan ma nata ne baka buqata ai zaka iya daukar
mata kuku ko wane su girka maka acikin gidanka
Mami na fadar haka gaban maryam ya bada rasss "kuku a gidanta a'a ?ina bazai yuwu
ba bata son kowa atsakaninta da mijinta tafi bukata ganin gidanta daga ita sai
mijinta gabanta na fad'a uwa ta zubawa ATA idanunta taji abinda zai fad'a."ba
d'aukar kuka bane matslata sweetheart" meye matsalarka adamcy fad'a min meye
matsalarka?"ko kuku nawa zan d'auka basu ta'ba min abinda sweetheart dina zata min
ba"wani boyayyen ajiyar zuciya maryam ta sauke "haka mami yadda yayi maganar sai
kuma taji tausayinsa ya lullubeta “duk abinci nan da nake order nake ci wallahi ina
dai turawa cikina ne kawai amman maganr gsky ni abincinki nafi bukata fiye da
kowani abinci a duniya, idan kina son na daina order abinci sai dai idan zaki
dinga mana kina aiko mana amman sai ta qara hade rai tana zabga masa harara ".
“Ai ba sakar uwa bace ni ,kayi aure yanzu dole ka canza adamcy ka koma kamar tsarin
kowani ma gidanci “kai sweetheart ki ajiye wannan batun magidanci ko menene ni har
yanzu empty nake jina “kai fa sam bakasan mutunci ba bakasan rarrashi ba bakasan
meye hakin aure akanka ba allah ya gani nida mahaifinka muyi Iya qoqarin mu akanka
mahaifinka mutumin kirki daya san darajan iyali kafi kowa sanin kirkinsa akan
iyalinsa kai ne dai bamu san a inda kaje ka kwaso wannan halin ba tana kaiwa nan a
zafafe ta mike saurin riko hannunta yayi cikin nashi "haba sweetheart wai laifin me
nayi miki haka ?Kallonsa tayi ta tabe baninta "bazata lamunce wannan iskancin ba ko
ya bari matarsa ta dinga girka masa ko kuma ya dauko mata masu aiki cikin biyu yayi
d’aya “kiyi hakuri sweetheart idan wani laifi nayi miki am very sorry ma zan
d'auki masu aiki shikenan ki zauan kici wani abu sannan Kiyi zamanki kiyi mana
kwana biyu ya zaunar daita kusa dashi mami yana shagwabe mata kamar wani qaramin
yaro tace "aa banzo da niyyar kwana ba koma zan kwana ban zo da magungunan ba
"wannan ai mai sauki ne ai sai naje na dauko miki ."
Yadda ya kwantar da kai yau yasa zuciyar mami ta sauko ta sausauta masa daman kuma
tsakanin da d’a uwa d’an ma gilashi,ta sauke numfashi tace "karka damu zan dawo
nayi maku kwana biyu in sha allahu amman yanzu gida zani "No sweetheart babu inda
zaki kin ma dawo nan kenan ko kuma mu tattara kawai mu koma gidanki gabad'aya "dan
murmushi tayi kamar ba ita tagama daukar zafi ba "kai adamcy ba dai rigima ba
shikenan naji zan kwana dan tunda ka nace sai dai a sallama maka amman gobe goben
nan zan kama gabana maryam tayi murmushi har ta qasa boye farincikinta dan jin mami
zata kwana suka cigaba da hira mami ta jawo ledar gaban maryam ta bud'e mata "maza
só ma ci duk an ramar dake abanza ATA ya saci kallon mami da alamun akwai magana
abakinta “ aiko maryam kamar jira take ta soma cin abincinta hankali kwance tana
cewa "kai gsky mami kici ko kad’an ne abincin yayi dadi sosai " ATA yaja tsaki
"nonsense kawai kin iya cin na wasu kice yayi dadi amman idan cewa akayi Kiyi
bazaki iya kamarsa ba sai dai ki kashe mutane da .."ya isa ya isa !! dan allah
maryam tashi muje dakin ki kar a kashemu da gori suka mike suka soma qoqarin barin
parlour’n.”
D’akin qasa suka shige suka barshi zaune ."basu jima da barin parlour’n ba ya fita
ya bar gidan gabad’aya sosai maryam ta kasance cikin farinciki tare da mami basu
bar farincikin iyasu kadai ba sai da suka rabashi dasu aunty shahida yayinda jifa
jifa umma take kiran wayar maryam sai dai da zarar ta duba taga itace sai taki
dauka dan bata son mami ta fahimci wani abu sallah ne kawai yake tashinsu daga
hirar da suke . karfe bakwai ATA ya dawo har lokacin suna a d’akin ya shiga ya
ajiyewa mami qaramar jaka da wasu ledodi wanda ko baa fad’a nama rago ne aciki dan
tuni kamshinsa ya bayyana “ sweetheart ga magungunanki har da kayanki na hado miki
dashi da naman rago “lallai adamcy yau abun ya motsa bai ce komai ba yasa kai zai
fice daga d’akin tace “na gode allah yayi albarka .”yana zaune a falo yana kallon
labarai suka fito tare da maryam suka hau sama har kusan karfe shadaya saura suna
hira .”
cikin wani irin yanayi ATA ya shigo d'akin maryam wanda ranar ne karo na biyu
daya shiga dakin ya tsaya yana kallon mami wacce fuskata ke kwance da annurin
farinciki tamkar mai koyan magana ya bude bakinsa yana wa mami sallama
"Sweetheart ni zan shiga na kwanta sai da safe ya soma taku cikin isa da
kasaita don barin dakin, cikin sanyi murya mami ta kira sunanshi adamcy !d'an
tsayawa yayi tare da juyowa suna fuskarta juna da mami idanunta ta xuba mishi
kawai Tana kallonsa tare nazarinsa ganin yadda gabadaya yanayinsa ya sake sauyawa
cikin dan kankanin lokaci meke damunka naga yanayinka haka ?"babu komai
sweetheart "hakika mami tafi kowa sanin koshi waye ta fannin halayyarsa da
abinda ke tattare dashi bata rai mami tayi tare da ajiye wayar hannunta "meke
damunka ?dan qaramin tsaki yaja "kaina Ke dan min ciwo shiyasa nake son na kwanta
da wuri tunda taji haka bata sake cewa komai ba dai ina da sabo ta rigada tasa ba
da rashin son hayaniyarsa daman shi mutun ne ba mai san hayaniya ba ballanantana
gashi yau tasashi magana "allah ya tashemu lafiya ta fad'a adaidai lokacin daya
kusan fita daga dakin "kai tsaye bedroom dinsa ya wuce ,yasoma cire kayan jikinsa
yaja towel ya daura Tare da shigewa bathroom ya sakarwa jikinsa shower byn ya gama
wanka ya dauro alwala yana fitowa bai wani tsaya shafa mai ba ya bude wordrob dinsa
sai kamshi turaren ne ke tashi a gurin , ahankali yasa hannu ya zaro jallabiya
milk colour ya zira a jikinsa ba qaramin kyau ta maisa ba ya qarasa inda daddumar
salla take ya dauka ya shimfida shafi’I da wutiri ya gabatar sannan yayi addua ya
mike batare daya nade daddumar ba ya zare Jallabiyar jikinsa yayi fillinging daita
ya sanya vest da boxcer ya canza wutar dakin zuwa mara haske ya d’auki remut ya
qara karfin ac sannan ya fad'a Kan bed dinsa ya lullube jikinsa da bargo mai taushi
."
Bangaren mami kuwa har karfe shabiyu ta buga suna tare da maryam wacce bacci ya
soma daukarta kasa kasa ta soma kiran sunanta "maryam ki tashi kije dakin mijinki
mana kema fa na fahimci baki kulawa dashi kamar yadda nake zato maryam ta mike ta
zauna tana duban mami da fuskarta da d’an mamaki ,sosai mami ta shiga mata fada
tare da bata shawarar hanyoyin da zatabi gurin shawo kan mijinta cikin sauki ,
sosai jikin maryam yayi sanyi likis ita kanta tasan" inda mami bata kasance
yar,uwa,ce ga mahaifinta ba ,hakika bazata dinga damuwa akan damuwarta ba kullum
burinta ta gansu suna zaman lafiya tare da nusar daita yadda zata sake mallakarsa a
tafin hannuta cikin ruwan sanyi batare da biye biye ko wani abu ba, hakika mami
dabance acikin mutane km zuciyarta may kyau ce ba kmr irin ta mahaifiyarta ba km
gashi Allah yayi ta may tsananin zumunci ce mami takarasa zanceta " da maza tashi
ki sake shirya kanki kije ki kula da mijinki "km cire wannan tsoron nasa da nake
hangowa acikin kwayar idanuki da kyar maryam ta samu ta mike tana may dagawa
Mami kai alamun taji .”
Gaban mirrow dinta ta qarasa ta feshe ilahirin jikinta da turaruka masu sanyi
kamshi sanna ta dauki hijab ta daura a saman rigar baccin dake jikinta ta fito zuwa
dakinsa sai datayi addua sannna ta tura kofar dakin ta shiga ."acikin hasken da bai
gama haskaka dakin ba ta hangosa kwance cikin bargo ahankali ta dinga daga
kafafunta dan kar mostinta ya tayar dashi ta dan tsaya gabansa tana kallon kyakkwar
fuskarsa ahankali yake sauke numfashi inda tasan mami zata bukaci tazo dakinsa data
zuba masa magani acikin coffe ya sha ta samu natsuwar kwana tare dashi cikin
salama ta zare hijab dinta ta ajiye bayansa ta zagayo ta hau saman gadon ta dan
yaye bangon dake lullube dashi ta kwanta bayan ta cire hijab din jikinta bai motsa
ba hakan yasa tayi tunanin baccinsa yayi nisa ta sake matsosa tana shakar kamshi
jikinsa da kamshin turarensa. jikinta daya hadu danashi yaji kamar an ta’ba shi da
wuta yayinda ita kuma sauyin yanayi taji a ilahirin jikinta kusan awa daya da wani
abu suna kwance haka yadda bata runtsa ba haka shima bai runtsa ba .”
Zuciyarta ce ta bata kwarin gwiwar kai hannunta jikinsa ta soma shafasa tana aika
masa wasanni stil bai motsa ba kuma bai ji komai ba sai tarin bakinciki mamaki da
karfin halinta ya kamata shi Kmr ya tashi ya rufeta da duka amman ya kyaleta saboda
darajan sweetheart dake gidan ganin bai motsa ba yasa maryam tayo kasa da hannunta
daidai kasan marasa nan ne fa yaji bazai iya barin ta cigaba da iskancinta data
tsiro dashi ba a yau ,zaraf ya damke tsintsiyar hannunta tare da jijiyo ya zabura
ya mike zaune tamkar wani zaki mikewa tayi zaune Kmr yadda yake ,kallon da yake
mata yasa qirjinta dokawa da sauri sauri saboda kallon ne mai tattare da tsana da
gargadi ."a matuqar tsawace yace "uban wa yace ki shi go min daki ?kinga nayi kama
da wanda zaki ta'ba? Ko jikina saanki ne ?yayi mata tmbyr ajere nan da nan yasa
maryam ta gigice "tmbyarki naki "tayi shiru wallahi komai zaki min bazan ta'ba jin
komai ba saboda bana kallonki amatsayin mace kmar yadda nasha fad’a miki idan kika
sake gangancin kai hannunki jikina wallahi sai cakawa zuciyarki wuka .”kallonsa
tayi da bayananen tsoro “wannan ya zama karo na qarshe da zaki shigo min daki
domin har abada bazaki zamo abokiyar rayuwata ba jikina ma bazaki samu ba bare
zuciyata fuskarsa babu annuri ya nuna mata kofar fita oya get out from this room
kafin na miki mugun bugu cike da sanyi jiki ta rarumo hijab dinta ta soma qoqarin
jirawa ajikinta sai dai ta kasa fita daga dakin tana tunanin me zata koma tacewa
mami ganin taki fita ya sauko ya kamo hanuta bai tsaya wata wata ba ya soma janta
ya bud'e kofar tare da hankadata waje da sauri ta tokare hannunta da bango batayi
mamaki ba dan tasan zai iya aikata fiyye da haka ."
Makalewa tayi a bangon koridor hawaye masu dumi da ciwo suka zubo mata tasa bayan
hannunta ta goge shi kuwa rufo kofarsa yayi ya murda key a galabaice ya fad'a bed
dinsa ya runtse idanushi ya sake jan laulausar bargo ya lullube jikinsa maryam kuwa
natsuwarta take qoqarin daidaitawa amman ta kasa dan hawayenta ya gagara tsayawa
bata koma dakinta ba sai wajen karfe daya wanda a tunaninta zuwa wannna lokacin
mami tayi bacci sannan ta nufi dakinta tana danne sheshekar kukanta Koda tashiga
dakin mami na kwance , maryam ta haye saman gado ta kwanta lamo abayan mami
tare da kamkame jikinta wani irin kewa da son mijinta ce ke damunta amman shi
babu halittar daya tsana kamarta , kuka take son yi dan rage damuwarta amman bbu
dama domin damuwarta zata iya haifawar da mami damuwa , a dalilinta mami zata iya
muzgunawa yaya Adam , ita km abinda bazata so ba kenan, batason abinda zai sake
hassalashi akanta
ta kai hannunta ta dafe daidai satin zuciyarta dake mata ciwo bayan Kmr minti goma
mami ta tashi zaune ta dubeta tana mata kallon tsab batare da tayi magana ba
sannna ta sauko ta shiga bayi ta dauro alwala ta fara gabatar da nafilflii .”
" juyi tayi tare da sake kamkame jikinta “yanzu ita yaya zatayi da
rayuwarta ?”mayye zatayi ?”ga soyayyarsa ga tsananin sha,awarsa duk sun taru sun
hade mata ,take zuciyarta ta bata amsa da kima kama kanki da rashin hakurinki dan
muddin kikayi kuskure sake zuwa inda yake zai iya kasheki tunda har ya rantse “ya
allah ka taimakeni kasa na samu ciki a karon mu na biyu dashi yanzu ta shiryawa
kowani rigima zaiyi idan ciki ya bayyana ajikinta a boye take goge hawayen dake bin
kuncinta ,har mami tagama tayi laziminta da sauran addu'o,inta
.bacci bai yi nasarar daukar maryam ba kuka take qasa qasa . Tana jin motsin
mikewar mami ta shanye kukanta Tare da goge hawayen idanunta amman hakan bai hana
mami gane wani abu ba ,daidai inda fuskarta take tazo ta zauna tare da kamo
hannuta ,"me kike tunanin maryam ko kuma nace me ya dawo dake dakin nan har ya
hanaki bacci ?
Kafin maryam tace wani abu mami ta km jiho mata wata tmbyr “sai ma naga kmr kuka
kika yi ko?
Maryam ta Mike zaune suna fuskartan juna da mami ,yayinda hawayen dake makale a
idanunta suka yi nasarar zubowa...."mayye km abin kuka tmbyrki kawai nayi fa?
sai km ki kama min kuka.” wani abu adamcy yayi miki ?ahankali ta girgirwa mami
kanta “ki fad’a min idan wani abu yayi miki da kyar maryam ta iya bude
bakinta ..." ammi me yasa yaya Adam ya tsaneni haka ?kullum so nake naga na rayu
dashi har qarshen rayuwa amman shi kullum burinsa ya ruguza rayuwar gidan aurenmu
da ni kaina bansan yadda zanyi abubuwa su dawo min daidai tamkar kowasu maurata
".
“basan abinda na aikata masa ba da kullum yake son ganina cikin qaqa na
kanyi .Ida abubuwa da yake min suka cigaba da faruwa bana tunanin zuciyar dake
kirjina zata cigaba da bugawa , mami tambayar min shi laifin me nayi masa ?”wallahi
ni ina qaunar zama dashi muddin raina .”mami ta rungumeta ajikinta tana mai tausaya
mata "kukan ya isa haka babu abinda kika masa halinsa ne haka
halin bakar zuciya irin tasa yana damuna ni kaina na gaji da halinsa ,amman
matsawar Ina raye ba zaki taba kasancewa cikin bakinciki ba , bugu da qari har
yanzu kina da sauran damar rabuwa dashi dan bazan cigaba da baki hakuri ki cigaba
da zama dashi ba dan duk wani abinda zaa masa anyi masa idan dai ba rayuwarmu
yake nema ba .”
Mmn sudais
💗💗💗💗💗💗
MAR'ADAMS
💖💖💖💖
💗💗💗💗💗💗
*AYSHA A BAGUDO*
WATTPAD @HAUESH
AREWABOOKS USERNAME
AYSHAABAGUDO
bismillahirrahmanirrahim
Wannan littafin na kudi ne mai bukatar karantashi byn na kammalashi zai biya
1000 ta wannan account number din 1438775094 Aishat abdullahi access idan an tura
sai a turawa wannan 09136918331 alert domin tabbatar da an tura domin sauraron
littafaina a tuntubi chaneel dina (Hausa bakwai ) a YouTube.
Page 19
Sosai mami ta dinga rarrashin maryam tana masu addua “allah ya daidaita tsakaninku
,Allah ya saka tausayinki acikin zuciyar adamcy ,allah ya kawo zaman lafiya a
tsakaninku har qarshen rayuwarku “ahankali maryam Ke amsawa da “Ameen mami ,sai abu
na gaba maryam na fahimci kina sakaci da addua ,Ina son kinsan wani abu ba’a nasara
sai an rike Allah,idan ka rike Allah,Allah ta’ala zai taimakeka ki jajurce da
adduoi maryam “ki rage wasu abubuwa ki maida lamarinki zuwa ga Allah maryam ta
gyad’a mata kai alamun taji ,tana nan kwance ajikin mami har ta fara gyangyad’i
alamun bacci .ahankali mami ta d’an buga bayanta tana cewa “maryam kwanta kiyi
bacci da sannu allah zai kawo mana saukin wannan tashin hankali sannan ya kawo
fahimtar juna a tsakaninki da mijinki .“maryam ta tashi daga jikin mami tana shafa
idanunta sannan ta zame ta kwanta zuciyarta cike da soyayyar mijinta mami ta mike
itama ta samu gurin nan kusa da maryam ta kwanta sai dai ita sam bacci yaki
d’aukarta, kwakwaluwarta ne ya shiga cajin tunani
dan dole tasan abun yi tun kafin adamcy ya kashe maryam da bakincikinsa dan zuwa
yanzu hakurinta ya fara qarewa akanshi .”
Juyi kawai mami take akan katifa kafin ahankali ta taashi ta sauko daga saman
katifa ta tsaya gaban maryam tana kallon fuskarta bacci take, sai dai kana
kallonta zaka san a matuqar wahale take baccin dan kana kallon yadda take sauke
numfashi da ajiyar zuciya da karfi .”d’auke kwayar idanunta mami tayi ta fara
zagaye d’akin kafin ta fara zance zuci ita kad’ai “dan dole zulai kiyi wani abu
akan zaman ya’yanki “ to mai zanyi ?mai zanyi ? ta tambayi kanta har sau biyu tana
cure hannuwanta waje d’aya “Kiyi qoqari adamcy ya kusanci maryam ko Allah zai basu
rabo wata killa sanadiyyar hakan ya sauko ya sausauta mata ya rungume aurensu.
“tabbas haka zakiyi zuciyarta ta bata wannan shawarar “to ta yaya zan masa magana
ya fahimci abinda nake nufi ?”ta sake jefawa kwakwaluwarta tambaya shiru tayi
yayinda ta koma ta kwanta akan katifa tana sauke numfashi tana mai sake had’e
hannuwanta guri d’aya kafin ahankali ta soma sakin wani irin murmushi sakamakon
abinda zuciyarta ta shirya mata wanda zai kawo mata saukin al’amuran ta, alokaci
d’aya ta sauke wani naunayen ajiyar zuciya “dole dai kina bukatar shawarar shahida
kafin ki aikata komai .”
Washegari da misalin karfe tara na safe maryam tana zaune akan kujerar sofa tana
danna waya yayinda mami ke zaune akan salayya tana lazimi ATA ya shigo bakinsa
d’auke da sallama sallamarsa kawai maryam ta amsa batare da ta kallesa ba ta cigaba
da daddanna wayarta shima ko kallonta bai yi ba ya cigaba da tsayuwa mami ta d’an
kallesa yana sanye da jallabiya yayi mata kyau sosai sai dai bata jin dadin ganin
yadda ko yaushe fuskar nan tashi take a had’e’ ,sannan bata jin dadin ganin shi da
maryam haka zaman su sam babu sha’awa kana ganin yanayinsu kasan gabad’aya
zukatansu basa cikin walwala da jin dadi most especially adamcy wanda zaka fahimci
baya son ko bisa kuskure ya kasance a duk inda maryam take .yayinda ita kuma tafi
qaunar su kasance tare akoda yaushe ya rungumeta babu kyama ,mami na kallonsa ya
juya cikin takun isa ya fita daga d’akin ganin tana lazimi ,bayansa mrym tabi da
kallo har ya fice gabad’aya tasa hannu d’aya ta dafe goshinta tana jin wani
tuttukin bakinciki tana jin zafi da ciwon abinda yake mata na kyarma da rashin son
kallonta inda take ,amman ita ta rasa dalilin da yasa zuciyarta kullum take sake
macewa akanshi ,a kullum zata d’aura kwayar idanunta akanshi to wallahi son shi da
qaunarsa ne Ke sake huda zuciyarta da gangar jikinta” zata so ta mallakesa kamar
yadda mahaifiyarta take buri amman hakan taki samuwa kullum babu abinda take
hangowa attare dashi sai zallar qiyayyarta sam komai nata baya burgesa ita kuwa
kwarjininsa kesa bata iya d’aukarwa kanta mataki ,bata iya tunkurarsa da komai tana
matuqar jin tsoronsa aranta “da sanyi jiki mami ta qaraso inda take zaune ta kai
hannunta ta dafata, ta d’ago tana duban mami da idanunta dake cike da ruwan hawaye
mami tasa gefen hijab dinta ta goge mata hawayen da suka zubo mata batare da
saninta ba wani wahallen ajiyar zuciya ta sauke tana kawar da fuskarta gefe“
“maryam !”
Mami ta kira sunanta ahankali maryam ta waigo inda mami take ta sake zuba mata
idanunta tana kallonta fuskarta da tsananin damuwa ahankali ta sauke idanunta “ki
daina damun kanki akan adamcy idan ba haka ba zaki rasa lafiyarki idan hakan kuma
ta kasance babu ruwansa hasalima bazai ta’ba zama damuwarsa ba sai dai ta zama
damuwarmu “kiyi hakuri ki dinga kawar da damuwar nan aranki sannan ki dinga kaiwa
allah kukanki ,nasani maryam kina hakurin zama da adamcy ne saboda Kina matuqar
ganin girmana da mutuntani da kuma qaunar da Kike masa nima kuma haka ne acikin
zuciyata maryam ina qaunarki ina qaunar ku kasance a inuwa d’aya dashi .”numfashi
ta sauke da karfi tana kallon mami “eh shine ma dalilin da yasa bakya son na rabaku
maryam .
Maryam ta tsurawa mami idanunta “ko karya ne bakya sonsa ?zazzafan numfashi maryam
ta sauke ta kasa cewa komai dan tasan gsky mami ta fad’a “kina dai danne sonshi ne
saboda rashin qaunar da yake nuna miki amman ni naji ajikina kina qaunar
adamcy ,maryam taji dadin yadda mami ta fahimci hakan sai dai kuma zuciyarta tayi
rauni wasu sabbin hawaye suka zubo mata mami ta sake share mata “kuka bayayi miki
kyau maryam hakan ya sake karya wa maryam gwaiwa ta fashe da wani kuka
sosai .“wallahi mami ban san lokacin da son shi ya shigeni ba “nice silarsa maryam
kuma nayi danasani had’aku aure ,mami ta fad’a da matsanancin tausayinta ,duk
yadda mami take jin qaunar adamcy ji take tafita qaunarsa maryam ta tsananta kuka
tana tuna tun lokacin data fara jin qaunar yaya Adam din acikin ranta rungumeta
mami tayi tsam tana rarrashi alokacin wayar maryam ta soma ringing mami ta zare
jikinta tana kallon maryam itama d’agowa tayi ta kalli mami sannan ta kalli screen
din wayarta bata dauka ba ta cigaba da goge hawayenta yayinda kiran ya cigaba da
shigowa still maryam bata d’aga ba .”
mami ta d’an yi gyaran murya “wake kiranki ne tun d’azu ?ummah ce !ta bata amsa
atakaice idanunta na cigaba da zubar da hawaye “me yasa bazaki d’auka ba kika sani
ko kiran mai mahimanci ne ?shiru maryam tayi ta kasa cewa komai dan tasan kiran me
take mata, ita kuma ta gaji da abubuwan mahaifi yarta ,kullum abu d’aya kuma babu
wani biyan buqata “ki d’auki kiranta kar rashin d’aukar kiran yasa hankalinta ya
tashi tayi tunanin ko wani abu ne“.ahankali maryam ta gyad’a mata kai tana “cewa
mami bari naje na dafa miki ruwan zafi “to shikenan maryam amman ki hada min da
abinci “bamu da komai fa mami ,karki damu ki dafa min abinda kuke dashi . Mrym ta
mike tsaye ta fito tana qoqarin d’aukar kiran mahaifiyarta daya sake shigowa ta
sauko kunnenta manne da waya “umma dan allah ki daina kirana na tura miki sako
mami tana gidan nan bana son taji komai “ amman me yasa zaki fad’i haka ummah?”
kema Kinsan mami tana matuqar qaunata “a’a umma nifa gsky na gaji kawai abarshi na
hakura bazan iya ba dan duk abinda zaa zuba cikin abinci bazai ci ba tunda baya
cin girkina ,shiru maryam tayi tana jin yadda mahaifiyarta ta balbaleta da bala’i
ta inda take shiga bata nan take fita ba.”
“kiyi hakuri ummah ba wai bana ganin qoqarinki bane saboda mami idan ta fahimci
akwai abinda muke shiryawa d’anta zata ji babu dadi to shikenan gara ma wannan
zamu iya sake gwadawa ko za’a samu ya kwanta akai ,to shikenan amman dan allah
ummah karki kirani kiyi chart dina muyi komai ta chart ta qarasa mgnr tare da
shiga kitchen ta soma qoqarin d’aurawa mami abinda zatayi breakfast dashi cikin
kankani lokaci ta gama dafa ruwan zafi ta zuba cikin flaks sannan ta dafa shinkafa
da miya ta fito tana qoqarin qarasawa dining mami ta sauko tana cewa “sannu da aiki
maryam ?murmushi ta saki tana cewa “kai mami wani aiki kuma byn shinkafa da miya
ce kawai na dafa miki. murmushi mami tayi tana cewa “kawo min nan diyata ta qarasa
inda kujeru suke ta zauna maryam ta biyo bayanta ta ajiye kular abinci akan center
table maryam tace “nasan idan kowa yaci abincina yace babu dadi mamina bazatace
babu dadi ba ?”ina sam bazan fad’a haka ba zuba min na matsu banji dandanon
abincin my daughter ba “abincin dai mami sai dai kiyi hakuri babu komai aciki ta
qarasa mgnr muryata a sanyaye “karki damu maryam fara had’a min shayi cike da
kulawa maryam take hidima da mami yayinda mami ke nuna mata farincikinki a zahiri
amman a bad’ani bakinciki ne cunkushe acikin zuciyarta suna zaune ata ya fito yana
taku a natse akan step sanye da kananan kaya jikinsa sai fitar da sihirtaccen
kamshin turarensa yake ,ya qaraso parlour’n qasa hannuwansa duka zube cikin aljihun
wondonsa tun daga nesa ya hango mami zaune tana breakfast da ruwan tea zalla
babu wani abun hadi danginsu soyayyen Kwai da bread ko arish da sauransu abinda
yasan ba d’abiarta bace, abun yayi matuqar bashi mamaki dan haka kai tsaye store
ya shiga adaidai lokacin maryam ta mike ta nufi hanyar sama d’auko chazar
wayarta .”
yana shiga dube dube ya fara bai ga komai ba ya fito ya shig kitchen duk sai daya
duba cabinet din kitchen din nan ma bai ga wani abun kirki da zaa had’awa mutun
breakfast mai kyau dashi ba dan haka jiki a sanyaye ya fito yana kwallawa maryam
kira yayinda mami tana nan zaune tana kallon tv tana cigaba da kora ruwan tea da
sauri maryam ta sauko tana dubansa gabanta na wani irin bugawa da karfi muryarta a
raunane tace “ yaya gani ?“meye haka ?me ya faru kuma ?itama tayi karfin halin
tambayarsa har ya d’aga hannunsa ko me ya tuna ya sauke ya dafe goshinsa a fusace
ya cire hannunsa ya d’an saci kallon mami ita kuma ta zuba masa idanu tana ji da
ganin abinda zai faru maryam taja baya tana jin yadda zuciyarta ke rawa “meye
wancan agaban mami ?ya sake wulla mata tmbya tayi shiru tana dubansa a tsorace ya
zira hannunsa daya cikin aljihunsa yana sake yin magana a tsawace “meye haka ina
magana kina jina ?abinci ne !”what ?!ya furta a tsawace .”
ta sake ja baya kar ya wanka mata mari dan a yanayin da yake kallonta babu sausauci
“amman zaki iya bawa mahaifiyarki irin wannan breakfast din ? gabanta yayi wani
irin mugun fad’uwa ya tsura mata ido hakan ya bala’i bata tsoro gbdy ya sake canza
mata ya fara taku zuwa inda take tsaye tana yar kyarma tana baya baya yana biyota
har sai data kurewa bango “wallahi ba da gangan nayi ba babu komai a store ne komai
ya qare iya abinda muke dashi na bawa mami .” afusace ya d’aga hannu zai wanka mata
mari cikin wani irin masifaffen tsawa yaji sautin muryar mami “wallahi idan ka
ta’bata ban yafe maka ba .” cak ya tsaida hannunsa tamkar an dasashi zuciyarsa na
tafasa cike da zafin zuciya ya sauke hannusa yana furzar da iska mai zafi daga
bakinsa sannan ya juyo ya soma taku cike da ‘bacin rai ya qaraso ya zauna kusa
daita kamar mai neman gafara ya fara kame kame “umm umm ummm nace ba “kace
me ?”shiru yayi yana kallon mami yayinda maryam tayi sauri ta haye sama tana wai
wayensu “ina jinka adamcy ?”Kiyi hakuri sweetheart banji dadin yadda naga kina
breakfast haka ba “ bana zama a gida bansan babu komai a gidan nan ba sannan wannan
yarinyar bata fad’a min babu komai ba ya qarashe maganar kamar zai yi kuka.”
mami ta kallesa sosai ta gano halin damuwar daya shiga adalilin breakfast dinta,
daman kuma tayi hakan ne dan ya gani numfashi ya sauke yana sosa keyarsa yana
cigaba da kallon mami ahankali mami ta tabe baki “to ka bata damar da zata
fuskanceka bare ta fad’a maka babu komai acikin gidan nan “?amman !”sai kuma yayi
shiru yana runtse idanunshi .”amman me adamcy ?kai kanka kasan baka da wata kalmar
da zaka fad’a min na yarda a matsayinka na magidanci baka bawa matarka wannan damar
ba sam matarka bata da cikakken iko acikin gidan nan yadda kake nuna baka qaunar
jamaa da yanuwanka haka kake nunawa matar aurenka ,kai kanka kawai kasani baka damu
da damuwar kowa ba dan haka karka rainawa kanka hankali ka nemi daurawa yar mutane
laifi “ta qarashe maganar cikin fad’a saboda halin adamcy baqaramin damunta yake ba
,shi mutun ne wanda babu ruwansa da damuwar jama’a sai dai kanshi da aikinsa ya
kamo hannun mami ya soma rarrashinta “sweetheart Kiyi hakuri kema Kinsan yanayin
aiki ne sai ahankali ,ni kaina bana samun time din kaina kamar yadda kika sani
amman at least data fad’a min zan sa a kawo komai “ta bishi da wani mummunar kallo
“wai yaushe ka bawa maryam wannan damar yarinyar nan haka take rayuwa cikin qunci
acikin gidan nan ga rashin so ga yunwa dame zataji ?”allah sarki maryam baiwar
allah allah dai ya qara miki hakuri amman na cuceki na hadaki da damuwa ,na hadaki
da mutun mara kirki ,na hadaki da mutun mara zumunci wanda ko yan’uwansa baya so
bare wata aba maryam wallahi adamcy baka da tausayi da amana nayi danasanin hada
auren nan allah dai ya gyara maka wannan bakar zuciyar taka .”
Kuka yaci karfin mami .”
jikin ATA yayi mugun sanyi babu abinda ya tsana kamar hawayen mahaifiyarsa da bai
da kamarta jin kukanta yake har cikin zuciyarsa ya sake matsowa kusa daita yasa
kanshi akan cinyarta yana jin yadda zuciyarsa yake tafasa yana jin kukanta yana
ganin laifinsa amman yafi ganin laifinta domin kuwa itace sanadin da yasa ya kasa
sauke nauyin da allah ya daura masa sannan ya kasa mata biyayya ta matsawa
rayuwarsa dayawa akan maryam ,shi kanshi baya jin dadin abubuwan dake faruwa ,jin
kukanta yake aransa yana jin kamar yayi kuka .“
ahankali yayi amfani da karfin zuciya irin tashi ya fara bata hakuri da rarrashinta
“sweetheart Kiyi hakuri nasan bana miki yadda kike so Kiyi min addua wallahi a
shirye nake da na canza in zama mai faranta miki ,kuma wallahi ina son yan’uwana
sweetheart wani dadi ne ya ziyarci zuciyar mami dan abinda tafi bukata kenan ta
dade tana adduar ya canja .”
ya qara gyara kanshi akan cinyar sweetheart dinsa “sweetheart ki yafe min ko zan
samu sausaucin abinda nake ji araina kada zuciyata ta buga sweetheart ,damuwa tayi
min yawa wallahi ni kadai nasan halin da zuciyata take ciki a haka kamar lafiyayyen
mutun ne amman sam ba haka bane mutun ne mai dauke da mummunar ciwo a qirjinsa da
zaki barni haka babu nauyin kowa akaina zanfi ji dadin rayuwata sai dai zuciyata
taji da damuwa daya amman yanzu damuwa tayi min yawa na rasa ya zanyi da rayuwata
wallahi zan gwamaci mutuwa sweetheart akan rayuwar da nake .”mami tayi saurin saka
hannu ta rufe masa bakinsa bata son taji batun zai mutu idan ya mutu tayi yaya ai
ita babban burinta ta mutu ta barshi a duniya, tana shafa kanshi tana jin sonshi
har acikin bargon zuciyarta “ki yafe min sweetheart “adamcy baka min laifin komai
ba ban ta’ba rikeka araina ba kullum addau nake maka d’ana sai dai abu daya nake só
kamo. ina son ka sausautawa maryam ka zauan da mace mafi cancanta ,maryam ta
cancanta kowani nmj idan ya sameta zaka ji dadin rayuwa daita mace ta gari ya dago
kanshi yana kallonta ya saka hannu shi ya rike kunnuwansa bazan iya ba sweetheart
“but I promise you in sha allahu zan kawo miki matar da zan aura in sha allahu
zan faranta miki zakiyi farinciki da zabina amman batun wannan yarinyar fa gsky
sweetheart sai dai kiyi hakuri .he ending the talk with a smile .”
mami tayi shiru tana dubansa sam adamcy baya ganin girmanta baya tausaya mata duk
son da yake ikirarin yana mata abaki ne bai kai har zuciyarsa ba .”shiru kawai
tayi tana jin babu dadi ko kadan acikin ranta tana son zubar da hawaye amman data
tuna irin matsifar da hakan zai jefa rayuwarsa da alamuransa sai ta fasa sai dai
yadda zuciyarta take tukuki ta tabbatarwa kanta tana cikin tsannain damuwa akanshi,
idan batayi gaugauwan kawar da hakan aranta ba shima wani bala’i ne ga rayuwarsa
runtse ido tayi zuciyarta na shirya mata yadda zata kawo qarshen komai “Sweetheart
me kike tunani haka ?”muryar ATA ne ta katse mata tunani , harara ta maka masa tana
cewa “ina ruwanka da abinda nake tunani ?wayarsa ya ciro ya kira daya daga cikin
yaransa ya bashi umarnin a shigo da komai na kayan abinci enough .”
Cikin kankanin lokaci aka dinga shigo da kayan abinci sai daaka cika store tab da
kayan abinci babu abinda babu na amafani haka ma fridge tun a ranar komai ya
sauyawa maryam sunci mai kyau ita da mami su sha mai kyua, sai abinda suka ga dama
suka girka kuma basuyi wa ATA tayi ba shima bai damu ba tsabgogin gabansa kawai
yake yi sai da yamma ne ya dan saci kallon mami yace “sweetheart ko zan samu irin
coffee da kike min ?zaka samu mana amman a wajen matarka ba “tun da yaji ta fadi
haka bai sake cewa um ba bare um um, ya cigaba da danna wayarsa maryam najin haka
ta matso kusa da mami tace “mami dan allah Kiyi masa mana “wani kallo mami tayi
mata na rashin zuciya irin nata ,mutun bai damu da kai ba amman kai kabi ka damu
kanka akanshi “please mami ai kema kin iya kije kiyi masa ta rage murya sosai tace
“idan nayi bazai sha ba amman muje muyi masa tare zai sha mami ta tsura mata ido
kawai tana kallonta cike da tausayawa tare suka shiga kitchen din sukayi sai dai
koda ta fito parlour bata gansa ba a d’akinsa ta sameshi zaune akan kujera yana
amsa kira taja qaramin table din glass din dake tsakar dakin ta dora tray din akai
ta tsiyaya masa acikin a cup tace “gashi !”ba tare daya kalleta ba ya dauka ya fara
sha dan a bukace yake .”
ta juya ta bar dakin tana rufo masa kofa kwanan mami uku a gidan wanda hakan ya
haifar da sukuni da kwanciyar hankali ga maryam har mamakin kanta tayi yadda
yanayin jikinta ya canza, domin mami nayi mata duk wani abinda zai kwantar mata da
hankali tare da kawar mata da damuwarta da zarar taganta cikin damuwa sai tayi duk
abinda zata kawar da damuwar sannan hankalinta zai kwanta sosai take kula da cin
abincinta mussaman ta dinga had’a mata fruit masu gyara skin da qara ni’ima ajiki
most especially yankakkiyar ayaba da soyayyiyar gyada da kankana da madarar ruwa
a had’a waje daya wannan kam kullum sai mami ta had’a mata ta bata ,wannan had’in
mai dadi yana aiki abu biyu ne ajikin nmj ko mace yana gyara skin sannan yana
qara ni’ima ajikin mutun. zaman mami a gidan ya dan kawo sauyi domin duk abinda ATA
zai yi na rashin mutunci tana taka masa burki da fushinta domin dai idan ba
fushinta ya gani ba baya kin abinda yayi niyya kuma yanzu babu laifi yana cin
abincin gidan .”
Da misalin karfe shida na yammacin ranar da mami ta cike kwana biyar a gidan
ATA ya tashi da rashin lafiya na ciwon kai mai tsanani wanda har sai da doctor
dinsa yazo ya dubasa inda yayi wa doctor bayanin yadda yake jin ciwon Kan kuma koya
sha magani baya masa sauki yadda yake buqata, doctor yayi gwaje gwaje ,a inda yace
akwai kwayoyoyin da yake sha wanda sune suke haddasa masa wannan ciwon, dan shiru
yayi yana tunani dan shi a sanin da yayi wa kanshi baya shan wata kwaya dama sigari
yace itama yanzu ba koda yaushe yake shanta ba amman kwaya kam baya sha “doctor
bana shan kowani irin kwaya amman ko zaa iya duba wace irin kwaya ce ?”eh zaa iya
dubawa kuma zaa gano kowani iri ne amman dole sai kaajiye ayyukanka na gobe kazo
hospital .” ATA ya gyda kai alamun zai zo .”
tun zuwan doctor maryam ta fahimci bashi da lafiya ne dan duk sanda kagansa to
rashin lafiya ne bayan doctor ya gama duba ATA maryam ta shigo dakinsa hannunta
dauke da tray ta sameshi zaune akan doguwar kujera yana sanye da singlet da gajeran
wando kallo d’aya tayi masa ta dauke idanunta sakamakon yanayin data tsinci kanta
d’an kwantaccen sumar jikinsa kawai ya isa tadawa mutun shaawarsa ,taja dan karamin
table din glass din dake tsakar dakin ta dora cooler din abinci a kai ta zuba mishi
a cikin plet tasa spoon tace “ga abinci shiru bai ce uffan ba ta sauke numfashi ta
sake bud’e bakinta akawo maka coffe ?ya girgiza mata kai kawai alamun baya
bukata wani sanyayyen numfashi ta sauke a boye a raina tace “alhamdulillah yau
dai da alamun mutane kirki ne a kusa babu rashin mutunci,kamar baka jin dadi ?sannu
allah ya baka lafiya meke damunka “?ba tare da ya kalleta yace “ki kama kanki dan
naga kina wani jin dadi dan kinga sweetheart atare damu kisani ba tabbata zatayi a
gidan nan ba zata wuce idan ta wuce kuma kema Kinsan me zai faru ?tace babu abinda
zai faru sai alkhairi allah dai ya baka lafiya baby nah tana rufe bakinta daya daga
cikin wayoyinsa ta soma ringin zuciyarsa cike da mamakinta karo na biyu kenan da ta
kirasa da wannan banzar sunan kamar ya tashi ya gaugaura mata mari amman jikinsa
babu kwari shine ma yasa ya qasa tashi kuma yana jin yadda zai ce tabashi wayar
maryam ta fahimci haka, dan haka cike da sanyi jiki ta qarasa inda wayar take
akan katifarshi ta dauko ta duba fuskar wayar nan take gabana yayi wani mummunan
faduwa sakamakon ganin hoton wata kyakkwar yarinya a fuskar wayar mijinta .”
yarinyar kyakkyawa ce duk da fuskarta kamar zane ce aranta tace”ko dai wannna ce
yarinyar mafarkin sa?kwakwaluwarta bata kai ga bata amsa ba “tajiyo sautin
muryarsa can qasan makoshi yace “bani wayata “jiki a matuqar sanyaye ta kai mishi
sañan tace bari na wanke maka toilet shi dai bai ce mata uffan ba har ta shiga ta
wanke ta fito yana cin abinci yace “bani abinsha a fridge da sauri ta bude demsino
na gwangwani ta dauko masa ta hado masa da ruwa nestle ta ajiye tana jin zuciyarta
babu dadi duk da yarinyar mafarki ce amman abun ya damu zuciyarta zata cigaba
tsayuwa ad’akin yace “please leave! simi simi ta fito daga d’akinsa yaja tsaki
tare da cewa nonsense mace sam babu class ,to wani aji zatayi wannan ?allah na tuba
ai isasun mata né masu aji shi yaji ajikinsa muddin zai had’u da princesa dinsa
tabbas zata fita dabam acikin mata ranar da wuri ya kwanta bacci sakamakon maganin
bacci da alluran da doctor yayi masa .”waahegari kuwa karfe biyu a office din
doctor tayi masa duk wani gwaje gwaje anyi masa, inda doctor yace zai zo gida ya
kawo masa abinda suka gani daga nan kai tsaye gidan mb yace a wuce dashi sun jima
tare,bashi ya dawo gidan ba sai bayan ishai.”
Da misalin karfe goma sha daya na dare maryam ta fito daga dakinta sanye da kayan
bacci iya cinyarta sai dai ta daura zani a saman kayan baccin kai tsaye d’akinsa
ta shiga bata gansa ba dan haka ta sauko qasa cikin tsananin tashin hankali har
zanin jikinta ya fita bata sani ba “yaya Adam kazo mami bata iya numfashi
sosai ,ai da wani irin mugun sauri ya zabura ya mike yayi wulli da remut din
hannunsa bai san yaakayi ba sai ganinsa a dakin maryam yayi har tsakiyar gadonta ya
daga kan mami ya daura bisa kafafunsa yana qoqarin tallabota ya sauko daita ta
girgiza masa kai “dan girman allah sweetheart wallahi baki san yadda naji a
zuciyata ba “ke tsayuwar me kikayi kije ki dauko min wayata” yayi mgnr a tsawa ce
yayinda maryam ta juya da sauri ta fita “haba adamcy ka dinga sausautawa maryam
mana .tayi maganar da kyar”
furzar da iska yayi yana kamo hannun mami cikin nashi “adamcy nah! mami ta kira
sunansa”na’am sweetheart sannu gobe gobe nan zan bar kasar nan dake “duk inda zaka
kai ni bazai hanani mutuwa ba ,dan haka ma gara ka barni kawai a kasata idan
mutuwar ce allah ya bamu ikon cikawa da imani ta qarasa maganar da kyar tana sauke
numfashi “kinji abinda naji kuwa sweetheart da kikayi zance mutuwa nan dan girman
allah ki daina fad’a min haka “to adamcy mutuwa ai dole ce maryam ta shigo ta mika
masa waya ta hawo har saman gadon ta riko hannun mami cikin nata suka sakata a
tsakiyarsu mrym tana mata sannu yayinda ATA Ke qoqarin kiran layin Aunty shahida
“karka kira shida ka daga mata hankali sannan kiranta bazai hanani mutuwa ba idan
mutuwar ce.” saurin runtse idanunshi yayi .”
Bai kula maganar mami ba ya cigaba da kiran layin shahida sai dai kiran na shiga
bata d’auka daga adamcy har maryam duk suka zubawa mami ido hankalinsu a matukar
tashe “maryam adamcy ku yafe min had’aku aure da nayi “haba mami dan allah kiyi
shiru numfashi ki har yanzu bai daidaita ba kuma aurenmu da kika hada baki mana
laifin komai ba inji cewar mrym “idan Ke ban miki laifi ba ai nayiwa adamcy “ki
kwantar da hankalinki mami shima baki masa laifi ba muddin muna raye zai faranta
miki har ma bayan ranki “shi kam ATA gabad’aya ya nemi natsuwar ya rasa dan har
layukan mijin aunty shahida ya kira bai zuwa haka ma layin likitan dake dubasa yana
qoqarin durowa daga kan gadon mami ta riko hannunsa ya dawo ya zauna cikin tsananin
tashin hankali “dan allah sweetheart karki bari sanadiyar careless dinki na
rasaki,wallahi bazan iya daukar zafin jarabawar nan ba “yayi mgnr kamar zai yi kuka
“ haka rayuwa ta gada adamcy kuma ita rayuwa cike take da qaddarori da jarabawa
iri iri sai dai idan baka cikin duniyar nan, yau dadi ne gobe kuka dukkanin rayuwa
rubutattacen lamari ne daga rabbi da d’an adam yana gane wannan da bazai tsaya
batawa kansa lokaci ba kamar yadda ka kasa ganewa “tana gama fadar haka idanunta
suka juye numfashinta ya soma qoqarin tsayawa .”
“sweetheart sweetheart!! Kawa yake iya kira yayinda maryam ma ta dinga kuka tana
kiran sunanta atare suka nemi durowa daga kan gadon suka jiyo sautin muryarta can
kasa “maryam bani ruwa kishi nake ji .” ya dawo da sauri yana cewa “shikenan
sweetheart mutuwa zakiyi ki barni ,dan allah karki min haka sweetheart, dan girman
allah karki min haka ya allah ka d’auki rayuwata ka bar ta mahaifiya ta” ya fad’a
yana damke hannunta cikin nashi gam wasu hawaye masu zabi suka gangaro masa “adamcy
Nah kuka kake yi ?ya sauke numfashi yana kai hannunta bakinsa inda hawayensa ke
diga “kayi hakuri haka rayuwa ta gada ,kana cikin jin dadi sai allah ya jeho
jarabawa cikin rayuwarka “ka rike yanuwanka adamcy saboda kai ne kamar babba
agaresu ,ka kyautata masu ,ka tsaya masu a dukkanin lamarinsa “dan allah sweetheart
ki daina fad’ar haka “dole fa zan mutu adamcy fatana allah yasa mu cika da kyau da
imani .”
Tayi shiru can ta motsa bakinta “ka min wani alfarma adamcy ya d’ago ya tsura mata
ido yana sake damke hannunta cikin nashi “me kike so sweetheart just tell me
matsawar zakiyi farinciki ki dawo daidai “ka ta’ba kusantar maryam ne amatsayinta
na matarka ?shiru yayi yana duban mami zuciyarsa na bugawa da karfi ganin haka
yasa mami ta soma tari wanda da kyar tarin yake fita “sweetheart sannu ya furta
yana kwallawa maryam kira” ki kawo ruwan mana ko dan ba uwarki bace kike westing
time “cikin yanayi na ciwo mami ta cigaba da magana “na tambayeka baka bani amsa ba
“a’a sweetheart babu abinda ya ta’ba shiga tsakaninmu “yanzu ka kyauta kenan adamcy
?wata shida kenan da aurenku amman ka kasa sauke wannan nauyin kana ganin allah zai
barka haka né ?shiru yayi yana daura hannunsa a goshin mami “me maryam ta tsare
maka adamcy ?ta fad’a tana wani irin numfashi mai zafi idan laifi ko haushi ne
nawa zaka ji domin nice silar komai .”
“Kiyi hakuri sweetheart ya fad’a adaidai lokacin da maryam ta shigo hannunta rike
da roban ruwa ya fixge da karfi “idan mutuwa ne tuni ta mutu kawai kije ki kawo
ruwa kinje kinyi zamanki saboda ba mahaifiyarki bace cike da rawar jiki ya bude
murfin roban yana mai tallabo kan mami ya kai goran ruwan bakinta ta sha sosai
sannan ta kawar da bakinta tana cewa maryam koma d’akin adamcy zai zo ya sameki
kinji allah yayi miki albarka, jiki a sanyaye ta juya ta bar dakin sai dai ta qasa
shiga dakinsa ta tsaya corriedor ta jingina bayanta da bango tana zubar da
hawaye.”yanzu idan mami ta mutu ya zan yi da rayuwarta “?tayiwa kanta tmbyr tana
fashewa da kuka .”
“Kayi min wannan alfarmar adamcy baka sani ba ko iya alfarmar da zan nema kenan
daga gareka ya matso da kunnensa daidai bakinta dan yaji alfamar da take so
“sweetheart ki fad’a min abinda kike bukata in promise you zanyi “ina son ka
fad’a min gsky kana da cikakkiyar lafiya kuwa kamar yadda sauran maza suke ?
numfashi ya fesar yana mai dagowa ya tsura mata ido “yau ba ranar wasa bace bare ya
kawo rainin hankalin da ya saba ,dan hk da sauri yace “lafiyata kalau
sweetheart ,amman wannan tamvayar ba yau bane karo na farko da kika min ,idan bani
da lafiya kece mutun ta farko da zan fadawa “to na yarda tunda kai ma ka tabbatar
da lafiyarka kalau ina son kaje ka sauke nauyin da allah ya rataya akanka na aure
da maryam “lumshe idanunshi yayi kana ya bud’e ahankali yana dubanta ko kifta idanu
bayayi ko bata fito fili ba ya fahimceta sosai “idan kayi min haka ko na mutu
ruhina zai samu salama adamcy ,lalla a illalla muhammadu rasulillahi sallahu alaihi
salam,dan allah adamcy ka cika min wannan burin , kayi min wannan alfarma kuma a
yanzu ta damke hannunsa gam cikin nashi jikinta na rawa kamar yadda jikinsa yake
rawa yana furta inna lillahi wa inna ilaihi rajiun ita kuma mami tana salati tana
furta ya cika mata burinta .”
Gabad’aya ATA ya gigice ya fita haiyacinsa ganin halin da mahaifiyarsa take ciki ya
juya da sauri ya fita daga cikin dakin a corriedoor yaga maryam tsaye ta daura
hannuwanta duka a saman kanta tana rusa kuka ya tsura mata ido cikin tsnanin
tashin hankali bashi da wani lokacin ‘batawa gara yayi abinda zai yi ya faranta ran
mahaifiyarsa ko bayan ta mutu din ruhinta zai samu salama kamar yadda ta fad’a masa
hannuta ya riko da karfi yajata zuwa d’akinsa nan fa gabanta ya shiga faduwa suna
shiga dakin ya nuna mata Kan bed dinsa ,gabanta yayi wani irin mummunar faduwa ta
tsura masa ido tana kallonsa cike da matsanancin mamaki yayinda idanunshi sukai
balain canzawa suka koma ja ,ta taki hawa Kan gadon kamar yadda ya umarceta dan
batasan me hakan yake nufi ba ya kalleta da fuskasa dake murtuk “ke bakiji abinda
nace bane ?me kace yaya wallahi banji kayi magana ba,” ki hau gado .”
still maryam taki hawa sai ma qoqarin fita daga dakin take aiko cikin zafin nama
ya fixgota da karfi ya maka ta akan gado da karfi ta zabura zata tashi ya buga
mata wata muguwar tsawa ganin tana son ‘bata masa lokaci “Ke ki tsaya nayi abinda
aka sani idan kuma kika nemi ‘bata min rai har Mahaifiyata ta mutu ban mata wannan
alfarma ba zakiyi nadama har qarshen rayuwarki “ jin haka yasa maryam sauke wani
wahallen numfashi tana mai jin sanyi aranta amman a zahiri fuskarta da jikinta babu
komai sai tashin hankali.” ya kai hannu ya kashe wutar d’akin dan bazai iya kallon
fuskarta ba ,ya hau saman gadon batare daya cire kayan jikinsa ba yayi mata runfa
da fad’a den qirjinsa wani sanyi dadi ya mamaye zuciyar maryam hakika mami ta
taimaki rayuwarta ,allah dai yaja da kwana mami domin duk ranar daakace babu ita a
rayuwarsu akwai babban tashin hankali.”
wata irin matsa yayi mata kafin ya shigarta tayi shiru kwalla na gangarowa akan
kuncinta dan bai tura dan sakon a tsakaninsu ba kamar yadda sharia muslinci yace
hakan yasa taji zafi sosai taji gara ma ace baya cikin haiyacinsa ne ya kusanceta
bangaren ATA kam bakinciki ne cunkushe acikin zuciyarsa jin kofarta a bude ,a
ranshi yaja tsaki cike da bakinciki ya cigaba da abinda yake sai dai baya jin dadin
komai ganin kawai zai yita batawa kanshi lokaci ne ya kawo tunanin princess aransa
yadda yake zuwan masa a mafarki da yadda yake sarrafashi nan da nan yaji wani abu
ya tsarga masa da tunanin princess ya samu yayi abinda zai yi ,ya mike ya kunna
wutan dakin ya tsura mata ido cike da bakinciki baasi yake son ji amman ya kasa
sarrafa harshensa illa tsaki yaja , ita kuwa maryam da sauri ta sauka daga Kan
gadon ta fito ta nufi d’akinta inda mami take kwance tana numfarfashi .”
Bayan fitarta shima ya fito kai tsaye dakin maryam ya shiga inda ya iske mami
kwanace tana fidda numfashi sam sama “sannu sweetheart ya kike jin jikinki
“alhamdulillah ta fad’a tana yafitosa da hannunta ya matso sosai kusa daita “kayi
abinda nasaka adamcy ?”nayi mami ! yauwa dan albarka allah yayi maka albarka ka
gama cika min burina ko yanzu na mutu burina ya cika adamcy “kiyi shiru mami ki
samu natsuwa barin naje nazo da shahida “to adamcy amman daka bari zuwa gobe da
safi “girgiza mata kanshi yayi ya fice da sauri ya shiga dakinsa ya sanya jallabiya
ya dauki wayarsa ya fito da sauri yana duba agogon wayarsa karfe daya saura .” masu
tsaronsa ya kira tun kafin ya qarasa fitowa haraban gida har sun juya Kan
motacici guda biyu gaban motar ya shiga suka bar gidan ya gyara zamansa sosai ya
rungume hannuwansa duka a kirjinsa yana tunanin halin da zai shiga idan ya rasa
mami .”
“duk iskancinsa yana matuqar shiga tashin hankali idan ya tuna zata mutu ta barshi
kuma duk baccin da yake da zarra ya tuna zata mutu sai baccin ya dauke masa bazai
manta ba lokacin yana da shekara ashirin da takwas duniya cikin baccinsa wai aka
fad’a masa sweetheart dinsa ta rasu da mugun sauri ya farka ya shiga dakinta tana
kwance abunta tana bacci ya Kai hannunsa daidai hancinta nan yaji tana numfashi
wani naunayen ajiyar zuciya ya sauke gudu motar yake amman sam ATA gani yake kamar
motar ba gudu take ba dan gabdaya ya rasa natsuwarsa daga jajayen idanunshi yayi ya
sauke akan wayarsa daya har da wasu mintuna tsaki yayi yana jin zuciyarsa kamar
zata buga sam baya ganin gudun motocin nasu yaji kamar ya karbi tukin watakila
nashi zai fi nasu, tsaki yaketa yi yana qarawa kamar bazasu kai ba haka yake gani
duk jikinsa tsuma yake kwakwa luwarsa ta hargitse kamar wanda sabon hauka ya kama a
haka suka qaraso bakin get din gidan Aunty shahida tun baa gama daidaita tsayuwar
mota ba ya fito da sauri ya shiga buga get din gidan da iyakacin karfinsa domin
kana ganinsa zaka fahimci hankalinsa a matukar tashe yake tunda yayi bugun farko
kowa dake cikin gidan ya farka a matukar tsorace ,mai gadi ma yayi takansa sai
dayaji ya ambaci sunan aunty shahida sannan ya fito ya bude qaramin hujin get din
nan take ya ganensa duk da cikin duhu ne .”
ya bude masa get da sauri ya shiga haraban gidan yana kwalla mata kira” shahida
shahida !!”wani irin bacci ne haka?” meye amfanin wayoyinsku da karfi ya dinga
buga kofar shiga falo masu aiki suka bude masa yaranta da masu aiki ya gani tsaye
cirko cirko ya shiga yana cewa “ina shahida taje ?””mumy na sama inji cewar
hamdiya second born din aunty shahida ,zuciyarsa duk a jagule ya diga kiran sunanta
sai gata ta sauko da sauri “lafiya Adam ?lafiya zaki gani by this time ?” shima ya
wulla mata tmby yana mata wani kallo “dan allah meye amfani wayarki data
mijinki ?”zatai magana yace yanzu dai dauko kayan aikinki ran sweetheart a hannun
Allah zan iya rasata akowani lokaci “ka kwantar da hankalinka zuwa da safe zan zo “
what “?ya fad’a yana mata wani irin mugun kallo sannna yace “dan allah idan wasa
mike ki dawo hankalinki ki dauko kayan aiki muje ya riko hannunta .”
“bari na dauko kayan aikina “okay Kiyi sauri please cikin kankani lokaci ta daura
hijab akan kayan baccinta ta sauko tare da mijinta yana rike da kayan aikinta yana
ma ATA magana “a she mami ce babu lafiya “tsaki ATA yaja Tare kwace qaramin
alkwartin kayan aikin aunty shahida dake hannunsa ya ja hannunta suka fice yana
cewa “idan kukayi aure shikenan damuwar iyayenku ma bakwa damuwa daita sai ta
mazajenku “karka sake ka fad’a min magana “an fad’a miki idan ma akwai abinda yafi
haka zan fad’a miki ,nazo miki da matsala sai wani jan jiki kike yi kamar ba
mahaifiyarki nace ranta a hannun allah yake ba har da wani jerawa da miji nonsense
kawai “kai ne nonsense ai gara ne tun daga farko rayuwata har zuwa yanzu akan
mata biyayya nake kai fa a matsayinka na nmj wanda hakinsa ne yayi biyayya ko dole
ne ,kuma hatta aljannarka tana qarqashin tafin kafarta amman ka fad’a min meye kake
wa mami na farantawa bare yanzu ka d’aga hankalinka akan rashin lafiyarta ?wallahi
ko yanzu mami ta rasu alhamdulillah mun gama daita lafiya kai fa ?
“Wallahi sai kafi kowa shiga damuwa da tashin hankali “gori zaki min?” ya
tambayeta cikin tsananin damuwa “eh anyi maka idan kayi zuciya ka canza rayuwa
kayiwa mahaifiyarka biyayya ,kaso duk wani abinda take so “tana gama fad’ar hk ta
shige bayan mota, shima kuma ya shiga gaban mota ya zauna maganarta na ci masa
rai “abun har ya kai ayi masa gori ?uwarsu daya ubansu daya ma tayi masa gori inaga
mutanen waje ?”allah ne kadai yasan abinda jama’a suke fad’a akansa” ya salam ya
furta yana dafe goshinsa ahaka suka kawo gidan da sauri ya fito yana bud’e mata
mota kallo d’aya zaka masa ka fahimci yana cikin damuwa da tashin hankali hannunta
ya riko cikin nashi suka nufi kofar shiga parlour’n gidan .”
Mmn sudais
💗💗💗💗💗💗
MAR'ADAMS
💖💖💖💖
💗💗💗💗💗💗
*AYSHA A BAGUDO*
WATTPAD @HAUESH
AREWABOOKS USERNAME
AYSHAABAGUDO
bismillahirrahmanirrahim
Wannan littafin na kudi ne mai bukatar karantashi byn na kammalashi zai biya
1000 ta wannan account number din 1438775094 Aishat abdullahi access idan an tura
sai a turawa wannan 09136918331 alert domin tabbatar da an tura domin sauraron
littafaina a tuntubi chaneel dina (Hausa bakwai ) a YouTube.
Page 20
Tunda ATA ya bar gidan hankalin mami a matuqar tashe yake ganin maryam rasa
babu wata alamun an kusanceta domin ta lura kamar babu wani abu daya sauya
atattare daita "kar dai qarya adamcy ya girba mata bai aikata abinda tayi masa
umarni ba?" hakan yasa taji wani sabon tashin hankali ya shigeta . bangaren ATA
kuwa tafiya yake hannunsa rike dana aunty shahida har suka shigo parlour'n gidan,
sauri sauri yake janta suna taka step, kallonsa kawai aunty shahida take zuciyarta
cike da matsanancin bakinciki da tausayinsa ,bakincikinta saboda yadda yake janta,
tausayinsa kuma saboda yanayin da yake ciki dan yanayinsa kawai zai tabbatar maka
da baya ciki natsuwa da kwanciyar hankalinsa . kai tsaye d'akin maryam suka nufa
inda suka iske maryam zaune rike da hannun mami tana zubar da hawaye nan da nan
hankalin ATA yayi matuqar tashi , jikinsa har rawa yake ganin yadda maryam take
hawaye ,ba iya jikinsa ba hatta zuciyarsa rawa take .jin motsin shigowa d'akin ne
yasa da sauri maryam ta d'ago tana duban kofa idanunta ya sauka akansu ta share
hawayenta da sauri ckin muryar kuka tace "aunty shahida ina kika ajiye wayarki ?"
“mami tana cikin wani hali har ta fita haiyacinta numfashinta baya sauka da kyau
please aunty shahida ki taimaka banason wani abu ya samu mami ."ta qarasa maganar
tana wani irin kuka ."
Jin ba mutuwa mami tayi ba yasa ATA yayi mata wani mugun kallo tare da yi mata
alama da ido ta fita ta basu wuri ."babu musu maryam ta mike ta sauko daga kan
gadon cikin mutuwar jiki ta biyo ta ra'ba ta gefensa ta fita tana kuka .bayan
fitar maryam jingina bayanta tayi da bango corriedor tare da sake fashewa da wani
kuka mai ta'ba zuciyata "mami bana son na rasaki ,domin kuwa ke din babbar jigo
ce ga rayuwata da kuma rayuwar aurenta allah ya baki lafiya allah ya tashi
kafad'arki".cikin taku mai tattare da damuwa da tashin hankali ATA ya matso inda
mami take kwance numfashin ta na fita ahankali ,kafin ya bawa aunty shahida umarni
ya tsurawa mami idanunshi tare da zama a gefenta yana qare mata kallo yana jin
kamar ya fashe da kuka ya d'auki zazzafar qaddara rasa mahaifinsa na tsawon shekaru
yanzu kuma idan ya rasa mahaifiyarsa a halin da yake ciki na tarin damuwa da
matsalolin rayuwa ya zai yi ?"yaja zazzafan numfashi tare da sa tafin hannunsa ya
share hawayen daya d'an cika gefen idanunshi . duk yadda mami take jin idanunshi
akanta batayi kuskuren bud'e idanunta ba tana jira daga garesu ,lallausar tafin
hannunsa ya kai saitin wuyan mami yana jin saukar numfashinta yana jin d'umin
jikinta ahankali mami ta bud'e idanunta tana cewa "adamcy nah har ka dawo ?ina
shahidar take ".
kai ya gyad'a mata tare da kallon inda aunty shahida ke tsaye yace "ya kika tsaya
dan allah ki fara aikinki mana "ya fad'a kamar zai fashe mata da kuka alokacin
ya d'auke hannunsa akan wuyan mami ganin bata da alamun qarasowa yace "wai meye
haka dan allah naje na taho dake da kyar yanzu kuma kinzo kin ja kin tsaya kin
zuba mana ido kodan kinsan idan wani abu ya sameta ni ne zan fi kowa shiga damuwa
yasa kike min haka ?.yayi mata tamabyar a rud'e yana zufa "wai ..."mami tayi saurin
katse shi ta hanyar cewa "adamcy nah zan sha tea "da sauri ya mike tsaye ya fita
cikin tashin hankali yana fita maryam tayi wuf ta fad'o d'akin ,sai dai abun mamaki
mami ta gani ta dawo haiyacinta ba kamar sanda ta barota ba tana kallon aunty
shahida, bata gama mamakin ta ba taji fitowar muryar mami rasa. "zo nan maryam" ta
yafitota da hannunta ta nuna mata kusa daita tana cewa "shahida sai kuma kika ga
wannan rigimemen yarona yazo d'aukarki ?.
“wallahi kuwa mami ,da yake nasan shirinki shiyasa nayi masa wulakanci, yana fad'a
ina fad'a har muka baro gidan mami tayi murmushi kawai"amman fa ya bani tausayi
sosai ,da fatan dai komai ya tafi yadda muka shirya ? tô ya dai ce min ya aikata
amman bansani ba ko karya yayi min duk da nasan karya ba d'abiarsa bace idan bai yi
ba ,zai ce bai yi ba " mutuwar zaune maryam tayi agurin tana dubansu a matuqar
gigice saboda tsananin tsoro "kenan ciwon mamai shiri né dan yaya adam ya kusanceta
? “Ita kuwa wani irin só mami take mata haka ?kwakwaluwarta bata kai ga bata amsar
tambayoyin ba taji sautin muryar aunty shahida tana cewa "ke maryam !"maryam tayi
saurin d'agowa ta kalli aunty shahida a gigice "wani abu ya shiga tsakaninki da
adam né ?maryam tayi shiru alamun kunya "kinga karki 'bata mana lokaci idan kinsan
babu abinda ya shiga tsakaninku a canza wani shiri ?"ahankalai ta gyd'a mata kai
kawai "ki bud'e baki mana ki min magana ita kam bazata iya amsa wanan tambayar
agaban mami ba fahimtar haka yasa aunty shahida tace "zan yi magna idan wani abu ya
shiga tsakninku ki gyada min kai idan bai shiga ba kuma ki girgiza min kai.”
mami kam maganar aunty shahida kusan dariya yaso bata ,dan haka ta kawar da kanta
gefe tana murmushi "wani abu ya shiga tsaknain ku ?maryam ta gyad'a mata alamun "eh
"alhamdulillah ! ta furta a fili tare da cewa yanzu kuma sai muyi fatan allah yasa
ya zame mana alkhairi " in sha allahu zai zama alkhairi fara dubani kafin ya shigo
ya gane shiri ne kinsan halinsa da shegen ganiyar tsiya ". Inji cewar mami batare
da 'bata lokaci ba aunty shahida ta bud'e qaramin jakar kayan aikinta ta soma duba
jikin mami suna magana qasa qasa."otsin shigowa d'akin maryam taji hakan yasa tayi
saurin waiwayo
wa ATA ta gani yana qoqarin shigowa hannunsa rike da cup din tea ganin ana duba
mami ya ajiye cup din akan bedside ya tsaya idanunshi kyam akansu ko kifta idanu
baya yi ,burinsa kawai mahaifiyarsa ta samu sauki . yayinda maryam take kallonsa
kawai ta rasa abun yi saboda jin ciwon mami duk shiri ".
wani irin numfashi mai zafi ya fesar kamar ance ya kalli inda maryam take zaune
yaga shi take kallo wani mugun kallo ya bita dashi mai tattare da tsana taga irin
kallon tsanar da yake mata amman tayi kamar bata fahimta ba ta cigaba da kallon
faukarsa har alokacin tana cikin yanayi na damuwa da tashin hankali ,mami kuwa
hankalinta na kansu addaua take masa acikin zuciyarta "allah yasa qarshen
wahalarsu ne yazo, allah ka dubeni ka shirya min adam ka fidda shi acikin halin
da yake ciki ka dauke masa tunanin mafarkinsa ka mantar dashi komai akanta ka
daidai tsakaninsa da matarsa ."kamar wanda aka tsinkara haka yayi kanta yana cewa
"kallon iskanci me kike min ?".wani irin tari mai karfi mami tayi tana kiran
sunansa da yafitosa da hannunta dole tasa ya dawo da sauri ya rike yatsun hannunta
gam yana mata sannu amman idanunshi na Kan aunawa maryam mugun kallo da harara ."
har tsawon mintuna talatin aunty shahida tana Kan aikinta sannan ta samu
numfashin mami ya dawo daidai ta mata allurar bacci sannna taja baya kad'an ta
tsaya tana yiwa mami sannu ."yauwa shahida allah yayi maku albarka gabad'ayaku da
ya'yanku allah yasa ina da rabon ganin ya'yan adamcy da auta "in sha allahu mami
zaki gani allah dai ya baki lafiya "wani mugun kallo ATA ya watsa mata yana jan
tsaki "da fatan dai baku sheidawa kowa halin da nake ciki ba ko ?nasan babu wanda
d'an naki ya sheidawa dan nasan daya sheida masu da yanzu sunzo ko sunyita kira a
waya amamn yanzu zan kira khadija , zabiba da auta na sheida masu halin da'ake
ciki sai su zo gobe su duba jikikin zazzafan numfashi ya sauke dan kuwa babu
wnada ya sheidawa cewar mami ta kusan mutuwa ya kai hannu ya d’an d’ago mami yasa
mata pillow ya jingina bayanta ya d'auki cup din tea din daya shigo dashi ya kai
bakinta yana bata tana kur'ba ahankali rud'ewarsa bai bawa mami mamaki ba dan
tasan halinsa akan ya rasata zai iya aikata fiyye da haka dan duk iskancinsa idan
zai ga 'bacin ranta ko rashin lafiyarta yanzu né hankalinsa zai tashi ,bai son ya
rasata gashi kuma mutuwa tana Kan kowani bawa dole watan wata rana zaa wayi gari a
sheida masa ta mutu ko ta mutu a hannunsa allah dai ya bata ikon cikawa da imani
shine fatanta ".
bayan ta gama sha tea ya gyara mata kwanciya yana mata sannu tare da lullu'be mata
jiki ya zauna a gefenta hannunsa na rike cikin nata yana jin qaunar mahaifiyarsa
fiyye da komai, ahaka bacci ya d'auke mami ,ya tsura mata ido "ya allah ka bani
karfin zuciyar yiwa mahaifiyata biyayya ba komai ya hanashi son abinda mahaifiyarsa
ke so ba illa soyayyar princess daya ma zuciyarsa mummunar kamu ."hannun maryam
aunty shahida ta kamo suka fito daga cikin d'akin,ahankali suke takowa zuwa
parlour'n qasa "maryam ina tayaki murna allah yasa ku samu rabo a wannan had'uwar
farkon da kukayi da adamcy." cikin yanayi na tashin hankali maryam ta sauke
numfashi tana jin sabon tashin hankali na shigarta "abinda basu sani ba ai wannna
had'uwar itace kusan ta biyar a tsakninsu dashi har bakin mota ta raka aunty
shahida tana karfafa mata gwiwa ta bud'e mata gidan baya ta shiga ta zauna "allah
ya tsare min aunty nah zaki shigo gobe né ?sosai kuwa zan zo gobe ai idan ban zo
ba wannan muskililin zai iya kiran likitansa kuma zai iya gano komai allah ya kai
mu gobe aunty shahida ta wuce gida ta barsu duk da taso tayi magana da adam amman
ganin yanayinsa akwai tsananin damuwa koma tace haushinta yake ji .
Acan d'akin kuwa a hankali ATA ya runtse idanunshi tare da motsa labbansa
"princess you want to kill me ba ?kina son sonki ya kasheni ba ?duk tsananin
soyayyarki ne ya hanani yiwa mahaifiyata biyayya why kika kasa bayyana min kanki a
zahiri gashi komai zanyi sai da tunaninki ".ya fad'a yana sauke ajiyar zuciya da
numfashi atare ya tuna lokacin da yake saduwa da maryam karfin tunaninta ne yayi
tasiri a zuciyarsa har mazakun tarsa ta mike if not da bazai iya aikata komai
daita ba "nima ina sonka sosai zuciyata da gangar jikina kai kad'ai suke jira
saboda zuciyata da gangar jikina mallakinka ne har abada ,yaji sautin muryarta
acikin dodon kunnensa suna masa kuwa ahankali ya bud'e idanunshi yana kallon
d'akin .wani naunayen ajiyar zuciya ya sauke yana furta "why princess ?ina son na
ji sautin muryarki a zahiri kullum sai dai naji a bad'ini ya fad'a da wata irin
murya kamar tana tare dashi ya dade zaune har goshin asuba sannan ya zare hannunsa
cikin na mami ya fito ya nufi d'akinsa kamar ya d'an kwanta ya huta dan wani irin
sara kanshi ke masa amman yasan ko ya kwanta bazai ta'ba iya runtsawa ba saboda
halin da mahaifiyarsa take ciki ."
kai tsaye hanyar bathroom ya nufa ya tura kofar ahankali ya shiga domin tsarkake
jikinsa bayan ya zare jallabiyarsa wanka tsarki ya soma alokacin da ruwa ya fara
sauka ajikinsa zuciyarsa ta fara hasko masa komai daya faru a awanin da suka gabata
"sweet heart kinga irin matar da kika za'bawa rayuwata ko ?" Kin aura min
mazinaciya ,kin aura min macen data gama zubar da mutuncinta a waje “Ko adadin maza
nawa ne suka kusanceta ?yayiwa kanshi tamabayr yana furta kalmar subhallah acikin
zuciyarsa "a gaskiya sweetheart baki kyauta min ba ,shiyasa raina yaki amsarta
zuciyata taki sonta, babu shakka wannan dabi'ar ce yasa zuciyata ta qasa amsarta
amatsayin mamata "nan da nan zuciyarsa ta fara tafarfasa yana jin tuttukin
bakinciki sakama kon yadda yaji maryam akan gado "sweetheart kin sadaukar da
rayuwarki akan mazinaciya batare da kinsani ba wani zazzafan numfashin ya fesar
kana ya cigaba da wanka da wannan tunanin yayi wankan tsarki Ya gama ya d'auro
alwala ya fito ya sauya wani jallabiaya mamadin ya kwanta ko ya zauna sai kawai ya
tsinci zuciyarsa da són gabatar da nafila "gara ya koma zuwa ga ubanginsa ko zai
fita daga cikin maseefun da yake ciki na tsawon shekaru ."
Cike da tashin hankali maryam ta shiga d'akinta ta samu waje ta zauna tana duban
mami "wani irin soyayya mami take mata haka ?ta furta a saman lip's dinta tasan
mami na matuqar qaunarta amman bata ta'ba tunanin zata aikata haka akanta ba ,kanta
ta kifa a daidai hannun mami hawayenta na zuba "allah sarki mami kina sóna da
yawa ,kina son cigabana ta kowani hanya kina nan kina shirya min yadda zanji dadi
a gidan d'anki ni kuma mahaifiyata tana nan tana shirya yadda zan cutar da d'anki
domin kuwa da magungunan da sukai masa sunyi tasiri sai abinda tace masa zai yi
amman duk runtse duk wuya bazata ta'ba barin yaya adam ya juya wa mami baya ba idan
sukai nasara akanshi sake kwantar da kanta tayi tana tunanin irin kallon da ATA
yake mata wanda ke d'auke da tambayoyi kuma tasan duk akan yadda ya sameta
ne ."hakika maryam kinyi gaugau wa arayuwarki "ko a wani matsayi yaya adam zai
dauketa fatanta allah yasa yau né cikin zai shiga dan kuwa idan ya shiga kafin yau
akwai kutirin bala'i a gidan ."
sosai tayi zurfi cikin tunani qarar wayarta ce ya dawo da ita daga tunanin da take
ta yunkura ta mike da kyar ta d'aga tana duba screen din wayarta sunan
mahaifiyarta ce ta kalli agogon wayarta tana mamaki kiran me take mata adaidai
wannna lokacin ? kamar bazata d'auka ba sai kuma ta kara wayar a kunneta ta shige
bayinta tana magana qasa qasa ."ummah lafiya ?okay to shikenan amman karki aiko da
komai sãi mami ta wuce “bayan ata ya idar da nafila ya zauna yana addua tare da
neman zabin allah arayuwarsa ,wannan shine karo na farko da yayi wannna tunanin da
kuma addua wa mahafiyarsa yana zaune har aka kira sallah asuba ya mike yayi alwala
ya fita zuwa masallaci ya gabatar da sallah sannan ya dawo bai shiga d'akinsa
ba ,ya shiga d'akin maryam domin duba mami wanda alokacin itama mrym tayi sallah
tana kwnace abayan mami tsaki yaja tare da jan qafarta d'aya ."
firgigib ta bud'e idanunta ta mike zaune tana shafa idanunta bai tsaya wata wata ba
yaja hannunta hanyar waje yayi daita ,maryam wanda keta rokonsa ya barta a kusa da
mami amman bai kulata ba yana kaiwa waje yayi fillinging daita ta zube qasa tana
dubansa "yayinda shi kuma yake jifanta da wani mummunar kallo,"bai ce mata komai
ba dan idan ma ya nuna mata yaji ciwon rashin samunta a cikakkiyar budurwa zata
iya cewa kishinta yake wanda shi kuma har ga allah ba kishinta yake ba, kawai
yadda ta munafurci mahaifiyarsa ta nuna mata cewar ita din mutuniyar kirkice yafi
damunsa "kiji abinda zan fad'a miki kar na sake ganinki a kusa da mahaifiyata
domin ita din mutun ce mai tsarki "hannuwanta duka ta d'aura bisa kanta tana kiran
"wayyo allah na shiga uku dan ko bai fito fili yayi mata dalla dalla ba ta
fahimcesa fiyye da haka "shiiiiii ! karki kuskura ki tasa min uwa daga bacci idan
ba haka ba wallahi kinji na ranste sai na d'agawa uwarki da ubanki hankali kin dai
san halina, Kinsan abinda zan iya yi dan haka stay a way from my mum ."yana gama
fad'ar haka ya juya ya koma d'akin ya zauna kusa da mami yana kallon yadda take
sauke numfashi normal ba kmar d'azu ba ."
Maryam kam komawa tayi Kan step ta zauna ta raku'be jikinta waje d'aya tana tunani
yadda zatayi "wani hanya zanbi ni maryam ya fahimci shine mutum na farko da ya fara
sanina ya mace ?"babu wata hanya tunda rashin hakurinki ya janyo kika mallaka masa
kanki baya cikin haiyacinsa zuciyarta ta bata amsa da haka “amman kuma ai kina da
sheida ?tabbas kina dashi sister itace sheidata ta d’an ji natsuwa kad’an amman
duk da hk hankalinta ba’a kwance yake ba .a hankali ta mike tsaye ta fara tafiya
kamar mara laka ajiki jikinta ba qaramin sanyi yayi ba ganin irin kallon zargin da
yake mata duk yadda taso taji haushinsa ko kuma taga laifinsa zuciyarta ta kasa
kar'bansa amatsayin mai laifi ko wanda zataji haushi sai ma taga kamar ya fita
gaskiya kuma kowaye dole irin kallon da zai mata kenan . idanunta taga suna ganin
duhu akan kujera mai zaman mutun uku ta zube ta kwanta tana runtse idanunta ."
Karfe takwas saura maryam ta farka ta sauke idanunta akan agogo bata sake
yunkurin komawa bacci ba ta tsaya ta gyara ko'ina tare da shiga kitchen da yin
abincin da zasu yi breakfast dashi sai dai har lokacin zuciyarta cikin dar dar
take ta kasa jin sukuni dan hango katoton matsala wa rayuwarta take . Karfe goma
gabdayansu ya'yan mami suka harllara a gidan kuma a dakin maryam .maryam din ce
kad'ai bata cikinsu tana parlour’n qasa cikin jimami yayinda ATA ke gabana mami
yana magana cikin tsananin damuwa "dan allah sweetheart ki bari na fitar dake zuwa
kasar Índia a duba min lafiyarki murmushi iya baki mami tayi tana cewa "adamcy
kenan baka son na mutu ko ?mami tayi masa tambayar idanunta na kanshi "wallahi
banaso sweetheart!"Yayi maganar kamar zai yi kuka kallonsa kawai mami take without
saying a word to him sai dai wani irin tausayinsa ne ya mamayeta da sauran
yanuwansa tabbas ta yarda kuma ta amince d'anta na mutuqar qaunarta damuwar dake
yawo cikin rayuwarsa ne ya hanashi yi mata biyayya runtse idanunta tayi sai ga
hawaye sharr yana sauka akan quncinta ".
hannunta ya riko gam cikin nashi yana cewa "why sweetheart?me yasa zaki zubar da
hawayenki "ki daina kuka please idan wani abu kike so ki fad'a min am ready do
anything for you sweetheart idan kuma tafiyar ne bazakiyi ba wallahi na hakura
bazan takura miki ba amman dai bana son na rasaki, dan a yanzu idan kika mutu ba
iya yan'uwana ba hatta mutane gari ma sai sun min gori akan rayuwata aunty shahida
ta kallesa tasan sarai daita yake maganarsa ."an waye gari wai yar'uwata ce da
kanta tamin gori sweetheart a karon farko naji na tsani kaina duk da nasan tayi min
né akan abinda nake miki ,nasan na sakaki cikin damuwa sweetheart ki yafe min
lafifukan da nayi miki abaya da wanda zanyi a gaba nasan kina sona da wannna
yarinyar ne yasa kema kike takura min amman dan allah ki yafe min tsanar da nake
fad'a miki inawa yarinyar a gabanki nasan tana sakaki cikin tsananin damuwa
"wallahi sweetheart na sha fad'a miki Kiyi min addua ko allah zai saka min
soyayyarta acikin zuciyata amman har yanzu shiru babu wata alama ta qaunarta "ya
qarashe maganar muryarsa na rawa mami ta kallesa idanunta cike da ruwan hawaye
tace "tabbas yawon fadar tsanar da kakewa maryam tana bata min rai amamn adamcy na
yafe maka duniya da lahira burina allah ya had’a hankulanku waje d'aya ."
d’aya bayan daya yan'uwansa suka baro d’’akin zuwa parlour suka had'u gabadayansu
suna hira har da maryam nan aunty shahida take basu labarin abinda ya faru "kai
auntynmu dan allah da gaske ?wallahi ga maryam ku tambayeta "gaskiya auntynmu kin
gama da yayanmu "inji cewar zabiba maryam ta mike tana mai jin tsananin farinciki
yadda yan'
uwanta kuma dangin mijinta suke matuqar qaunarta aunty khadija tace "ai gara da,aka
gama dashi baki ga yayi laushi ba duk ya canza kala kamar bashi ba ,yaro sai shegen
taurin kai da fadin ran tsiya ai ni wallahi mami tayi min daidai ai da mun san d'an
wannan shirin film din zai dawo dashi haiyacinsa da tunin an dade da wuce gurin
aunty khadija ta qarasa maganar tana miqawa zabiba hannu suka tafa ."
“Allah dai yasa buqata ta biya." nana hauwa'u tayi murmushi tare da mikewa tana
cewa “in sha allahu ta biya sai fatan alkhairi ta shiga kitchen inda maryam take
qoqarin gama tuwon shinkafa da
miyar agushi .”
tun daga falo kamshin miyar ke shiga hancin nana hauwa'u har sai da yasa yawunta
tsinkewa "matar yaya wannan kamshi haka kamar zaa tafi gasar abinci "kai sister yau
kuma tsiya zaki min "?”ke mu bar wannan maganar yaya had’uwarku da yaya ta kasance
daren jiya ?"nan da nan yanayin maryam ya sauya idanunta suka canza kala alamun
zatai kuka "babu wani jin dadi sister yayanki wani kallo yake min wanda bazan iya
fitowa na bayyana shi ba .nana hauwa'u ta dafa kafad’anta "karki wani daga
hankalinki ko sarewa "me yasa zaki fad'i hka wallahi sister a matukar tsorace nake
"ba gani ba meye abun tsoro ?nana hauwa ta fad'a cike da kulawa maryam bata san
sanda ta rungumeta ajikinta ba tana share hawayenta ."shadaya da rabi daidai ata
ya sauko ya fita daga gidan kuma alokacin maryam ta gama komai har da miya suna
tsaye suna hira da nana hauwa’u inda nana hauwa’u take fad’a mata ciki gareta wani
ihu mrym tayi ta rungumeta “gsky sister am very happy for you Allah ya hada miki
komai da komai “kema sister kiyi ahankali fa dan baki sani ba ko ciki gareki mrym
ta zaro ido waje “sister ina jin tsoron abinda zai biyo baya “ina nufin an samu a
daren jiya “allah yasa ai da ni kad’ai nasan irin farinciki da zanyi dan ko baya so
zan rike abina bare ma da gudu zai kwace suka dariya basu gama rufe bakinsu ba
kawai suka jiyo sautin muryar ATA cikin hargagi da tashin hankali .”
"ku yanzu daku zaa had'a baki ayi min haka "? a she yadda nake qaunarku ku ba haka
kuke qaunata ba ?"daman na dade dasanin haka ,na gode allah ya saka da alkhairi ku
tashi ku bar min gidana gabandayanku bana son ganin fuskokinku” ya qarasa maganar
adaidai lokacin da su maryam suka fito rike da hannun juna a bakin kitchen suka ja
suka tsaya jikin maryam banda rawa babu abinda yake ".dan kwata kwata bata son
ganinsa cikin tashin hankali
“Ya kalli inda maryam suke tsaye ya nunata da yatsan hannunsa “kema bazan qara
zama dake ba ki tattara duk abinda kikasan naki ne acikin gidan nan ki bar min
gidana na sake ki saki u…”cike da tashin hankali aunty shahida tayi wani Irin
qarasowa inda yake ta rufe masa baki tana girgiza masa kai tare da nuna masa
yatsanta d’aya alamun d’aya zai furta maryam kuwa tun kafin ta gama ji ta d’aura
hannuwanta duka bisa kanta tare da shiga wani sabon tashi hankali"wani laifi suka
masa haka ?ta jefawa wankakkiyar kwakwaluwarta tambayar ."
inna lillahi wa inna ilaihi rajiun shine abinda nana hauwa'u ta shiga furtawa tana
maimatawa wanda yasa maryam ta kama tana yi bakinta na rawa wannan wace irin
maseefa ce inji cewar aunty khadija dan gabadayansu babu wanda jikinsa bai d’auki
rawa ba maryam kuwa tashin hankalin da take ciki ya hanata kwakwaran motsi a inda
take tsaye magana take son yi koda kalmar hakuri ce garesa amman ta qasa furta
komai numfashi kawai take ja ta bakinta tana fitarwa dashi da kyar .”
alamarin ATA ya girmi tunanin yan'uwansa suna kallonsa ya buga ma aunty shahida
razananniyar tsawa bayan ya cire hannunta “cikin tsananin tashin hankali da
fad’uwar gaba take rokonsa "Adam ba’a saki cikin fushi idan kuma ya zama dole sai
kayi kayi d’aya wani mugun kallo yayi mata yana mai janye jikinsa daga nata ya
sake maida kallonsa ga maryam “tsayuwar me kike yiwa mutane maza ki fara qoqarin
bar min gidana ,kuma haka banason ganin kowacce acikinku wallahi na tsaneku sannan
na cire kaina acikinku aunty khadija ma tayi karfin halin qarasowa inda yake yayi
saurin ja baya "bana son jin komai kawai kuje tunda kunfi son farincikin yarinyar
nan akaina shekara nawa ina fama da zazzafar qaddara amman acikinku ko sau d'aya
babu wacce ta zaunar dani ta fahimceni amman dan rashin Imani irin naku daku aka
had'a baki na kusanci wannan guntuwar yarinyar wallahi kun cuceni .””ai tun daga
zuwa d’auko shahida ya kamata ace na fahimci akwai wani abu a qasa amman babu
komai kuje na gode .”
mamaki da matsanancin tsoro suka kama maryam “daman akan ya kusanceta ne ya zartar
da wannan hukuncin akanta? ganin maryam bata da niyyar bar masa gidansa ya qarasa
inda take ya kamo hannunta yana ja bata iya ce masa komai ba sai ma binsa da take
har ya kai bakin kofa ya bud'e tare da hanka d’ata waje ya maida kofar ya rufe da
karfi wasu hawaye masu zafi da ciwo suka zubo mata tasa bayan hannunta tana gogewa
wasu na sake biyowa kuncinta ."ATA na gama juyo idanunshi ya sauka akan mami
tsaye ,cikin tsannain tashin hanakali take kallonsa muryata na rawa tace "me ka
aikata haka adamcy ?yanzu sweetheart har za’a had’a baki dake a cutar da
rayuwata ?ban shirya yin rayuwata da wannan yarinyar ba saboda me zaa min karya da
ciwonki ?numfashi mami ta sauke tana kallonsa "dan haka na saketa saki uku dan
bazan qara zama daita ba gabad’aya babu wanda bai furta kalmar “inna lillahi wa
inna ilaihi rajiun ba har mami dan kam sai data dafe qirjinta dan wani luguden bugu
yayi .”
nana hauwa'u ta qaraso inda yake cikin rud’ewa da rawar jiki ta riko hannunsa ya
fixge "har ke ban cireki acikinsu ba kuyi rayuwarku nayi tawa tunda bakwa sona nima
na hakura daku har abada zabiba ta bud'e baki ta soma magana cike da in ina
"ni ..ni dai yaya wallahi banda ni dan ba dani aka shirya komai ba hasalima yau
din nan nasan komai aunty kahdija ta ta'bata alamun tayi shiru amman ta zame
jikinta "dan allah yaya karka mana haka wallahi muna tsananin sonka muna qaunarka
ta durkushe kasa tana jan gwiwowinta zuwa garesa ya tsaidaita ya juya ya haye sama
a matukar fusace yake taka step ."wani irin naunayen ajiyar zuciya suka sauke atare
"mami ta kallesu daya bayan tace "garin yaya kuka yi wannan kuskuren ?yaakayi kuka
bari yasan komai ? tayi masu tambayar ajere cikin tsananin tashin hankali,gbdynsu
sukai shiru dan basu da bakin magana ta sake sauke ajiyar zuciya "ina maryam take ?
tana waje ! nana hauwa’u ta bata amsa cikin kuka kai tsaye kofar mami ta nufa ta
bude inda taci karo da maryam durkushe tana zubar da hawayen mami ta kai hannunta
ta d'ago ta ta rungumeta ajikinta tana shafa bayanta .”
jinta ajikin mami yasa ta sake fashe da wani sabon kuka mai ta’ba zuciya " dan
allah mami ki fad’awa yaya bani da masaniya akan komai ,kuma allah danasan shiri ne
ciwonki da bazan ta'ba amincewa ba gara na cigaba da rayuwata haka dashi "kukan
ya isa haka abinda ya faru ya wuce ba kuma zai gogu ba ta zareta ajikinta suka
koma parlour'n ta zaunar daita akan kujera sannna ta zauna a gefenta tana
rarrashinta "yanzu mami ya zaayi kenan ? "ku da kuka tona asirin komai sai kusan
yadda zakuyi dan babu ruwana ,ban da son jawa mutane tashin hankali meye abun baje
hira a gidansa alhalin kusan halinsa? Kiyi hakuri mami ki yafe mana inji cewar
aunty shahida "mami dan allah kije ki shawo kansa ya janye sakin ya maidashi d’aya
Ke kadai ce zaki iya shawo Kan yaya nana hauwa’u ta fad'a tana share hawayenta "da
sauri maryam ta kalli inda take zaune “sister saki ukun yayi min kenan ?nana
hauwa’u ta gyad’a mata kai alamun “eh!ahankali ta runtse idanunta gam tana jin wani
irin rad’ad’i da ciwo acikin zuciyarta wallahi tayi wa kanta alkawari muddin ba
ita ce acikin gidansa ba babu wacce zata zauna cikinsa cikin jin dadi, duk inda ake
zuwa dan biyan buqata zata domin ta hanashi jin dadin rayuwa kuma duk runtsi sai
ta dawo gidan zaman lafiyarsa ya janye sakin kamar yadda sister ta bada shawara
bata gama fita daga wannan tashin hankalin ba taji muryar aunty zabiba ta karad’e
parlour’n “.
“gsky mami ya kamata mu ajiye son rai a tsaya a duba lamarin yaya shima tunda ya
nuna baya son aurenta kar a wani maidashi a hakura kawai allah ya hada kowa da
abinda yafi zama alkhairi .” da sauri maryam ta bud’e idanunta ta kalli inda take
zaune qirjinta na wani irin bugawa "bayan ya gama maidaita qaramar bazawara zaki
fad'i haka ? aunty khadija ta fad'a a fusace "to meye amfanin wannna auren tun
kafin ayisa yace bai so ?tunda akayi auren nan ku fad'a min rana daya wanda muke da
kwanciyar hankali ?”kullum zuciyarmu cikin fargaba take, yin aure halal ne haka
barinsa halal ne idan ma zai gare rayuwarsa haka abarshi mana matsawar bazai dinga
biye biyan mata ba ,”tunda suka fara magana a tsakaninsu mami bata ce uffan ba har
Qarfe uku ATA bai sauko ba gabdaya cikin damuwa da tashin hankali suke most
especially maryam wacce har wani rama tayi nana hauwa’u dake kusa da maryam ta
dinga kwantar mata da hankali “sister karki d’aga hankalinki yaya zai janye sakin
da yayi miki yanzu fa kin rigada kin zama jinin jikinsa jininsa gauraye yake da
naki wata killa ma akwai ajiyarsa ajikinki shiru kawai tayi dan bakinta bazai iya
furta komai ba dan hatta miyon bakinta ya qafe idan tayi qoqarin had’iye wa jinsa
take tmkr mad’aci ."
Da misalin karfe biyar ne mami ta mike ta haura sama ta shiga dakin ATA ta iske
shi zaune akan kujera kwaya d'aya dake dakin yayi baya da kujerar yana kallon saman
d’akin ganin shigowarta ya runtse idanunshi gam .da sanyin jiki mami take
qarasowa inda yake stood ta janyo ta zauna gabansa ta zuba masa ido tana kallonsa
tana nazarinsa dakin yayi shiru tamkar babu kowa aciki har tsawon minti goma mami
na zaune agabansa yadda batayi magana ba haka bai bud’e idanunshi ba ta kira
sunansa "adamcy nah! shiru ne ya sake biyowa baya ta kai hannunta ta kamo hannunsa
ta kai bakinta tana sheshekan kuka saukar hawayenta yaji a hannunsa ya d’an bud'e
idanunshi akanta tabbas hawaye ya gani yana sharara akan kuncin mahaifiyarsa abinda
ya tsani gani kenan naunayen ajiyar zuciya ya sauke da karfin gaske sannan ya kai
dayan hannunsa yana d’auke mata hawayen fuskarta dake kwarara sannan ya motsa lips
dinsa da kyar "why sweetheart?Bata ce masa komai ba illa cigaba da zubar da hawaye
"da fatan ba Adam bane yayi sanadiyar zubar hawayen nan ?ahankali ta gyada masa
kanta alamun shine.”
numfashi ya sauke yana son sanin dalilin kukanta "adamcy kana son saka sweetheart
dinka kuka,baka jin damuwa yadda kake saka sarauiyar dad dinka kuka ?mami ta
furta tana dago da idanuwanta ta zuba masa da matuqar damuwa "ina cikin damuwa
adamcy !"nima acikin damuwar nake” jin sautin muryarsa cikin tsanani bacin rai ya
qara d’aga mata hankali ya zame hannunsa ya mike ya qarasa qarahen dakin ya tsaya
rike da kugunsa yana jin zafi da ciwon abinda mahaifiyarsa da yan'uwansa suka masa
"."Adamcy na !ta sake kiran sunansa a karo na biyu yana jinta yaki juyawa mami ta
cigaba da magana "ka sake min wani alfarma a karo na biyu adamcy .” ya d’an juyo a
natse ya kalleta "kayi hakuri ka janye sakin da kawa maryam ka maidashi d’aya
sannan ka maida maryam d’akinta saboda allah da girman mahaifinka da darajan
haihuwarka da nayi "ya bud'e baki yi zai magana "karka ce aa adamcy ta katse shi ta
hanyar fad’ar haka “kayi dan allah da mahaifinka da kuma ni da nayi silar zuwanka
duniya domin muddin ka rabu da maryam zata shiga damuwa mai tattare da tashin
hankali idan ta kasance cikin damuwa nima zan shiga domin nice silar komai .”
ya juyo sosai ya fuskanci mami "abu na farko tana rayuwarta batare da kai ba na
shigo daita cikin rayuwarka, abu na biyu yanzu kun zama abu daya wayasani ma ko
rabo ya shiga tsakaninku "gaksy ni sweetheart bana son abinda kike min akan
yarinyar nan ban gama fita cikin matsala ba zaki sake shigo min da wata damuwa "ba
zancen shigo da damuwa bane adamcy naji hakan ajikina akwai rabo a tsakaninka da
maryam .”yayi shiru kawai yana mamakinta a ransa yace “ai kuwa badani ba dan
bazan sake gigin kusantarta ba kuma ni bana jin haka ajikina domin spam din daya
fitar ba d’a bane dan duk spam din da zai zama d’a fitarsa nada matuqar wahala
daga jikin d’an adam mami ta d'an yi gyaran murya "ni mahaifiyarka ce zan iya
sakaka kayi min abu dole koda kuwa ranka bai so amman a wannan karon banason na
maka dole alfarma nake sake neman da baka hakuri saboda dalilai masu yawa dan
allah ka janye ka kuma maida maryam iska ya fesar mai zafi daga bakinsa sannan
yace "shikenan naji na janye na maida ita ."iyakar abinda ya fad'a kenan ya fice
daga dakin domin idan ya cigaba da tsayuwa zata nemawar yanuwnasa afuwa abinda
bazai so ba kenan shi dasu har abada .”
“Alhamdulillah! mami ta dinga furtawa tana nemammansa afuwa da sauki a wajen Allah
suna zaune jugun jugun ya sauko ya nufi kofa "zabiba ta zabura ta mike zata bishi
aunty shahida ta dakatar daita tana cewa "da alamun kin fara manta waye adam
arayuwarki wallahi zamanki matar aure da ya’ya bazai hanashi yi miki mugun bugu ba
mu barshi har ya sauko da kanshi "ni dai zan wuce gida dan bazan bari wannan fuskar
ta sake shigowa muyi ido hudu ba inji aunty khadija gabdaya suka kwashe da dariya
ban da maryam wacce idanunta sukayi jajur tsabar kuka” nima tashi zanyi na wuce
nasan mami zata shawo kansa suna shirin mikewa mami ta sauko "mami ni zan wuce gida
inji cewar aunty khadija itama zabiba ta gyara zaman mayafinta nima zan gudu dan
yau sai wani ikon allah ,allah yasa dai ya sauko "kun gama hadasa mana tashin
hankali shine zaku gudu daya bayan daya ?"dan allah mami Kiyi hakuri bamu san zai
dawo ba tunainmu fitarsa yayi nisa "ai shikenan tunda ya janye sakin .""
Wani irin ihu nana hauwa ta saka tare da zuwa inda maryam take ta rungumeta "sister
yaya ya maidake ai na fad'a miki yanzu kin zama wani bangare na rayuwarsa "kunga
kuzo ku wuce sai qarshen wata kenan "in sha allahu mami suka hada baki gabdayansu
sukai mata sallama gidan ya saura daga mami sai maryam nasiha da kwnatar da hankali
mami tayi tawa maryam muryata a dashe tace “mami na gode “har karfe goma suna zaune
a parlour'n sallah ne kawai Ke tashinsu amman babu ATA babu alamunsa har shabiyu ta
buga suka rufe kofar parlour'n batare da sun murd’a key ba koda zai shigo suka hau
sama daga maryam har mami babu wanda ya runtsa sai faman juyi suke bayan sunyi
sallar asuba ne suka kwanta inda wani naunayen bacci ya d’aukesu sai karfe shadaya
suka tashi da sanyi jiki maryam ta sauko domin samawar mami abinda zata ci kawai
ta gansa kwance akan kujera ya daura tafin hannunsa d’aya a daidai mararsa yayinda
d’ayan hannunsa ke saman goshinsa idonsa biyu sai dai tunaninsa yayi nisa domin
likitansa bai dade da wucewa ba abinda sakamakonsa ya nuna ne yake yawo acikin
brain dinsa “wai anyi masa amafani da wasu kwayoyin jima’i ne wanda shine ya
haddasa masa azababben ciwon kai da bai jin magani “ how come ?ya tambayi kanshi
Idanunta na kanshi ta shige kitchen ta fara aikinta .”
Maryam ta girgiza kai alamun “a’a ! “mami karki wani damu da masu aiki dan ni bana
ra’ayi masu aikin. bbu abinda na fi tsana a rayuwata sama dasu dan wallahi wasu
masu aikin ba aiki yake kawo su ba , mami tayi murmushi dan ko bata fad’a mata ba
ta fahimceta “ to ai shikennan Allah ya bada sa'a Amman dai yanzu ki bari ki dan
hutu haka. naga ko karyawa bakiyi ba ,ai yanzu nan zankarasa nama kusan
gamawa.mamaki ya cika zuciyar mami ganin irin aikin da take wanda bata yinsa a
lokacin da take gidanta komai masu aiki suke yi mami ta gyara zamanta tare da
kunna TV tana kallo daga nan inda take zaune suke hira da mrym din ,kafin wani
lokaci mrym ta gama komai har abinci .”koda yamma tayi ma zagaye mami tayi ta
shiga kitchen ta shirya masu lafiyayen abinci , farar shikafa ce da miyar
pepesoup din kayan ciki ,sannan da miyar pepesoup din freshe fish dataji kayan
hadi da ganye ugu aciki sai kamshin ke tashi .”sannan taje ta shirya komai tsaf
tsaf a dinning ta bude kulolin abinci ta dinga d’aukar girkin hotuna da vedio
byn ta gama ta rufe komai taje ta sheka wanka ta hade cikin daguwar rigar atamfa
wacce ta sha stone work sai kalli take zubawa ga wani kamshi na musamman dake tashi
ajikinta. karku manta mrym akwai son kwalliya da posting a social media tana gama
kwaliyar ta fara zubawa kanta hotuna kala dabam dabam kamar yadda ta yiwa girkin
sai datayi posting sannan ta soma qoqarin fitowa ”
ahankali take saukowa zuwa parlour kasa tayi maseefar kyau sai kyali take abu
ga farar mace kusa da mami ta samu guri ta zauna sai dai idanunta na kallon
tsaitin kofar shigowa mami ta kalleta tana murmushi tace “ kai Kai maryam kinyi
kyau ,yau adamcy bazai ganeki ba “mrym ta saki wani murmushin jin dadi tana cewa
“kai mami har wani kyau nayi . ?”wallahi kinyi kyau sosai kuma naji dadin ganin
wannan kwaliyar daman inata son nayi miki magana akan kin rage kwalliya ba kamr
sanda kike gida ba, marym ta sake yin murmushi “gsky kinyi fine sosai allah yasa
adamcy yaga kyan kwaliyar nan “Ameen ta amsa a cikin ranta .”bayan kamar mintuna
goma suka jiyo sallamarshi a ciki suka amsa alokacin da yake taku cikin parlour,
kunnenshi makale da waya yana magana da saurinta ta mike ta tarbeshi zata karba
briefcase din hannunsa ya hanata batare da ya kalleta ba ya nufi hanyar sama yana
jan tsaki dan baqaramin jin haushin nacinta yake ba“.
jiki a sanyaye maryam ta shige kitchen ta zauna tana runtse idanunta yayinda
zuciyarta ke mata wani irin zugi mami sarai ta fahimci damuwace tasa yin haka nan
da nan itama taji damuwa zuciyarta ta sosu ta mike ta shiga kitchen din ta iske
mrym zaune har lokacin idanunta a runtse suke ta kai hannunta ta riko hannunta ba
tace daita komai ba suka fito kai tsaye dining area suka nufa ta zaunar daita itama
ta zauna tana ta’ba qirjinta alamun ta kwantar da hankalinta .”byn kmr minti
talatin ATA ya sauko jikinsa sanye da riga white t shirt da wando jeans three
quater sai kamshin turarensa Red ne yake tashi ajikinsa , kai tsaye dinning
area ya nufa inda ya hangi su mami zaune da alamun zaman jiran fitowarsa
suke .'ahankali ya karaso gurin tare da samu guri ya zauna kusa da mami yana
gaisheta “ai na d’auka bazaka gaisheni bane ?dan ka wani shigo ko kallon inda
mutane suke bakayi ba ta fad’a cikin rashin sakin fuskar numfashi ya sauke yace
“barka da dare sweetheart ?barka ya aikin ?alhamdulilllahi ya fad’a atakaice
sannan ya ciro wayarsa yana operating .”
ahankali mami tayi wa mrym alamar ta koma kusa dashi ta tashi ta koma kusa dashi
ji yayi kamar ya tashi ya canza guri amman ya share ya cigaba da dandana wayarsa
“maryam bismillah kiyi serving dinmu wani irin mikewa tayi wanda yasa gabadaya
santsar jikinta girgiza most especial qirjinta d’agowa yayi da niyar sauke mata
ruwan bala'i idanunshi yaci karo da girjinta kallo daya yayiwa Rabin nonuwanta ta
saman rigarta ya d’auke idanunshi amman duk da haka say da yanayinsa ya d’an
canza nan da nan kwalkwaluwarsa ta shiga circulating ya dinga jin wani iri a
sansar jikinsa abinda bai ta’ba ji akanta ba kenan sai yau .”cike da natsuwa
tayi serving dinsa. bawani abinci kirki ya ci ba ,ya ture plate din gefe
'ahankali ya maida bayansa ya jingina da kujerar da yake zaune akai Tare da dan
zamowa kadan yana duban mami itama mami shi take kallo tana tabe baki “ba dai
har ka koshi ba ?”
ya dage mata girarsa daya alamun haka ne ,”yanzu duk yadda girkin nan yayi dadi ?
ya yatsina face dinsa kawai batare da ya cewa mami komai ba dan bai ji wani dadin
da yayi ba murya a sanyaye mrym tace” to ko na hado maka coffee ne?bai ce uhm ba
bare um uhm parlour ya dauki shr har kusan tsawon minti goma batare da ko tari
yayi ba , sai da mrym din ta km maimaitawa tmbyrta tukun muryarsa a dake yace “
please banason damuwa dan Allah“
“maryam je ki had’o masa zai sha tsabar jin kai ke damunsa jin haka yasa mrym din
mikewa 'ahankali tana jujjuya mazaunanta har ta nufi kitchen mami tace “adamcy
kalli can ya kai idanunshi inda ta muna masa bayan maryam ya hango ya waigo ya
kalli mami”sweetheart me hakan yake nufi kuma ?me nayi ?na nuna maka ne kaga irin
halitta dirin da allah yayi wa matarka ,mrym nada daidai nata kyau adamcy “takaicin
da ya tsaya masa a makwashi ne ya samu ya hadiye da kyar yana hango tahowarta da
yadda take motsa qirjinta saurin d’auke idanunshi yayi ya kamo lip's dinshi na
kasa yana cizawa da karfi har ta karaso ta’aje masa coffee a gabansa bai dana
cizan lip's dinshi ba,yana son shan coffe din amman yaki d’auka ya sha .”
Mami ta zuba masa ido tana kallonsa kafin ahankali ta d’auki cup din coffe ta
mika masa babu musu ya kar’ba ya fara sha yana lumshe ido mami ta cigaba da kallon
yadda yake shan coffe sak mahaifinsa kusan har ya so ya zarta tariq abdallah da
komai ya d’an dubi mami yace “ ya’akayi sweetheart ?ta hararesa tana cewa “ban
sani ba nan kafi kauri ga abinci ka zauna kaci yadda ya kamata aa sai ruwa
“tsam ya mike tsaye ya soma taku rike da cup “sweetheart ni zanje na kwanta bacci
nake ji tabi bayansa da kallo ,”to Allah ya tashemu lfy “daren ranar sam ATA kasa
runtsawa yayi kwana yayi yana juyi yana watsa jikinsa ruwa hannuwanshi yasa duka
ya dafe jijiyarsa dashi yana juyi da kyar ya samu ya runtsa sakamakon wani
irin feeling da ya dinga tasoma masa sai wuraren asuba bacci mai nauyi yayi nasarar
daukar shi.”washegari da sassafe ya bar gidan ya wuce office .”
zaune yake a office dinshi aiki yayi masa yayinda kanshi ke duke yana fama da
aiki rubuce rubuce dake gabansa yaji Knocking din kofa , kansa na duke ya bada
izinin shigowa batare daya dago kansa ba yaga ko waye ba ammar ne ya shigo cikin
office din da sallamarsa ATA ya amsa batare da ya dago kansa ba ya cigaba da
abinda yake" ganin haka Yasa ammar ya tsaya abakin window , yana kallon haraban
ma’akatan wanda ma’aikata ke kai kawo dan yasan tunda ya iske ATA kan aiki bazai
taba sauraransa ba matsawar bagamawa yayi ba dan sanin da yayi masa kenan na maida
hankalinsa matuka akan aiki idan yana yi .Kusan minti shabiyar yayi tsaye , sannan
ya soma takowa ahankali izuwa bakin makeken tablet din da ATA ke zaune ,yaja
kujera daya ya zauna yana dubansa, Sai lokacin ATA ya d’ago tsumammun idanunsa ya
dubeshi har ka gaji da tsayuwar kennan ?
“Ba dole nagaji ba dan naga alamun sai nakai ga zama tukun zakiyi lokacina ya
fad’a hk yana mikowa ATA hannu suka gaisa ,yaushe ka dawo qasar ? Dariya ammar
yayi yana cewa “shekaranjiya na dawo yau km nace nazo naganka ,ko bai yi bane ?
Wani irin farinciki ya lullube zuciyar ATA ya danyi murmushi har dimple dinsa ya
lotsa tsantsar kyawunsa ya sake bayyana ,yana son a dinga nuna masa kulawa da
soyayya ,ammar yace aboki lfy kuwa irin wannan farinciki haka ?”babu komai nima
haka na tsinci kaina ya jingina bayansa da kujerar da yake zaune yana jujjuyawa
dashi , ammar yace “ya mami da dolen dolalo ?sai da ATA ya yamutsa fuska sannan
yace “sweetheart tana lfy ita dayar ce dai gsky bansani ba ammar ya sake yin
dariya kace zaka qara aure har yanzu shiru ko ka canza shawara né zaka cigaba da
zama da dolen dolalo?
“Ammar kafa dawo kenan “ya fad’a yana jan tsaki “dan kaki bin shawarata ne wallahi
da kaga maryama zata maka yarinyar abar tausayi ce ga maraici ga rashi “bana jin
zan iya auran irinta koda zan yi aure ,kai ina ganin na hakura ma .ok zaka
cigaba da zama da mrym din kenan ? ya gyada masa kai kawai ,amman to why not ko
sau daya kaga maryama ni ina dalilina son ku had’u da juna “dan Allah ka rabani da
wannan shirmen ai tunda sunansu ma yazo d’aya da yarinyar nan naji na tsani had’uwa
daita ammar ya bud’e baki zai sake yin mgnr d’aya daga cikin wayoyinsa ya dauki
kara 'ahankali Yasa hannunsa ya janyo wayar maganar second biyu yayi ya sauke
wayar ammar na zaune yana kallonsa har yagama wayarsa , yana shawarar yadda zai
bullo masa yafi son ya ganta yana son yaga rud’ewar da zai yi akanta ,hira suka
cigaba dayi kafin daga bisani ammar yayi masa sallama ya wuce .”
Satin mami biyu ta soma tattara kayanta babu yadda maryam batayi ba akan tayi
zamanta tace aa “dan allah mami ki zauna banason ki tafi “aa maryam shiyasa nace
akawo miki masu aiki bakin kishinki ya hana tayi murmushi “kai mami wani kishi kuma
?aikin gidan bashi da wani yawa fa koma dai menen Ya rage naki ni dai tafiya zanyi
gobe .
da daddare da ATA ya dawo ta sheida masa “ in sha allahu gobe zata koma gida
“sweetheart kiyi zamanki mana “a’a bazan cigaba da zama ina ganin wulakacin ba
dan banga abinda zamana yake tsinana maka a gidan ba hassalima qaro sabon wulakanci
kayi lada ya isa haka idan ka ga dama ka duba allah kayi wa matarka adalci idan
kuma kaki zakaje ka had’u da allah né sai abu na gaba idan zaka zo qarshen wata
kazo min da maryam washgari ta kasance asabar da misalin karfe hud’u na yamma suka
rako mami haraban gidan inda ATA ya bud’e mta bayan mota ta shiga ta zauna maryam
ta zagaya dayan bangaren ta ajiye mta jakar kayanta mami ta dubi ATA “ka tabbatar
kazo qarshen wata sannna kazo da maryam "in sha allahu ya fad’a tare da rufe mata
murfin mota yana cewa direbanta ya jata Ahankali mami tayi warning din glass din
mota tace “bani wayarka !babu mutsu ya mika mta number mrym tasa masa tayi saving
number da sunanta “ga number mrym nan na saka maka ka dinga qoqarin sauke nauyin
dake kanka .”
Itama maryam tace mata “nasan kina da numbersa ki dinga kiran mijinki koda kuwa
bazai d’auka ba duk runtse ki sauke nauyin dake kanki allah ya had’a hankulanu tace
“Ameen tana daga mata hannu suna tsaye har mota data shiga da masu tsoron motar
suka bar gida sannan suka shiga ."bayan tafiyar mami da kamar awa d’aya ya sauko
sanye da wasu kaya ya ajiye wayoyinsa akan center table ya samu waje ya zauna ya
dauki remut ya kunna tv ya qara karfin ac ya daura kafafunsa akan center table
yana duban tashar labarai ahankali maryam ta fito daga dakinta cikin sand’a take
saukowa sakamakon yunwar da take ji dan tun abincin safe ne acikinta ko kallonta
bai yi ba ta shiga kitchen ita kuwa tayi haka né dan tasan yanzu sai wani ikon
allah tunda mai shiga tsakaninsu bata nan bata ki bin umarnin mami ba kullum tana
iyakar qoqarinta na kiransa kmr yadda mami tace wani lokacin ya dauka ya danqara
mata bakar magana wani lokacin kum bazai dauka ba ahaka har suka zo qarshen wata .”
******
Alhamdulillah DG m malik ya fara samun lafiya sai dai baya iya magana sosai idan
baka matso da kunnenka kusa da bakinsa ba bazakaji abinda yake fad’a ba ,haka
zalika sansar jikinsa ba koina yake iya sarrafawa ba yana kwance yayi wa
matarsa alamar ta d’auko wayarsa ,byn ta dauko ta tsaya kusa dashi kamar yadda
ta saba, ganin magana zai yi ta rankwafo daidai bakinsa anatse ya fara magana
sunan wanda ya ambata da abinda yake son tayi masa ne yasa ta soma rubuta text
message ta turawa ATA sakon ya samu ata alokacin da yake zaune a a gurin
shakawata a gidansa tare da yaronsa V.O ahmed ya d'auki wayarsa ya soma karanta
sako Kamar haka "Assalam, mai gida yaushe zaka shigo saboda ina da magana da
kai . ATA ya ajiye wayar cikin jin haushi yana kallon Ahmed "M Malik na yi maka
uzuri saboda tunaninka ya canza idan ba hk ba zakayi magana dani me yasa bazaka
fad'a min ba ko ta hanyar text message ne tunda zaka iya rubutu ya qarasa mgnr
tare da yin shiru "ranka ya dade wannan gsky ne DG m malik yana cikin wani hali sai
dai addua kawai "to allah ya bashi lafiya amman ni ko zan shiga wannan kasar ba
yanzu ba watakilla ma har su dawo qasar nan bazan samu damar shiga ba ya juya ya
kalli Musa. "musa Kai !"musa ya qaraso da sauri ya iso gaban ATA cike da ladabi
"dauki buhunhuna nan na Ahmed ka kai masa bayan motarsa "to yalla'bai!ya juya da
sauri suka cigaba da tautaunawa ."
"Gaskiya kema maryam da laifinki, taya zaayi ace har wata shida cikin na bakwai
da yin aure amma ki kasa shawo kan mijinki ku zauna lafiya bare har wani abu ya
shiga tsakaninku maryam ta girgiza kai tana cewa “ya kusanceni sau d’aya bayan
nan ne dai har yanzu shiru gashi nayi duk abinda zanyi dan mu zauna lafiya dashi
amman yaki bani lokacinsa "ki bude masa aiki kawai ko zama ko rabuwa maryam tayi
saurin zaro ido tana cewa "kai ni’ima bazan iya ba gskiya ai sai ma ya kasheni da
duka ."ni’ima diyar yayar mahaifiyar maryam ce da suke ciki daya aikin soja né ya
kawota lagos daga zuru “duka ?”Ke kuma sai ki tsaya ?”idan dai zai huce idan ya
dakeni sai na tsaya mana "to dama fa an fada min bakya son laifin mijinki,kowa yaga
wannan abun yasan mijinki baya sonki kuma bakya gabansa amman ke har wani side
dinsa kikeyi maryam ta zauna a kujera a sanyaye ko da yake " illar wani auren
zumuncin kenan “wallahi ni’ima ba side dinsa nake ba kawai soyayyarsa ce tayi min
yawa shiyasa nake hakurin zama dashi dan ko na bar gidan nan gangar jikina ne ya
bar gidansa amman ruhina yana gidan nan “.
“Ai kuwa kina da aiki ta yaya ma kike bashi kulawa muji idan akwai inda kuskure
yake ki gyara ?babu abinda banayi masa na kyautatawa duk ta zayyane mata amma duk
a banza ko kallona fa baya son yi “amman maryam kuma bakya tunanin ko wata ce
take dauke masa hankali a waje ? maryam ta girgiza mata kai tana cewa “bana
tunanin haka! dan miskilancinsa bazai bari ya kula mata ba abinda na fahimta kawai
shine, yaya Adam yana son wata yarinyar mafarkinsa amman azahiri bai san meye so ba
"ta yaya zaace mutum kamar wannan bai san meye so azahiri ba ?"To in ma dai ya
sani banga hakan a zahiri ba sai a mafarkinsa ya sani , amma ina fatan wata rana
ya dandani radadin so irin wanda nake dandana a zahiri ko hakan zai sa ya tausaya
mini ya bani kulawar data dace. " ina zai dandana tunda kince bai san meye so a
zahiri ba ?ni’ima ta fad'a sannan ta soma cin abincin da maryam ta kawo mata
maryam tayi shiru dan itama bata san mai zata sake cewa ba .”
ATA V.O d Ahmed duk suna inda suke zaune Ahmed ya russuna cikin fara'a yace
“nagode sosai sir ! Allah ya kara arziki yasa kafi haka.ATA bai ce uffan ba tunin
musa ya soma daukar buhuhunan ya nufi bayan motar ahmed ,atare ahmed da ata suka
mike suka biyo bayan musa ahmed ya shiga motarsa , masu gadi suka bude masa get
ya fita.ATA ya kalli kofar fitowa daga falo a tunaninsa zai iske mrym a wajen
tunda tasan fita zasuyi yau ya kalli agogon hannunsa ya d'an ja tsaki. “me wannan
yarinyar ta tsaya yi ne tana bata min lokaci ? ya sake jan tsaki yasa hannu a
ajihu ya ciro wayar sa ya soma kokarin kiran layinta ya saka a speaker ,wayar
maryam dake ajiye a kujera ta soma ringing.ni'ima dake cin abinci da maryam wadda
ke zaune a kujerar dake fuskantarta suka juyo suka kalli wayar ,maryam ta mike ta
karasa ta dauki wayar ta duba sannan ta kalli ni'ima cikin alamun tsoro "mijinki
ne ko? maryam ta gyada mata kai alamun"eh " Kar ki dauka, kyale shi ya karaci kira
har ya gaji cikin tsoro maryam tace "saboda me?”wallahi Ina mugu mugun jin tsoron
fad'ansa ke bai ma ta'ba kirana ba sai yau fa yau din ma nasan dan fitar da zamuyi
ne “ tana rufe bakinta kiran ya katse cikin jin haushi tace"wai ke baki da 'yanci
ne? bai ga kinyi bakuwa bane da zai dameki ? wallahi Ki rage jin tsoronsa
haka ,idan ba haha ba bazaki ta'ba yin martaba a idanunsa ba "haba ni'ima ya kike
irin wannan maganar bakiji nace miki fita zamuyi ba ? gidan mami zamu kuma Ko babu
aure a tsakanina da yaya Adam, dan uwa nane fa!"To sai me...?ta fad'a adaidai
lokacin da ATA ya shigo falon fuskar shi a daure yana kallon maryam a kaskance
"bakya ji ina kiran wayar ki ne .”?
Mmn sudais
💗💗💗💗💗💗
MAR'ADAMS
💖💖💖💖
💗💗💗💗💗💗
*AYSHA A BAGUDO*
WATTPAD @HAUESH
AREWABOOKS USERNAME
AYSHAABAGUDO
bismillahirrahmanirrahim
Wannan littafin na kuɗi ne mai buƙatar karantashi bayan na kammalashi zai biya
1000 ta wannan account number ɗin 1438775094 Aishat abdullahi access idan an tura
sai a turawa wannan Number 09136918331 alert domin tabbatar da an tura domin
sauraron littafaina a tuntuɓii chaneel ɗina (Hausa bakwai ) a YouTube.
Page 21
Shiru maryam tayi tamkar ba da ita yake magana ba, sai dai ta tsura masa idanunta
yayinda acikin zuciyarta tsoro ne daskare muryarsa a tsarƙe ya cigaba da magana.
“fito mu tafi karki ɓata min lokaci” jarumta ta aro ta sanyawa jikinta tana faɗin.
“kayi haƙuri kafin nayi picking ne kiran ya katse kuma kaga ai nayi baƙuwa bai
kamata na tafi in barta ba” ATA ya kalli Ni'ima dake zaune a wulaƙance sannan ya
kalli maryam. “Ke ban son iskanci ni zaki faɗawa kinyi baƙuwa ?ina ruwana da ita?”
yayi maganar a tsawace wanda yasa hantar cikinta kaɗawa nan da nan tsoro da
matsanancin firgici ya bayyana a gbdy ilahirin jikinta. “darajan sweetheart kikaci
if tace nazo mata dake kema Kinsan har abada bazan taɓa haɗa tafiyata dake ba”
yana gama faɗar haka ya juya da sauri ya fita daga parlour'n . “maryam ta dubi
Ni'ima cikin tsananin damuwa tace . “Kinga abinda nake gudu ko? gashi har yayi
fushin nashi zuciyarsa iya wuya ne kamar jira yake ya hau zubama mutun faɗa”
Ni'ima ta miƙe tsaye tanabin ƙofar daya fita da kallo sannan ta kalleta cikin
fushi. “wallahi maryam wannan mijin naki bai ɗaukeki da daraja ba, hatta komai ma
dake cikin gidan mai amfani da mara amfani ya fiki muhimmanci agurinsa” maryam
tayi shuru kawai tana kallon Ni'ima da sauraronta “wannan auren zumuncin da
akayi muku gsky ke aka cuta”
Maryam ta karkata kai tana cigaba da kallon Ni'ima “haka kike gani?ai kinfi kowa
sani wannan maimaci ne nayi miki amman kinsan ke aka cuta” “nifa ba cuceni ba
ni'ima dan ina son yaya adam tun asali in takaice miki tun kafin mahaifiyarsa tayi
tunanin haɗamu dan gsky da ban samesa ba da haƙurina zai gaza domin kuwa ciwon
zuciya ne zai kamani”
“ke da Allah rabani da maganar wata shegiyar soyayya uwarsa tasan duk wannan cin
kashin
da yake miki?” “tasan komai kuma tana iyakacin ƙoƙarinta, bata son duk wani abinda
zai ɗaga min hankali duk abinda yayi muddin zata gani ko taji labari sai inda
ƙarfinta ya ƙare” “dai-dai kenan idan ya ɗaga miki hankali ki dinga kirata ki
ɗaga mata hankali, idan kuma tsoronsa ya hanaki aikatawa sai ki zauna da baƙin
ciki” Ni'ima ta soma yafa gyalenta tana kallonta “zo mu jera sai mu rabu a titi”
maryam ta gyara zaman mayafinta ta ɗauki wayarta tare da sakala hand bag suka nufi
kofar fita daga parlour'n .
Mai gadi ya buɗe tafkeken get ɗin gidan motocin ATA suka nufo kofar a hankali
zasu fita a dai-dai lokacin maryam da Ni'ima suka fito daga parlour suka ga
motocinsa. “lah Ni'ima kinga bai tafi bama ashe, bari in tsaida shi basai naja mota
ba kema ki shiga mu rage miki hanya” ta nufi motar da sauri tana ɗaga masa hannu
“yaya Adam! Yaya Adam..!!” yana kallonta amman bai bada umarnin a tsaya ba
motocin a guje suka fice daga gidan ."maryam ta tsaya tana kallon Ni'ima mai gadi
ya rufe get din Ni'ima ta iso gaban maryam cikin fushi tana kallonta. “haba
maryam! akan me zakiyi irin wannan zaman rashin darajar kamar wata baiwa?wallahi in
baki ƙwaci ƴancinki ba ciwon zuciya ne zai kasheki a banza da wofi” cike da damuwa
Maryam tace.“To ni yanzu ya zanyi? babu abinda ban masa ba tun daga Kan tsafta
biyayya duk nayi kamar yadda na fad’a miki hatta taimako umma tasha aiko min
akansa amman duk a banza ko kallon arziki ban ishesa ba” “na baki shawara?” da
sauri maryam ta gyaɗa mata kai. “Kawo kunneki” maryam ta matso kusa daita sosai
tayi mata raɗa a kunne nan take maryam ta girgiza kai “ke kan wannan mutumin fa
baya jin komai gara kawai na cigaba da zama haka idan da rabon zai canza ina
fatan haka .”
Tare suka jero inda motar maryam take a parking space ni’ima na cewa “ki samu
lokaci ki shiga Zuru da kanki yarinyar wallahi sai yadda kikayi dashi duk wannan
taurin kan sai kin nema kin rasa “akwai wata tukunya da umma tace zaa aiko min daga
can , “eh nasan dashi ai zuwa wani sati zaa aiko zan sa a hado miki da wasu abubuwa
ma ,”ta fad’a adaidai lokacin da suka shiga mota suka bar gidan niima na cigaba da
magana “ai ina fad’a miki muddin kikayi masa amfani dashi zakiyi mamakin yadda zai
rikice ai wallahi sam ya’yan zuru basu cancaci wulakanci a gidan miji ba mu dake
juya maza son ranmu amman ace ke kin bigi a wulakance a gidan mini “wallahi ni’ima
ni kaina abun na damuna kamar na tattara na bar gidan amman bazan iya ba darajan
mami da kuma karfin soyayyarsa “masu aikin mami ne a sunkuye a gaban dinning suna
jere food flask.
Mami ta fito daga kitchen Riƙe da tray me ɗauke da lemuka a hannunta ta nufo dinnig
dasu.tabawa mai aikinta ta iso gabanta da sauri ta karɓa taje ta ajiye mami ta
ɗauki air-frshner ta soma feshe falon sannan ta ɗan tsaya alamun sauraro, ta juyo
ta kalli tabawa mai aikinta tabawa ta juyo ta kalleta sanda take ƙara gyara zaman
kujerun. “Tabawa!” “Na'am mami” “naji tsayuwar mota ina zaton adamcy ne suka iso ,
hanzarta ki bawa sauran masu aiki umarni su ƙarasa gyara wajen su bar nan tun
kafin ya ƙaraso”
ATA ya shigo cikin parlour'n da sallama mami ta amsa da “Amin wa'alaikas salam”
ATA ya iso gaban mami ya rusuna yana gaisheta “sweetheart barka da rana” cikin
sakin fuska mami tace. “barka da zuwa adamcy Nah ɗan albarka ya gida ya kuma ƙarfin
jikin?” “Alhamdulillah” Mami tace. “ka ganmu muna ta shirin tarbanku kamar wasu
baƙi ko?” ya miƙe yana kallon ɓangaren dining sannan ya zauna.
Yana cewa. “sweetheart da kanki kikayi komai?” “Ƙwarai kuwa, ni da tabawa muka
shirya muku abinci sai sauran masu aiki da suka taimaka ” ATA yayi shiru kawai suna
cikin magana suka jiyo sallamar zabiba ta karaɗe falon mami ta ɗago ta kalleta
tana cewa. “Zabiba har kin ƙaraso?” Zabiba tace. “Eh mami na ƙaraso suma suna
hanya yanzu muka gama waya dasu ina yini?” “lafiya lau zabiba ya yaran suke?”
“suna lafiya suna gida tare da babansu khaira ce ta maƙale wai lallai sai ta biyoni
taga hajiya mami nace ban zuwa daita tazo takurawa rayuwata” “ai wannan
takwarartawa sai ahankali last time da kuka zo ta dameni da aunty girl”. mami ta
faɗa cike da farinciki tana murmushi .”
muryar zabiba cike da tsoro tace. “yaya ina yini?” bai ce mata komai ba dan tunda
ta shigo ya maida fuskarsa wani ɓangare. Mami tace. “adamcy ana gaisheka” a
taƙaice yace. “Lafiya” ahankali ta samu waje kusa dashi ta zauna “yaya Adam!” yana
jinta yayi mata banza ahankali tace. “please yaya kayi hakuri ka yafe mana wallahi
bazamu sake ba” tsaki yaja yace. “ai daman haka kukeyi idan kuka ɓatawa mutun rai
kuyita nacin ban haƙuri kamar bazaku sake ba amman da zaran mutun ya haƙura ƙoƙarin
aikata wani kuke yi dan haka gara ku riƙe haƙurinku dan ni tuni na cireku a
rayuwata” nan da nan zabiba ta shiga aikin nan wato bashi hakuri da kuka amman ko
ajikinsa girgiza kafarsa ɗaya kawai yake zabiba kuwa kuka take kamar ranta zai fita
ahaka sauran ƴan'uwanta suka shigo suka isketa gabaɗayasu suka sakashi a tsakiyarsu
suna masa magana amma ko motsa laɓɓansa bai yi ba. “ku rabu dashi Ke kuma zabiba
ki daina asarar hawayenki kuna zaune zai huce” cewar Mami dogon numfashi ya sauke
yana taɓe baki.aransa yace “ai kuwa zan baku mamaki .”
Nana hauwa'u tace. “mami ina auntynmu take?” nan da nan mami ta kallesa sai
lokacin kanta ya kawo wuta “Ina Maryam ɗin da nace kazo min daita Ko tana cikin
mota ne?” ATA ya ɗan sosa ƙeya “na barota a gida a cewarta tayi baƙuwa” da
mamaki mami ta tsura masa ido “ka barota a gida adamcy acewarta tayi baƙuwa
kuma?”eh !haka tace idan ta gama zata taho don bazan iya zaman jiranta ba, kuma
wallahi sweetheart kiyi ma yarinyar congret warning dan kwanakin nan wasu ƴan iska
qawayenta take tara min a gida alhalin ni gidana ba dan ƴan iska na ginashi ba”
cikin fushi mami tace. “adamcy kasan me kake faɗa kuwa? Ƴar tawa da take aurenka
zaka cewa Ƴar iska tana tara ƴan iska ?” “ai sweetheart wannan yarinyar ta wuce ƴar
iska a gaban ita wanna Ƴar iska ƙawartata take ce min wa..” hannu mami ta ɗaga
masa cikin fushi ta fara magana. “saurara! bana son jin komai daga bakinka, ka
tashi yanzu ka koma gidan ka ɗaukota tun rai na bai gama ɓaci ba...” ATA ya gyara
zamansa cikin damuwa yana kallonta kafin ahankali ya motsa laɓɓansa “haba
sweetheart me yasa kike nuna mini wariyar launin fata a tsakanina da yarinyar nan ?
Ni fa kika haifa ba ita ba” cikin fushi tace.“dan kana ɗan cikina sai in goyi
bayan riƙon sakainar kashin da kake mata?” ATA yace. “To ai bata gama shiryawa bane
tana hira da Ƴar iskar ƙawarta”
“Yanzu ka tashi ka koma gidan ka jirata har sai ta gama kimtsawa idan ma sai ta
sallami ƙawarta ne ka jira sannan kuzo min tare yanda nace” mami bata kai ga rufe
bakinta ba Ni'ima da maryam suka shigo cikin falon Ni'ima na riƙe da Maryam a
kafaɗarta wanda goshinta yake a fashe yana ɗigar da jini, mayafinta da ɗankwalinta
yana a hannun Ni'ima nana hauwa'u ce ta fara lura dasu ta soma salati tare da
faɗin.“lnnalilahi wa'inna ilaihir raji'un!”jinj !
Nan mami da sauran ƴaƴanta suka juya da sauri suka kalli maryam “Subhanallahi!”
mami ta furta a ruɗe tana kallon ATA “Adamcy kaga abinda ka janyo ko? don me ka
barta a gida Kashe min ƴa zakayi?”Adamcy ya kalli mami a natse ya juya ya kalli
inda maryam take gbɗy ya kasa magana juwa ne ya ɗibi maryam ta sulale ƙasa a sume,
nana hauwa'u ta ƙarasa da gudu suka tallafo ta ita da Ni'ima
mami da ƴaƴanta suka nufi wajenta da sauri suna jijigata jikin mami na rawa tace.
“ku kwantar da ita akan kujera shahida taimaka ki duba min ita” duk mami ta ruɗe
shi kuwa gogan ko ajikinsa dan haka nan yaji ajikinsa suman ƙarya tayi.Mami banzo
da kayan aiki na ba, a kira doctor nasir” da sauri mami tace. “Auta maza shiga
ɗakina ki ɗauko min wayata” da sauri nana hauwa'u ta nufi ɗakin mami ta ɗauko wayar
tana niman layinsa yayinda aunty shahida ke bata taimakon gaugauwa shi kuwa ATA
mikewa tsaye yayi yana jan tsaki ya ra’ba ta gefensu ya fice yama bar gidan gbdy .”
Maryam na zaune a kujera tana sauke numfashi ansa auduga da plasta an rufe raunin
goshinta yayinda mami ke zaune a gefenta riƙe da hannunta Dr.Nasir Ya miƙe tsaye
sanye da coat da farin gilashi hannunsa riƙe da first-aid box ya miƙawa mami
Ƙaramar takardan magunguna “hajiya ga wannan takardar magungunan da zatayi amfani
dashi ne insha Allah da zarar tasha a hankali ƙarfin jikinta zai dawo baboda naga
Allah ya taƙaita babu wani babban rauni da zai sa muyi admitting ɗinta asibiti ko
kuma yiwa cikin jikinta illa Wannan treating ɗin ma da nayi mata is okay for her”
mami ta jinjina kai tana faɗaɗa fuska cikin farinciki tace. “doctor kace ciki
gareta?” Doctor Nasir yace. “ƙwarai kuwa hajiya in sha allahu ranar monday akawota
hospital domin yi mata scan dan mu san iya adadin kwanakinsa” “masha Allah
Dr.Nasir nagode sosai ka min albishiri mai daɗi” na dade ba’a fada min maganar data
saka zuciyata farinciki ba dr nasir ya kalli maryam da murmushi a fuskarsa “to
hajiya Mar-Adam zance ko Mrs Adam? Allah ya bada lafiya” maryam tayi murmushin
ƙarfin hali tana kallonsa zuciyarta na rawa dan tun daya fara maganar ciki ta
shiga damuwa mai tsananin dan ita kanta tana zargin ciki gareta duba da watan ta na
uku kenan bata ga period ɗinta ba. “Allah ya sauwaƙe ya bada lafiya” da “Amin” ta
amsa cikin ƙarfin hali.
Dr.Nasir Ya juya ya fita daga gidan farinciki agurin mami da ƴaƴanta ba'a magana
kowa ka kalli fuskarsa kwance yake da annurin farinciki gabaɗayansu murna suke har
sun kasa ɓoye murnarsu mami ta riƙo hannun maryam cikin nata tana kallonta cike da
kulawa tace “ke kuwa Maryam garin ya akayi kika samu rauni?” maraym tace. “walalhi
mami muna qoqarin karya kwana ne akayi akasi wani me mashin ya kwaso a guje,
ganin kamar zai yo kan motar ne sai ido na ya rufe daga hk ni dai bansan yadda
akayi ba kaina ya bugu da stearing” mami tace. “yanzu banda Allah ya taƙaita ai da
abun ya wuce haka ga ciki ajikinki” .nana hauwa'u tace. “Alhamdulillah da Allah ya
taƙaita” cike da murna ta ƙarasa maganar. “ai duk adamcy ne ya janyo da yanzu wani
abu ya samu cikin jikinta me za'ace?” nan da nan mami ta shiga zuba wa Adam faɗa
da baya nan akan me yasa bai jira Maryam ta gama shiryawa sun fito tare ba? cikin
raunin murya “daman ai duk shi yaja mana wannan matsalar, wallahi mami in kinga
abubuwan da yayi mata agabana sai kin tausaya mata” cewar ni'ima “kamar wata
baiwa ya ajiye a gidansa ba matarsa ba” mami ta tsurawa Ni'ima ido tana kallon
fuskarta kar dai itace Ƴar iskar ƙawarta da yake faɗa? “ko abinci ta girka sai yaga
dama yake ci, komai tayi bata masa gwaninta, sai yayi tayi mata tsawa yana
hantarar ta wannan wani irin aure ne?” mrym tayi saurin take ƙafar Ni'ima “kinga
malama ki bari ayi magana yanzu an daina auren wahala idan bazai iya ba ya sallame
ki, ki kama gabanki idan kin haife abinda yake cikinki ki kawo masa ki dire ai
namiji goma ba uba goma bane " Hjy zulai da mamaki take cigaba da kallon Ni'ima
tana tunanin in da tasan fuskar “haba Ni'ima wai meye haka ne ?dan Allah kizo ki
wuce gida dan Allah nace miki ina son rabuwa da mijina ne? koni na faɗa miki yana
min duk abinda kika furta “au karesa zakiyi saboda baki da hankali ai duk abinda
idanuna suka gane min kamar na faɗawa ummah na gama” tana gama faɗar haka ta juya
cikin tsananin fushi.”
Cike da ɓacin rai nana hauwa'u tace. “sister wannan fa wacece ita? Jiki a sanyaye ”
Maryam tace. “ɗiyar sister ɗin ummammu ce “kai shiyasa nake ta mata kallon sani kar
dai ɗiyar umaima ce?” Maryam ta gyaɗa mata kai alamun eh. “shine zata dinga faɗar
magana akan yaya? kuma ai kice kika bata wannan damar” “kamar ya sister?” maryam
ta faɗa jikinta na ɗan rawa “idan baki faɗa mata komai akanshi ba ya'akayi tasan
irin zaman da kuke yi?” aunty shahida ta faɗa ranta a ɓace “karfa kiga duk muna
bayanki ki ɗauka bama son shi ne, adam rayuwarmu ne kema kuma kinsan da haka
Maryam ta runtse idanunta sai ga hawaye masu zafi cike da tashin hankali take jin
yadda numfashinta ke sauka da ƙarfi. shi kenan Ni'ima ta haɗa mata bala'i “duk
muna bayanki sakamakon irin tsanar da yake nuna miki da kuma irin ƙaunar da
mahaifiyarmu ke miki” “ dan Allah aunty shahida kuyi hakuri ba'a bakina taji komai
ba ummace ta faɗa amman..” katseta aunty khadija tayi ta hanyar cewa. “ita umman
taki meye amfanin faɗawa mutane? mun sani sarai adam bai kyautawa amman kuma meye
abun faɗawa mutane anan? mufa mun sani sarai ummanki bata ƙaunar danuwanmu, amman
mu dai-dai rana ɗaya mun taɓa sauke haushin haka akanki ? kullum yanda rayuwarki
zata samu cigaba a gidansa muke" .
Maryam tasa kuka cikin tsananin damuwa .”
“dan Allah ya isa karku saka min yarinya gaba da bala'i dame zataji ?da maseefar
ɗan'uwanku ko da naku sai kun harbe mata zuciya ta mutu kowa ya huta ? kuma ai bai
barku ba bare ku shigar masa” kuma karya aka fada akanshi ?halinsa ne fa ?“koma dai
menene mami bazamu lamunta ba kuma kar mu sake jin taje gidanki daman shima yace
ayiwa ƴar iskar ƙawarki congrent warning karta sake shigar masa gida ilai kuwa
ashe ƴar iskar ce ai duk abinda kika ji yaya yayi mgn akai mai mahimanci ne”
cewar zabiba nana hauwa'u kam tun maganar farko bata sake cewa komai ba, atare suka
miƙe aunty shahida aunty Khadija da zabiba sukai ma mami sallama tayi masu addu'a
tare da yi masu fatan alkhairi nana hauwa'u bata sake cewa komai ba mami ta
laluɓo wayarta daga gefenta ta ɗauka ta soma ƙoƙarin kiran ATA “Bari ina zuwa na
kirasa dani yake zancen wato cin mutunci da tozarci har agaban mutane?" maraym
tayi saurin riko hannun mami tana kuka tace. “dan Allah mami ki rufa min asiri kar
kiyi masa magana yanzu idan ma son samu ne karki ce masa komai” mami ta ƙara wayar
a kunnenta tana cewa. “rabu dani gara na faɗa masa halin da'ake ciki tun kafin
baƙin cikinsa yasa a rasa cikin jikinki .”
alokacin da mami take neman layinsa yana zaune acikin wani ƙayataccen gida me
ɗauke da komai na manyan masu kuɗi da manyan ƴan boko gidan kamar aljanar duniya
tsabar haɗuwa wannan gidan bana kowa bane face gidan ammar ATA na zaune a gaban
ammar suna tautaunawa akan kasuwanci kiran mami ya shigo ya ɗauki wayar ya manna a
kunne “hello kana ina?“ina gidan ammar” abinda ya faɗa kenan yana lumshe ido “to in
ka fito kazo gida da gaggawa ina son ganinka” katse ta yayi da faɗin. “lafiya
sweetheart?” Mami tace. “ita ta kawo haka bazaka ma tambayi Jikin maryam ba kaji
halin da take ciki? ka bar ƴar mutane cikin wani hali gashi..” tun kafin ta faɗi
abinda take son faɗa taji ya katse wayar “Hello.. Hello... adamcy” tuni ya
sauke wayar daga kunnensa ya kalli screen ɗin sannan ya sauya kujerar sa yana dafe
goshinsa da hannuwansa duka ammar ya dawo gabansa ya fuskancesa yan faɗin.
“lafiya ?waya kiraka ?ya ɗaga maka hankali gashi bamu gama tattaunawarmu ba?”
“sweetheart ce ni dai allah yasa karsu kashe ni akan ƴar iskar yarinyar nan..”
“yanzu me ya faru kuma?” “ban sani ba ni dai na barsu wai ta suma” “wa kenan ta
suma?” shiru yayi na second biyu sannan ya ɗago kanshi ya kalli ammar “Sweetheart
ke son ganina amma zamu iya ƙarasa maganar Okay, Sai dai kuma ya kamata a ce ka
ɗau tsanttsauran mataki akan sauran yaran daka faɗa min saboda har kullum shi
kasuwanci tattalinsa ake. bana son kabar wata kofa da wasu zasu samu damar janyo
mana asara dan bazan ɗauki asarar ganganci ba” “shikenan zan haɗa taron gaugauwa
ranar monday zan yiwa P.A ɗina magana, zamu san abin yi kafin matsalar tayi nisa”
ATA ya jinjina kai sannan ya buɗe wani file ya duba bayan ya gama dubawa ya miƙe
“ni zan wuce” ammar ya jinjina masa kai a sanyaye atare suka fito .”
Can ɓangaren maryam kuwa kuka take sosai abun ya haɗe mata tana kallon nana hauwa'u
ta miƙe ta yafa mayafinta tana yiwa Mami sallama “kema wucewa zakiyi ?” “eh Mami
yaya hisham yana jirana” “to ai Shi kenan Allah ya tsare hanya” mami ta fada ranta
a dagule saboda ganin ya’yanta sun hadewa mrym kai ,nana hauwa’u bata kalli in da
maryam take ba ta nufi ƙofar fita, takun maryam taji abayanta tana magana cike da
raunin maryam tace. “sister kema fushi zaki yi dani bayan kinsan kece ƙarfin
gwaiwata” juyowa tayi ido cikin ido suke kallon juna “kiyi haƙuri sister nayi
kuskure” nana hauwa'u tayi murmushi tana kallon cikin idanunta “shi kenan komai ya
wuce Allah ya inganta mana babynmu” jiki a sanyaye sukai sallama tana jin kamar
zata rasa rayuwarta ne dan gbɗy jin tana ɗauke da cikinsa bai saka zuciyarta samun
natsuwar ɗari bisa ɗari ba ta dawo kusa da Mami ta zauna “ki rabu dasu karki wani
ɗaga hankalinki akan ɗan wannna abun” Maryam tace. “allah Mami hankalina a tashe
yake su aunty shahida sunyi fushi dani” “zan kirasu babu abinda zai faru ni dai
fatana ki kwnatar da hanaklinki kar wani abu ya samu cikin jiknki”
Numfashi ta sauke sannna tace. “Mami dan allah karki faɗawa yaya batun cikin nan
tukun Kinsan halinsa” Mani tace. “kai babu abinda zai yi sai farinciki aj wannna
cikin sai ya kawo miki sauy arayuwarki Maryam tace. “ walalhi yadda yaya baya sona
bana tunanin zai so abinda nake dauke dashi Shiru mami tayi tana sauraronta “ai
kuwa da Adamcy bai kyauta mata ba idan yaki abinda mrym take dauke dashi “ko kuma
za'a iya ƙin fad'a masa har ya gano da kanshi” kai kawai mami ta gyda mata
ahankali mami ta dinga janta da hira sai dai jikin Maryam a mace yake kana kallonta
zaka fahimci hakan.
A galabaice ya shigo parlour'n mami ya zauna tare da runtse idanunshi gam mami dake
zaune ta tsura masa ido ruwan bala'i take son sauke masa amman yanayin yanda ya
shigo yasa tayi tunanin kar ta masa faɗan sai tasa aka kawo masa abinci buɗe
idanunshi yayi ahankali yace. “gani sweetheart ina son na wuce gida na kwanta na
huta” mami tace. “kaci abincin da akawo maka tukun sai muyi magana” kaɗan yaci
abincin sannan ya tsurawa mami ido yana son yaji kiran me take masa suna zaune sai
ga maryam ta fito daga ɗakin mami jiki a sanyaye ta zauna kusa daita wani mugun
ɓata rai yayi “Adamcy!” mami ta kira sunansa ya ɗan kalleta tare da faɗin. “ina
jinki sweetheart” mami tace. “me yasa kaci zarafin Maryam a gaban ƴaru'warta?”
baƙaramin fusata yayi ba shi kam bai san randa mahaifiyarsa zata barshi ya huta da
maganar yarinyar nan ba “amma ajiye wannan maganar ma tukun, ka fita ka bar matarka
cikin wani hali baka kira kaji a wani hali take ciki ba bare ka mata sannu da jiki”
daga haka ya miƙe ya fice daga parlour'n dan bazai zauna ya cigaba da jin magana
akanta ba “maza tashi ki bishi kuje zan zo wani sati sai na daukeki muje scan din
“to mami na gode allah ya qara girma “Allah ya tsare da ɗan saurinta ta ɗauki
mayafinta ta fito alokacin tuni ya shiga mota ta zagaya da sauri ta bude bangaren
da yake ta shiga ta zauna suka wuce gida ."
Bayan kwana biyu da misalin ƙarfe goma kiran Ni'ima ya shigo wayarta tana kallo
kiran na shigowa taƙi ɗauka sai a karo na biyar ne ta ɗaga tana ɗauka tace “lafiya
Ni'ima kiran me kike min bayan kin kusan jefa rayuwata cikin uku bala'i ? babu
ruwanki da duk halin da nake ciki zan gargaɗeki da babban murya karki sake zuwa
mijina yace baya son ganinki a gidansa idan kuma kinyi taurin kai zaki gane ke
ƙaramar mara mutunci ce” shiru tayi tana sauraron Ni'ima “ni dai nace karki shigo
tunda kince saƙo ne daga umman zuru ki tsaya a wajen get idan kinzo zan fito na
karɓa amman karki zo ” washegari kuwa da misalin karfe bakwai Ni'ima ta kirata ta
fita cikin sanɗa kasamcewar ranar tun safe ATA na gida bai je koina ba wanda
alamunsa Ke nuna tafiya zai yi taje ta karɓo saƙon umma zuru irin tukunyar farko da
aka aiko mata dashi ne. cikin sauri ta shige ɗakinta dashi ta fito parlour'n ta
zauna , tana zaune ATA ya shigo ya haye sama bayan Kamar mintuna talatin ya sauko
yana fita, ta miƙe da sauri ta haye sama kamar a mafarki taga kofar ɗakinsa a buɗee
wani kyakkyawan murmushi tayi da sauri ta faɗa ɗakinta ta ɗauko tukunyar ta dawo
ɗakinsa ta tsaya tare da buɗe tukunyar tsafi ta soma ambatar sunanshi da abinda
take son yayi mata kamar yadda aka fad’a mata bayan ta gama ta ajiye tukunyar ta
ɗaga katifa ta ajiye a gefe, ta ɗauko tukunya zata saka taji taku tare da tafi daga
bayanta ai da wani mugun sauri ta juyo ganinsa tsaye yasa ta saki tukunyar aiko
nan take ta fashe sai ga wani mummunar hayaƙi ya shiga fitowa daga ciki .
Cikin zare ido yace “Meye wannan?” tambayar daya jefa mata kenan bakinta da jikinta
ya kama rawa “kina son kashe ni saboda bana sonki ko?" Girgiza masa kai tayi tare
da faɗi. “a'a ba kashe ka zanyi ba.." cikin daka tsawa yace. “shut up with your
dirty mouth! you want kill me?” zatayi magana ya sake buga mata tsawa “shut up how
dare you enter my room kuma riƙe da tukunyar tsafi?” nan da nan jikinta ya kama
rawa “daman naji ajikina kina son kasheni” sake girgiza masa kai tayi jikinta na
wani irin rawa “why you this girl ?me nayi miki da zaki kashe ni ? duk da bana
sonki duk da yanda nake ji araina kamar na kashe ki na sha faɗa miki ni ne ajalinki
amman na taɓa ƙoƙarin kashe ki?” jikinta na rawa ta girgiza masa kai “why you want
to kill me ?” cikin rawan murya tace. “Wallahi ba kashe ka zanyi ba, ka fahimceni
wallahi ba wata illa zan yiwa rayuwarka ba kawai dai..” sai kuma tayi shiru ta kasa
ƙarasa maganarta “baki da abinda zaki iya kare kanki kije na sakeki saki ɗaya " .
mutuwar tsaye tayi cikin tsananin tashin hankali da matsanancin gigita jin
furucinsa, yayinda hawayen idanunta ya ƙaru suka shiga kokuwa da juna gurin
silalowa ga wani irin ƙyarma da jikinta ke yi, sai dai rawar da jikinta ke yi
ya sanyata saurin durƙusawa a gabansa domin ƙafafunta sun tabbatar mata bazasu
iya cigaba da ɗaukar gangar jikinta ba, baya ga haka ma ga wani iri jirin
tashin hankali dake ɗawainiya da ita .Wani irin bugawa kanta ke yi tamkar zai
rabe gida goma , cikin wani matsanancin rashin Hankali muryanta na rawa tace. “da
gaske ka sakeni yaya adam? dan Allah ka janye sakin zan maka bayanin komai domin
idan kana tunanin zan...” dakatar da ita yayi ta hanyar faɗin. “shiiii na sake
ki kuma babu wanda ya isa ya sake takurani nayi rayuwa dake, dan haka ba abinda
ya rage miki a gidana gari ya waye ki bar min gidans kuma bance kije gidan
mahaifiyata ba, ki wuce gidanku gidan ubanki tunda ke ɗin ba shegiya bace” shiru
kawai tayi tana dubansa cikin tsananin faɗuwar gaba domin dai a kallon da take
masa ta rigada tasan bazai taɓa daina tsananta ba a cikin zuciyarsa” maganar
sa ne ya katse mata tunaninta. “bazan taɓa daina tsanarki ba, abinda kika kasa
ganewa shi so halitta ne..” cikin matsanancin kuka ta dakatar dashi da faɗin.
“yanda yake halitta nima haka nake ji akanka me yasa zaka rabu da zuciyar da
batasan sanda ta fara sonka ba ?sonka shine mafarin kasancewata a karkashin
mahafi....” cikin daka tsawa yace. “bar ɗakin nan stupid! tun kafin nayi
losing control , dan ina jin baƙin cikin kasancewata dake ahalin yanzu yayi
maganar a zuciye cikin tsananin fushi da tashin hankali mara misaltuwa.”
bata bar ɗakin ba kamar yanda ya furta sai rarrafawa tayi ta koma gefen
doguwar kujerar kushin ƙwaya ɗaya dake ɗakin ta rakuɓe , tana kallonsa ya
miƙe ya shiga bayi batare daya cire kayan jikinsa ba saukar ruwa a bayin
yasa ta fahimci wanka yake a hankali ta rike gefen kanta dake sara tana
haɗeye wani ƙululun baƙin ciki tare da share hawayen dake tsiyoyo mata, ta
tattara tukunyar tsafin ta kai dakinta ta ajiye ta dawo ɗakinsa ta zauna dan babu
in da zata aurenta dashi mutu ka raba ya saketa amman bata saku ba dan tayi imani
mami naji zata maidaita."Da mamaki ya fito ya isketa kallon mamaki da naci irin
nata yake “zaman me kikewa mutane a d’aki ?” ya faɗa Yana kallonta “babu fa inda
zani har sai ka maidani ” wani mugun kallo yayi mata sannan ya ɗauki jug din coffee
da zafinsa wanda ta kawo masa bai sha ba ya dawo inda take ya juye mata tsab a
jikinta wata razananniyar ƙara ta saka da sauri ta shiga kakkaɓe rigar dake
jikinta , cikin faɗa wanda bai hana zazzaƙar muryarsa fitowa ba yace. “banace ki
bar min ɗakina ba ?” Ya faɗa yana ware mata idanunsa dake cike da bala'i jikinta
na rawa sosai ga kuma zafin coffee da yake ratsa illahirin fatar jikinta wanda har
cikin naman jikinta take jin zafin, babu shiri ta bar masa ɗaki zuwa nata tana
zubar da hawaye .”
ranar Maryam bata runtsa ba kuma tayi dauriya domin dai bata kira kowa acikin
ahlinsa ba washe gari kuwa tun da asuba tabi mota zuwa abuja taso shiga jirgi
amma saboda bata da kuɗin jirgi kamar ta tambayi mami kuɗin ticket amma tasan
hakan zai sa ta gane akwai matsala shiyasa ta shiga motar haya
Tunda suka ɗau hanya kanta na kife ,rufe ido tayi sosai tana zubar da hawaye
masu zafi sannan acikin ranta tana ƙissima yanda zata hana rayuwar adam samun
kwanciyar hankali yadda bata ji dadi agidansa ba bazata bari Ya kawo wata yaji
dadin rayuwarsa daita yadda gallazawa rayuwarta wallahi tayi alqawarin sai ya
gallazawa duk wacce ta rabesa zatayi komai akan yanke masa duk wani jin dadin
rayuwa .” ɓangaren ATA shima tana barin gidan ya bar ƙasar zuwa hollond .”
Mmn sudais
💗💗💗💗💗💗
MAR'ADAMS
💖💖💖💖
💗💗💗💗💗💗
*AYSHA A BAGUDO*
WATTPAD @HAUESH
AREWABOOKS USERNAME
AYSHAABAGUDO
bismillahirrahmanirrahim
Wannan littafin na kudi ne mai bukatar karantashi byn na kammalashi zai biya
1000 ta wannan account number din 1438775094 Aishat abdullahi access idan an tura
sai a turawa wannan 09136918331 alert domin tabbatar da an tura domin sauraron
littafaina a tuntubi chaneel dina (Hausa bakwai ) a YouTube.
Page 22
Kwanaki hamsin kenan da ATA yasa anemo masa kwararrun masu zane wanda yayi daidai
da sauran sati uku daurin auren maryama da yaya sadam acikin lokacin nan babu
abinda maryama take sai zariyar zuwa AGC domin gabatar da zanenta, haka zalika ta
saki jikinta sosai da yaya sadam domin ta fara cire rashin son da bata masa tana
ta qoqarin dasa soyayyarsa mai karfi acikin zuciyarta ,shima kuma bangarensa yana
qoqarin kyautata mata shiyasa a yanzu damuwarta ad’auketa aiki akar ka shin AGC
ne .” idan kaga maryama da yaya sadam a yanzu zaka d’auka tun asali masoya ne
wadan da suka d’auki tsawon lokaci suna son juna, abu d’aya ne kawai dai har yanzu
yake damun zuciyar maryama shine yawon shiru da shiga tunani mai zurfi da yaya
sadam din yake ko suna tare ko yana shi kad’ai ko ayita kiransa a waya baya
d’auka agabanta wanda ita hakan na damunta, kuma haka nan take ji ajikinta kamar
akwai wani abu dake damunsa wanda yake boye mata , tayi iyakar qoqarinta tasan meye
damuwarsa amman abun ya cutura domin dai abu d’aya ne kullum yake fad’a mata babu
komai al’amuran aiki ne .”
mami na zaune a had’ad’den parlour’nta na farko idanunta na kallon tv yayinda
hannunta Ke rike da casbaha tana ja ahankali kira ya shigo wayarta, tasa hannu ta
d’auki wayarta tana dubawa sunan d’anuwanta data gani yana yawo a screen din wayar
ne yasa tayi saurin kara wayar a kunneta bakinta d’auke da sallama “wani irin
mikewa mami tayi jikinta na rawa tare da furta kalma “inna lillahi wa inna ilaihi
rajiun ,ya hayyu ya qayyum bi rahmatika astagisu aslili shaani kulluhu wala takilni
ila nafsin d’urfata’ai “kace yau kwana biyu kenan da faruwar sakin ?ta tambayesa
cikin tsananin damuwa da shiga tashin hankali “yayinda cikin tsananin fushi d’an
uwanta ya cigaba da sheida mata abinda ya faru .”“wallahi Abdul ban san komai akan
sakin nan ba”
ta fad’a jikinta na wani irin ‘bari haka ma zuciyarta
bayan ya katse kiran kuka mami tasa tare da jin wani kullin bakinciki ya tsaya
mata a qirji yaki gaba yaki baya wayarta ta lalubo ta soma neman layukansa amman
shiru bata shiga dan haka ta kira Amar nan ta samu labarin tafiya yayi zuwa hollond
abun yayi mata ciwo fiyye da tunanin mai karatu ammar din ma yana tambayarta ko
tana son wani abu amman tuni ta katse kiran .”
batayi sanya a gwiwa ba ta kira ya’yanta a waya ai kuwa washegari gabdayansu suka
hallara a gidan cikin tsananin tashin hankali aiko mami tasa masu kuka tana kiran
“adamcy zai kasheni shikenan ya zama sila shiga tsakanina da d’anuwana muna
zamanmu gwanin sha’awa, kana ganinmu kasan akwai shakuwa da soyayya a tskaninmu,
muna ta qoqarin had’a kanmu dana ahlimu, mun rungume juna babu kyarma muna tsananin
son juna amman yau sanadiyar adamcy ran d’anuwana ya sosu yayi min abinda bai
ta’ba min ba .Abdul ra’uf bai ta’ba min magana cikin fushi ko ‘bacin rai ba sai a
jiya “ni zulai na shiga uku nah me yasa na had’a auren nan ?”wallahi dana san
abinda zai biyo baya kenan da ban had’a ba dana bar adamcy ya cigaba da rayuwarsa
haka babu aure dan duk abinda zai lalata zumuncina da yan’uwana bana qaunarsa”.”
“kiyi hakuri mami ki daina kuka haka Allah ya qaddara kowani bawa da kalar
qaddararsa wannna rabon dake tsakaninsu fa idan baa yi auren ba ta ina zaa samu ?
inji cewar aunty shahida ,”kuka fa ya zamammin dole abdul’rauf na min biyayya duk
abinda nace shi yake yi bai ta’ba sa’bawa umarnina ba "wai mami zaginki yayi ne ko
me ?zabiba ta tambayeta “ko d’aya zabiba abdul bazai ta’ba zagina ba amman yayi
min magana cikin fushi abinda bai ta’ba min ba sai jiya” nifa na kasa gane abubuwan
nan na yaya adam mutun kamar babu tausayi a cikin zuciyarsa gsky mami yakamata
ki san yadda za'ayi da yaya ga ciki ga saki dame sister zataji wallahi ni
tausayi take ba ya dawo daita kawai .”nana hauwa’u ta qarasa mgnr tana sheshekan
kuka aunty shahida ta numfasa kana tace “karki d’aga hankalinki auta kinga kema
bake kad’ai bace za'a haukatar dashi bari ya dawo daga hollond lafiya amman dan
dolensa ya maidaita ta haihu a gidansa idan ba haka ba wallahi wannan karon zai
had’u da tashin hankali da bai ta’ba gani ba “ku dai bi komai a hankali domin dai
acikinku babu wanda bai san waye yaya adam ba kusan yafi buqatar rarrashi da
lalama muddin da tashin hankali zakuje masa wallahi bazai maku abinda kuke so ba .”
“da mamaki aunty khadija ta kalleta “abinda muke so kuma ke banda ke ?”gsky banda
ni abinda kuke so am sorry to say dani yanzu bazan sake goyawa zaman aurensu
baya ba ,ya kamata zuwa yanzu abarsu haka kada a takura masa ku kyalesa ya huta
idan yayi ra’ayin maidaita da kanshi zai yi idan kuma iyakar zamansu kenan Allah
yasa ya zama alkhairi ,sun d’auki lokaci suna tautaunawa a tsakaninsu sai dai
zabiba ta tsaya akan raayinta wanda bai yi masu ba har mami .”
Bayan kwana uku ahankali oga ATA yake saukowa daga cikin jirki tare da yaransa mutu
biyu kai tsaye in da driver da masu tsaronsa ke jiranshi suka nufa, ya qara kyau
aciki kwanaki uku kacal farinsa ya sake fitowa ga cigaba da ya samu da nasarori
akan business ,yana sanye da royal blue three piece suit daya daga cikin yarasa
na sak'ale da bak'ar jakarsa daka ganshi kaga wayayye wanda yasan duniya ko nace
duniya ke damawa dashi, yayinda idan ka kalleshi zaka d'auka d'an shekara talatin
da biyar ne amma gaskiyar lamari shekararsa arba'in da wani abu yake, da sauri aka
bude masa gidan baya ya shiga ya kame yana shan kamshi daya daga cikin wayoyin ne
ta soma ringin ya dauka ya soma magana a natse yana ciccin magani har suka qaraso
unguwarsu waya yake bai ji komai ajikinsa ba sai da suka shiga cikin haraban
estate dinsu yaji gabanshi ya fad'i sakamakon bai san abinda zai tarar ba amman a
kudurtawa ransa komai zai faru sai dai ya faru amman har abada bazai qara zama da
mrym ba".
ahankali ya fito daga cikin motar ya nufi babban falon cikin isa da iza ga
kamshin daddan turarensa Reed na tashi ,yasa hannu ya tura kofar glass din
parlour’n ya shiga ya iske mami zaune kamar koda yaushe yayi sallama aciki fuskarsa
a had’e tamkar zaki , itama aciki ta amsa masa ya ta’be baki yadda ta amsa masa
yaso ya bashi dry amman sai ya maze ya d’age girarsa duka tare da dakewa ya
gaisheta “sweetheart barka da rana “wannan karon kam shiru tayi bata masa ba bai
qara cewa komai ba kai tsaye samansa ya nufa mami ta karkace tabi bayansa da kallo
yana taku d’ay d’ay batare da wata damuwa ko tashin hankali ba sai ma wani kyau da
kwanciyar hankali daya samu matsuguni ajikinsa su kuma ya bar zuciyarsu da tashin
hankali.duk wani tarba da rawar jiki da mami take akanshi idan ta gansa yau kam
babu dan kana kallon fuskarta zaka fahimci akwai damuwa .”yadda mami bata masa
maganar wata maryam ba shima bai yi mata maganar ba abun ma yayi masa dadi ya
cigaba da tsabgogin gabansa da mulkinsa daya saba dan babu abinda ya canja har
kawo yanzu dan ji yayi kamar an raba zuciyarsa da matsala ne dan da kullum
zuciyarsa cikin tuttukin bakinciki da kunci take idan ya tuna zai koma gida ya ga
fuskarta kuma amatsayin matarsa .”
mami dai bata gaji ba ta sake tara ya’yanta “har yanzu shiru adamcy bai ce min
komai ba ga mrym da ciki har wata uku akace dame zataji saboda Allah ga ciki ga
kuma gurb'ata mata raywua da yayi, gashi ya dawo yayi wa mutane shiru kamar bashi
yayi sakin ba , ni na gaji wallahi nayi waya daita mrym din ta fad’a min abinda ya
faru akayi sakin taki sai kuka take min ,shi kuma ya dawo ya min dif wallahi na
kasa komai gashi bana son lokaci ya tafi batare data koma dakinta ba dan da
zarar mrym ta haihu a gidansu shikenan abu ya sake dawowa baya bazai ta’ba
maidaita ba mami ta fad'a tana kallon ya’yanta d’aya byn d’aya da suke zaune.aunty
khadija tace "kwantar da hankalin ki mami zamu san abun yi bubuwa daya ne kawai ya
tabbata a aurensu samun cikin mrym in sha allahu sauran ma zasu tabbata ne"Yaushe?
Kusan shekaru ana abu d'aya ace har yanzu an kasa cimma komai babu wanda adam
yake shaka daga mami har mu na gaba dashi kowa shakkarsa yake gsky zuwa yanzu dai
ya kamata mu tashi tsaye .”inji cewar aunty shahida .”
kallonsu kawai mami take zuciyar na karye wa “zaku cimma daman amman dole sai
kunyi hak'uri sannan ku bisa ahankali dan karku dinga mgn kuna manta waye shi
b'angaren zafin kai da zuciya dole sai kun sha wahala kafin ku samu ku ya sauko ya
saurareku ni wallahi dan tani da an bar kome nan kowa ya huta “wai meye haka
zabiba?” sai ki dimga magana kina cire kanki acikinmu idan Kinsan bazaki goya wa
mami baya ba me yasa kika zo ?Inji cewar aunty Khadijat “to yanzu me nayi kuma ?ai
bazan ki zuwan kiran mahaifiyata ba haka zalika bazan goyi da bayan a sake tursasa
wa yaya ba “haba Auty zabiba ya kike magana kamar babu tausayi a zuciyarki ?karki
manta kema fa mace ce inji cewar nana hauwa’u “hk ne nima mace ce amman da zaku
fahimceni ma gata nayi mata dan banga amfani aure da wulakanci ba shi yace bayayi
ita tace tana yi ita Ke aure ko shi ?“dan allah yasa isa karki sake saka baki tashi
ma ki wuce an sallameki nan da nan parlour’n ya hargitse sai da mami ta tsawatar
masu sannan sukai shiru suna cika suna batsewa “wannan wani iri bala’i ne adamcy
duk ya dagula min lissafi ya hadani da dan’uwana yanzu kuma zai raba min kan
ya’ya .” a zuciyar zabiba tace “babu ruwan yaya duk kece kika dagula lissafin komai
.”
Bayan kwana biyu wanda ya kasance weekend tun karfe tara suka hallara da niyyar
ayita ta qare ahankali yake saukowa daga saman mattakala jikinsa sanye da farin
yadi inda kafafunsa ke sanye da farin silifas , agogon rolex ke daure da tsintsiyar
hannunsa ,idanunshi na manne da wani hadadden farin glass ,a hankali ya cigaba da
takowa cikin isa da izza shi din wani ne a fadin nigeria ,yana saukowa sanyayen
kamshin turarensa REED ya soma tashi kamshin turarensa ne ya kaiwa hancinsu sakon
fitowarsa . gabad’ayasu suka dago idanuwansu a natse suka tsura masa suna
kallonsa tamkar ranar suka soma ganinsa shi kuwa ko kallo su bai yi ba hasalima yi
yayi kamar bai ga wasu halitta a wajen ba .kai tsaye dinning área ya nufa yana
shan kamshi , har ya samu guri ya tsaya tare da soke hannunsa daya cikin aljihun
wondonsa ,basu dauke kwayar idanunsu akanshi ba ,gabdayansu an rasa wanda zai
fara masa magana shi ya kamata yayi gaisuwa amman yaki “aunty khadija ta zunguri
aunty shahida ta kalleta “gashi ya fito ya kenan ?
“Da alamun abinci zai ci bari ya gama ya samu waje ya zauna ya had’a coffee ya
fara sha yana lumshe idanu su kuwa sai faman satar kallonsa suke ba qaramin kyau
yayi musu ba cikin shigar da yayi ko dan bai fiyye saka kayan hausa bane yasa yayi
masa kyau haka yunwa yake ji sosai amman ya kasa zuba ma kanshi abinci dan haka ya
ja dogon tsaki mami ta fito sanye da doguwar rigar atamfa itama tayi kyau sosai ga
tsufa ga tarin damuwa amman dake jikinta mai kyau ne wallahi bazakace tana da diya
mai shekara 49 a duniya ba dauke kallonsa tayi ta girgiza kai kawai sannan ta
zauna acikin ya’yanta .
zabiba ce ta fahimci abinda yake buqata dan haka ta mike a natse ta qarasa inda
yake “ina kwana yaya ?lafiya !ya fad’a aciki batare da bata lokaci ba tayi serving
dinsa ta ajiye masa plet din abinci gabansa. a hankali ya dauki cup ya kai
bakinsa ya kurbi tea yana lumshe sexy eyes dinsa yana sosa keyarsa .”
Ahankali aunty shahida da aunty khadija suka mike suka nufi inda yake hajiya
zualai tabi su da kallo gabanta na wani irin faduwa nana hauwa’u ta riko tafin
hannunta “mami ki kwantar da hankalinki kiyi addua cike da sanyin jiki take
duban kyakkya wan fuskarsa ya hade fuskarsa sosai ta yadda idan ba jarumta kayi ba
bazaka iya fuskantar sa ba “karki damu mami everything will be fine “Allah yasa
auta allah ya sanyaya zuciyarsa dan mrym na bani tausayi ina jin duk nice silar
shigarta cikin damuwar nan nana hauwa’u ta damke hanunta sosai cikin nata tana
danne kukanta dan itama mrym na bata tausayi tun shekaranjiya da sukai waya bata
qara daukar wayarta ba saboda qara mata damuwa take .”a tare suka zauna suna
fuskantar shi tun daya gansu ya fahimci abinda Ke tafe dasu kusan minti shabiyar
suna zaune yaki daina cin abinci yasa ahankali aunty shahida ta soma magana
“adamcy me yasa ka saki maryam ?”laifin me tayi maka ka saketa alhalin ga mami a
raye baka sanar daita ba ka yanke hukunci kai tsaye ?”.
“bani ya kamata ki tmya ba ita da tace an saketa me tayi ?kuje ku tmbyeta abinda
tayi aka saketa “nan da nan ran aunty khadija ya baci “wannan wace irin maganar
banza ce ?”ta fad’a a fusace “ai mun san daita muka zo tmbyrka mara mutunci kawai
so kake ka kashe mana uwa ka barmu da asara dan tuni mun kula baka da buri sai na
ganin kasa mahaifiyar mu cikin bakinciki,to wallahi kasani zamanka da marym dole
ne dan shi kadai zai sanyaya ran kowa acikin gidannan ,wallahi sam baka ma mami
adalci ba kai kadai gareta amman kullum cikin sakata hawaye kake, kamata yayi ka
dinga share mata hawaye amman tun baka kai haka ba kake sakata cikin damuwa.jin
haka yasa mami ta share hawayenta . ta inda take shiga bata nan take fita ba sai
zazzaga masa ruwan bala’i take shi kansa yayi mamaki maganganunta amman yayi
shiru yana sauroronta yana tsakurar abincin gabansa batare da ya furta komai ba “.
“To kasani idan ka saki maryam dan ka yar da kwallon mangaro ka huta da kuda
kasani kayi aikin banza dan ciki ne daita na wata uku kaga kayi aikin banza duk
kinka daita kun zama abu daya “What ?” ya furta da mugun karfi yana sakin spoon din
hannunsa “eh !yanzu haka jininka na can a jininta yana yawo idanunshi ya tsura mata
yana nazari kafin ahankali ya mike tsaye yana girgiza mata kai
dukkansu kallonsa sukeyi yadda jikinsa ke rawa kamar anjona masa shocking , nan
da nan idansa yayi wani irin canzawa " impossible! waitt,hw can dis even b possible
?tana dauke da cikina na wata uku alhalin ni duka wata guda kenan da sati biyu dana
kusanceta”to kaga dole dai cikin dake jikinta naka ne, a ina aka tabayin haka?
ya fad’a a fusace taya za'ayi cikin jikinta ya zama nawa “?gbdy hankalinsu ya
tashi har mami wacce batasan sanda ta qaraso inda suke ba tana dubansa “bamu gane
nufinka ba ?ko dai ka sha wani abu ne ?babu abinda na sha garas nike amman wallahi
cikin jikinta ba nawa bane cikin wani kato ne a jikinta kuje ku tambayeta uban da
yayi mata ciki wata uku .”
da wani uban murya mami tace" kalleni adamcy ka san da wacce kake magana ka
kuma dinga tauna min mgn kafinka sakosu, niba tsohohuwar banza bace, kai har ka
isa kace cikin wani kato ne a jikin maryam dan ubanka ai kaine katon kenan tunda
kai kamata cikin dan iska yaron kawai “.mami ta fad’a tana hawaye domin karo na
farko kenan da ta furta masa wannan kalmar garesa. hakan yasa ta fashe da wani
sabon kuka jin kalamn da ida wani ne ya jifesa dashi Allah kawai zai rabata dashi
amman gashi itace da kanta ta furta masa haka gbdyn suka rikice sai suka dawo
bawa mami hakuri ,ya isa haka mami don Allah karki sake zaginsa suka fada suna wani
irin kuka mai tsuma rai “ku daina bani hakuri shi zaku bawa hakuri abinda mami take
fad’a kenan "yanzu bayan ya sake nayi shiru yanzu har da cikin jikinta zai yi
rejecting yanzu adamcy ka kyautawa
danka ?d’a daya tak tilo, daza fara samu a duniya zakayi wa haka .da wanne mrym
zata ji da sakin daka mata ga sharri”. sweetheart trust ur son wIhh wannan
cikin ba nawa bane ni ban mata ciki ba, nana hauwa’u ta goge hawayenta “Kace
bakai kayi mata ciki ba “? Ki lissafa sweetheart ranar da kika bani umarni zuwa
wajenta yau kwanaki nawa ne ?mami tayi shiru tana lissafi byn Kmr second biyu ta
d’ago tana dubansa tabbas baayi wata uku ba to meke faruwa ?”
“Sweetheart idan kin gama lissafi ku san yadda zakuyi daita domin mazinaciya kika
aura min baki sani ba yana gama fad’ar haka ya juya da nufin fita daga parlour’n
da sauri nana hauwa’u ta tareshi tana kallonsa fuskarta da tsananin damuwa karara
ya dago yana kallon idanunta itama shi take kallo eyes to eyes muryarta cike da
kuka tace “wallahi yaya mrym ba mazinaciya bace cikin jikinta naka ne jininka ne
acikinta “ni babu wani jinina dake yawo ajikinta dan ban mata ciki ba and wIh wlh
idan kuna yi dan na maidaita ne bazan maida auren nan ba na gama zama daita kenan
“naji yaya amman ka yarda ni cikinka ne hannunsa ya d’aga zai sauke mata mari yaji
an rike hannunsa ta baya .”
Mmn sudais
💗💗💗💗💗💗
MAR'ADAMS
💖💖💖💖
💗💗💗💗💗💗
*AYSHA A BAGUDO*
WATTPAD @HAUESH
AREWABOOKS USERNAME
AYSHAABAGUDO
bismillahirrahmanirrahim
Wannan littafin na kudi ne mai bukatar karantashi byn na kammalashi zai biya
1000 ta wannan account number din 1438775094 Aishat abdullahi access idan an tura
sai a turawa wannan 09136918331 alert domin tabbatar da an tura domin sauraron
littafaina a tuntubi chaneel dina (Hausa bakwai ) a YouTube.
Page 23
A matuqar fusace ya juya bayansa yaya hisham ya gani tsaye cikin kananan kaya
fuskarsa dauke da murmushi ,a natse ya sakar masa hannu yana cewa "ranka shi dade
babban yaya laifin me auta tayi haka ?" maganarsa cikin sanyi rai yayi wanda yasa
nana hauwa'u ta fashe da wani rikitaccen kuka, ina ma yayanta zai kasance kamar
mijinta mai sanyi hali da tausayi tare da shagwaba mace da kyautata wa ?bata san
tayi sa'ar samun miji ba sai da komai ya daidaita a tsakninsu tasan wa take
aure ,kuka take sosai tana kiran "wallahi yaya cikin jikin maryam naka ne, ni
sheida ce tana gama fad'ar
haka durkushe a gabansa tana zayyane masa komai daya faru tun daga farko. a matuqar
tsorace yake kallonta "take kwakwaluwarsa ta shiga caji na tunani babu abinda yazo
zuciyarsa sai maganar doctor nasir akan ciwon kan da yake fama dashi wanda yayi
tunanin duniya ya rasa a inda ya sha maganin da yayi masa illa "shi kam wasu irin
yan'uwa allah ya bashi masu son kansu dayawa ?"laifin me yayi masu ?duk wani
bala'i da yan' uwana ake had'a baki."yadda taga yanayinsa ya canza har tana iya
hango yadda jijiyon kanshi sukai rud'u rud'u yasa ta zabura ta mike tsaye gabanta
na wani irin fad'u wa da matsanancin karfin gaske ."
ya tsura mata ido ya balain canza mata daga yanayin farko ganin ya fara taku zuwa
inda take ta fara yin baya yana biyota kafin ya qarasa inda take yaya hisham ya
shiga tsakaninsu yasa hannuwansa duka ya qare matarsa yana bashi hakuri ,yaya
hisham bai san ya'akyi ba sai gani yayi ATA ya fixgota da karfi zai buga bayanta
da bango a matuqar agigice ya rungume matarsa yana cewa "kayi hakuri tayi laifi
amman dan girman allah ka yafe mata ,idan ba cikin jikinta ba wallahi zan barka ka
yi mata duk irin hukuncin da kake so amamn kayi hakuri ciki ne ajikinta ."sai
lokacin idanunshi ya kai ga cikin jikinta wanda har ya fara nuna alama ,saurin
sakar mata hannu yayi yana dungule hannunsa yannayin bugun zuciyarsa bai saisaita
ba, yannayin tsoratarsa kuwa sai ya baka mamaki gabad'aya tsigar jikinsa suka mike
"ciki hisham yayi mata ?ya tamabyi kansa yana mai furzar da iska mai zafi jiki a
sanyaye ya yake dubanta cike da tsananin fushi yana sauke numfashi da karfi dan
bancin zuwan hisham wallahi da wata killa ba wannna zance ake yi ba."
ahankali take cigaba da rera kuka Kiyi shirunki baby yayanmu zai miki
afuwa ."cikin kaukausar murya ATA ya soma tashi acikin parlour'n "ba ciki ba idan
duniyar nan gbdy zata haifa min ku saka aranku ni adam tariq abdullah bana só ba
kuma na bukata gabadayansu suka kallesa cikin tsananin tashin hankali aunty
shahida zatai magana ya d'aga mata hannu "wlhh yadda bana só auren nan ba zai yiwu
na karbi komai daga gareta ba, sai abu na gaba kafin na saketa nayi tunanin qarasa
rayuqata daita amman na kamata da abu mafi muni wanda nasan bazata ta'ba sheida
maku laifin da tayi ba abinda yasa na saketa kamata nayi dumu dumu da tukunyar
tsafi zata saka min akarkashin gadona "hakika Mahaifiyata bata cutar dani ba kamar
yadda auta ta cutar dani domin cikin nan an samesa kafin umarnin mami if not haka
zamu rabu daita zero amman koma menene ni dai banaso sai dai idan ku ku zama
ubansa amamn bani ba idan kuma akace zaa tursasa ni na rantse da girman Allah ran
kowa zai yi mummunar baci yadda mami ke kallonsa a tsorace haka sauran yan'uwansa
ke binsa da kallo zukatansu na rawa dan bakinsu ya mutu da girman laifin mrym
yana gama fada ya haye sama ya barsu cikin jimami da tashin hankali ."
Wani irin naunayen ajiyar zuciya suka sauke kafin ahankali yaya hisham ya zaunar da
nana hauwa'u akan kujera ya zauna kusa daita yana rarrashinta d'aya bayan d'aya
suka samu waje suka zauna duk jikinsu a sanyaye yayinda zuciayarsu ke cike da
mamaki mami kam kasa cewa komai tayi domin daman ita ta d'an yi zargin wani abu
akan haka sai dai taki yarda zuciyarta ta amince da hakan "mai yasa marym ?"me
yasa zaki min haka ?duk qoqarina baki gani ?ta furta acikin zuciyarta "yaya hisham
dake rike da yatsun hannun nana hauwa'u ya sakar mata hannu yana gaishe da mami
numfashi ta sauke tana amsawa "mami karki d'aga hankalinki dan kin rigada kinsan
halinsa ,kubishi ahankali har zuwa sanda zai sauko zai amsa ai mutun bazai ki
jininsa ba "hisham ina jin tsoron zuciyar adamcy idan yace bai son abu to kamai zai
faru sai dai ya faru ni yanzu ba sakin yafi damuna ba kmar yadda yace bai son cikin
jikin maryam" ko yaso ko kar yaso jininsa ne abinda Ke cikin kuma dole ya amsa
sunansa addua kawai zaa cigaba da yi masa Allah ya sanyaya masa zuciyarsa yana
gama fad'ar ya tashi yana ma nana hauwa'u magana kasa kasa ."
Bayan fitar yaya hisham "ya'yan mami suka sakata a tsakiya "yanzu mami ya zaayi ?
ya kuwa zaayi banda hakuri kowa ya kawo ido ya saka masa Allah ya kawo masa
sauki ,zan kira Abdul rauf nayi masa bayani "allah yasa ya fahimceki " inji cewar
aunty shahida to "ameen zai fahimceni in sha allahu "basu wani zauna ba kowace ta
d'auki gyalenta da jakarta ta yafa atare sukai wa mami sallama suka fito kowacce ta
shige motarta nana hauwa'u ce kawia ta saura tsaye tana kiran layin mijinta tana
tsaye yayi parking tare da fitowa ya karbo jakar hannunta ya bud'e mata gaban mota
ta shiga ta zauna tare da cewa "na gode zumana !"ya maida murfin mota ya rufe ya
zagaya ya shiga mazaunin direba suka kama hanya gida ."yana tuki ya dan kalleta
"baby me yasa kuka aikatawa ATA haka ?tayi shiru "kisani kunyi kuskuren aikata
amman dai Allah ya kawo saukin wannna tashin hankali numfashi ta sauke tare cewa
"amen ! ta kamo hannunta d'aya cikin nata tana massaging tun nan ya fara jin wani
iri ajikinsa wanda ita ba wai tayi da wata manufa bane .
suna isa gidan d'akita suka shiga ya cire rigarsa ya ajiye sannan ya janyota ta
fad'o jikinsa tare da ciremata mayafi sannan yace "habibty na yau dai baza'a
hanani na shoshale ba koh" nok'e kanta tai cikin k'irjinsa sannan ta fara magana
cikin shagwab'arta wacca take k'ara birgeshi take kuma k'ara sakashi ya rikice tace
"kai yayana gaskiya ni yanzu agajiye nike kuma kasan fa kayiwa doctor alkawarin
zaka dinga d'aga min kafa na kwana biyu biyu har cikin nan yayi kwari sosai "ai da
kin daku yau a wajen wannan yayan naki da kin gane agajiye kike "tasa dariya tana
sake makalewa ajikinsa tare da d'an cizon qirjinsa da" ai tunda naganka nasan bazan
daku ba " tak'arasa maganar tana matsa kan nipples dinshi, "aaashhh....!!!" yai
y'ar k'ara sannan
ya kalleta da sexy eye's nashi da ya dan fara canzawa
yace baby ni dana taimaki zaki ciza zaki " dariya tai sannan tace "ai kai naka yafi
zafi sosai wannan ai ba zafi" wani kallo ya mata "ok ba zafi koh toh bara na maki
kiji idan ba zafi" nan ya juyata ya maidata k'asa sannan ya fara kiciniyar rabata
da rigar dake jikinta ganin da gaske yake kuma tasan halinsa ta fara kuka tana
neman tuba bai saurara mata ba sai daya sucking brest dinta son ranshi sannan ya
barta.”
Batun sakin maryam ya bazu acikin abdullahi estate masu murna nayi ,masu bakinciki
nayi aunty abida kam tafi kowa murna faruwar wannna sakin dan lokacin da taji har
wani tsalle da rawa tayi a bangarenta batare da kid’a ba tana cewa “shikenan nan
sultana zaki dawo a saa, kece zaki maye gurbin kowace mace a wajen adamcy ,inganga
inganga !!rawa tayi sosai tamkr wata zararriya a qarshe ta suri wayarta ta shiga
neman layin mahaifiyarta sun d’auki mintuna talatin suna waya sannna sukai sallama
ta kira sultana tana d’auka tace “wai zaman me kike yi ne har yanzu ?” Kiyi qoqari
ki dawo dama biyu ta samemu ya saki matarsa ga kuma neman masu kwararrun zane da
yake nasan yana ganin zanen Kanwata zai rud’e daga nan kuma shinkenan “okay to
shikenan dan girman allah ki ajiye komai ki dawo kar murasa damarmu okay bye ta
katse kiran tana cigaba da rawa yesmin ta fito daga dakinta tana kallonta murmushi
ta sakar mata tana cewa “yesmin kin kusan zama cikakkiyar ‘ya a wajen babanki AD
“‘ya kuma mum ?yes auntynki sultana zai aura ta qarasa maganar tana
rungumeta“.tsabar murna washegari aunty abinda ta shirya walima gabdaya estate din
babu wanda bata aikawa da snks da drink ba duk wanda ya kalleta zai fahimci tana
cikin murna .”
nan da nan zance ya kai kunnen mami babu abinda tace face “allah ya shiryeta
domin duk mace mai hankali bazatayi murna dan an saki yaruwarta mace ba ita yanzu
bazata sake matsawa adamcy ba amman kullum cikin yi masa addua take idan da rabo
allah ya daidaita su. .allah sarki maryam ta dad'e kwance akan gado tana sak'e-
sak'e a ranta, dan ta ji zafin abinda aunty abida tayi ,tsaki taja tare da mik'ewa
tsaye tana d'an zagaya d'akin "dole ne na nuna ma
abida kuskurenta,zan nuna mata baa kishi da irin mu yaran zamani, tunda na lura
shiru baya mata sosai abinda aunty abida tayi ya 6ata ma maryam rai, zan nuna
mata iskancinta wasa ne wannan karon a bayyane tayi maganar tana wani shu'umin
murmishi.”
*********
Zaune yaya sadam yake a haraban gidansu akan daya daga cikin kujerun dashi ne ya
ajiyesu saboda abokansa domin zama yana sanye cikin farin yadi idanunshi manne da
farin glass idanunshi kar akan wayarsa yana karanta sakon Nadia a natse ta fito
zuwa garesa ahankali ya soma ganin tahowarwata ta kasan idanu shi cikin tafiya ta
Kamala sanye cikin doguwar riga yellow ya dago kanshi ya tsura mata ido tana kyau
sosai dan maza zai had’ata da nadia ba har ta gama qarasowa garesa fuskarta dauke
da murmushin farincikin ganinsa tace "sannu yaya dan allah kayi hakuri na barka
zaune ka kadai“
murmushi ya sakar mata tare da lumshe mata idanunshi "karki damu ko zan kwana ina
jiranki bazan gaji ba sauraniyar kyawawan mata duniya kuma zabin umma nan ki zauna
ya nuna mata kusa dashi ta zauna a natse tana kallonsa cike da jin kunyarsa "ina
yini ya aiki da fatan komai Lfy ?tayi masa tmbyr a jere tana sunkuyar da kanta
kasa tare da kamo yatsun hannunta tana wasa dashi "maryama duk Alhamdulillah mun
godewa allah ya mumcy take ?ta gyda masa kai kawai alamun lafiya a hankali ya soma
janta da hira sai dai bata wani mgn daga uhm sai uhm take cewa "maryama ! Ya kira
sunanta ta dago a natse ta kallesa na second daya ta sake maida kanta ta sunkuyar
"ga dukkanin alamun kamar agajeye kike ? Tai murmushi batare data dago ba "nan da
sati uku zaki kasance a gidana a yanzu nake jin na matsu naga kin kasance a
gidana” ajiyar zuciya mai karfi ta sauke tana dago kanta ta tsura masa idanunta "ta
so ya kurewar tamvayarta aikin da take fita nema kullum amman sai ya wani kawo
mata maganar aure .”
ta fahimcesa sosai shi mutun ne da bai da caring me taci ko me tayi ko a wani hali
take duk ba damuwarsa bace idan ma yazo gurinta ba wani hirar soyayya yake mata ba
wanda zai dauki hankalinta zai kama gabansa shiyasa duk tsawon lokacin da
mahaifiyarsa ta hadasu bata ta'ba jin komai akansa ba sai dai tana danne komai
saboda mahaifiyarta da mahaifiyarsa .”yana ganin girman mahaifiyarta sosai yana
kula dasu sosai tun kafin a had’asu aure "kinyi shiru kina kallona kice wani abu
mana ?shiru ne dai Ya sake biyosa baya har sanda wayarsa ta dauki qara sauti Ya
dauki wayarsa dake ajiye a gefensa ya duba sunan nadia ya gani yana yawo a screen
din wayar cike da firgic ya dubi inda maryama take sannan ya sake maida idanunshi
akan wayar da kyar ya sauke naunayen ajiyar zuciya yayi disconnecting din kiran ya
cigaba da magana " a she dai ni ne wanda zanyi wuf da wannna kyakkyawar yarinyar
magana yake amman zuciyar maryama ta kasa samun natsuwar allah sarki yusif
ashe Ke din ba rabonsa bace ?naunayen ajiyar zuciya ta sauke “kina da kyau sosai na
godewa ummah datayi tunanin hadani dake na gaji da ganinmu haka ina son na
killaceki a gidana "kana son ka killaceni agidan cike da rashin yanci ba ?tayi masa
tmbyr a zuciyarta .”
“maganar da nake miki yanzu haka komai da zan saka agidanmu ya kammala zamu yi
rayuwa mai dadi ko kina son na ajiyeki a wajen umma ne saboda yanayin aikina.”?
yana gama fadar haka Ya mike sakamakon wayarsa data sake daukar qara "excuse me!
ya kamata ace kana duba yanayina yaya sadam har yanzu ban ji amincewarka akan
aikina ba zaka yarda na cigaba da yiwa kafanunka zane ko kuwa ?.”“bana son sai
bayan munyi aure kace bakasan da zance ba wannan aikin rayuwata ce kuma ina son ya
kai ni matakin da ya zarta yadda nake a yanzu babban burina bai wuce na samu aiki
kafanin AGC ba .taí shiru tana jiran taji mai zai ce amman yayi mata shiru saboda
raayinsa amman dole yanzu kam ya amince dan yasan idan yaki amincewa zai ta’ba
zuciyar ummansa ya tsura mata ido yana nazarinta a yanayinta zata iya komai akan
aikinta ." ta mike a natse tana dubansa "kayi shiru yaya sadam kace wani abu mu
kawo qarshen maganarmu banason muyi aure daga baya muzo muna samun matsala akan
aikina "ka amince zaka aureni da aikina sannan zaka min hanya naga mai kafanin AGC
? ta fad’a hk sbd tasan su yusif nada hanya da karfin iko shiru yayi yaki cewa
komai yana sauke numfashi da kyar, domin kuwa abu biyu né suka hade masa guri daya
ga tambayar maryama ga kiran da nadia ta damesa dashi wanda baya jin zai iya duka
abu biyu din ."
“Ina duba yanayi na zaman takewar aurene yaya sadam domin kuwa kai kana cikin
mutanen da suka san koni wacce irin rayuwar gidanmu mahaifiyata da mahaifina taí
mgnr tmkr zatai zubar da hawaye dan gbdy idanunta har sun canza kala daga fari zuwa
yellow "ya kamata mu tsara komai yaya sadam domin kuwa banason damuwa arayuwar
aurena ta qarasa mgnr tare da kai yatsun hannunta biyu ta dauke hawayen dake
kokarin saukowa kuncinta ".
numfashi ya sauke da karfi sannan yace "shikenan zakiyi aikinki “bari naje ana
nema zamuyi waya ya fada yana kokarin barinta tsaye tare da manna waya a kunnensa
ya nufi kofar fita taí shiru tsaye tana duban bayansa "yanzu irin wannan mijin
zata aura tai rayuwar aure dashi ?anya kuwa idan ta auresa zata ji dadin rayuwar
aure kuwa yadda yake da rashin nuna caring ?” yanzu a halin da take ciki kowa Ya
ganta yasan tana cikin damuwa dan gbdy komai nata Ya canza amman kalli yadda ya bar
gabanta batare da Ya tsaya ya fahimci matsalarta ba bare ya kawo mata mafuta oh
allah karkasa nayi Kuskuren aure irin wanda Mahaifiyata tayi ya allah ka taimakeni
kasa ya canza duk da banason shi saboda rashin caring dinsa dan kusan matan
duniya shine matsalarsu a gidajen mazajensu a yanzu, cike da sanyin jiki har ya
bacewa ganinta tana tsaye a wurin rungume da hannunwanta a kirji jiki a sanyaye
ta nufi kofar part dinsu ."
*******
motarsa na shigowa haraban ma'aikatan yaji gabansa yayi wani mummunar faduwa da
karfin gaske shiru yaki fitowa daga cikin motar yana tunanin abinda yasa yaji hk
byn tun a gida bai tsinci kansa cikin wannan yanayi ba sai daya shigo ma'aikatan
iskar ya furzar ya daga kafadunsa alamun babu komai a hankali ya zuro kafafunsa dan
tuni an bude masa kofar mota ya fito yana gyara zaman suit din jikinsa sannan ya
soma taku a hankali qirjinsa na cigaba da luguden bugu yayi qoqarin kawar da
yanayin da gangar jikinsa ya shiga ta hanyar tura hannusa daya cikin aljihun
wondonsa." duk inda ya wulga maaikata ne Ke kokarin kawo gaisuwa sai dai kai kawai
yake gyada wasu ,wasu kuma yayi masu banza har ya hau lift da zai kaisa sama na
uku inda anan office dinsa yake yana sauka yaji wani sabon faduwar gaba wanda ya
rasa dalili nan ya dan rage tafiyar da yake ya dawo yana daga kafafunsa da kyar
saboda sanyin daya ziyarcesu alokacin daya tun daga nesa ya hango bayan wata
yarinya suna magana da wasu daga cikin maaikata kamar ya tsaya sai kuma ya karya
kwanan da zata kaisa office dinsa cak yaja ya tsaya sakamakon jiyo sautin muryar
yarinyar shiru yayi yana cigaba da saurara maganarta tamkar dai mafarkin da daya
saba yi “anya kuwa muryar tace ko dai mafarkin daya saba yi daita ne suna hira ?.
hannunsa ya kai yana shafa daidai satin zuciyarsa dake bugawa tmkr zata fasa
qirjinsa tayo waje ya dinga jin tamkar yayi reves ya dawo ya shiga inda yake jiyo
murayarta ya tabbatar ita din ce ko kuwa muryar ce kawai tazo daya amman sai
zuciyarsa ta kwabesa wankakkiyar zuciyarsa ta sake yin magana dashi kaje ka duba
ko itace wata zuciyar tace kai ba itace ba ,ba yarinyar mafarkinka bace, dan haka
a natse ya daga kafarsa daya bai kai ga ajiyewa ba ya sake jiyo sautin
muryarta"."ku ne fa kuka bukaci kwararrun masu irin aikinmu yau tsawon wata guda
kenan ina zariya a ma'aikatan ban samu nasarar ma hawowa saman ba sai yau ,yau din
tun karfe bakwai na safe nake cikin compaing dinku kafin ma ku yarda na hawo saman
nan sai da kuka bata min lokaci na samu da kyar na hawo yanzu kuma kuna kawo min
qabli da baadi kunsa irin wahalar dana sha kafin na kammala aikin nan kuwa ?"kunsa
lokacin da yake daukar mutun kafin mutun ya kammala ,shikenan shikenan!! tunda
bakwa bukata ku bari na wuce na kama gabana daman an fada min wahalar banza kawai
zanyi byn hka bakwa girmama masu tallata kasuwancinsu tana gama fadar hk ta juya
haka zalika fuskarta a rufe take "no madam bamuce bama bukata ba mutane dayawa sun
kawo nasu zanen maganar da nake miki har yanzu mai gida bai duba ba bare ya
tantance bazamu iya cewa komai ba a yanzu dole sai an agwadawa boss ".
Ta juyo ta fuskacensu sosai.” har zuwa wani lokaci kenan zaa gwada masa sannan zuwa
yaushe zanji feed back ?zai iya daukar wata uku zuwa ..tsaki taja ta sake juyawa
tana tafiya tana cewa "gashi nan na bar maku bana da bukata domin ko na koma dashi
gida babu amfani da zai min ."snyayen Kamshin turarenta ya bugi hancinsa yayi
saurin lumshe idanushi zuciyarsa na cigaba da mugun bugawa ta kusa dashi tazo ta
wuce har tayi taku uku ta fahimci ba ta nan hayar fita take ba dan haka ta sake
juyo wa ta nufi kofar da lift yake ahankali Ya juyo yabi bayanta da kallo yana
kallon every step of her doguwa ce sosai kuma bakar mace ce yayinda tsayinta ya
fito da ainin shape dinta na cocacola iya haka kawai ya iya fahimta domin hannunta
da kafafunta abayyane suke haka hijab din dake sanye ajikinta qaramin ne hkn ne ya
bashi damar dan fahimtar wani abu a tattare daita "
ATA yana tsaye tamkar gunki yana kallon tafiyar yarinyar da bai san ko wacece ba
amman jin sautin muryarta da yanayin tafiyarta yasaka zuciyarsa jin wani irin tsoro
mai tsanani da shiga tashin hankali shi gani yake ma babu tantama itace ba anya
kuwa ba gizo tayi masa ba kamar yadda yake ganinta a mafarkinsa har yanzu kwayar
idanunshi yana Kan hanyar databi ya kasa kwakwaran motsi wani irin ajiyar zuciya ya
sauke tamkar ya dakatar daita ya daga black nikaf din dake manne da idanunta yaga
fuskarta amman gangar jikinsa da komai nasa yayi rauni zuciyarsa kuwa sai bugawa
take babu Kaukautawa ba shiri ya dafe daidai saitin zuciyarsa ya a manne jikinsa
da bangon wurin dan yanayin da yaji akanta ya wuce misali hakan yasa kafafunsa
suka kasa dauakarsa ."ya sake kurawa hanyar data bi ido har lokacin tafiya take
mai hade da rasauya tamkar fure hankalinta kwance take taka kasa tana gyara zaman
qaramin hijab dinta wanda akewa lakabi da haif sunnah, gyara tsayuwarsa yayi sosai
tare da zura hannunwansa duka cikin aljihun wondonsa zuciyarsa na cigaba da bugawa
da sauri sauri yayinda gabadaya ma'aikatan dake aiki a office din da maryama ta
shiga suka fito domin binta da makeken hotonsa wanda ta zana ."
turus sukai gabadaya suna kallonsa kowannensu ya gyara tsayuwarsa yana kare masa
kallon abinda basu ta'ba ganin ya faru ba, basu ta'ba ganin abinda ya dauki
hankalin mai gidan nasu ba sai yau ya kusan miniti goma yana tsaye yana fama da
zuciyarsa dake karkarwa" Wayyo allah ina ma zai iya da yasa an dakatar daita ko
sau daya yaga fuskar ko mafarkinsa ce har ta shige lift bai motsa ba ,sautin
gaisuwarsu ce ta dawo dashi hankalinsa a natse .kallo daya yayi masu ya juya batare
daya amsa ba yana tafiya yana sauke numfashi a natse ya dinga daga kafafunsa
tamkar mara laka a jiki jikinsa baqaramin sanyi yayi ba har ya shiga office dinsa
ya wuce sectary dinsa zaune tana ganinsa ta mike da sauri cike da girmamawa ta
biyosa office dinsa har sai data ga ya samu wuri ya zauna "good morning sir cewar
sectary ya gyada mata kai ta wuce domin komawa bakin aikinta , a can waje kuwa
tabe baki ma'aikatan sukai sannan suka koma office bakin aikinsu ."wanda yake rike
da katon zanen adam Ya nufi inda aka ajiye sauran zanen da mutane suke kawo ."
, ATA ya zauan tare da kunna system dinsa sai dai zuciyarsa ta kasa samun
kwanciyar hankali amman haka ya cigaba da aikinsa amman ya kasa samun natsuwar yin
aiki ji yayi duk wani kuzari nasa yayi kasa wata irin soyayya princess dinsa ce ta
dinga taso masa daga zuciya yana jin kansa muddin babu ita arayuwarsa tabbas nashi
rayuwar bashi da wani amfani ya furzar da iska mai zafi yana ture system zuwa gefe
ya dauki waya ya kira number sectary dinsa mgnr daya yayi ya katse ya sake janyo
system gabansa ,byn kamar second uku ta bayyana a gabansa rike da wani file cike
da girmamawa tace "sir !"yaake ciki game da masu zanen danace?sir ai kwararrun
masu zane sun kawo irin zanensu "me yasa baki fad'a min ba ?sir ganin baka da time
shiyasa ban maka magana ba "ni nace miki bani da time ?yayi mata tambayar a tsawace
nan take jikinta ya kama rawa ta sake kankame file din hannunta "kayi hakuri sir
nayi kuskure numfashi ya sauke yana cewa "get out ."
Ta rusuna masa sannan ta juya byn Kmr mintuna talatin ya fito yayi hanyar waje
yana kiranta ta biyosa da sauri bai tsaya akoina ba sai bakin koridoor ya tsaya
yana bata umarni " call ja....kafin ma ya qarasa ta nufi office dinsa ,basu wani
jima ba suka dawo tare dashi "good morning sir “amm james muje naga creations din
da'akawo "okay sir !
Da sauri yayi gaba ATA na biye dashi wanda da kyar yake iya daga kafafunsa yayinda
sectary dinsa ke biye dashi har zuwa babban dakin daaka tanada domin ajiye duk wani
creations din da'aka kawo yana gama shiga dakin ya já Ya tsaya batare daya basu
umarni ba suka shiga bude masa duk wani creation da'aka kawo yayi shiru yana
kallon creation daya bayan daya wasu zanen kaya sukai doguwar , wasu suit da riga
wasu kuma zanen mutane haka yayita kallo duk babu wanda ya dauki hankalinsa dan
haka yayita jan tsaki yana qarawa har ma ya soma gajiya da kallon creations din har
ya juya James yace "sir kalli wannan ka gani juyowa yayi sosai yana kallon zanen
da shine aka zana sak
Mmn sudais
💗💗💗💗💗💗
MAR'ADAMS
💖💖💖💖
💗💗💗💗💗💗
*AYSHA A BAGUDO*
WATTPAD @HAUESH
AREWABOOKS USERNAME
AYSHAABAGUDO
bismillahirrahmanirrahim
Wannan littafin na kudi ne mai bukatar karantashi byn na kammalashi zai biya
1000 ta wannan account number din 1438775094 Aishat abdullahi access idan an tura
sai a turawa wannan 09136918331 alert domin tabbatar da an tura domin sauraron
littafaina a tuntubi chaneel dina (Hausa bakwai ) a YouTube.
Page 24
yadda yake fari tas tmkr balarabe da yadda idanusa suke da d'an girma da dogon
hancisa yanayin tsayinsa fuskarsa sai gashin bakinshi dake zagaye da
gemunshi komai shine hatta yanayin fuskarsa da take a d'aure ba'a bari
ba."muryarsa a kasalance "very nice !ya fad'a yana sauke numfashi had'e da gyara
tsayuwarsa yana kallon zanen kansa ."cike da tsinkewar zuciya yace "a kira number
wayar wanda yayi zanen nan kasancewar yaga kowani creations dake ajiye ajikinsa
akwai farar takarda makale mai dauke da number waya da address sai dai ita
maryama iya number wayarta kawai tasa "okay sir cewar James cikin abinda bai wuce
one second ba ya juya har ya kai bakin kofa ya tsaya batare daya juyo ba "ka biyoni
da creations din "James ya sake cewa "okay sir!"Cikin abun da bai wuce minti goma
ba James ya shiga neman layin maryama da number compaing dinsu amman number a
kashe ya jaraba kiran yafi sau goma still dai swcth off ake maimaita masa dan haka
ya shiga office din ATA cike da girmamawa ya rusuna yana cewa "sir nayita qoqarin
neman layin amman swcth off ake cewa "okay keep trying !ya fad'a yana cigaba da
operating system." wuni ranar James duk akan kiran layin maryama ya qare amman
still the same thing ake fad'a masa ."
Washegari ATA na zaune akan kujera yana kallon screen din system dinsa gefe guda
kuma yana jin bayanin James bai ce uhm ba bare uhm umm har sanda ya dasa aya inda a
karshen maganarsa ya dan nemi ya rikitashi a natse ya ture system din gabansa ya
mike tsaye ya zagayo ya zauna akan table yana dubansa "okay itace girl din jiya
kenan ?cike da tashin hankali yayi shiru ya kasa bashi amsa "da kai nake magana fa
cike da matsanancin tsoro yace"Yes sir itace !shiru yayi yana sake jin bugun
zuciyarsa na qaruwa akan na jiya ya kai idanunshi kan tangamemen zanen dake ajiye
a office dinsa yana kallo yana jin wani irin sanyi ajikinsa tunda yake bai ta'ba
jin abinda ya tsaya masa arai ba Kmr princess dinsa sai yarinyar jiya da kuma
wannan zanen "wanna duk kuskuren ku ne mutun yazo da irin abu haka mai matukar
mahimanci ai ko dan darajan kokarin da mai shi yayi wurin zanani ya kamata ku bashi
kulawa ta musaman sannan kafin ku aiwatar da komai ku nemeni but wannan laifi
stupid sectary ce bani da time dinta yanzu zanji daita later gabdaya zanenta yafi
na kowa kyau ina son ganinta eyes to eyes ina son nasan yadda akayi ta zanani haka
bansan me yasa kuke wa masu zuwa ma'aikatan da wata bukata haka ba ?yayi maganar a
matuqar fusace “we are sorry sir “ shiru ATA yayi yana ciza lip’s dinsa da karfi ."
Maryama suna zaune a parlour’nsu tare da yaya sadam suna hira kira ya shigo wayarsa
kamar koda yaushe shiru yayi gabansa na faduwa ya rasa dalili yasa bata kiransa sai
lokacin da yake tare da maryama daga maryama har yaya sadam shiru sukai suna
kallon juna muryarta a matukar sanyaye tace “yaya sadam ko akwai damuwa ne ? ya
girgiza mata kai alamun babu komai “no yaya sadam karka boye min idan akwai damuwa
ka fad'a min zan fahimceka “nace babu wata damuwa still kira ne ya sake shigowa
wannan shine karo na biyar ana kiranka baka dauka kuma kace babu komai kuma duk
sanda zamu kasance tare zayita kiranka bazaka d’auka ba amman shikenan tunda ni ban
kai matsayin da zaka sharing problem’s dinka dani ba gara kawai a fasa auren nan
dan ina ganin Kmr akwai damuwar da kake boyewa “ta fad'a tana mikewa tsaye zata
shiga da sauri ya rike hannuta yana cewa " haba sauraniyata Kiyi hakuri babu wani
damuwa kema kinsan idan akwai zan fada miki idan kika fasa auren nan ai sai dai
kisan yadda zakiyi dani da ummah nah dan mutuwa zamuyi ya qarasa mgnr a
marairaice.”
murmushi tayi wanda ya bayyana wushiyarta sama da kasa sannan ta koma ta zauna
tana cewa “haba yaya sadam wasa nake maka amman bani wayar naga su wa ke kiranka
haka “ ta kai hannunta zata d’auki wayar ya dauke wayar da sauri yana cewa “no
no!!” oh am sorry shikenan kayi hakuri na shiga rayuwarka ,no karki damu kace kana
sona yanzu ?
”sosai kuwa dan zan iya rasa raina idan kika barni amman me yasa baka son fad'a
min damuwarka matsalarka sannan ni ina son ka dinga tmbyta wasu abubuwa da suka
shafi rayuwata sirrikana me nayi da sauransu "yanzu duk abinda nake miki bakya gani
? Ta gyada masa kai alamun a’a “zan fashe miki da kuka fa maryama yana rufe bakinsa
kira ya sake shigowa wannan karon yace “ excuse me tare da mikewa tsaye “ am very
sorry yaya sadam saboda ni ka kasa daukar kiran daake maka ,babu komai kaje daga
waje ka amsa kiran ya gyad’a mata kai ya fito waje yana amsa kiran muryarsa can
qasa qasa.”
Mikewa tayi cike da sanyin jiki ta fito haraban gidan tana tafiya a hankali tana
tunanin yanayin yaya sadam wayarta ce ta dauki qara ta duba taga number compaing
din da taje neman aiki ne suka mata wulakanci "taja dogon tsaki ta katse kiran
wani kiran ya shigo still tayi discounting kira na uku ya sake shigowa " ta sake
jan tsaki "ina ganin sai na kashe wayata gabad’aya zasu daina kirana ta kashe wayar
tana cewa “marasa mutunci bayan kun gama wulakantani sannan ku dawo kuna kirana
kiran me kuke min? .dan girman Allah nadia ki daina damun kanki da yawon
kuka ,nima ina sonki amman maganar da nake miki yanzu aurena ma ya kusa ana daf
da daura min aure da yaruwata , ki manta dani kawai komai ya rigada yazo karshe a
tsakaninmu Allah ya baki wanda ya fini , look nadiya dan allah karki sake
kirana ..” yana juyowa yaga maryama tsaye a bayansa “kai dawa kuke waya har kake
cewa karta kara kiranka aurenka ya kusa ?”shiru yayi ya rasa amsar da zai bata
dan haka ta juya zata bar masa wurin ya riko tsintsiyar hannunta "please maryama!
ta juyo tare da tsura masa narkakkun idanunta wad’an da ‘bacin rai ya qara narkar
dasu “ka tsaya kana kallona tambaya ce mai sauki nayi maka.”
“ shikenan wata yarinya ce dake sona tare mukai karatu daita amman na rigada na
fad'a mata bazai yuwu muyi aure daita ba dan na kusa aure nan bada jima ba ,amman
gbdy ta kasa fahimtata numfashi ta sauke tare da cewa “ maza Kenan " allah ki yarda
dani Kiyi hakuri idan kinji babu dadi aranki yaya sadam mai yasa zaka wani damu
kanka haka ai babu komai? “ tayi shiru tare da kamo lip’s dinta tana jin zafi a
zuciyarta , yanzu taji da kunnenta yana furta mata yana sonta amman kuma wai ita
Ke sonshi tô su maza zuciya nawa garesu ?”numfashi ta sauke tace “amman duk lokacin
da zamu kasance tare tana kiranka amman idan na tmbyarka sai ka boye min why
yaya sadam alhalin zuciyarka na sonta ?” shiru yayi ya kasa furta komai yana
kallonta gabad’aya yanayinta ya canza har kwayar idanunta ? ni kinji na fad’a miki
ina sonta ?da mamaki take kallonsa lallai halin maza sai su idan suna da mata biyu
soyayyarsu biyu ce fa byn ta gama kallonsa tace “yaya sadam ban san me yasa ba
zuciyata ta kasa yarda da baka son yarinyar nan domin gbdy yanayinka ya nuna akwai
soyayyarta mai karfi a zuciyarka ,do you know something yaya sadam ?cigaba da
kallonta yayi ya kasa cewa komai “idan kasan tsakani da Allah kana sonta ka aureta
dan ni bana son boye boye arayuwata komai nafi son gsky da gsky amman kai gbdy baka
son mu gina soyayyar mu akan hakan“.
“no karki yi wannan tunani “ ni dai idan kasan zuciyarka ta rabu gida biyu dan
allah ka hakura dani ka tsaida zuciyarka wuri daya” tana gama mgnr ta zare
hannuwanta zata juya ya riko tsintsiyar hannunta bata juyo ba ya zagayo ya tsaya
gabanta yana kallonta tare da kamo d’ayan hannunta ya kai bakinsa yayi kissing
sannan ya cigaba da mgn “ina sonta amman nafi sonki maryama akanta ki yarda dani
tunda har zan iya hakura daita na aureki ya kamata ki gane sonki yafi nata ,amman
wannan ba adalci bane yaya sadam ya kake son tayi da sonka ?ka kuwa san yadda mace
take ji acikin zuciyarta idan an kayi breaking heart dinta ?kasan halin damuwar da
take ciki a yanzu ?ya zanyi maryam kafin na shigo da maganarta ummah ta zarta da
hukunci akaina kin fi kowa sanin komai ya kamata ki fahimceni ki min adalci .
magana ta gskiya ni yanzu Ke nake so shiyasa nake bata hakuri ,kiyi hakuri karki yi
fushi dashi ahankali ya dinga kwantar mata da hankali . hankalin maryama ya kwanta
“kin hakura ? na hakura tana gama fad’ar haka ta zare hannuwanta cikin nashi shige
part dinsu shiru yayi kafin a hankali ya juya ya bar wajen ."
***
ATA na zaune a office haka nan zuciyarsa ta kasa samun natsuwa James ya shigo
hannusa rike da cup din coffee ,sir ga coffee ATA ya karba ya curbi kadan ya ajiye
"dan allah sir ko zan iya cewa wani abu yace “uhm !”me yasa ka damu kanka sosai
dan an kira yarinyar nan taki dauka ? sai akayi ya kenan ? ya fad'a yana d’ago
kansa” wannan shine abinda ya shigo da kai ?”no sir kawai dai bana son ganinka
cikin damuwa ne ya numfasa kana ya cigaba da motsa lip’s finds “ni ba damuwa nayi
daita ba yadda aka wulakantata ne ya dameni ,amman sir babu abinda aka mata na
wulakanci kawai bayani aka mata akan lokacin da zata samu amsarmu, ni ina ganin
damar kamar ranta a bace yake. “enough James ka dameni zaka iya fita please “james
ya daga kafafunsa ya bar office din bayan kamar minti goma ya sake neman izinin
shigowa cike da girmamawa ya tsaya gabansa “sir akwai wani dayazo yana son
ganinka "babu wanda zan gani yanzu sai dai gobe ya fad’a tsawace .”
James ya juya da sauri zai bar office din yajiyo sautin muryarsa cikin fushi
idan ka fita kace wa umar da sauransu suzo ina son ganinsu a conference room “okay
sir ya qarasa fita da sauri "ATA ya mike yana zariya a office can kuma ya tsaya
cak gaban zanensa yana kallo ya kai hannu yana shafa fuskarsa dake cikin
zanen”hakika zuciyata na matuqar qaunar son ganin yarinyar nan zan so ta zana min
zanen princess dina a qarshe na ajiyeta a qarqashin ikon AGC domin zatayi mata
amfani .ya kai hannunsa ya shafa sumar kanshi yana furzar da iska mai zafi sannan
ya d’auki zanen ya nufi wani d’aki dake cikin office dinsa “ kafin kace me
manyan ma’aikatansa sun hadu conference hall a natse ya soma magan fuskarsa a hade
“abinda zan fad'a maku shine ina bukatar ganin yarinyar data zana zanena acikin
kwanaki biyu kacal a nemota a duk inda take acikin garin nan idan ba haka duk zaku
rasa aikinku . a lokacin da yakewa maaikatansa magana system ne a hannunsa yana
operating yana masu bayani “fatan kun fahimceni .”
Tsaye James yake a gaban ATA a office dinsa cike da girmamawa yana masa bayani
“sir yarinyar nan dana baka labari kwanakin baya akan tana da kwarewa sosai akan
ilimin lissafi duk wani calculations na Z&A itace take yi wanda yasa ta samu gurbi
aiki a karkashin Z&A amman taki, itace the same yarinyar da tayi zanenka ,kaf a
garin nan itace ta iya zane mai matuqar daukar hankali ,intakaice maka sir yarinyar
ta had’a komai na samu nayi waya daita amman tace bata bukatar yi mana zane “da
mugun sauri ATA ya d’ago yana dubansa cikin tsananin fad’uwar gaba yace “ what ?
She rejected our job again duk yadda masu zane suke shan wahala a kasar nan kafin
a karbi zanensu .”wallahi sir nima nayi matuqar mamakinta babu yadda banyi daita
ba amman ta kafe bata son aiki damu .”ATA yayi murmushin ciki sannan ya koma ya
zauna sosai akan kujera yana jan numfashi da kyar “wannan shine karo na biyu da aka
fad’a masa baa son yin aiki a masikatarsa, yaji abun ya damesa matuqar . “
***
“Heartbeat! firgigib maryama ta farka daga baccinta tana cewa “after dad ta kirasa
tana hamma hade da mika tana dubansa” a ina ka kwana habib anan na kwana ina jiran
shigowar ka ? “yanzu ka shigo ? shiru yayi yana dubanta “ kasan bana son kana kwana
a waje habib mai yasa baka jin magana na kiraka yafi sau babu adadi wayarka
akashe ,mai yasa baka jin magana “kiyi hakuri heartbeat wani abokina bello ne bashi
da lafiya shine gabday nida sauran abokanmu mukaje dubasa to kuma babu wanda zai
kwana awurinsa shine nida atiku muka tsaya” okay ! ta fad’a tana sakin fuska “gsky
wannan abu ne mai kyau nasan dole zaka rama bacci da ganin idanunka bacci bai
isheka ba, dan allah ka dinga kiyayewa karka daukowa mahaifiyarmu magana ka dai
ga yanayinmu dan Allah ka rufa mana asiri karka bari abokai su koya maka shaye
shaye ,domin shaye shaye shine abinda mutun zai yi ya gurbata rayuwarsa dan shi da
samun kwanciyar hankali har abada “in sha allahu zan dinga kiyayewa amman fa yau ma
acan zan kwana babu damuwa ai taimako ne amman ka kiyaye dan Allah ,ya shiga dakin
mahaifiyarsu ta sake yin mika ta shiga dakinta .
Bai samu aunty a daki ba dan haka ya fito ya nufi kitchen adaidai bakin kofa suka
hadu ya gaisheta male ki dafa min indomi amman a soya” kai kuma daga ina haka
amman ba gidan nan ka kwana ba ?ta fad’a tare da bin gefensa ta wuce tana rike da
kular shiru yayi “a ina ka kwana ? uhmm aunty laifina ne da ban fad’a miki ba
dan ya fad’a min bazai samu damar kwana a gida ba “wai a wurin abokinsa bello zai
kwana a hospital maryama ta bawa mahaifiyarsu amsa tana karba kular hannunta “wai
mai yasa aunty bakya bari na miki aikin komai ne byn na iya ?ai sai na sangarce
naje gidan mijin na kasa yiwa mijina komai “ ai kina aiki kuma ma girki ai na
safe kawai nake “babu wata matsala da zaki samu dan kin kware in dai wurin girki
ne maryama tayi murmushi farinciki samu nasarar kare danuwanta da tayi “kai aunty
banda yabo fa kar azo aji kunya ta fad’a tana ware idanunta “.
babu wani yabon kai ai gsky na fad’a bazanji kunya ba matukar akan girki ne kai
dama komai ma “wannan gsky ne male muna alfahari dake ,nima ina alfahari daku
yarana shiru sukai gbdy har habib suna tunani maryama ta dubesu yau fa a
lissafina sauran sati day’a a daura min aure gashi har yanzu aunty bakiyi maganar
zuwa wajen yanuwanki damu ba “kai heartbeat kina son damun kanki akan wad’an nan
mutanen idan mu bamuje ba su me yasa bazasu zo nememu ba ?”kawai ki sharesu mu
cigaba da rayuwarmu cikin qaddarar rayuwar iyayenmu tare da yiwa mahaifinmu
addua ,muje muyi breakfast suka zauna kusan atare suka saka aunty a tsakiya sannan
suka fara breakfast maryama na cin abinci taji shigowar sako wayarta ta dauka ta
duba tare da yin shiru ta dafe goshinta da hannu daya ta shiga dogon tunani
“ya’akayi naga kinyi shiru ina tunanin yadda zan bar gida ne na rigada na saba da
danuwana ,muyi hira tare muci abinci tare muyi kuka tare muyi dariya tare in fact
komai ma “gara dai kiyi aurenki shine kwanciyar hankalinmu gbdy inji cewar habib
maryam ta dungure masa kai” tana cewa “kenan bazakayi missing dina ba ?” zanyi mana
ni ne ma zan fi kowa kewarki amman ya zanyi tunda aure zakiyi kuma zamu dinga
ganin juna a duk lokacin da muka so kinga ai banga abun damuwa ba zamuyi komai Kmr
yadda muka saba ya fad’a yana kallonta komai dai menene zan fi jin kewarka
sosai .”
“ karki damu heartbeat idan ma kikace mu tattara kayanmu mu dawo gidanki mu zauna
tare zamuyi tunda nasan yaya sadam ba mai damuwa bane inji cewar habib wani sako
ne ya sake shigowa wayarta ta duba tana gama dubawa taja tsaki” yakayi princess ya
kikayi tsaki “ wani kafanin ke son nayi aiki dasu na tura masu yanayin zane na
tun da dadewa to basu tashi bukatata ba sai yanzu , at the same time ga wani sako
daga ogun state wai suna son naje har kamfaninsu dake ogun state nayi masu zane ,
ni bama zanen bane damuwata ba yadda kmr yadda date din da zaa masu zanen ya
zamo date din daurin aurena bari kawai na tura masu bazan samu dama ba su kuma
wad’an can zan tura masu sako nan da qarshen wata zan zo na fara aiki dasu .“ fine
daidai kenan amman zuwa ogun state din ma ai ba damuwa bane ta dubi habib taya
zakace ba damuwa bane ?Ko nace zanyi hankalina bazai kwanta ba ,”zaki iya zuwa
Kiyi bayan an daura aure idan kin dawo sai ki cigaba da hidimar bikinki tunda abun
kwana daya ne “ ni dai gsky ban yarda kije har ogun state ba aunty ta fad’a gara
ki hakura idan ba haka ba bazaki samu natsuwar hidamar yin biki ba daga yau
hankalinki zai rabu gida biyu shiru sukai gbdy can maryama tace “ gsky kika fad’a
“ni dai ina son kike ki fad’awa yaya sadam sai ya rakaki kuje tare “okay bari
zan yi masa mgn muji meye raayinsa Kiyi masa mgn idan ya amince sai kuje tare .”
Tsaye yaya sadam yake a d’akinsa muryarsa can qasa qasa yana waya da nadiya “haba
nadiya nasani nasan ban miki adalci ba amman kema Kinsan yadda nake mutuwar
sonki ,soyayyar shekaru biyar fa ni kad’ai nasan me nake ji ajikina tabbas nasan
laifina ne da ban shigo da maganarki da wuri ba har aka zartar da wannan
hukunci ,No bazan iya cewa mahaifiyata haka ba . zan dai san abun yi ki kwantar min
da hankalinki ki saurareni at anytime .a natse ya fito cikin jallabiya ruwan qasa
kawai yaga maryama zaune ita kad’ai a falon .”sai daya zauna sannan suka kalli juna
shi da maryam gano yanayin maryama kamar tana cikin damuwa ya matsota sosai har
suna iya shakar numfashi juna dan a tunaninsa ko taji wayarsa ne ahankali ya kamo
yatsun hannunta wanda yasa taji wani irin zirrr a sansar jikinta nan da nan tayi
qoqarin zare hannunta bai damu ba yace “lafiya na ganki haka ?daman magana nake son
muyi “ina jikin me zaki fad’a min ?”amm amm daman akan wani aiki ne daaka kirani
nace na fad’a maka nan dai tayi masa bayanin komai ajiyar zuciya ya sauke yana
dubanta “kinji abinda naji kuwa ?wani irin aiki ne har ogun state kuma a ranar
daurin aurenmu ?nan da nan jikin maryama ya kama rawa “kayi hakuri bansan mgr zata
bata maka rai ba na hakura ba sai naje ba na cigaba da aikina anan daman ba wai
zasu d’auke bane aiki ne na lokaci zuwa lokaci kuma ba aikin kwana bane amman kayi
hakuri karkayi fushi dani ta qarasa mgnr muryarta cike da rauni .”
ya kalleta cike da tausayinta sakamakon yadda take magana cikin sanyin murya da
tsoro ,ita kanta a yadda take maganar tana jin babu dadi har cikin ranta “shikenan
ki kwantar da hankalinki yanzu me kike ganin zamuyi ?”ya tambayeta cikin sanyin rai
“tô wai idan ka amince sai muje tare da kai ,idan kuma baka amince ba wallahi babu
komai na hakura allah ya zaba min abinda yafi zama alkhairi murmushi ya sakar mata
yace “shikenan karki damu amaryata zamuje tare ai ni yanzu duk abinda kike so ina
so ko bangon duniya kika ce zamuje tare allah ya nuna mana ranar nan da nan
murmushi ya bayyana a fuskarta “amman naji dadin amincewarka wallahi baka ta’ba
sakani farinciki irin na yau ba na gode sosai allah ya jikan iyayenmu Allah yasa
suna aljanna Allah ya saka maka da alkhairi Allah yaja da kwanan ummah ,Allah ya
bamu zaman lafiya a arayuwar aurenmu “Ameen Ameen ya Allah Allah ya nuna min kin
haifa min yara masu yawa tasa hannu tana rufe fuskarta nan suka cigaba hirarsu.”
Ranar lahadi 14 ga watan October shekara ta dubu biyu da bakwai aka daura auren
maryama da yayanta sadam .ana gama daurin aure suka fara shirin tafiya ogun state
wanda kusan yaya sadam ne yayita matsa mata ta d’auko kayan aikinta tare suka shiga
wajen ummah lokacin tana tare da yan’uwanta dana mijinta tayi masu fatan alkhairi
fuskarta dauke da farinciki maryama ta zama mallakinta gabdaya lokacin da zasu wuce
aunty hassna tace “yanzu dan lalacewa aunty har da murna kike tun baaje koina ba an
mallake miki d’a “cak maryama ta tsaya cike da sanyin jiki “me zanyi hassana
matarsa ce kuma ya amince tunda ya amince meye nawa aciki ?kunga kuyi maza ku kama
hanya Allah ya tsare min ku suka sa kai zasu fice har sun kai bakin kofa umma tace
“sadam ya juyo daga inda yake “ka kular min da maryama da kyau ,Allah ya tsare
hanya “to ni ummah bazakice ta kular miki dani ba ?tayi murmushi shikenan “maryama
ki kular min dashi Allah yayi maku albarka suka ce “ameen suka fito suka shiga mota
suka d’auki hanyar ogun .”
Cikin sauri sauri ATA ya fito daga dayan bedroom dinsa cikin wasu had’ad’den
kanana kaya bakake ajikinsa ,ya shiga dayan dakinsa wanda kusan abubuwansa masu
mahimanci anan suke, yadda jikinsa ke fitar da kashin turarensa reed akoda yaushe
haka dakin Ke dauke da kamshin turensa, cikin sauri ya dauki farin glass dinsa
ya manna a kwayar idanunshi sannan ya qaraso ya dauki agogo baki ya daura a
tsintsiyar hannunsa ya bude bedside ya dauki wallet dinsa ya tura cikin ajihunsa
ya daura facing cup yayi mugun kyua ya fito sanyayyen kamshin turarensa na binsa
cikin sauri yake taka step cikin . a zaune ya iske mami tana waya ya d’an tsaya
yana kallonta dan ga dukkanin alamun da wannan yarinyar take waya gyaran murya yayi
yana sham kamshi ta waigo tana dubansa “ina zuwa kuma ? wani aiki !ya bata amsa
atakaice yana had’e gira sama data kasa dan kar ma tayi masa mgnr mrym “naga yau
weekend ce ?eh ogun state zani zan iya dawowa a yau watakilla kuma sai gobe dan
aikin nada matukar mahimanci .”yana gama fad’ar haka ya nufi kofar fita .”
To adamcy mami fatan nasara
Mmn sudais
💗💗💗💗💗💗
MAR'ADAMS
💖💖💖💖
💗💗💗💗💗💗
*AYSHA A BAGUDO*
WATTPAD @HAUESH
AREWABOOKS USERNAME
AYSHAABAGUDO
bismillahirrahmanirrahim
Wannan littafin na kudi ne mai bukatar karantashi byn na kammalashi zai biya
1000 ta wannan account number din 1438775094 Aishat abdullahi access idan an tura
sai a turawa wannan 09136918331 alert domin tabbatar da an tura domin sauraron
littafaina a tuntubi chaneel dina (Hausa bakwai ) a YouTube.
Page 25
Tafiyar awanni hud'u ta kawosu maryama ma'aikatan ATA dake jahar ogun
state yaya sadam yayi parking din motarsa acikin haraban ma'aikatan sannan suka
fito atare yana gyara zaman farar shaddar jikinsa yayinda maryama ke qoqarin neman
layin mr segun kira d'aya mr segun ya d'aga sukai magana na second biyu sannan ta
fuskanci yaya sadam fuskarta kwance da annurin farinciki mara iyaka tace "kad'an
yi hakuri yanzu za'a yi mana iso zuwa ciki " yaya sadam ya gyad'a mata kai kawai
alamun babu komai yana sakar mata tsadaddaden murmushinsa ,suka tsaya suna magana
kasa kasa kafin ayi masu iso .wani matashin saurayi ne ya sauko sanye da bakaken
kaya ya shigar dasu ciki .
a wani dogo office aka shigar dasu wanda gabad'aya nsa glass ne dan ana iya hango
duk wanda yake ciki ,basu d'auki cikakken mintuna goma ba mr segun ya shigo yana
tmbyr saurayin daya shigo da
su maryama "niyi ina bakuwar daka shigo daita ?
"sir itace a gabanka zaune” mr segun ya d'an ware idanunshi akan maryama dake
zaune yana mata barka da zuwa yana mai sake masu iso zuwa wani office din dabam
wanda daga shi sai wanda ATA yake cikin zaune zaman jiran qarasowarta .
"kusa da maryama yaya sadam ya samu waje ya zauna kamar zai mata
numfashi "madam ya hanya ?"
mr segun ya tambayeta cike da kulawa yana kallonta "alhamd sir tunda gamu mun samu
mun qaraso lfy amman fa da kyar dan hanyar nan taku bata da kyau tafiyar da ya
kamata ace one to two hour's ne ya kawomu shine ya d'aukemu har four hours amman
alhamdulillah "wannan gsky ne mutane na yawon complain akan hanyar nan tamu amman
dai alhamd tunda kun qaraso lafiya tun mai gida bai gaji da zaman jiranki ba
dan awaninsa biyu da qarasowa bari nasa akawo maku abun sha, idan kin gama wancan
office din dake kallonki zaki shiga kafin nan ma zaki same aciki "yana gama fad'ar
haka ya fita da d'an sauri ya barsu zaune maryama ta zuba ma yaya sadam ido har
sanda aka kawo masu abun sha ta d'auka ta tsiyaya masa a glass cup ta mika masa ."
ahankali yasa hannu ya amsa cup din hannunta ya kur'bi kad'an yana mai lumshe
idanunshi sannan ya ajiye cup din hannunsa yana dubanta a tsanake "ya naga duk
kinyi wani iri ?"naji yace idan na gama na shiga ni kuma nafi son mu shiga tare da
kai banason na barka kai kad'ai zaman jirana "
Gajiyayyun idanunshi ya ware sosai akanta kafin ahankali ya hadiye wani abu daya
tsaya masa a makoshi sannan yace "karki manta aikinki kika zo ,kuma kema Kinsan ke
kad'ai zasu bukaci gani banda ni ?" duk da haka idan a son raina ne mu shiga tare
"ta fad'a tana mai tsareshi da narkakkun idanunta ." suna zaune wnn saurayin da
yayi masu iso ya shigo yana cewa "madam ki shiga ke kad'ai mai gida yake jira "ok
but dan allah ko zamu iya shiga mu biyu ?cike da jin haushin maganarta yace "tare
zakuyi aikin ne ?no ni kad'ai ce !to ke kad'ai ake buqatar gani aciki dan mai gida
baya son hayaniya "ya qarasa maganar tare da ta'be baki sannan ya fice ya shige
wani office ."
hankalin maryama ya tashi matuka dan har ga allah haka nan taji bata son shiga ita
kad'ai qarara damuw ta bayyana acikin kwayar idanunta da shi kad'ai yaya sadam yake
iya gani har ya fahimci halin da take ciki ,ahankali yaya sadam ya tsiyaya mata
drik ya miko mata ta girgiza masa kai alamun bazata sha ba ,"why ?! ya tmbyeta
yana sake tsareta da idanunshi dafe goshinta tayi tana cewa "bana jin shan komai a
yanzu ,tun daya ga haka yasan ko me zai yi 'bata lokacinsa kawai zai yi dan bazata
kar'ba ba, dan haka ya mike tsaye suka fito tare tana gabansa yana take mata baya
har suka fito dogon hanyar da zata kai su office din ATA wanda alokacin yana tsaye
acikin tangamemen office dinsa ya hard'e hannuwansa duka a faffad'an qirjinsa
idanunsa kyam akan maryama da yaya sadam ta cikin glass door ,har ta fara taku
domin qarasowa zuwa inda office dinsa yake yaga ta tsaya ta koma baya kad'an tana
magana da wani da bai san ko waye ba ,sai dai idanuwanta yana kansa ,kwakwa
luwarta na hasko mata fuskarsa daga nesa kamar tasan fuskar yayinda shi din ma
kallonta yake cikin shigarta ta mutunci kamar ranar farko daya fara d'aura kwayar
idanunshi akanta ."doguwar riga ce sanye ajikinta har qasa mai dogon hannu da
qaramin hijab dinta mai zip a gaba,sai nikaf kalar hijab din da take sanye dashi
wanda iya kwayar idanunta kad'ai ake iya gani ,tsaki yaja da karfi fuskar nan tashi
babu wani annurin kirki dan babu abinda ya tsana arayuwarsa kamar 'bata
lokaci ,yana wasa da komai arayuwarsa amman baya ta'ba wasa da lokacinsa ,ita kuma
abinda ya fahimta kenan daga gareta tana da matukar wasa da lokacinta da kuma
damarta ".
"ya kuma kika tsaya madam bayan an fad'a miki ke kad'ai mai gida yake jira ?"ta
jiyo sautin muryar segun daga bayansu ta juyo a natse idanunta kyam akan yaya
sadam sannan tace "yanzu zan shiga na d'an tsaya muna magana da mijina ne "miji
kuma alokacin aiki ? yayi mata tambayar da mamaki akan fuskarsa dan shi a tunaninsa
bata da aure tunda ta amsa gayyatarsu a weekend mutumin daya gansu tare kuwa ya
d'auka d'an rakiya ne ko kuma saurayinta ."a natse ta gyad'a masa kai tana cewa "Eh
mijina ne kuma yayana ne ". ATA wanda yake tsaye yana ciza lip's dinsa da karfi
cikin zafin rai bai san wainar da'ake toyawa ba amman haka nan yake jin
matsanancin bugun zuciya da kuma 'bacin rai mara misaltuwa "any way kiyi sauri ki
shiga kiyi abinda ya kawoki dan mai gida baya wasa da lokacinsa ,akan lokacinsa zai
iya aikata komai kafin ta bashi amsa yaya sadam yayi murmushi ya matso kusa daita
sosai tare da zuba hannuwansa duka cikin aljihu wondonsa fuskarsa a sake "karka
damu yanzu zata shiga kuma zata maku abinda kuke so "ya fad'a masa haka sannan ya
maida hankalinsa kan maryama kamar zai mata numfashi"k'anwata kuma amaryata karki
wani damu da jiran da zan miki ni kad'ai abinda nake so dake ki natsu sosai kiyi
abinda ya kawoki ina sonki ina kuma alfahari dake na kuma yarda dake a duk inda
zaki kasance nasan zaki kame min kanki da kuma mutuncina "nan take idanuwanta suka
cicciko da ruwan hawaye "yaya sadam na gode sosai ,na gode da yarda daka min ya
allah ka yarda dani kamar yadda mijina ya yarda dani "ameen ya hayyu ya qayyum "ya
fad'a tare da ciro handkey fari daga gaban aljihun rigarsa ya goge mata hawaye
then ya kai bakinsa yayi kissing foring head dinta yana mai karfafa mata gwiwa
murmushin gamsarwa ta sakar masa sannan tayi gaba tana d'aga masa hannu ."
bayanta yabi da kallo cike da tausayawa take taka kasa kamar bata son takawa yana
tsaye har sai daya ga ta tura kofar office din ahankali ta shiga kusan second biyar
ya d'auka tsaye yana kallonta ya kasa d'auke idanunshi akanta ,ATA wanda yake rike
da waya a daidai bakinsa da hananu d'aya yayinda d'ayan hannunsa ke rike da wata
farar takarda yana magana yana kai kawo acikin office din hakazalika segun na
tsaye a gefe guda cike da girmamawa bai kalli inda take ba .”
ahankali yaya sadam ya juya ya fara taku zuwa kasa jikinsa a matukar sanyaye ya
bud'e mazauninsa na direba ya shiga ya zauna yana sauke wani irin naunayen ajiyar
zuciya sannan ya d'auki wayarsa ya rike yana dubawa missed call's din nadiya ya
gani rututu ya sauke numfashi sannan ya kirata tana d'auka ta fashe masa da kuka
"menene kuma abun kuka ?"na fad’a miki zan cika miki alkwarin da nayi miki bazan
ta’ba cin amanarki ba nan da wasu watanni masu zuwa zamu kasance tare amatsayin
ma’aurata ,oh my god dan an d'aura aurena shi yake nufi me ?kinga nadiya banason
abinda kike min wallahi kukanki yana mugun 'bata min rai ."
"a natse ATA ya juyo mata fuskarsa sosai tare da tsayawa ya tokare hannunsa dake
rike da farar takardar a makeken table din gabansa yana cigaba da wayarsa ."idanun
maryama suka sauka kan kyakkyawar fuskar ATA wanda zuwa lokacin ya runtse
idanunsa gam zuciyarshi da bakinsa ne kawai ke aiki ,ta tsura masa idanuwanta sosai
tana cigaba da kallonsa " tabbas ba gezo idanuwanta suke mata ba shine shararren
d'an kasuwan nan data d'auki tsawon lokaci wajen zanashi wanda a qarshe ta kai
zanensa ma'aikatansa babu wata gamsashiyar magana mai dadi daga ma'aikatansa ."tayi
shiru tana dubansa a tsanake tana shakar kamshn turarensa mai sanyi da ratsa zuciya
"tun daga ranar data kai masu zanensa suke nemanta a waya "to mai yasa suke
bibiyarta ?"mai yasa suka jawota zuwa nan ?"
ta yiwa kwakwaluwarta tambyr da bata da mai bata amsa wani irin mummunar fad'uwar
gaba take ji babu abinda kwakwaluwarta bata hasko mata akansu ba amman tai
qoqarin sharewa ta cigaba da tsayuwar jiransa ."bakinta na furta hasbiyallahu la
ila a illahuwa alaihi tawakkaltu wa huwa rabbul arshil azim sakamakon wani sabon
tsoro da ya shigeta ."
maryama na tsaye har kusan mintuna shabiyar ATA bai gama wayar da yake ba haka
zalika bai bud'e kwayar idanunshi ya bata umarnin zama ba haka ma segun na tsaye
bai zauna ba adaidai lokacin da qarfe d'aya na rana ta buga wanda a daidai lokacin
wasu masallatan sun tada sallarsu dan haka ranta ya soma 'baci ta soma tunanin an
janyota ne kawai dan a sake wulakantata a karo na biyu ji tayi kamar ta juya ta
wuce shi da segun ta kama gabanta ,ta kalli inda segun yake tsaye shima ya kalleta
haka nan ya tsinci kansa da shafa mata qirjinsa alamun tayi hakuri "segun !yes sir
ya fad’a cike da girmamawa ya mika masa farar takardar dake rike a hannunsa
batare daya bud'e idanunshi ba "ina bukatar copy's dinsu "okay sir ya amsa ya fita
da sauri ."ko bayan fitar segun ata bai bud'e idanunshi ba bare yayi mata magana
sai kuma taga bai kamata ace tana jiran sai shi ne zai fara mata magana ba dole
dai sai itace zata fara masa magana kafin ya saurareta ,dan haka ta qara taku
d'aya ta tsaya daidai saitin kunnensa cikin muryar dake nuna alamun gajiya "ta
gaishesa bai amsa ba sai ma ya matsa baya ransa a 'bace yayinda zuciyarsa na
tafasa dan ya tsani yazo jira duk abinda zaayi masa dole shi zaa jira karo na
farko kenan daya zauna jira jiran ma akan itace zata qaru dashi .”
wulakanci da yayi mata yayi mata ciwo, dan ta tsani disgi da wulakanci kamar taja
masa tsaki ta fice daga office din sai kuma tayi wani tunani su manyan nan haka
halinsu yake kafin kayi nasara akansu dole sai ka kwantar da kai dan haka ta
sanyawa zuciyarta hakuri tayi kasa da muryarta da kanta tana wasa da yatsun
hannunta "ranka shi dade lokaci na tafiya yana da kyau abani aikin daya kawoni nayi
ga kuma lokacin sallah yayi ina buqatar nayi sallah "sake jin sautin zazzakar
muryarta ya sanyashi bude idanunshi ahankali tamkar mai tsoron ganin wani abun
agabansa ,ya zuba mata tsumammun idanunshi masu mugun rikitarwa yana kallon
cikin qwayar idanunta dake d'auke da zara zaran gashi ido itama shi take kallo
tana jira daga garesa ".
shiru yayi yana cigaba da kallon cikin kwayar idanunta gabansa na wani irin luguden
bugu da karfin gaske,kallon da yake wa kwayar idanunta kallon né na sani "jiki a
sanyaye ya nuna mata wata kofa dake manne da office din "ki shiga kiyi alwala
"yana gama fad'ar haka ya juya mata baya .”
shiru tayi kafin ahankali cikin sanyin jiki ta juya ta shige toilet ta d'auro
alwala ta fito ta tada sallah a natse yana zaune yana kallonta yana waya ,ganin har
ta idar da sallah bai tashi ba bare shima yayi tunanin ya tashi yayi sallar yasa
tayi zaton ko ya manta daita acikin office din ne hakan yasa ahankali ta matso
kusa dashi ta motsa labbanta"sir abani aikin da zanyi bani da ishashen lokaci da
gefen idanunsa ya kalleta a d'age sannan muryarsa ta biyo baya a dake "kece kika
zana ni? muryarta a sanyaye tace "eh nice sir !kinsan ko ni waye ?"shiru tayi har
kusan mintuna goma tana nazarin maganarsa sannan cike da girmamawa tace "eh sir !
"Waye ni ?ya sake tmbyrta a dake tamkar bashi yayi maganar ba "kai ne shararren dan
kasuwan nan da kasar nan dama duniya gabad'aya take ji dashi "tana gama fad'ar ya
juyo a matuqar fusace ya fuskaanceta yana furzar da iska mai zafi daga bakinsa
"shine dan iskanci kamfanina ya buqaci yin aiki dake amman kikayi rejecting?ya
qarasa maganar a matukar tsawace yana zare mata idanunshi .”
nan da nan hankalinta yayi matseefar tashi tayi saurin matsawa baya jikinta na
kyarma "aikin banza kawai yanzu haka ke din ba diyar kowa bace amman kin d'auki
girman kan tsiya kin d'aura wa kanki nonsense" yana gama fad'ar haka ya mike ya
barta tsaye sake da baki "nice nonsense? ta tambayi kanta cike da mamaki jin abinda
ya fad'a mata “nonsense!ta sake maimaitawa a fili tana mai jin d’acin kalmar domin
tunda take ba’a ta’ba dangantata da kalmar ba .tana kallonsa ya nufi wani d'aki
tana mai jin wani irin tuttukin bakinciki tare da damuwa mai tarin yawa har ya
tura kofar zai shiga sai kuma yaja ya tsaya yana jan tsaki "give me ten minutes "
yana gama fad'ar haka ya qarasa shigewa .”
runtse idanunta tayi "wannan kuma wani irin sabon salon wulakanci da 'bata lokaci
né ? ya kuwa san me ake kira da zane ?"abu ne da yake bukatar isashen lokaci "ita
bama kanta take ji ba kamar yaya sadam mutumin daya sadaukar da farincikinsa ya
biyota cike da zafin zuciya ta juya zata fita daga office din sai ga mr segun , ya
tsaidaita yana cewa "ina zuwa kuma ?zan wuce ne dan bana tunanin aikin nan zai
yuwu "calm down madam ki samu natsuwa kiyi abinda ya kawoki baqaramin sa'a kika
taka ba da mai gida ya bukaci yin aiki dake "yana 'bata min lokaci gashi tare da
mijina muke "nasani yanzu me yace ko tunda na fita bai yi magana dake ba ?"Yayi a
qarshe wai na bashi ten minutes ."tayi mgnr kamar zatayi kuka "ok kiyi hakuri ki
bashi lokacin dayace kin 'bata sama da awa acikin office din nan sai mintuna goma
né kawai zai gagara watakilla ma bazaki yi aikin a yau ba ,zai baki ne kije gida
kiyi idan kin gama sai ki kawo cike da jan hankali ya dinga karfafa mata
zuciyarta dan haka ta cigaba da tsayuwar jiran ATA ."
kusan mintuna goma sha ya d'auka sai gashi ya fito tare da furta "kika ce kice kika
zana ni? Kamar tace masa a'a dan taga abun nasa akwai rainin hankali ciki .amman
sai ta tsinci kanta da jin tsoro dan haka ta maida kwayar idanunta ta lumshe masa
tana wasa da agogon tsarka hannunta wanda ya qara wa zanen lallenta kyau ,lallen
yabi da wani shu'umin kallo tun da yake bai ta'ba ganin zanen lallen da yayi masa
kyau har ya d'auki hankalinsa ba sai nata yaji kamar ya kamo yatsun hannunta ,ya
d'ago idanunshi a natse ya kalli fuskarta nan da nan idanunsu ya tsarke cikin
juna wannan karon sauri cire kwayar idanunta cikin nashi tayi tana mai kawar da
fuskarta gefe tare da danne bugun zuciyarta "shi kuwa wani yanayi ya tsinci kanshi
ciki mai sarkakkiya da wuyar misaltuwa sakamakon idanunsu da suka sake tsarkewa
cikin juna abinda ya lura atattare daita itama tana da jin kai da miskilanci"a
natse ya sake bin zanen lallenta da kallo wani irin kallo ta watsa masa gabanta na
fad'uwa wanda ta rasa dalilin jin haka ."
Ahankali ya samu waje akan kujerun kushin dake office din ya zauna batare daya
bata umarnin zama ba "bata zauna ba sai ma idanunta data tsura masa tana kallonsa
tana sauke numfashi dan itama taci alwashin bazata yi mgn ba har sai yagaji dan
kansa yayi . abinda batasani ba shi ko ajikin ATA da zasu kwana a haka ma bazai
damu ba abinda yasani ne ba zai barta taje koina ba har sai tayi masa abinda yake
buqata daga gareta ."ya lumshe tsumammun idanunshi yana jijiga kafarsa d'aya yana
jira daga gareta ."a qalla sun kusan minti talatin yana zaune ita da segun suna
tsaye ta kalli agogon dake d'aure a hannunta a karo na kusan biyar a kasan ranta
taja qaramin tsaki bata san me ya janyota zuwa wannan aiki ba nan take
kwakwaluwarta ta shiga aikin neman mata mafuta ."kafin ahankali ta samo zance
zuci"maryama dole ki ajiye komai ki qarasa gabansa Kiyi masa magana idan aikin nan
zai yuwu ayi idan bazai yuwu ba ya sallameki ki kama gabanki tun kafin hakurin
mijinki ya qare"da sanyi jiki take qarasowa zuwa inda yake ahankali ahankali har ta
iso ta zauna a kujerar dake facing dinsa "wani irin zane zanyi "? tayi tmbyr cike
da sanyi murya "ahankali ya motsa lip's dinsa "ina kayan aikinki ?da hanzari ta
bud'e jakar kayan aikinta ta fito da kayan aikinta tare da janyo kujerar gabanta
zata ajiye ta jiyo sautin muryarsa "ba'a nan zakiyi ba” ya fad'a tare da mikewa
tsaye "biyoni ! "
fitowa sukai daga office din yana gaba tana biye dashi haka ma segun yayinda gbdy
hankalinta ya rabu gida biyu wani yana gurin mijinta wani yana gurin ATA ."wani
office ya shiga daita kai tsaye gaban wani farin baod yaja ya tsaya tare da
jingina jikinsa da bango segun yayi saurin janyo kujeru guda biyu daya a gaban
baod din dazaayi zane d'aya kuma a inda ATA zai zauna "sir ka zauna ! ya zauna
tare da daura kafarsa d'aya akan d'aya jiki a sanyaye maryama ta zauna tana
jiransa sai daya gama shan kamshinsa sannna ya sallami segu ya fara mata bayani
tana jin ya fara magana ta d'aura hannunta akan boad ta fara fidda kyakkyawar shep
din jikin zanen da yake buqata , yana mata bayani tana zanawa lokacin data zana
karan hancinta taji wani mummunar tsoro ya shigeta cak ta tsaya ta kasa cigaba da
zanen da take ta tsurawa baod din gabanta ido kwaayr idanunta ta zana da hancinta
har ma da yanayin jikinta babu abinda yazo zuciyarta kamar zanenta data gani a
office din m . malik “ nan da nan gumi ya shiga tsatsafo mata a goshi da karan
hancinta.shi kuwa gyara zamansa yayi sosai yana kallon zanen lallen hannunta da
yadda take tafiyar da aikinta bai san ya'akayi ba yaji saukar hannunsa akan
hannunta yana shafawa ."
Cikin gigita gangan jikinta ya kama rawa wanda yasa ATA ya dawo haiyacinsa sai
dai ya kasa d'auke hannunsa ajikinta da kwayar idanunshi wani irin tsoro da
matsanancin firgici ATA yaga ya bayyana afuskar maryama ,yayinda zuciyarta ta
shiga bugawa da karfi numfashinta ya soma barazanar d'aukewa, cikin sanyin jiki ta
sabule hannunta cikin bacin rai tace "meye haka ?"dan allah aiki nazo yi banason
irin
wannan wasan iskanci mai barazana ga rayuwata wannan ya zamo karo na farko da
qarshe karka sake kuskuren sake kai hannunka jikinta "ta fad’a tana jan tsaki"
ajiyar zuciya ya sauke tare da kafa mata tsumammun idanunsa cikin sayin murya yace
"look at me “ta kallesa Kmr yadda ya buqata babu wasa acikin kwayar idanunshi
"Kinga nayi miki kama da dan iska ?sosai kuwa dan gashi naga alama daga zuwa aiki
sai ka bige da kai hannunka jikina batare da kayi laakari da ni din matar aure bace
ko kuwa budurwa bace ".hakan nan yaji ya tsinci kanshi da adduar allah yasa single
ce ba matar aure ba ya sake kai hannunsa tsintsiyar hannunta tayi saurin zare
hannunta har agogon dake d'aure a tsintsiyar hannunta ya zame cikin nashi “wai meye
haka dan allah nifa matar aure ce kuma tare da mijina nazo aikin nan “ta fad'a
hankalinta a matukar tashe shiru yayi yana qare mata kallo qirjinsa na wani irin
bugawa da matsanancin karfi wanda baya jin haka akan kowace mace sai akan
mafarkinsa.”
ahankali ya motsa labbansa "ko zan iya ganin fuskarki ?"ya tmbyeta yana qara gyara
zamansa
"no !ta bashi amsa a matukar tsorace ya sauke numfashi tare da mikewa tsaye ta sake
ja baya tana cewa "karka matso kusa dani domin bazan ta'ba kasancewa cikin wawayen
mata masu cin amanar mazajensu ba ganin tana nema ta fice daga hayyacinta ya
sanyashi kamota hadi da zaunar da ita "lokacin daya kamota wani irin socking ne
ya ziyarci zuciya dama gangar jikinsa nan take bugawar da zuciyarsa take ta qaru
fiyye da kaida sai dai ya kasa magana a fili sai a zuci "ki natsu wallahi babu
abinda zan miki ni kaina bansan meke damuna ba yau , tun da kika kasance tare dani
naji komai nawa ya sauya .”
Yayi shiru tare da tsura mata ido ita kuwa banda bugawa babu abinda zuciyarta
keyi, neman hanyar guduwa take daga garesa ."yayinda wasu irin hawayene masu azabar
zafi suka taru a kurmin idanunta "wallahi ka cuceni tun da nake babu wani nmj daya
ta'ba kai hannunsa jikina tun ina matsayin budurwa sai yau dana kasance mallakin
wani tana gama fad’ar haka ta fashe da wani irin kuka "okay ki zauna ki qarasa
min aikina na sallameki and ki yafe min bisa kuskurena kafin ya gama mgnrsa har ta
soma tattara kayan aikinta ta zuba cikin jaka ta fice da sauri ."da sauri ya fito
ya biyota yana kiranta "ke!!!
"ita kuwa da sauri sauri gudu gudu ta shiga lift ta danna grand segun ne ya fito da
sauri sakamakon jin sautin muryar mai gidansa , cikin gigita segun yace sir meke
faruwa ne ?"karka bari yarinyar nan ta wuce ka tsayar min daita !ka tsayarda ita
segun amman ina cikin kankani lokaci maryama ta sauka kasa tana goge hawayen
fuskarta cike da tashin hankali ta nufi inda motar yaya sadam yake a pake jikinta
na wani irin kyarma ta bud'e ta shiga ta zauna kallo d'aya yayi mata ya fahimci
tana tattare da damuwa nan da nan ya rud'e ya shiga jera mata tambayoyi "ka
taimakeni yaya sadam ka bar garin nan dani akwai matsala "wacce irin matsala ?zan
maka bayanin komai idan mun isa gida daga haka bai sake cewa komai ba yaja motarsa
a guje suka fara qoqarin ficewa koda segun ya fito har motarsu ta fice daga
ma'aikatan ."
Wani irin gudu yaya sadam ke falfalawa akan titi yana cikin gudu ya hango wasu
motoci gudu uku abayansu suna biye dashi idan ya rage gudu suma sai su rage gudu
haka idan ya qara gudun motar zasu qara "maryama kamar ana binmu ki fad’a min meke
faruwa ? ta kasa magana kawai ta fashe masa da kuka dan bazata iya fad'a masa
abinda mai kamfanin creation yayi mata ba ,ya zama abun kunya gareta ace ta fad'a
masa wani kato ya ta'ba mata jiki ya zai dauketa ina yarda da yayi mata ?"kuka ta
cigaba da yi shi kuma yana falfala gudu akan titi shi kansa kana kallonsa kasan a
matukar tsorace yake sun yi tafiya mai dan nesa sannan suka nemi motocin uku dake
biye dasu suka rasa sai daf daa zasu fita daga ogun state kawai sai ga motocin
guda uku sun sha gabansu."cak yaya sadam yaja burki ya tsaya cikin tsananin
fargaba wasu tika tikan murd'ad'd'un mutane suka shiga firfitowa daga cikin motar
d'aya bayan d'aya har suka fito gaba d'ayansu sanye da kaki wanda ke nuna alamun
sojojin nigeria ne wani irin matsanancin tsoro da firgici ne ya kama marayam tayi
saurin riko hannun yaya sadam gam cikin nata jikinta na kyarma shima ya riketa
gam bai yi tunanin ko yan fashi da makami bane sakamakon kakin dake sanye
ajikinsu zuciyarsa tafi bashi wani abu dabam ,mutun uku daga cikin sojojin suka
qaraso da sauri suka bugi kofar motar da karfi batare da 'bata lokaci ba kofar ta
bude basu tsaya wata wata ba suka fito da yaya sadam tare da buga masa bakin
bindiga nan take ya zube kasa .”
maryama ta saki qara mai sauti ta fito ta durkushe gabansa cike da matsanancin
tsoro yaya sadam ya janyota zuwa jikinsa ai kuwa ta kamkamesa dan gabad'aya a
tsorace take hawaye né ya soma bin kuncin maryama cikin sheshekar kuka maryama ta
soma magana "bayin Allah laifin me mukayi maku ?dan Allah karku cutar da ni da
mijina ,dan allah ku barmu mu wuce tunda nasan bamuyi maku laifin komai ba "ke ce
bakiyi mana laifin komai ba amman shi wannan bakin munafikin yasan abinda yayi
mana "inji cewar daya daga cikinsu da sauri maryama ta tsurawa yaya sadam idanunta
tana kallonsa "wai kai dan rainin wayo ko ?mu zaka rainawa hankali ?".a d'an rud'e
yaya sadam yace "Nifa duk ban fahimceku ba hasalima ban san laifin da nayi maku
ba ,su waye ku ?meye hadina daku ?laifin me nayi maku ?ya jera masu tambayoyin yana
sake riko maryama jikinsa "kai karka nemi ka rainawa kanka hankali dan ubanka kayi
tunani laifin daka aikata acikin satin nan wanda kai kanka kasan dole zaa iya
bibiyarka?".
yaya sadam yayi shiru yana nazarin maganr shi dai asaninsa bai aikatawa kowa
laifin komai ba baya ga auren maryama da yayi "har kusan minti biyar yaya sadam bai
ce uffan ba yasa suka cigaba da magana "me taurin kan tsiya kawai amman tunda baka
tuna ba idan kaje lahira zaa maka bayani dalla dalla akan taurin kan da kayi ,kai
jojo ku daukosa mu aikasa lahira yadda yayi taurin kai dan son more duniya bazai
zauna a duniyar ba "nan da nan suka rufe masa ido da bak'in kyalle ,suka d'aure
masa hannayensa duka abayansa kafafunsa ma a d'aure ,suka rufe masa baki suka
ciccibosa suka watsa shi acikin mota "itama yarinyar kuyi mata kamar yadda kuka
masa ku sata acikin mota ku had'a daita batare da 'bata lokaci ba aka rufe fuskarta
aka tasa keyarta cikin mota tunda tashiga motar take rutsa kuka mai ta'ba zuciya
tare da kiran sunan Allah yayinda yaya sadam yasa hannuwansa duka ya dafe goshinsa
yana zurfafa tunaninsa alokacin da motocin suka karya kwana cikin wani kungurmin
daji mai cike da duhu da ban tsoro suna sharara gudu."
tunanin duniya yaya sadam yayi amamn iya tunaninsa bai ga wanda zai iya masa haka
ba idan safiya ce yasan baa akansa zata huce ba sai dai akan maryama tunda tasha
fad'a masa muddin taganta sai ta aikata lahira ."nadiya kuwa yasan kwata kwata
bazata masa haka ba shi kuwa wa yayiwa laifi ?"idan ma laifi ne to sai dai akan
auren maryama da yayi ne to waye wanda zai masa hk ?bai samu amsar tambayarsa ba
yaji motocin sun ja wani irin burki sun tsaya a daidai karshen dajin tare da
bubbud'e kofofin motocinsu a zuciye, na karshen ne ya fito rike da kwalar rigar
yaya sadam wanda babu halin yin kwakwaran motsi ballantana yasamu damar yin ihun
ceton ransa da'ake barazanar raba shi dashi, ahankali suka shiga jansa a k'asa suna
tafiya dashi cike da tsansar rashin imani , wanda kallo daya zaka masa kasan a
rikice yake d'aya daga cikinsu ya rike hannun maryama ."
Basu tsaya akoina ba sai a bakin wani katon rami suna huci "ku binnesa da ransa jin
haka yasa maryama ta rikice ta gigice tashiga wage wage tana kiran sunan yaya sadam
"dan girman allah karku kashesa karku binnesa da ransa gara ku kasheni wallahi
banason na rasashi yana da matukar mahimanci arayuwata na bada rayuwata fansa, gara
ku dauki raina ku barshi dan Allah karku kashesa duk wani abu da zaku masa kuyi min
ni daman nafi bukatar mutuwa da rayuwata dan bana jin dadin rayuwar nan na rasa
komai karku bari na rasa mijina tausayinta ya kamasu "d'aya daga cikinsu ya jawosu
gefe yace "me kuka ga zaa yi ?"ya tambayesu "kar mu batawa kanmu lokaci wajen
tausayi mu cika aikin daaka ba mu "shikenan a wuce gurin .”
aiko suka dauki yaya sadam suka jefa cikin rami suna shirin jefa maryama mutun daya
acikinsu wanda shine yafi jin tausayin maryama yace mu barta tunda daman shi kadai
aka bamu aiki "okay! suka amsa. a matukar gigice take batasan ya’akayi ba ta zare
kyalen da suka rufe mata ido dashi tana gama bude idanunta yaya sadam dinta ta gani
acikin rami suna zuba masa kasa zuciyarta ce ta tsaya cak ta daina aiki a lokaci
har suka rufesa da ransa ."
Bayan sun gama suka hau jijigata a gigice ta dawo haiyacinta idanunta na zubar da
hawaye wani razananniyar qara ta saki da karfi tana kiran "ina mijina yake ?idan
har kun kashesa ku had'a dani ku kashe dan allah karku barni a raye dan bazan iya
rayuwa babu shi ba haka ma mahaifiyarsa ." numfashi suka sauke atare "aikin gama
ya gama yarinya tuni mijinki mai taurin kai yana cikin nan suka nuna mata inda
suka binnesa, an gama da labarinsa sai dai uwarsa ta haifi wani idan an sake
haifosa a duniya bazai sake kinjin magana ba "ai tana gama jin maganarsu
numfashinta ya soma barazanar d’aukewa "me yasa ?me yasa zaku masa irin wannan
hukuncin inna lillahi wa inna ilaihi rajiun me yasa zaku kashesa tayi taku biyu
zata isa inda suka binne mata miji kafafuwanta suka gagara daukarta ga wani irin
nauyi da kanta yayi idanunta suka fara rufewa jiri take gani nan take ta zube kasa
sumammiya ."
Mmn Sudais
💗💗💗💗💗💗
MAR'ADAMS
💖💖💖💖
💗💗💗💗💗💗
*AYSHA A BAGUDO*
WATTPAD @HAUESH
AREWABOOKS USERNAME
AYSHAABAGUDO
bismillahirrahmanirrahim
Wannan littafin na kudi ne mai bukatar karantashi byn na kammalashi zai biya
1000 ta wannan account number din 1438775094 Aishat abdullahi access idan an tura
sai a turawa wannan 09136918331 alert domin tabbatar da an tura domin sauraron
littafaina a tuntubi chaneel dina (Hausa bakwai ) a YouTube.
Page 26
Ran ATA a matukar 'bace yake zaune acikin jirginsa yana tunanin maryama ,wani
irin ciwo yake ji a zuciyarsa dan bazai iya misalta yanayin bugun zuciyarsa ba ,ga
wani sara da kanshi ke masa har baya iya bud'e idanunshi sosai yayinda kowani
second 'bacin ransa na sake nunkuwa wanda baya raba d'ayan biyu damuwar maryama
ce bai san dalilinsa na kai hannunsa jikinta ba ."mai yasa yaji sauyi ajikinsa
adalilin sake d'aura kwayar idanunshi akanta ?"mai yasa yaji yana buqatar ganin
fuskarta a zahiri ?
yana jin wani irin sauyi akanta lallai yana buqatar ganin halittarta a zahiri
zuciyarsa ta amsa masa kuwan haka ." da wannan tunanin ya isa gida alokacin da
magariba ta kawo kai .jirginsa mai saukar ungulu na gama tsayawa a haraban gidansu
rai a 'bace yake tattaka matattakala yana qoqarin saukowa , kai tsaye ya shiga
bangaren mami sosai yake jin damuwa acikin zuciyarsa qoqarin danne damuwarsa yayi
dan kar hankalin mami ya tashi sai dai kallo d'aya tayi masa ta fahimci akwai
damuwa atattare dashi ."
"muryarsa a kasalance ya gaishe da mami ."kamar ko yaushe ta amsa masa
tana mai tsura masa kwayar idanunta kamar wacce taga wani sabon halitta ,cike da
kulawa tace "sannu da zuwa adamcy ya hanya ka dawo lafiya ?da sauri ya amsa mata da
"lafiya !"yana qoqarin hayewa samansa hannunsa d'aya soke acikin aljihun
wandonsa .bayansa tabi da kallo "shigowarsa cikin wannan yanayin yasa duk mami ta
d'an rikice kasa samun kwanciyar hankali tayi ,cike da tashin hankali ta mike tsaye
tabi bayansa .
ahankali ta tura kofar parlour'nsa ta shiga duhu falon dan haka ta kunna wuta nan
da nan haske ya haskaka koina a parlour'n sai dai bata gansa ba dan haka ta nufi
hanyar bedroom dinsa ta shiga nan ta iskeshi tsaye ya jingina jikinsa da bango
d'akin yayi sama da kanshi hawaye ne kwance acikin idanunshi yana jin yadda
zuciyarsa ke tafarfasa ya rasa meke masa dadi arayuwarsa bai san ta ina zai fara ba
,komai ya rigada ya tsaya masa gabad'aya baya jin dadin rayuwarsa ,ya kasa
fahimtar kansa ko kuma yace yau tazo masa da abubuwa da yawa wanda duk tarin damuwa
ne akan wanda yake ciki ya dinga jin kamar ya kashe kansa ya huta da rayuwar da
yake ."
lumshe tsumammun idanunshi yayi sai ga hawaye sharrr na bin kuncinsa "adamcy nah !
".mami ta kira sunansa cikin tsananin tashin hankali har jikinta na rawa . amatukar
firgice ya tsaida kwayar idanunshi dake cike da ruwan hawaye akanta qirjinsa na
wani irin dokawa da sauri dan bai ji motsin shigowarta ba sai sautin muryarta wani
irin zazzafan numfashi ya sauke yana sake maida kanshi sama tare da ciro hanky ya
shiga d'auke hawayensa"lafiyarka kake zubar da hawaye adamcy ?ta tambayesa cikin
tsananin tashin hankali dan duk abinda zai sashi zubar da hawaye baqaramin abu
bane da muninsa ya wuce misali. shiru yayi ya kasa magana dan bai san me zai fad'a
mata ba "kayi min magana mana adamcy dan kasa har zuciyata ta fara tsinkewa."
da yatsan hannunsa ya nuna mata daidai saitin zuciyarsa dake bugawa fiyye da
kaida ."sake matsoshi tayi sosai tana cewa "meke damunka "?"zuciyata sweet.."
yana kai wa nan yayi shiru ya kasa cigaba da maganar idanunshi na sake cikowa da
ruwan hawaye"me ya samu zuciyarka ?" ta sake tambayarsa hankalinta na qara tashi "I
don't know what's wrong with me sweetheart amman dai nasan zuciyata kullum ciwo
take min"."inna lillahi wa inna ilaihi rajiun " allahumma rahmataka arjun fala
takilni ila nafsiy d'arfata'ai wa aslihli shahni kullahu la ila a illa anta "abinda
mami ta shiga furtawa kenan tana sake maimaitawa " i know something is wrong with
my heart wallahi sweetheart akwai ciwo mai zafi acikin zuciyata wanda zai iya
kasheni nan kusa .."
nan da nan fuskar mami ta qara sauyawa hankalinta a matukar tashe tace "ka dinga
sausautawa kanka adamcy da yawon tunani ,ka dinga addua akan duk abinda ya dameka
addua tana canzawa bawa qaddararsa kuma tana saka natsuwa acikin zuciyar bawa
"numfashi ya sauke da karfi yana furzar da iska mai zafi daga bakinsa ,magana yake
son yi amman zafin da zuciyarsa keyi ya hana shi cewa uffan "kasamu natsuwa adamcy
ka dinga furta wannan adduar zaka samu natsuwa da sausauci a wajen Allah zai yaye
maka dukkanin damuwarka "allahumma rahmataka arjun fala takilni ila nafsiy
d'arfata'ai wa aslihli shahni kullahu la ila a illa anta ahankali ya sauke
idanuwanshi ya tsura ma mami kawai yana kallonta cikin yanayi na tsanani damuwa
"ka sani idan wani abu ya sameka nice farkon wacce zata fara shiga damuwa ga kuma
d'an cikin jikin maryam wanda bamu san abinda zata haifa ba karka bari muyi
maraicinka. adamcy kasan yadda nake sonka idan na rasaka zan shiga damuwa a
kullum adduata na mutu na barka a duniya ba ka mutu ka barni ba tunda ta fara
magana bai ce mata uffan ba sai ma ciro wayarsa da yayi ya soma neman layin
likitansa muryarsa ce ta katse mami daga maganar da take masa ahankali yake magana
tamkar mara lafiya "doctor kazo ka dubani please ".daga haka bai sake cewa komai ba
ya katse kiran d'akin yayi tsit tamkar babu mutane acikinsa ."
Ahankali ya soma d'aga kafafunsa zuwa Kan gado ya fad'a ya kwanta flat ransa duk
babu dadi yayinda idanunshi na kallon saman d'akin babu abinda yake gani sai kwayar
idanun maryama da yatsun hannun ta da sautin zazzakar muryarta mami tazo ta zauna
kusa dashi tana daura hannunta saman kansa tana masa sannu "bayan mintuna
shabiyar sai ga doctor ya shigo tare da sallama tashi yayi ya zauna ya jingina
bayansa da abun gado yana sauke numfashi da kyar tare da yiwa doctor bayanin yadda
yake ji batare da 'bata lokaci ba doctor ya fara masa gwaje gwaje bayan doctor ya
gama yayi masa allura sannan yace "ranka ya dade jininka ne ya hau kad'an yana da
kyau ka dinga saukakawa kanka wasu abubuwa dan zuciyarka na bukatar hud'u yanzu
dai nayi maka allurar bacci in sha allahu kana tashi zakaji daidai Allah ya baka
lafiya ya ajiye masa magunguna yace zai wuce ."mami tayi masa godiya adaidai
lokacin da doctor ke had'a kayansa yayi mata sallama ya wuce ."
"Ka tashi kayi sallah magriba kafin bacci ya d'aukeka sannan me za'a kawo maka
coffe ko tea "any one sweetheart." ya furta tare da mikewa da kyar ya shiga
bathroom ita kuma mami ta fita kawo masa coffe dan tasan shi yafi bukata wanka ya
fara sannan yayi alwala ya fito ya cire kayan jikinsa ya canza zuwa jallabiya
brown colour mai ratsin baki ya isa inda abun sallarsa yake ya gabatar da sallah
bayan ya idar ya koma Kan gado ya kwanta lamo tare da janyo bargo ya rufe jikinsa
koda mami ta dawo d'akin ATA na bacci ta zauna gefensa tare da zuba masa idanunta
tana jin wani irin qaunar d'anta na ratsata bata iya dogon fushi dashi hakazalika
bata son ta rasa shi. hawaye ne ya fara bin kuncinta ji take a duniya data rasashi
gara ta rasa komai dan idan ta rasashi ta ina zata cigaba da rayuwa?" ina bazata
iya ba bazata iya jurar rasashi ba gara ita ta bar duniyar tun kafin taga mutuwarsa
ahankali ta mike tana goge hawayen idanunta ta qarasa ta rage masa karfin ac sannan
ta canza masa wutar d'akin zuwa mara haske ta duka daidai fuskarsa tayi masa addua
sannan ta fita daga d'akin ."
Washgari tun da yayi sallah ya koma bacci har karfe goma bai tashi ba yana
kwnace yana sharar bacci shigowar mami yafi sau uku dubashi yana bacci sai dai ta
kalli fuskarsa ta fita sai wajen shadaya da wasu mintuna ya tashi hanyar
bathroom ya nufa ya fad'a yayi wanka ya fito yana goge sansar jikinsa ya sanya
kananan kaya masu matukar kyau he look very attractive kullum ka kallesa qara kyau
yake ya d'auki kwalbar turare yana feshe jikinsa yana fesa turare kwakwaluwarsa na
tunanin maryama da sauri ya ajiye kwalban turaren hannunsa ya qarasa inda ya ajiye
kayansa na jiya daya cire ya dauki dogon wondonsa ya shiga laluba wondon cikin
kankanin lokaci ya ciro agogon sarkarta .yayi shiru yana kallon agogon yana ganin
tsinysiyar hannunta aciki "mai yasa zuciyata ta damu akanki ? zuciyarsa tace
"kasani ko ubangiji ne ya turo maka ita cikin rayuwarka da wata manufa a boye kayi
duk yadda zakayi tayi aiki akarkashinka sosai ya dinga jin damuwa akan abinda yayi
mata abu ne da bai tabayi ba .wai ya kai hanunsa jikin wata mace da sunan ta
burgeshi ya dauki kusan mintuna goma yana kallon agogon tsarkar sannan ya bud'e
durowarsa ya jefa ciki ya fito yana taku . "
cike da isa yake taka step, tun daga kan step yake jiyo sautin muryar baba qarami
yana tafiya da kyar har ya sauko kasa ya tarar da mami zaune a inda ta saba zaman a
parlour'n gabanta kuma baba qarami ne zaune yana magana cikin tsananin fushi tunda
yayi masa kallo d'aya ya dauke kanshi bai sake kallon inda suke ba ya wuce dining
ya dibi abinci da kanshi ya a zauna akan kujerar dake kallon step bayansa kawai
zasu iya hangowa haka zalika duk abinda suke fad'a yana jinsu bayan ya gama cin
abinci ya d'aga kanshi yana kallon agogon dake manne a parlour'n dake walwalin
haske karfe 12:00 na safe ne yanzu mikewa yayi ya qarasa gurin mami yace
"sweetheart ni zan fita mami tace "kai da baka da lafiya ina kuma zaka ka dinga
hutawa dan Allah ?" numfashi kawai ya sauke batare da yace komai ba "ka zauna akwai
maganar da babanka yazo dashi shiru yayi yaki zama "banason musu kayi abinda nace
"a natse ya samu waje ta zauna still bai kalli inda baba qarami yake ba bare ya
gaishesa "magana ce yazo daita akan hindu me kasani akai ?zuciyar ata a dake ya
fad'a mata komai game da abinda ta aikata ."
baba qarami ya kalli ata yana jin haushi irin haushin da mutun zai iya kashe mutun
"na dauka ko wani ka ga yayiwa hindu haka sai inda karfinka ya qare kuma zaka
taimaki rayuwarta amman wulakanci ka bar min 'ya a tsare har tsawon watani sannan
aka wuce daita gidan yari bancin na tashi tsaye da haka rayuwarta zata qare .
tsakanina da kai adamu allah Ya isa ban yafe maka ba duniya da lahira "kayi hakuri
baba qarami duk abun bai kai haka ba zai sa a sakota in sha allahu "wani irin kallo
ata yayiwa mami ta juyo ta kallesa a tsanake tace "me yasa kayi haka adamcy ?
dokarki nabi kikace a dauki mataki akan duk wanda yayi yunkurin kashe miki maryam
ko ba haka ba ?mami tayi shiru tana dubansa sam bashi da tsoro akan komai "naji
amman kasa a sakota bana jin ma itace zata aikata haka "kiyi hakuri sweetheart babu
ta yadda zaayi na saka baki saboda abinda ta aikata mummunar laifi ne kuma ta amsa
da bakinta ta aikata "a gidan ubanka ta amsa haka ?"
"mugun kawai mai mugun hali ni nasan hindu bazata aikata hakan ba sai dai idan
azabtar daita akayi yasa ta amsa laifin da ba nata ba gefen bakinsa ya ciza da
karfi "nifa duk abinda zaa fad'a akaina ba damuwata bace idan kuna da hujjar da
zata wanke kanta tayi ,ku kuma ku sake shigar da qara kotu amman ni Adam bazan saka
baki a fito da tantiriya yar tasha irinta ba." tayi laifi kuma ta amsa laifinta
dole hukuma ta hukuntata ni na gama magana sweetheart ko zan iya tashi ?"daga baba
qarami har mami suka zuba masa ido suna kallonsa ranshi fess ya mike yayiwa mami
sallama ya wuce yana fita ya iske masu tsaronsa a inda suka saba tsayawa suna
ganinsa suka qaraso da sauri cike da girmamawa suna gaishesa atakaice ya dinga amsa
masu batare da bata lokaci ba aka bude masa bayan mota ya shiga suka bar gidan a
can parlour'n mami kuwa hakuri kawai take bawa baba qarami tana tabbatar masa
lallai hindu zata fito ya bar komai a hannunta da kyar ta samu ya wuce sai dai
kallo daya zaka masa kasan ransa a bace yake kuma zai iya aikata komai akan adam ."
*****
Bangaren maryama kuwa har karfe goma na dare babu su babu labarinsu, aunty da umma
da habib da sauran yanuwan ummah wadan da suka zo biki da dangin mahaifinsu da
basu wuce gida ba duk suka damu sukai ta neman layinsu amman shiru ga dai
wayoyinsu yana ringin amman ba d'agawa nan fa hankalinsu ya tashi matuka zuciyarsu
ta fará tsinkewa gabad'aya suka taru acikin parlour'n umma cikin jimami da tashin
hankali ."Allah sarki umma duk yadda take jin mummunar faduwar gaba da tsinkewar
zuciya amman sai ta dake ta kasa nunawa kowa damuwarta da yanayin da take ji sai
ma ta dinga kwantar masu da hankali tana cewa "babu komai wata killa yanayin aikin
ne ko kuma ababen hawa né sukai yawa a hanya "haka suka kwana zaune cikin tashin
hankali da zullumi ."
washegari kuwa tun da asuba fari habib da a bokinsa faisal suka d'auki hanyar ogun
state kasamcewar duk inda maryama zata aiki tana tura masa address gabad'aya habib
baya cikin natsuwarsa ji yake kamar zuciyarsa zata buga hakan ne ma yasa sam baya
ganin gudun da motar tasu take akan titi har ma yaji kamar su fita su canza wata
motar kamar bazasu kai ba sai gashi sun karaso jikinsa na tsuma kamar wanda ake
zubawa ruwan zafi suka dauki hanyar ma'aikatan isarsu ke da wuya aka sheida masu
sunzo amamn tun a yammacin jiya suka wuce
cikin tsananin tashin hankali habib ya shiga kiran number aunty kira d'aya ta
dauka tana kiran sunansa nan dai habib ya sheida mata komai
tunda aunty ta kira sunan habib idanun ummah ke kanta tana jiran ta gama wayar
taji mai zata fad'a ganin yadda ta fashe da kuka tana salati yasa ummah ta dawo
kusa daita jikinta na wani irin rawa "balkisu meke faruwa mutuwa sukai ko me ?
"Cikin muryar kuka aunty tace "ummah wai tun da yammacin jiya suka baro kamfanin
salati ta saka tana addua tare da karfafa zuciyarta data aunty "karki damu balkisu
babu abinda zai samesu koma menene in sha allahu Allah zai kawo masu mafuta ta
fad'a tana share hawaye "gsky ummah ina ji ajikina akwai wani abu dake faruwa
dasu." numfashi ummah ta sauke cikin karfafa ma aunty zuciya "haba bilkisu ki daina
wannan tunani kisa aranki babu abinda zai samesu "Allah yasa amman tun jiya da
yammaci suka baro kamfani amman har zuwa wannan lokacin babu su babu alamunsu "ke
dai kiyi masu addua kawai ta fad'a cike da tausayawa kanta dan ita kanta tana ji
ajikinta akwai wani abu dake faruwa dasu sai dai tana fatan ya zama alkhairi
arayuwarsu gabad'aya."ta mike ta shiga dakinta ta zauna cikin tsananin tashin
hankali hawaye ne ya dinga zuba daga idanunta ahankali idanunta ya sauka akan frem
din hoton sadam dake ajiye akan qaramar durowarta yana sanye da kananan kaya ya
daura rigar sanyi akan kayan idanunshi manne da bakin glass ,tayi shiru kawai tana
kallonsa kallonsa take saboda shi kadai ne ya rage mata a duniya bata da uwa bata
da uba bata da miji yanzu idan wani abu ya samesa dole zata shiga damuwa ta qarasa
zancen zuci tana fashewa da kuka mai ban tausayi "in sha allahu bazan rasaku ba
sadam da maryama ina maku fatan alkhairi a duk inda kuke Allah ya dawo mun daku
cikin koshin lafiya ."
suna nan zaune cikin tsananin jimami da tashin hankali har yamma sai ga habib da
abokinsa ajigace suka karaso gida sakamakon yanayin damuwar da suke ciki cikin
tashin hankali aka kira baba gali da sauran yan'uwan dangin mahaifinsu cikin
kankani lokacin suka hallara dan daman suna bangaren aunty hassana .bayan sun gama
jin komai suka fara zuba ruwan maseefa hajiya fatima tace "ai duk abinda ya faru
laifin umman sadam ne dan itace ta basu gudunmuwa tafiya , inda take shiga batan
take fita ba nan da nan sauran yan'uwa suka kama ita dai ummah shiru tayi kawai
tana karanto duk adduar datazo bakinta ita yanzu batasu take ba yadda ya'yanta zasu
dawo gareta take ."yadda suka wuni jiya cikin tashin hankali haka suka wuni yau din
ma dan har karfe 12:00 na dare ba labarinsu ummah tace kowa yaje ya kwanta aga zuwa
gobe ."washgari baba gali da habib da sauran yanuwa maza suka bazama nemansu har
ogun state din aka sake komawa sai dai babu wani labari duk hankulansu a tashe yake
aunty kuka kawai take ummah kam tayi dauriya habib ma kuka yake yana kiran sunan
maryama da yaya sadam abun gwanin ban tausayi ."
bangaren aunty salma kam abun yayi mata dadi fiyye da tunanin mai karatu ,dan
adduar mutuwa ma ta dinga masu ,allah yasa mummunar hatsari suka samu a hanya
"burinta daman maryama ta bar duniya ko kuma tayi rayuwar kaskanci ko zama babu
aure. sai gashi burinta ya cika batare da ta 'bata kudinta ba ,tana zaune baba
gali ya shigo ya tsaya akanta "salma ina fatan dai babu hannunki cikin rasa sadam
da maryama ?wani irin kallo ta watsa masa "idan da hannuna me zai faru ?Aa to gsky
ni dai babu ruwana kuma muddin da hannunki Kiyi maza kisa a dawo dasu "gsky a wasu
lokutan sai naga kamar kana bin bayana amman kuma wani lokacin sai naga kana nuna
min wariyar launi ,kai yanzu meye damuwarka dan an nemesu an rasa kai daya kamata
kaji dadi kayi farinciki an nemesu an rasa maryama bazata yi rayuwar jin dadi a
gidan ba zata bar ya'yanmu suyi rayuwarsu cikin jin dadi ko da yake shi kanshi
yusif din yanzu mun rasa gane kanshi ko shekaranjiya da suka zo daurin aure da
abbansa bai leko inda muke ba da alamun aikin daakayi masa ya fara barin jikinsa
sai an sabanta wani sabo ".
"ni yanzu ba wannan bane damuwata ki fad'a min gsky da hannunki a rashin dawowar su
gida ko babu hannunki ciki ?"ta sosa idanunta da hannunwanta duka tace "babu hanuna
!"to amman ai shekarajiya naji kina waya da malaminki kina cewa ayi duk yadda zaayi
a salwantar da .."kaga dakata daka ji ina magana cewa nayi a salwantar dasu duka
ko maryama ?to ai ni ko maryama ma bana son ta rasa rayuwarta bare kuma sadam
"tsaki taja tana turo masa baki "ai daidai ne ma idan sadam ya mutu idan bakasani
ba bari na fahimtar da kai, idan sadam ya mutu kai ne zakaji dadin rayuwarka dan
duk wani abu daya mallaka zai zama naka halak malak kai da sauran yanuwanka
hassalima naka ne zai fi na kowa yawa tunda bashi da magaji ,mahaifiyarsa ce kawai
ita kadai ranta kuma bazata gajesa ba "kinji zaki sake lalata komai ni dai bana son
ran kowa ya salwanta a hannuna ".yana gama fad'ar hk ya fice tabi shi da kallon
kaskanci tana ta'be baki "ina ganin shima wannan sokon sai nasa an gama min dashi
gabad'aya na huta tai murmushi "wallahi ina farinciki da rashin dawowarsu allah
yasa ko gawar su kar agani ."
Maryama kam cikin wani jahili gida su jojo suka nufa daita a sume can wajen gari a
tsakanin lagos to ile ife , gida ne na sirri wanda ba kowa yasan dashi ba gida ne
da mai gidan ya gidana domin taronsa na sirri ko kuma duk sanda zai holewarsa ko
kuma wani meeting sannan yana ajiye mahimman abubuwansa agidan ,gida ne mai hawa
daya kuma agyare yake babu abinda babu acikinsa najin dadin rayuwa gida ne
wanda babu wanda zai san an shigar da mutun sai su da kansu idan sunyi raayin asani
." a babban parlour'n sukai masauki tare da wanda ya basu aiki shima kuma ba
gidansa bane gidan abokinsa ne ya amshi key a hannunsa kai tsaye ya nufi bedroom
suka biyosa da maryama kan wani makeken bed din dake dakin ya nuna masu suka
shimfideta "aikin
ku yayi kyau sosai fa .gabad'aya suka kwashe da dariya shikenan an kashe boss kowa
ya huta sosai kuwa suka amsa masa atare tsaye yayi yana kallonta yana sauke
numfashi yana lashe lip's dinsa "kusan wani abu ?gabadaya suka girgiza masa kai "da
alamun yarinyar nan ta shiga comer?nima abinda na fahimta kenan "idan dare yayi ku
dawo ku dauketa ku bar nan daita domin bata da wani sauran amfani agareni , ku
dauketa ku kaita duk hospital din da kuka ci karo dashi amatsayinku na sojoji
bazaayi wani bincike akanku ba, kuce kun tsinceta ne a hanya cikin wannan
yanayin ."an gama!" zuwa gobe zakuji alert dina "okay babu matsala ."
Da misalin karfe goma ba daren ranar mutun biyu acikinsu suka fitar da maryama
wacce bata san halin da'ake ciki ba suka nufi wani hospital daita yadda akace suyi
haka sukai suka ajiyeta da wayarta da jakarta suka qara haba taimakon gaugauwa aka
fara bata sai dai har zuwa washegari bata farfado ba har sanda aka kira number
number wayarta suka dauka tare da sheidawa wanda ya kira halin da'ake ciki ."
Kallo daya zaka yiwa su ummah ka tabbatar da cewa baa cikin nutsuwa walwala da
kwanciyar hankali suke ba, tunda suka duro hospital bayan wayar da sukai da
ma'aikatan hospital din ,daman kuma tun ranar farko da tafiyarsu sadam din basu
sake samun isashen bacci da nutsuwa ba har sai da suka daura kwayar idanunsu akan
maryama "me ya sameta haka da har ta fice hayyacinta bata gane kowa?,me ya kawota
asibiti "ina sadam da suka ganta ita kadai kwance rai hannun allah? kamar kar su zo
ta fara sambatu tana kuka tana kiran sunan yaya sadam tana fad'ar irin abinda
akayi masa aunty Kuka ta fashe dashi cikin tsananin tashin hankali tana bubbu
qasa tana fad'in "inna lillahi wa inna ilaihi rajiun "dan allah karku kashesa
dan Allah ku fito min dashi daga cikin rami ,su waye suka sakaku wannan aikin ku
fad'amin wanda ya sakaku zan mika masu rayuwata dan bana son na rasa yaya
sadam .wannan mummunar kissar dani yafi dacewa bada bawan Allah kamar shi ba dan
Allah ku fito min dashi "tana ihun fad'ar haka sai taji anfasa wani razanannen
kuka akanta mai kukan tana fad'ar "lahaula wala kuwwata " me ya samu sadam
shikenan kin kaishi an kashe mana shi"inji cewar aunty hassana ummah kam kalmar
innalillahi wanna ilaihi raji'un kawai take furtawa "wannan yarinya me yayi miki
da zaki sakamasa da wanna muguwar sakayya."?
farkawa maryama tayi ta ganta akan gadon hospital cikin yan'uwanta dana
ummah ,ummah ta riko hannunta cikin nata tana mata sannu aunty kam kuka kawai take
tana furta adduaoi, cikin haka doctor ya shigo ya sallamesu gabdaya domin duba
jikin maryama sai bayan daya fita suka dawo dakin suka cigaba da zage zage har sai
da ummah ta dinga taka masu burki , duk wanda zai yi magana sai ummah ta hana tare
da cewa yaje waje maryama na bukatar hutu a qarshe dai daya bayan daya suka fice
sai daga baya suka dawo har dare babu wanda ya sake cewa komai sai da irin kallon
da suke binta dashi babu sausauci ."maryama dake kwance cikin tsananin tashin
hankali ta zuba ma ummah dake zaune a gefenta ido tana dubanta ,itama umma ita din
take kallo duk ta fita haiyacinta yadda idanunta suka kunbura sukai wani irin girma
sun bata tsoro matuka yayinda gabad'aya fuskarta tayi jajur saboda kuka ahankali
ummah ke mata nasiha tana tofa mata addua wani irin yanayi maryama ta shiga
alokacin da idanunta da kwakwaluwarta suke sake hasko mata komai daya faru ."
a natse ta dinga bin kowa dake gurin da ido sai dai taga wani irin mugun kallo suke
mata zuwa can taji aunty hasana na cewa "ji yadda take bin mutane da kallo wannan
yarinyar fa muguwar munafuka ce dan allah tashi ki fad'awa mutane inda kika kai
mana d'anmu daga rakiya ai wallahi baki isa ba sai kin fito mana dashi dan shi
kadai muke kallo a matsayin mahaifinsa ."mikewa maryama tayi jikinta a sanyaye har
ga allah tafisu bukatar yaya sadam arayuwarta sannan yadda suke nuna mata baya mata
dadi duk da tasan basa qaunarta amman batayi tunanin zasu zargeta ba kanta ta
daura akan cinyar ummah tasa kuka tare da jin wani kullin abu ya tsaya mata yaki
gaba yaki baya "ummah ce ta dinga rarrashinta tana yiwa aunty Hasana fad'a "wallahi
ummah bansan mutane nan ba bazan iya cutar da mijina kuma danuwana ba wallahi ina
son yaya sadam ."
"nasani maryama bazaki ta'ba iya aikata hk ba cikin jin dadin kalaman ummah
maryama tasa kuka tana cewa "ku taimakeni ku nemo min yaya sadam domin ban san inda
zan saka rayuwata ba tana kuka ummah na share mata hawaye duk da itama hawayen take
sosai hankalin mutane ya tashi kowa kuka yake a wajen ".
"ummah Kiyi hakuri ki yafe min nayi nadamar fita wannan aiki ban san me ya jani na
aikata haka ba kuma wallahi na daina farinciki da iya wannan aiki da nayi
arayuwata ummah kuzo muje inda aka binne yaya sadam da ransa zaa iya samunsa a raye
ina ji ajikina bai mutu ba hawaye umma ta share amman maryama kwanaki biyar kenan
da faruwar wannan alamarin kina ganin zai rayu "?numfashi ta furza mai zafi
"ummah !"sai kuma tayi shiru tana wani irin kuka tana tuna kalamansa na qarshe
gareta "abinda nake so dake maryama ki natsu sosai kiyi abinda ya kawoki ina
sonki ina kuma alfahari dake na kuma yarda dake a duk inda zaki kasance nasan zaki
kame min kanki da kuma mutuncina wani sabon kuka ta fashe dashi "ummah ta riko
hannunta gam cikin nata itama kuka ta fashe mata dashi sosai cikin tsananin tashin
hankali tana kiran sunan allah tana cewa "laifin me d'ana yayi masu wannan
hukuncin yayi tsauri ga rayuwar sadam babu wanda zuciyarsa batai rauni ba aunty da
wasu daga cikin yanuwa hawaye suke dan tausayawa ga umma d'aya bayan suka dinga
barin dakin inda dakin ya saura daga aunty sai ummah da maryama "umma muje inda aka
binne yaya sadam a fito dashi jikina na bani yana nan a raye ummah ki tausaya min
wallahi bazan iya rayuwa babu shi ba "ki samu natsuwa maryama in sha allahu zamu je
gobe"iya abinda ummah ta iya fad'a kenan bata sake cewa komai ba dan bazata iya
magana mai tsawo ba ."
washegari aka kai maganar gurin hukuma aka shigar da qara tare da nuna hoton yaya
sadam daga nan aka yiwa maryama tambayoyin daya dace sannan aka saka maryama gaba
sai hanyar ogun state tafiya suke tana share hawaye tana addua duk kwanar data gani
sai ta rikice tace nan ne . sai an tsaya tace a’a ba nan bane ahaka suka kusan
kaiwa cikin ogun state dan daga inda suke suna iya hango sambaod din wel come to
ogun state tayi sauri tace “ kamar kafin mu kawo wannna sambaod din ne .”cak direba
dake tukasu ya tsaya tare da juya Kan motar suka koma dayan hannun sun sha wahala
sosai a qarshe dai ta gane daidai inda sojojin suka sha gabansu saka makon warin
takalminta data gani yashe a gefen titi .” jikinta na rawa ta soma kuka tana cewa
"ku tsaya nan ne !"batare da bata lokaci ba suka firfito “tabbas anan ne suka sha
gabanku “ta fad’a tana kuka .daya daga cikin jami’in tsoro yace a ina aka binnesa
nan maryama ta hau zazzare ido “tabbas daga nan suka rufe mana ido amman duk da
haka jikina na bani wannan kwayar suka shiga damu basu mutsa mata ba suka shiga
mota suka bi hanyar tafiya suke amman jikin maryama rawa yake dan bata son tayi
kuskure wajen gano wajen .”
gabad’aya babu inda baa duba ba ko zaa ga alamar tudun kasa amman babu ,jami'an
tsoro suka tsaya suna kallonta "kin tabbatar nan ne?tayi shiru tana share hawaye
dan gbdy ta rikice ummah Ummah duk ta rude sai zufa take fitarwa ta matso kusa
daita tace “maryama ki natsu da kyau a samu a gano inda suka binnesa” tayi mgnr
cikin rawar murya maryama ta fashe da kuka tare da zubewa kasa sakamakon ta rasa
mafuta.”dan kwakwaluwarta ta cunkushe waje d’aya yadda maryama take kuka haka umma
take kuka tana janyota jikinta gabdaya jikknta ya d’auki zafi kamar garwashin wuta
yayind jami’an tsaro suka cigaba da dudduba wajen ko zasu ci karo da tudun kasa
amman still dai babu wata alama inda aka binnesa ganin suna bata alokacin su ne
yasa suka ce su wuce zaa zaa sanar a gidan radio da tv maryama kam duk ta gama
rikice masu sai sunan yaya sadam dina kawai take kira “ku nemo min shi dan Allah
karku barni haka da kyar aka samu aka saka acikin mota suka kama hanyar gida .”
******
Shabiyu ne na rana yana tsaye acikin office dinsa sanye da t shirt long
sleeve light puppy da wondo baki sai tie baki zagaye da wuyansa ya tura hannuwansa
duka cikin aljihun wondonsa wani irin kamshi jikinsa ke fitarwa mai sanya natsuwa
da kwantar da hankali fuskar nan tashi a murtuke zariya ya soma yi acikin office
din yana tunanin maryama wanda bai san dalili ba tunaninta yaki barinsa babu
abinda zuciyarsa yake kwadayin sake gani kamarta kafin ahankali yayi burki a
daidai mazauninsa turo kofar office din akayi batare da an nemi izinin shigowa ba
ya kalli kofar ammar ya gani yanayin yadda yaga fuskarsa ya dan fahimci akwai wani
abu yana gama shigowa ya soma magana cikin tsananin fushi "burinka ya cika maryama
tayi aure “
“so what idan tayi aure what’s my business with her ?wai menene matsalarka
adam ?"da nayi me kenan ?wallahi ban san baka da sa'a arayuwarka ba sai da maryama
tayi aure "tô ni menene damuwa ta da aurenta ?kaga dan Allah karka sake min maganar
ta karka qara min damuwa akan wanda nake ciki "kai ne kuwa kake da damuwa
daita ."hade rai ata yayi sosai yana yiwa amar wani irin mugun kallo mai bugar da
zuciya "kasani inada dalilina na son ku hadu daita tun kafin tayi aure.ata yayi
taku daya biyu yana mai juya masa baya wallahi da ka daure kaga maryama da zaka
fahimci abinda na gani har yasa nake son ku hadu daita."
juyowa ata yayi ya fuskancesa yana hura masa hanci tare da kai hannu yana sunce
tie din wuyansa "kai ma tunda kaga na na nace ai ya kamata kayi amfani da sense
dinka ,bazaka ta'ba jin dadin wata mace a duniya ba sama daita" look ammar bana son
damuwa ,"my friend you have to use your common sense and think akwai dalili mai
karfi dayasa naso ku hadu "ata ya sauke hanunsa daga wuyansa ya maida cikin
ajihunsa yana nazarin maganar ammar "ba dai ka rasa maryama ba kasani zuciyarka
zatayi nadama fiyye da kowani nadama da d'an adam keyi a rayuwarsa "ya d'ago ya
tsurawa ammar idanunshi tare da cire hannunsa d'aya cikin aljihunsa ya rike
kugunsa," wasu ma suna janyota jikinsu domin su amfana daita bare kai da ..."wai
meye haka ammar ?ka dameni ka cika min kunne da surutun banza da wofi dole ne sai
na aureta ko dole sai na janyota jikinta ?"kaga enough please ka rabani da maganar
wata maryama din banza bana son jin ko sunanta bare na aureta "yayi maganar a
tsawace yana furzar da iska mai zafi "ai kuwa ka shiryawa shiga tashin hankali da
damuwa domin duk ranar da zaka ganta kuma amatsayin matar aure sai kayi nadamar
rashin haduwarku akan lokaci ,kuma lallai bazan daina fad'a maka rashin haduwa
daita damuwa ne akan damuwa kuma har qarshen rayuwarka bazaka daina da kasani ba
kai in takaice maka zaka iya rasa ranka ". ata ya dafe goshinsa da hannunsa daya
"ammar kana rikita min kwakwaluwa zuciyata tana tsinkewa magangunka gabad'aya suna
nema tarwatsa min zuciya gabad'aya na kasa fahimtar abinda kake nufi yayi maganar
kamar zai yi kuka tare da zama akan kujera yana kallonsu "you are mad adam yanzu
abinda ya rage maka ka zauna kayi tunani akan maganganuna " yana gama fad'ar haka
ya buga masa table din gabansa ya juya ya fita a fusace ."
ata ya kai hannu goshinsa kafin daga baya ya soma jujjuya jikinsa akan kujera wani
irin ihu yayi yana kai hannusa ya ture tarin file din dake Kan table sannan ya mike
tsaye zambur Kmr zaki ya dafe kanshi gabad'aya ya rasa meke masa dadi dan wani
irin abu yaji yana yawo acikin ilahirin jikinsa mai kama da abinda yake ji akan
mafarkinsa yau shine karo na biyu da yaji wani abu wanda ya shafi mafarkinsa akan
wata mace "wacece mai zanen creation wacece maryama datai aure coz the same abu
yake ji akansu wanda yake da kusanci da abinda yake ji akan mafarkinsa “karka matso
kusa dani domin bazan ta'ba kasancewa cikin wawayen mata masu cin amanar mazajensu
ba itama matar aure ce “ya rabbi what’s wrong with me ?yana cikin wannan halin
james yayi knocking yana neman izinin shiga sai da ata ya dauki lokaci sannan yace
"coming !" ya shiga cikin taka tsantsa "mai gida ina son nayi magana da kai ko zan
iya magana ?" leave!" mai gida magana ce mai mahimanci "I said leave bana bukatar
jin komai yanzu."da sauri ya juya ya fice .cikin company ranar kam kowa ya kama
kanshi dan dukkanin alamun sun nuna an tabosa, duk kuma wanda yayi kuskuren shiga
track dinsa zai sha bala'i idan ma bai ce ya kori mutun ba har ya dawo gida maganar
ammar na damunsa cikin rai sai yayi kamar ya kirasa ya sake masa karin bayani
sai muguwar zuciyarsa ta gargadesa "
Bayan sati d’aya wanda yayi daidai da kwanaki shabiyu da daura auren maryama da
yaya sadam sultana ta dirá a kasar kuma kai tsaye abdullahi estate aka nufo daita
murna wajen aunty abida abun baa magana ,tun daga lokacin da sultana ta shigo
estate din aunty abida ta fara aiwatar da shirinta kullum suna bangaren mami sai
dai basa samun ganin ata suna samun sa’banin shiyasa yau sukai sakamakon
yau .ahankali yake ssukowa daga Kan step cikin shigarsa na kullum sai kamshi yake
idanunsa bai sauka akan kowa ba sai akan aunty abida da sultana kallo daya yayi
masu ya dauke idanunshi ya cigaba da taku har ya wucesu ta mike ta sha gabansa
tana kiran sunansa “adamcy barka da saukowa.” ya tsaya kawai yana kallonta batare
da yace mata komai ba “ga sister ta kawo mana ziyara Ya ganta ta hadu ko ?still dai
bai tanka mata ba tayi murmushin yake tana cewa “daman nace bari na kawota ku gaisa
sultana ga cup din tea dinsa can dauko ki bashi .” jikinta na rawa ta juya ta
dauko Orenge cup din dake ajiye wanda daman dan shi aka tanada ta mika masa ,sai
dai bai kar’ba ba yace "am okay coz am oready late” zai wuce ta sake tsaidashi Ya
tsaya cak yana duba agogon dake daure da tsintsi yar hannunsa kamr yadda kasani
sultana kanwarmu ce kuma ta kware a harkar zane dan naji ance kana bukatar
kwararun masu zane shiyasa nace tazo dan tasan Kan aikinta sosai idan bazaka damu
ba ko zaka bata dama kaga irin nata kwarewar ?shiru yayi bai ce uffan ba “.
“nasan bazaka ta'ba zuba ma yaruwarka kasa a ido ba zaka gwada yaruwarka kaga irin
nata baiwar bayan shi ma ina son ka taimaka ka bata aiki a maakatarku Z&A idan ma
da hali ka barta a kusa kusa da kai wato P.A dinka dan na yi imani zaka ji dadin
aiki daita dan ....”duk naji bayaninki.” ya katseta ta hanyar fad’ar haka kafin ya
cigaba tayi saurin cewa “ zata joining compaing kenan ? kai amman na gode sosai
sultana bana fada miki ba bashi da matsala gashi da sauki kai ga kirki da son
yanuwa gyaran murya yayi yace " ammm karki yi Godiya tukun dan bani zan bata
aikin ba kiyiwa mijinki magana I know he can do more that for her “mijina kuma ?tai
masa tmbyr tana kallonsa tare da nazarin maganarsa tana kallonsa ya zagayesu ya
kama gabansa “nifa Aunty duk ba wannan bane matsalata ni dai kawai kisan yadda
zakiyi na kasance a kusa dashi nasan komai zai zo da sauki “amman yanzu a gabanki
kikaji ina masa magana zaki ce bakiji abinda yace ba, wai nayiwa Ibrahim mgn
Ibrahim din da ba wuri daya suke ba .”
Dan allah ayi min afuwa posting zai koma a sati sau daya sakamakon bana samu lokaci
ga hidima da mai gidana ga business ga typing sannan ina bukatar hutu Kunga abun
yayi min yawa ina maku fatan alkhairi sai Saturday ko sunday in sha allahu.”
Mmn sudais
💗💗💗💗💗💗
MAR'ADAMS
💖💖💖💖
💗💗💗💗💗💗
*AYSHA A BAGUDO*
WATTPAD @HAUESH
AREWABOOKS USERNAME
AYSHAABAGUDO
bismillahirrahmanirrahim
Wannan littafin na kudi ne mai bukatar karantashi byn na kammalashi zai biya
1000 ta wannan account number din 1438775094 Aishat abdullahi access idan an tura
sai a turawa wannan 09136918331 alert domin tabbatar da an tura domin sauraron
littafaina a tuntubi chaneel dina (Hausa bakwai ) a YouTube.
Page 27
Jiki a sanyaye ATA ya fito cikin 'bacin rai daga d'ayan bedroom dinsa wanda ya
rasa dalilin 'bacin ransa , a yanzu kusan kullum ransa a 'bace yake azaba yake ji
sosai a cikin zuciyarsa so yake ya rabu da damuwar dake damunsa amman ya rasa
yadda zai yi ,cike da natsuwa yake taku acikin d'akin yadda jikinsa ke fitar da
kamshi mai sanyaya zuciya haka d'akinsa ke d'auke da kamshin dad'ad'an turarukan
sa .a natse ya d'auki farin glass dinsa ya manna a kwayar idanunshi sannan ya
qaraso ya d'auki agogon fata mai tsada ya d'aura a tsintsiyar hannunsa, ya bud'e
bedside domin ya d'auki wallet dinsa." ya kai hannu ya d'auka ya tura a bayan
aljihun wondonsa yana qoqarin rufe bedside din ne idanuwanshi suka sauka akan
agogon sarka hannun maryama daya zamo cikin hannunsa a wancan ranar ,yayi shiru
yana kallon agogon yana jin wani iri a gaba d'aya ilahirin jikinsa, ya kusan minti
goma tsaye yana cigaba da kallon agogon gabansa na wani irin bugawa da sauri sauri
tunowa da yayi matar aure ce yarinyar yasashi jan dogon tsaki yana ciza lip's
dinsa."
A dogon koridoor suka hadu da sultan bai kallesa ba bare ya tsaya duk da yasan
wurinsa yazo ya ra'ba ta gefensa ya wuce ,har yayi taku biyu ya jiyo sautin
muryarsa " Adam...! ya kira sunansa a gadarance har yanzu kai muke jira da
mahaifinmu domin muna da bukatar wani kaso daga cikin kafanuni araba abamu namu
kowa yaci gashin kansa, cak ATA ya tsaya daga tafiyar da yake ya zura hannunsa
daya cikin ajihun wandonsa "idan naki fa ?yayi mgnr batare daya juyo ba " dole kabi
umarnin mahaifinmu dan bazamu cigaba da aiki akarkashinka ba alhalin dukiyar nan
gabadaya tamu ce dan dole kayi wani abu akai .”a fusace ATA ya juyo gabadaya ya
fuskancesa "kasani wannan dukiyar gabadayanta ta mahaifina ce kamar yadda na
fad'awa mahaifinka yau da rokona kukayi zan iya daukar wani bangare na bawa
mahaifinku amman tunda zalinci ne abun bazan bada ba kamar yadda na fad'a kuma zan
iya dakatar da duk wani mai numfashi dake d’akinku wanda yake karkashin ma'aikatar
nan idan kace karya ne ka cigaba da shiga track dina "shiru ne ya biyo baya"kafin
ahankali ata ya wucesa yana jan tsaki tare da furta "nonsense."
*****
Zaune ata yake akan kujera sanye da suit baki yana jujjuya jikinsa bayan ya watsawa
chief adisa tambayoyi cikin 'bacin rai ,cheif adisa yayi shiru yana nazarin abinda
zai fad'a masa "answer me !ya furta cikin tsananin bacin rai mara misaltuwa "komai
zance yanzu bashi da wani amfani sir tunda na rigada nayiwa sectary dinka bayani
komai "Eh nasani but ina son naji daga bakinka ,yayi maganr yana gyara zama tare da
daddana system din gabansa batare daya dago kanshi ba , dalilin dayasa muka daina
amsar produc din design dinku sunyi matukar tsaida ne,dan alal hakikanin gsky
kudin daaka sa sunyi yawa yayinda muke samun exactly irin design din a wasu wurare
akan farashi mai sauki atakaice dai wannan shine dalili."
shiru ata yayi byn ya gama sauraronsa ya cigaba da tura sakonni kafin daga baya ya
dago kanshi a hankali ya kafe cheif adisa dake zaune a gabansa da ido yana qare
masa kallo ta cikin farin glass dinsa sai daya furzar da iska mai zafi sannan ya
bude bakinsa da kyar yace "kasan abinda abu original yake nufi ? cheif adisa yayi
shiru ,"wadan da kuke siya a sauran compaing's copy din namu ne, namu kuma asalin
masu kyau ne ". ba maganr quality ake yi ba sir maganar contitie akeyi kafa san
dan kasuwa duk wani dan kasuwa yana bukatar farashi mai sauki wanda shine
business, da dai zaa cigaba da bamu farashin daaka saba ne sir da komai zai tafi
normal ".ATA ya sauke numfashi yana jan tsaki " ko ku siya a haka ko kuma ku barshi
domin bazan rage naira daya daga farashin dana saka ba yana gama fadar haka yace
"get out .cheif adisa ya mike tsaye tare da cewa "okay sir ya dauki system dinsa
ya qara gaba tsaki yayi ta ja babu kaukautawa ,ya mike tsaye ya shiga zariya acikin
office dinsa yana shafa sumar kanshi.”
ATA na tsaye a parlour'n mami ya zuba hannunwansa duka cikin aljihun wondonsa
dawowarsa kenan daga office ko cikakken minti biyar bai yi da shigowa ba sai ga
fahad ya shigo a matukar fusace kamar an jehoshi yana cewa "wai kai dame kake
takama ne ?yayi mgnr yana nunasa da d’an yatsantsa .""what do you mean ?ATA ya
tmbyesa a tsawace yana watsa masa harara a lokacin da hjy zulai ke qoqarin saukowa
daga saman ata "bani zaka tmby ba kamata yayi ka tmbyi dakikiyar kwakwaluwarka ,
taya ma zaka yanke wannan banza hukunci haka?"lafiya fahad ! ? " mami ta tambayesa
cikin rawar jiki “wannan yaron ne mana yake son jawowa mutane asara ,yana yin abu
tamkar shi kadai yafi kowa waye wa da ilimi
yau ko kamfanin ba group bane ai bai cancanta yayi haka ba bare yasan wannan
kafanin ba nasa bane shi kadai .ya qarasa mgnr yana kallon ATA a fusace .
Suna cikin haka sai ga yaya Ibrahim shima cikin tashin hankali ya rufesa da fad'a
nan mami ta koma kansa "ki duba ki gani mami yadda farashin komai na kaya ya
sauko daga sauran kamfanoni amman shi tashi daya ya qara farashi nikin baninkin
gashi costumers sunki karba kaya daga hannun kowa "very good ."ata ya furta yana
hura hanci “What ?
" I said very good ,"ya sake maimaitawa a natse tmkr maganar ba daga bakinsa ta
fito ba “very good ma zaka fad'a saboda baka da hankali da tunani "yes of course it
good and to be your last warning da zaka kirani da mara hankali ."yaya Ibrahim bai
damu da abinda ya fad’a ba yace “me yasa zakayi haka adamcy ?” me yasa zaka bata
kasuwancinmu maganar gsky muddin haka zaa cigaba da tafiyar da kamfanin gara kowa
ya watse a rufe kamfani kowa ya kama gabansa "okay wannan shine daman shirina ai a
rufe kowa ya kama gabansa "Ibrahim da fahad suka kallesa a rude suna mai mamakin
jin abinda ya fad'a " yes haka nake so "okay saboda kasan kana da wasu
compaines masu zaman kanka shiyasa kake son a rufe wannan ?"yayi kyau yayi kyau
gara daka fad'a mana muka sani ."ai daman mugunta ne acikin cikin wannan mugun mai
girman kan , kai ne dai ka kasa ganewa kake daukarsa amatsayin mutumin kirki ai ga
irinta nan zai janyo kowa ya rasa saboda tsabar bakinciki irin nasa da dai a rufe
gara a siyar a bawa kowa hakinsa "inji cewar fahad .
Dan allah fahad ka samu natsuwa kai ma Ibrahim ka natsu kar wannan abu ya zama
damuwa " karki damu mami ba wani abu bane ai bazamu biye masa ba zanyi komai
domin naga business din ya tsaya da kafafunsa "ko kuma a siyar ba nifa gara a siyar
dashi inji cewar fahad "wannan kuma karya ka fad'a dan matsawar ina raye babu
wanda ya isa ya siyar da AGC "mu zuba mu da kai dan halak ka fasa yadda kake ji
da taurin kai muma muna ji dashi a qarshe zan maka gargadi ka rage wannan zakewar
da jijji da kai idan ba haka ba wallahi zaka rasa rayuwarka a banza kuma babu
abinda zaayi "yana gama fad'ar haka ya juya fuuuuu ya fice har zai bi bayansa mami
ta sha gabansa da sauri tare da ware hannuwanta “karka kuskura kabi bayansa ,kana
jin mutun yana ikirarin zai kasheka ya kashe banza shine zaka bi bayansa
“sweetheart ki barni babu abinda zai iya yi “wallahi bazan barka ba idan kai baka
son rayuwarka ni ina da buqatar ka a raye ,oya koma can ka tsaya ko ka wuce
d’akinka, tsayawa ya kasa furta komai yana cin ransa .”
yaya Ibrahim yace" idan har baka bari an sauko da komai ba ina tabbatar maka gobe
goben nan zan bar aiki a kamfanin ."so what idan ka bar aiki ? ya kallosa a fusace
yana huci ,ka sani ni kasuwancina ba kamar na kowa bane kuma nasan kan business
dina kuma babu wanda ya isa acikinku ya janye daga hukuncina "enough adam ya fad'a
a tsawa ce shima tmkr zai maresa shima AD yayi kusa dashi sosai yana zaro masa
idanuwanshi da suka gama canza kala tsabar bacin rai "ka sausauta muryarka akaina
Ibrahim " idan ba haka ba me zakayi ? "Zan... zan canza maka kamani yanzu ya fad'a
yana huci kamar zaki .shima sai da mami ta shiga tsakaninsu "wallahi adam ka raina
ne kana magana dani kamr bakasan tazzrar dake tsakaninmu ba, kai duk abinda yazo
bakinka kake fad'awa mutane da wadan da suka girme maka da saaninka "adam ya
furzar da iska mai zafi daga bakinsa yana hura masa hancin "dan allah ku daina
fad'a akan dan wannan matsalar duk ku kwantar da hankalinku komai zai daidaita kai
adamcy wuce d'aki .
naunayen ajiyar zuciya ya sauke yana furzar da iska acikinsa sannan yayi wani juyi
ya hau step da sauri sauri yake taka step yana cewa "babu wanda ya isa ya canza
tsarina shi kuma wancan d'an iskan zai gane kurensa har ni zai yiwa barazana da
mutuwa ? bayansa suka bi da kallo har da suka daina hangosa sannan yaya Ibrahim ya
kalli mami "dan allah mami kiyi masa magana nasan ke kadai zaki fad'a masa yaji
mutane bila adadin ne suka dogara da wannan kamfanin me yasa zai yi qari ? ban san
me yasa zuciyar adam bata da tausayi ba wallahi idan bai sauke raayinsa ba akan
wannan matsalar am sorry to say mami zamu samu babbar matsala dashi ."
Mami ta riko hannusa ta qarasa dashi kan kujera ta zaunar dashi taje ta dibo ruwa
mai sanyi a glas cup ta dawo ta mika masa " sha ruwa Ibrahim ka samu natsuwa " bai
yi mata mutsu ba dan yana bukatar ruwan ya karba ya sha kadan ya mika mata cup
yana sauke numfashi "kayi hakuri kaji ibrahim ka bar komai a hannuna kamar yadda
kace maganata kawai yake ji ,zai ji da izinin allah duk yadda kuke so zaayi ya
sauke numfashi yana cewa "na gode sosai mami allah saka miki da alkhairi dan
allah kiyi kokari ki sauko da adam nasan yayi haka ne da wata manufa amman ya duba
mutane dake amfana da ma'aikatan ba wadan da suka bata masa rai ba in sha allahu
zai ji kuma zaka ga canji " allah yasa ya fad'a tare da mikewa ya rusunawa yayi
mata sallama ."
tsaye yake a d'akinsa yana faman zariya yana cika yana batsewa "har ni fahad zai
wa barazana da mutuwa ?daga yanzu bazan cigaba da daukar wulakancinsu ba a hankali
yake magana yana balbale botiran gaban rigarsa ya cilla rigar a saman gado ya saki
numfashi da karfi tare da kwance agogon dake daure a tsintsiyar hannunsa yayi taku
biyu ya ajiye a inda ya saba ajiyewa.jkinsa na tsuma ya tsura wa mirrow idanunshi
yana kallon kansa gabadaya sai yake jin rashin dadin abinda yayi sam sam bai kyauta
ba kuma ya tabbatar da maganar Ibrahim gaskiya ne mutanen da zasu shiga damuwa idan
mummunar abu ya samu da kanfani suna dayawa amman bazai ta'ba daga wa kowa kafa ba
ya furta a fili yana jan tsaki ya juyo ya fad'a kan katifa "
Mami ta hada abinci a qaramin tire kamar yadda ta saba dan abinci idan ba daga
hannunta bane baya ci saboda tsoro abinda zai cutar da rayuwarsa a natse ta nufi
kofar parlour'nsa ta wuce bedroom dinsa ta shiga yana kwance flat akan gado ya
daura hannuwansa duka à faffadan qirjinsa ."
Ta ajiye tiren abincin akan wani qaramin table wanda daman dan cin abinci aka
tanadeshi ya mike a hankali daga kwanciyar da yayi ya zauna ya hade hannunwansa
wuri daya bata tace masa komai ba kamar yadda shima bai ce mata komai ba ta dauki
plet da spoon din abinci data shigo dashi ta kai bakinsa ahankali ya dinga amsa
yana ci har sai data fahimci ya koshi ta ajiye sauran ta sakar masa murmushin
farinciki tare da kamo hannunsa cikin nata kafin tayi magana ya motsa labbansa
ahankali "na gode sosai sweetheart allah ya bar min ke "ameen adamcy nah kai ma
allah ya bar min kai bata nemi tayi masa mgn akan lamarinsa dasu Ibrahim ba ta
barshi har ya dan sauko hira ta soma janshi ."Ahankali ahankali ya dinga biye mata
suka shiga hira ta tsakanin uwa da d'a a qarshe ta shigo masa da maganar .”ka zama
mai hakuri da yanuwanka adamcy dan baka da kamarsu sannan ka zama mai tausayi
domin kai ma kana buqatar tausayawar ubangijinka , akwai mutanen da kamfaninku suke
ci suke sha suke komai na rayuwarsu ka duba allah da ire iren su ka sauko da komai
sai kayi tawassali da aikin alkhairin da kayi ka roki Allah wata buqata kaga yadda
Allah bazai maka ba “babu abinda nake buqata sweetheart kamar mafarkina ina
tsananin son kasancewa daita “ya fad’a acikin ransa.”mami ta dade tare dashi har
sai data ga bacci na qoqarin daukarsa sannan ta barshi ta shafa sumar kansa.”
tana tsananin son danta bata qaunar abinda zai kawo masa damuwa arayuwarsa yanzu
shiyasa ma tayi qoqarin danne damuwarta akan matsalarsa da maryam tunda yace bai
so ta hakura har abada Allah ya raya abinda zasu samu blanket ta janyo ta lullube
masa rabin jikinsa ta fito daga dakin ." bacci mai dadi ata yake yana rungume da
hannunwansa cikin baccinsa ya fara mafarkinsa wanda a qalla ya kusan wata uku bai
yi ba koma yace fiyye da haka ,yarinyar daya saba gani ita ya gani sai dai wannan
karon cikin mawuyacin hali ya ganta acikin wani kungurmin daji gashin kanta duk
ya hargitse ya zubo gadon bayanta tana gudu tana ihun kiran sunansa da iyakacin
karfinta cikin haka wasu mutune guda uku maza suka biyota tana gudu suna binta
har sai dai ta bace masu amman ita bata daina gudu acikin dajin ba juya ne ya soma
dibanta kanta ya soma juyawa tana kokarin zubewa kasa sai gashi ya qaraso gareta
ya tarota da hannuwansa duka sukai zube kasa tare ." lumtsatsun idanunshi ya tsura
mata yana kallonta yana kiranta da sunan da yake kiranta dashi dan tuni numfashinta
ya dauke ganin halin da take ciki yasa hankalinsa yayi mugun tashi ya kamo
hannunta yana murza tafin hannunta cikin sauri amman still bata tashi ba hakan yasa
ya hade bakinsu waje d’aya ya fara tsotsa yana sake hade hannuwansu ya cigaba da
murzawa ."
Yana shan bakinta hankalinsa na tashi dan jijiyarsa tuni ya tashi, ahankali
numfashi ta ya dawo ta soma bude idanunta har ta budesu akanshi still bakinsu na
hade ya kasa cire bakinsa cikin nata ,hannuta ta kai ta shafa gashin dake kwance a
fuskarsa wanda hakan yasa ya zare bakinsa a nata yana dubanta .ahankali idanunshi
suka sauka akan tudun brest dinta nan take yaji shaawarta ta kamashi ya rungumeta
ajikinsa tsam ajikinsa yana shafa bayanta naunayen ajiyar zuciya ya sauke Jin
yadda jikinta ya dauki zafi gbdy jikinta yayi sanyi ya sake "su waye wadan nan
mutanen dake binki ?shiru tayi babu amsa "me kika yi masu suke binki ?shima shiru
tayi masa ya zareta ajikinsa ya tsura mata ido ina ne gidanku ?sai lokacin ta
motsa jikinta ta nuna masa wani doguwar hanya ya mike daita rungume ajikinsa da
hannunta ta dinga nuna masa hanya har suka qaraso wani gida mai get kai tsaye suka
shiga da gudu yaga wata mata tayo kansu tana kuka , tasa hannu ta karbeta a
hannunsa ta kwantar daita ajikinta yana qoqarin bude bakinsa yaji "allahu akbar !!
Kiran sallahr daaka kwalla daga masalacin gidansu ne ya farkar dashi agigice ya
mike ya zauna a tsakiyar gadonsa gbdy zufa ne ke tsiyaya ajikinsa gabansa sai faman
bugawa yake ,jijiyarsa yaji ya harba da sauri yabi jikinsa da kallo yadda gabansa
ya tashi sosai gbdy ruwan shaawa ya jika masa qaramin wondonsa nan take ya dauke
idanushi dan ba wannan bane damuwarsa halin daya ga princess dinsa ne ya damesa ko
a wani hali take ciki "oh my god a ina zangaki princess ?ya jima zaune yana tunani
har lokacin sallah yyi ya sauko ya shiga bayi ."
Da misalin karfe goma na safiya yana zaune ya dan jingina jikinsa akan wani karamin
table a dakinsa yana tunani mafarkinsa na jiya bai ta'ba mafarki mara dadi akanta
ba sai jiya "ina jin sonki sosai princess ko a wani hali kike "wacece wannan? yaji
sautin muryar mahaifiyarsa da sauri ya dawo haiyacinsa yace "ba kowa ! ya bata
amsa Kmr zaiyi kuka "karka ce haka adamcy na shigo dakin nan kayi zurfi cikin
tunani ta qarasa mgnr tare nufar inda wordrobe dinsa yake ta ajiye masa kayansa ta
dawo kusa dashi" kana damun rayuwarka dayawa adam numfashi ya sauke yace "
sweetheart bazaki fahimci halin da nake ciki ba ta sauke numfashi tare da dafa
kafafansa" fad'a min naji zan fahimceka shiru yayi yana tunanin abinda zaice mata ,
ganinsa ko ya fad'a mata shirme zata dauki maganarsa kamar yadda ta saba kawai
gara yace mata babu komai ya hutar da rayuwarsa muryarsa a sanyaye yace babu abinda
ke damuna numfashi ta sauke "bazaka iya boyewa mahaifiyar komai dake damunka ba
fad'a min me kake tunani ?shiru yayi yayinda abinda ya gani a mafarkinsa yana sake
dawo masa kamar a zahiri ."
"sweetheart !
Sai kuma yayi shiru yana girgiza kai kana kallonsa kasan yana cikin damuwa "ya kayi
shiru ina jinka ka fad'a min abinda ke damunka adamcy fuskar yarinyar ya soma gani
acikin kwayar idanunshi cikin muwuyacin hali " tell me what's the matter ".dan
allah sweetheart ki fahimceni akan abinda zan fad'a miki "uhm ina jinka gskiya
akwai abinda yake damuna amman akan mafarkina daman har yanzu kana mafarkinta ne “?
ya d’aga idanunshi sama alamun tunani sannan ya saukesu akanta “na dan jima ban
ganta ba sai jiya na ganta cikin mawuyacin hali wanda yasani shiga damuwa sosai
nan ya shiga fada mata irin abinda ya gani duk sanda nayi mafarkinta tana min
murmushi tana min magana cikin sanyin murya sweetheart intakaice miki tana min
komai amman jiya duk babu sai tarin tashin hankali.”
shiru sukai gbdy byn second biyar ya motsa labbansa " sweetheart zan dage da yi
mata addua allah yasa ba wani abu ne ya faru daita ba "Ameen !"ya tsinci muryar
mami ta amsa da sauri ya kalleta "ina ma wannan yarinyar gasky ce adamcy ?amman
na sha fad'a maka mafarki ba gaskiya bane ."walalhi yarinyar nan da gsky ce da ina
tabbatar maka ko ina take zan nemo maka ita ka aurenta saboda na fahimci kana
tsananin sonta "."so much sweetheart ya furta yana dafe daidai saitin zuciyarsa
shiru hjy zulai tayi tana dubansa Kmr zatai masa kuka "ya allah kasa wannan
yarinyar gsky ce a duniya idan ba hk ba rayuwata zata qare cikin cakwakiya "Ameen
Ameen in sha allahu zata kasance gsky ta fad'a cike da tausayawa hawaye na kokarin
zubo mata .”ya mike ganin halin da mahaifiyar sa ta shiga sai dai saukowarta akan
mafarkinsa ya bashi gwarin gwiwa sosai da kuma tabbacin zai sameta” na gode
sweetheart bari naje na shirya naje office I have some work" bazakaci komai bane ?
"No !kawai ya furta ya nufi kofar bathroom yana layi .”tabishi da kallo ina ma tana
da halin ciremasa damuwarsa ina ma da yadda zatayi amman babu sai dai tayi imani
babu abinda yafi karfin allah zan tayaka da addua adamcy Allah ya sausauta
maka ."Idan kuma daga nice ya Allah ka sheida na yafe masa duniya da lahira ka
yaye masa wannan danuwar .”
****
bayan ya dawo daga d'aya cikin ma'aikatansa yana sauka idonsa da abida sukaci karo
dauke kanshi yayi ya cigaba da taku "AD !!!! ta biyosa tana kiran sunansa sai dai
bai tsaya akoina ba sai parlour'n mahaifiyarsa "ka tsaya kaji me zance mana cak ya
tsaya "uhm ina jinki ya fad'a yana duba file din dake rike ahannunsa "dan allah ka
bawa sister dina sultana dama just give her a chance wallahi zata maka abinda kake
so she can’t disappoint you zata maka zane kamar yadda zaka mata discreb din
abinda take so wallahi ta kware sosai kalli yanayin zanenta ka gani ."
Yayi shiru yana dubanta tare da dage girasa daya domin dai duk ya fahimcesu so take
ta karfi da yaji ta tura masa kanwarta batasan shi din kwararren mai basira bane ta
miko masa takadar zanen da take rike dashi "just one chance AD." ke kikasan takware
sosai amman ni babu abinda zanyi da zanenta "ni dai kayi hakuri dan allah to idan
bazaka amince ba ka bata aiki akarkaahinka kamar yadda na nemi alfarma a tun farko
do it sake of me please tayi kusa dashi sosai tana magana kamar zata shige jikinsa
yayi saurin ja da baya yana mata wani irin mugun kallo "kace ka amince dan allah
"nifa bazan kawota kanfani da sunana ba amman duk wanda zai kaita banida matsla da
hakan "ya fad'a yana barin wurin gabadaya ya haye sama ta juyo a hankali ta bar
parlour'n ."
Umma zaune a gefen gadonta cikin tsananin tashin hankali da alhinin rashin
d'anta a lissafinta Kwanaki 90 kenan wanda yayi daidai da wata uku da rasa sadam
dinta hawaye ne masu zafi Ke fitowa daga idanunta yayinda kwakwaluwarta ke
hasko mata fuskar tilon d'anta "ta yaya zan iya jure rashin sadam arayuwata ?
zuciyarta tai mata tambayar "duk runtsi duk wuya zan jure domin na barwa allah
komai zan cigaba dayi masa addua kamar yadda na kewa mahaifinsa,shikenan sadam
ya tafi ya barni ni kadai a duniya alhalin bani da kowa bani da komai sai shi
kad'ai." ta qarasa mgnr wasu sabbin hawaye masu ciwo da radadi suna sauka akan
kuncinta .”ahankali ta mike tsaye ta qarasa Inda tangamemen hotonsa yake manne
da bangon d'akinta ta tsurawa hoton ido tana kallonsa "allah na gode maka akan
wannan jarabawa da kamin kasan ina tsananin son sadam arayuwata amman ka rabani shi
domin ka gwada imanina “allah nayi imani da qaddara da hukuncinka gareni ,na dai
shiga damuwa ne saboda tsananin kewa da sabon da nayi dashi amman zan gargadi
zuciyata zan sata tayi hakuri da rashin sadam domin nayi imani rayuwa da mutuwa duk
naka ne zan daina kuka ..." a hankali ta dinga furta kalmar zan daina kuka amman
still bata daina zubar da hawaye ba ."
tana cikin wannan halin maryama ta shigo d'akin cikin yanayi na sanyi jiki dan
zaune take a falo kananan maganganun su aunty salma ne yasa ta baro falon dan
bazata juri jinsu ba .kowa ya ganta yasan ta zube sosai akan yadda take daman kuma
ba wata mai kiba kirki bace sosai ta d'ashe tamkar mara jini dan haka ramarta ta
sake bayyana .”ahankali ahankali take d’aga qafafuwanta har ta qaraso ta durkusa a
daidai kafafun umma "umma ki daina kuka ."ta furta mata idanunta na kawo ruwan
hawaye "umma ta d'ago idanuwanta ta kalleta da tarin damuwa sannan ta d'auke
idanuwanta "umma nasan da wuya ki iya mantawa sadam koni bazan iya mantawa da yaya
sadam a rayuwata ba bare ke da kikayi silar zuwansa duniya amman dan girman allah
umma kuka nan ya isa haka kar wani mummunar ciwo ya kamaki na shiga uku ,".
“ wallahi ummah ban san ina matukar son yaya sadam zuciyata ba sai dana rasa shi
zuciyata na cike da matsanancin soyayyarsa "nasani maryama allah ya jikan sadam ke
kuma Allah ya baki hakurin rashinsa "ki daina furta hakan umma jikina na bani yaya
sadam bai mutu ba tunda na ji ajikina bai mutu ba tabbas bai mutu ba zai dawo
garemu ."umma tayi shiru tana sauke numfashi tare da ajiyar zuciya a duk lokacin da
taji maryam ta furta hakan ta Kan samu saukin zugin da zuciyarta keyi cike da
matsanancin soyayya ta kamo kafad'an maryama ta d'agata tsaye bisa kafafunta ta
rungumeta tsam ajikinta"maryama maganarki tana kwanatar min da hankali duk da nasan
da wahala ace sadam dina yana raye ."kusan minti goma suna rungume da juna kafin
daga baya maryama ta zare jikinta ta tsurawa hoton yaya sadam ido ."
A hankali ta kai hannu ta d'auki hoton ta koma kan gadon umma ta zauna tana cigaba
da kallon hoton tana shafa fuskarshi yayi matukar kyau sosai fuskarsa kwance da
murmushi "umman kin tuna ranar daya d'auki hoton nan ?cewar maryama" na tuna ranar
daurin auren mashkur abokinsa ne ta fad'a tana zama kusa da maryama"yaya sadam ka
dawo garemu karka barmu zuciyar ni da umma na matukar qaunarka bazamu iya jurar
rashinka ba dan allah ka dawo garemu ." shiru sukai gabadaya zuciyarsu cike da
tunani umma ta janyo akwatin kayansa ta fito da kayan sawarsa tana nikewa tana
maidawa cikin akwatin ,maryama ta d'auki jeans dinsa ta rike tana kallo kafin
ahankali ta motsa bakinta "karki damu umma zai dawo fa ".umma ta kalleta kawai dan
ita tasan bazai dawo ba har abada mutumin da'aka binne da ransa ta yaya zaayi
tunanin zai rayu har ya dawo ?"cike da sheshekar kuka tace "ya allah kabamu hakuri
rashin sadam domin zuciyoyinmu sun gaza hakuri akansa maryama ta matso sosai ta
kwanta ajikin umma cike da tsananin qauna "d'ana sadam mutumin kirki ne, d'ana
sadam mai kyakkyawan zuciya ne ,d'ana sadam mai hakuri ne gashi ya tafi ya barni
batare da kowa nasa da zan kalla naji sanyi araina ba."
“shikenan na rasa mai sakani dariya na rasa mai kawar min da damuwa na rasa mai
dibe min kewa."
ta qarasa maganar tana zubar da hawaye."maryam ta kai hannunta ta shiga gogewa umma
hawaye tana cewa “ karki damu umma zanyi miki duk abinda yaya sadam yake miki
sannan kuma kisa aranki zai dawo garemu mu cigaba da yi miki komai tare "
"Zo zo!! ku ga wani abun mamaki Aunty salma ta jawo hannun baba gali da aunty
hasanaa zuwa bakin kofar d'akin umma, kalli ku gansu "wannan matar anyi shasha an
kashe mata d'a amman dan shashanci ku kalli shirmen da take "ke yanzu wannan ne ya
dameki ? baba gali ya fad'a tare da juyawa ya samu waje ya tsaya suka biyosa suka
tsya kusa dashi suna dubansa bakinsu na son furta wani abu "salma ki rabu dasu
kawai mu dai muyi yadda zata dawo daidai kafin wannan yarinyar ta gama takaba
araba gado ,aunty salma ta saki murmushin jin dadi burinta zai cika "kai wallahi
ina cikin farinciki saboda kaso mai yawa zaka samu “sosai kuwa dan kaso biyu zanci
tunda ni nmj ne "ya qarasa maganar cikin tsananin farinciki wannan kuma haka ne
bari kama gabanmu su kuma suje su qarata da kukansu hawaye ne yayi masu yawa"
wallahi nima allah allah nake lokaci yayi araba abani kasona inji cewar aunty
hasana baba gali ya saki murmushi "ni Allah yasa a mallaka min kamfanin burodi gbdy
aunty salma tasa dariya murna kmr su rungume juna a wajen ."baba gali da aunty
salma suka fice suna dariya aunty Hasana ta shiga kitchen domin daurawa umma abinci
dan tun daaka nemi sadam aka rasa kusan rabin yininta anan take yi ."
Umma ta kai hannu ta shafa sumar kan maryama "allah yayiwa rayuwarki
albarka ,allah ya qara mana hakuri, muyita hakuri da sannu allah zai mana sakayy..
“qarar wayar umma ce ta katseta maryama ta mike da sauri ta shiga duba inda wayar
take "gashi can a karkashin pillow ta fad'a tare da d'auko wayar ta mika mata
cike da ladabi ta d'auka "assalamu alaikum, wallahi alhamdulillah mun godewa allah
ya kunfan jiki Aa da kanki ai da kinyi zamanki hjy ba sai kin wahalar da kanki ba
to shikenan allah ya kawoki lafiya sukai sallama " umma waye zai zo ?granny ce
"shiru tayi tana tunani , tashi muje parlour'n tare suka fito zuwa parlour umma na
kiran sunan "hassana "kanwar hajiyata na nan zuwa in sha allahu gobe ,hasana ta
fito daga kitchen tana goge hannunta tana cewa "kai allah ya kawo mana ita lfy ta
kalli maryama ta galla mata katuwar harara "maza ki d'auke wad'an mugayen idanunki
akaina aí mu dai wannan yarinyar ki zame mana balai a danginmu wai aunty yaushe
zata bar bangaren nan ne ta koma can gurin uwarta kar muma ta lashe mana kurwa ?
wallah duk san dana daura idanuna akanta ina jin kamar na kasheta ta mutu kamar
yadda ta zama silar kashe min dan danuwana dan girman allah ki sallema ta bar
bangaren nan mu huta da jaraba "ke dan Allah ya isa haka ina zata alhalin tana
cikin takaba? wallahi hassana banason abinda kike wa yarinyar nan yana matukar
kona min rai dame kike son yarinyar nan taji ?Ko ance miki ita ta kashesa né ?Kiyi
hakuri aunty in sha allahu na daina umma ta juya mata baya tana danne hawayenta
".amman Aunty ya kamata ki fito da kayan sadam tunda yanzu ya zama na magada
sai bawa yara su yi amfani dashi tunda ya mutu kafin wannan mayar ta gama takaba
araba gadonsa .."
"sadam bai mutu ba"maryama ta fada da iyakacin karfinta tana juyowa ta fuskanceta
tare da dafe qirjinta "tabbas sadam bai mutu ba ta qarasa mgnr tana kuka "yanzu ke
hasana har kina tunanin abinda ya mutu ya bari sun zama na magada ku kenan ?dan
kune magadansa sai ni da matarsa maryama nan da nan idanun umma suka cika da
kwalla ta shiga girgiza kai "wallahi hasana ki bani mamaki sam banyi tunanin haka
daga gareki ba "idan ma kiyi hakuri ni da kaina zan nemi araba duk abinda ya bari
domin allah ne yace araba gado ni ban isa nayi jayayya da hukuncinsa ba amman at
least kunyi hakuri ku daina daga hankalinku ,baku barni na huta ba baku bar
yarinyar mutane ta huta ba wai me yasa haka né ?karki manta maryama jininki ce
domin kinfini kusanci daita dan diyar yayankice uwa daya uba daya wallahi naso
sadam ya rayu kodan ya kula min daita ya gatanta min ita ya bata kulawar da duk
wani miji yake bawa matarsa ."ta qarashe mgnr tana kuka ".
maryam ma ta fashe da kuka ."Umma ko zaa raba abinda sadam ya bari dan Allah a
d'an jirkinta tukun har zuwa wani lokaci saboda har yanzu police suna Kan
invesgetion idan ya zamo yana raye fa bai mutu ba kuma an rigada an raba komai
nashi ni dai a nawa shawarar kar a ta'ba komai nashi hatta suturarsa abarshi tukun
nan." da wani irin mugun kallo ta d'auketa dashi " yanzu ke maryama kina tunanin
yana raye ? " bai raye yana raye ya kamata abari hukuma ta gama bincikenta
alabashi komai zaa yi sai ayi amman for now abar komai gsky
Tunda tasoma magna Aunty hasana tayi shiru tsaye tana mka maka mugun kallo, da
ashariya daga cikin zuciyarta "kaji min tsinanniyar shegiyar yarinya suka jiyo
muryar aunty salma gabadaya suka juya bayansu suna kallonta ahankali ta dinga taku
har ta qaraso inda suke "lafiyarki ma kuwa maryama ?gsky akwai alamun kin zauce
ayi hanzari akaiki asibitin mahaukata a duba lafiyar kwakwa kuwarki,"kece fa da
kanki kika tabbatar mana yaro nan ya mutu tunda a gabanki kika ce an binnesa da
ransa amman ki kekashe kasa akan bai mutu ba " wallahi aunty bai mutu ba dan
ina ..."ke jaira kiyi mana shiru anan kafin na zuciya na soma yar yar fa miki mari
sadam ya mutu kuma bazai dawo ba har abada idan ma zaki cire hkn aranki ki cire ki
fara tunanin wata rayuwa."
ta fad'a tana huci “wallahi bai mutu ,kuma babu mai raba gadonsa hasalima babu
takabarsa akaina ina nan ma tsayin matarsa har tsawon shekaru hudu “lallai
hasashena ya tabbata yarinyar nan ta samu tabin hankali “to tsaya kiji da kyau duk
macen da mijinta ya bata ne zatayi dakon aurensa na tsawon shekaru hudu sannan
bayan haka tayi idda idan kin haukace ne gara tun wuri musani amman rabon gado
tabbas zaayisa acikin gidan nan inji cewar aunty salma .”
Mmn sudais
💗💗💗💗💗💗
MAR'ADAMS
💖💖💖💖
💗💗💗💗💗💗
*AYSHA A BAGUDO*
WATTPAD @HAUESH
AREWABOOKS USERNAME
AYSHAABAGUDO
bismillahirrahmanirrahim
Wannan littafin na kudi ne mai bukatar karantashi byn na kammalashi zai biya
1000 ta wannan account number din 1438775094 Aishat abdullahi access idan an tura
sai a turawa wannan 09136918331 alert domin tabbatar da an tura domin sauraron
littafaina a tuntubi chaneel dina (Hausa bakwai ) a YouTube.
Page 28
Kwanciya maryama tayi a kasa tana wani irin kuka mai ta'ba zuciya da ban tausayi
sai dai duk wannan kukan da take sautin muryarta bata fita sosai ,tana jin ina ma
sautin kukanta ya fito fili da hakan zai fiye mata sauki fiyye da rashin fitowarsa
bugu da qari ko yasa yan'uwan mahaifinta sun sauko daga tsatsauran raayinsu su
tausayawa rayuwarta ta jurewa kowance irin jarabawar da Allah yayi mata amman ta
kasa jurewa wannan jarabawar, ta kasa jurewa jarabawar rashin miji da kuma d'anuwa
gareta."meye tarin zunubina?tayiwa kanta tambayar hawaye na sake gangarowa akan
kuncinta "ya Allah ka sausautawa rayuwata domin idan abubuwan dake faruwa akaina
suka cigaba da faruwa zuciyata zata buga ."idanun umma dake cike da ruwan hawaye
ta zubawa aunty salma tana kallonta cikin wani irin yanayi na tsananin damuwa da
bakincikin mummunan kalamanta ga maryama ."cike da tsananin tausayawa maryama umma
ta qaraso gareta ta durkusa ta riko tafin hannunta cikin nata cikin yanayin tashin
hankali tace "kukan ya isa haka maryama kada kanki yayi ciwo ."
"mai yasa abubuwa suke zuwa min haka umma ?"ya zanyi da wannan rayuwar ? ya
Allah ka d'auki rayuwata na mutu na huta da wannan duniyar da babu komai acikinta
sai tarin bakinciki ya Allah ka d'auki rayuwata tunda haka rayuwar duniya take
"daga wannan tashin hankali sai wannan tashin hankali meye laifina ?nan take
tausayin maryama ya sake ninkuwa acikin zuciyar umma tare da jin wani irin tarin
qaunarta mara misaltuwa "kiyi hakuri maryama ki daina furta wad'an nan kalaman haka
rayuwa take cike da kudirorin ubangiji ,sannan dukkan rayuwa d'an adam rubutaccen
al'amarin ne daga Allah,na shafa fad'a miki duk mutumin da Allah yake so shi yake
yiwa jarabawa." wani sabon kuka ta fashe dashi tana jin kamar ranta zai fita ya bar
gangar jikinta aunty salma ta kwa'be baki tana duban umma da maryama a kaskance
kafin ahankali ta cigaba da cewa "da dai kin daina wannan kukan munafurci da kike
yi da bazai ta'ba miki maganin halin da kike ciki ba, mutuwa ce da bakinki kika ce
agabanki aka binne sadam da ransa to me kuma yayi saura ?Jin haka ya qara sa ran
umma yayi matukar 'baci ta d'ago idanunta cikin zafin rai ta kira sunan aunty
salma "salma !"
Yanayin yadda ta kira sunan cikin tsawa ya d'aga masu hankali gabad'aya sukai tsuru
suna kallonta domin wannan shine karo na farko da suka ga tarin damuwa da 'bacin
rai acikin kwayar idanunta,"salma karki bari 'bacin raina ya sake ninkuwa akan
wanda nake ciki ,nayi ta qoqarin na danne zuciyata akanku amman naga alamun so
kuke sai na nuna muku fushina da 'bacin raina"me maryama ta tsare maku ?wani irin
numfashi mai zafi umma ta fesar kamar an tsikareta haka umma ta tashi daga gaban
maryama "wallahi wallahi !!kunji na rantse akan maryama zan iya 'batawa da kowa dan
haka ku shiga hankalinku ku san irin magangun da zasu dinga fitowa daga bakinku
saboda kuma kuna da naku ya'ya,allah yasa mata kuka haifa dayawa kusani duk mugun
nufinku ga maryama kanku ko kan ya'yanku zai dawo domin allah baya zalinci kuma
baya son mai zalinci amman nasan rashin ilimi ke damun rayuwarku domin da kusan
dukkan rayuwar rubutaccen
lamari ne daga rabbi, kilan da baku tsaya ' batawa kanku lokaci ba gurin matsawa
kanku da hassada da hankoron neman duniyar da wani ba ."
aunty salma ta kalli umma wacce har lokacin kwayar idanunta na kanta cike da
tarin 'bacin rai sannan ta waiga inda baba gali da aunty hasana suke tsaye suma
cike da mamakin umma .aunty salma ta daure zuciyarta da maganar umma tace "irin
fatan da zaki mana kenan ?"irin fatan dai da kukewa kanku kenan." da sauri umma
ta bata amsa da haka sannan tana cigaba da cewa " maza ku fice min daga parlour
bana son ganinku kuma wannan ya zamo karo na farko dana qarshe da zaku shigo inda
nike kuyi lamarinku nayi nawa bana son ganin gaba d'ayanku a inda nake kowa ya
zauna inda allah ya ajiyesa ."saboda an ta'ba miki yar so zaki fad'a mana haka ?
Inji cewar aunty hasana "kwarai kuwa zan ma iya yin abinda yafi haka matuqar akan
maryama ne aunty hasana ta numfasa kana tace "idan bake ba aunty ai murna zakiyi da
abinda ake wa yarinyar nan yarinyar da ta zama silar rasa tilon d'anki "sadam dai
d'ana ne dana haifa da cikina duk kuma wanda rashinsa zai wa ciwo a bayana yake
to na barwa Allah kada wanda ya sake dawo min da hannun agogo baya kuje na
sallameku bana son ganinku, yadda baku qaunar maryama nima wallahi a yanzu bana
qaunarku daga yau na yanke duk wata halaka daku ." da sauri aunty salma ta qaraso
ta durkushe gaban ummah ta rike qafafuwan umma da duka hannuwanta ta soma girgiza
mata kai kamar wata kadangariya tana kuka tana bata hakuri "dan girman allah aunty
kiyi hakuri bazamu sake cewa komai akan lamarin mutuwar sadam da gadonsa ba ki
yafe mu dan Allah wallahi sai yanzu nake jin nadamar abinda nayi in sha allahu
bazan sake ba tabbas maryama tamkar diyarmu ce Allah ya huci zuciyarki wallahi
bazamu sake ba ."
gwalalo idanu aunty hasana da baba gali sukai suna kallon makirci irin na aunty
salma ,sam basu ta'ba tunanin zata aikata haka ba "lallai ta cika babba makira ta
qarshe "kiyi hakuri dan Allah aunty ta sake fad'a tana mai sakar ma umma qafafun
ta kamo hannunta numfashi umma ta sauke da karfi sannan ta samu waje ta zauna akan
kujera tana runtse idanunta tare da dafe goshinta" sigina aunty salma tayiwa baba
gali da aunty hassana alamun suma suce wani abu ai kuwa nan da nan suka matso kusa
da umma suna mata magiya da ban hakuri "shikenan komai ya wuce allah ya yafe muna
gabadaya amman dai kusani maryama bata cancanci haka daga gareku ba ,maryama a
yanzu tafi bukatar kulawa da tausayawa da soyayya tattare da rarrashi daga gareku
tun daga farkon rayuwarta baku qaunaceta ba wallahi kuji tsoron allah na rashin
rike zumunci tsakani da Allah da kukayi ,wani abun mutane sunayi ne dan ganin ido
wani dan zumunci zasu fake suci amana mussaman zumuncin wannan zamani amman ku
babu wanda kukayi aciki kona ganin idon ma bakuyi ba bare bayan ido amman wallahi
kusani zumunci a duniya wajibi ne duk kuma wanda bai yisa a duniya ba zai yisa a
lahira alahirar ma acikin wutan jahannama ta fad'a tana jin wata irin natsuwa a
cikin zuciyarta ".
"wannan tabbas haka ne allah ya shireyar damu gaba daya allah kuma ya bamu ikon
sadar da zumunci dan allah ba dan kwadayin ko neman wata biyan bukata ba "baba gali
ya fad'a yana mai cike da nuna tausayawa ga maryama wacce hawaye biyu biyu ke bin
kuncinta yace "diyata maryama Kiyi hakuri kinji in sha allahu kuka da damuwarki
sunzo qarshe domin a yanzu a shirye nike dana baki duk wata kulawa da uba zai bawa
diyar cikinsa ."da sauri maryama ta d'ago kwayar idanunta da suka jeme ta tsurawa
baba gali cike da mamakin jin furucinsa aunty salma tayi tsigil tace "ki daina
mamaki jin abinda babanki ya fad'a ,daa na shiga zuciyar mutun a ga abinda yake
ciki da mun bude miki zukatanmu a yau kinga irin tarin nadamar da mukayi a yanzu
babu wacce muke son gani cikin farinciki kamarki ki yafe mana duk da bamu dace da a
yafe mana ba saboda abubuwan da muka dauki tsawon shekaru muna yi miki "in a slow
voice maryama tace "babu aunty salma komai na wuce na yafe maku ." murmushin
bakinciki suka sakar mata kafin ahankali suka shiga wata hirar allah sarki umma har
ga allah ta hakura domin ta d'auka nadamar gasky sukai ,ta sake dasu sosai tayita
masu nasiha kuma duk akan zumunci ne bayan kamar mintuna shabiyar d'aya byn d'aya
sukai wa umma sallama suka fice suka bar umma da maryama .
*******
tsaye nuzlah take ajikin wondo d'akinta tana zubar da hawayen nadama a yanzu
damuwa tayiwa zuciyarta mummunar kamu dan ko abinci bata ci tunaninta kaf ya tafi
ne akan son sanin matsayinta a wajen yaya hisham ,shin zai aureta ne ko kuma zai
zillewa aurenta ne ?kanta yayi mugun kullewa mafuta kawai take nema "idan har bai
aureta ba tayi biyu babu kenan bata ga auren ata bata ga nashi auren idan kuwa haka
ne ta cuci kanta da kanta tana cikin wannan halin ta hango shigowar motar yaya
hisham din cikin haraban estate dinsu da sauri ta saki labalen ta qarasa gaban
mirrow ta soma gyara fuskarta ta d'auki bakin mayafin abayar da take sanye dashi
tayi rolling kanta ta feshe ilahirin jikinta da turare ta fito cikin sauri wanda
alokacin har sun samu waje sunyi parking din motarsu sun fito suna taku yaya hisham
na rike da jakar nana hauwa'u yayinda nana hauwa'u take takawa da kyar saboda
cikinta ya tsufa ."da sauri nuzla take daga kafafunwanta lokacin data qaraso daf
dasu ta kira sunansa "yaya hisham!" cak suka tsaya a tare shi da nana hauwa'u sai
dai ita bata juyo ba dan tasan muryar wacce ,muryar nuzla a raunane tace "yaya
hisham ina son muyi magana da kai "jin haka yasa nana hauwa'u ta daidaita
natsuwarta tare da danne zuciyarta da kishin mijinta ba dan komai ba sai dan ta
qara kankaro wa kanta mutunci a idanunsa domin ba komai ake magana akai ba hakan
yana zubar da martabar mace a idanun mijinta sai dai wani irin bugawa zuciyarta
keyi da karfin gaske saboda tsananin kishin mijinta ."
ahankali ta cigaba da d'aka qafafuwanta domin basu dama hakan yasa yaya hisham ya
juya bayansa tare da zubawa nuzla ido yana kallonta a tsanake " duk ta rame ta
d'ashe kamar wacce tayi shekara babu lafiya ko wacce babu jini ajikinta "idan na
kiraka baka d'aga kirana yaya hisham laifin me nayi maka ?tayi maganar cike da
rauni ,yayinda hawaye suka cika kwarnin idanunta" ban ta'ba expecting haka daga
gareka ba well duk a ajiye wannan maganar ya batun aurenmu dan naga kamar yanzu ka
fara canza raayinka akaina ?"Eh tô nuzla kamar haka ne dan a yanzu dai gsky bana
jin wannan abu zai kasance a tsakaninmu "me yasa yaya hisham ?ta tambayesa tana
mai kamo hannunsa cikin tsananin tashin hankali "babu wani dalili kawai matata ta
isheni daman can giyar soyayyarki ce ta hanani gane quality's dinta a yanzu kuma
idanuna sun bud'e na fahimci duk duniya babu salahar mace kamar nana hauwa'u mace
ce mai hakuri mai biyayya mai kyautatawa mai kawaici bazan iya had'ata da wata mace
ba ita kad'ai ta isheni na qarasa rayuwata ,na godewa allah na godewa mahaifiyata
da tayi silar da nana hauwa'u ta zamo mata agareni "dan girman allah yaya hisham
kayi hakuri ka aureni nima zanyi maka duk abinda ka lissafa "bazaki iya ba nuzla
bazaki iya hakurin da nana hauwa'u take dani ba "saboda me ?murmshin takaici yaya
hisham yayi yana girgiza mata kai "kayi tunani akaina yaya hisham karka hukuntani
akan laifin da nayi maka wallahi sharrin sheidan ne ,ita soyayya fahimtar juna ne
kuma tun farko bamu fahimci junanmu dake ba shiyasa muka samu matsala,ina sonki
baki sona zuciyarki na kan wanina wanda ke a karon kanki Kinsan bazaki ta'ba
samunsa ba "yanzu nake qara jin wannan nadamar da dana sanin abubuwan da nayi maka
dan girman allah kayi hakuri wallahi har da sharrin sheidan ".
" babu wani sharrin sheidan nuzla kisa aranki babu qaddarar aure a tsakaninmu ne
ana gobe fa daurin aurenmu kika gudu kika barni da tarin damuwa Kiyi hakuri kawai
haka Allah ya qaddaro miki sheidan bai isa ya raba abinda allah ya hada ba saboda
shi Allah daya hadani da nana hauwa'u yasan abinda yasa ya rabamu ya hadani
daita ,a yanzu soyayyar dake tsakanina da nana hauwa'u babu dalilin da zai sa na
ita had'ata da wata ina sonta da dukanin rayuwata kasa cewa komai nuzla tayi dan
gabad'aya ta lura hankalinsa naga matarsa wacce take can ta rasa yadda zatayi ta
shiga cikin parlour'n mami dan zuciyarta wani irin dokawa take da karfin gaske
wanda hakan ya haifarwa d'an cikin hantsilawa."
da nana hauwa'u tayi niyyar tura kofar parlour'n mami sai taji ta kasa tsoro take
ji zuciyarta na cike da tsoron bari mijinta a hannun nuzla da tayi shi kansa yaya
hisham din bai mata adalci ba daya cigaba da tsayuwa da nuzla ai ko babu komai ya
kamata yaji kunyarta sannan ya nunawa nuzla tana da matsayi ko yaya ne agurinsa
amman saboda bai dauketa da daraja ba yana kallonta ta wuce ya cigaba da tsayuwa
daita runtse idanunta tayi sai ga hawaye sharrr sun biyo kuncinta ."
da kyar dafe da qirjinta dake faman luguden bugu dum dum ta tura kofar ta shiga
allah ya taimaketa bata iske kowa acikin parlour'n ba numfashi ta sauke wani zufa
na karyo mata a saman goshinta da karan hancinta zagaye parlour'n ta shiga yi
zuciyarta na tafarfasa tana cikin wannan halin taji sautin sanyayyiyar muryarsa
kasa juyowa tayi ta kallesa dan zuwa lokaci hawaye sun qara cika idanuwanta "baby
nah!"tana jinsa amman ta kasa juyowa ta kallesa dan bata son yaga rauninta "baby
nah kukan me kikeyi diriricewa tayi tana qoqarin maida hawayenta "zo gareni !
qoqarin juyowa take amman kukan da take yasa ta kasa sai numfashi da take fixgowa
tana fitarwa da kyar "please baby nah maman abar qaunata ."still bata juyo ba ta
cigaba da tsayuwa tana jan numfashi ahankali ya qarasa ya tsaya abayanta ya had'eta
da qirjinsa ya daura hannunsa daya akan cikinta yana shafawa yana shakar kamshin
turaren jikinta kusan second goma suna tsaye haka tunani tayi kar wani yazo ya
samesu haka yasa ta zare jikinta kwayar idanunsa ya tsura mata yana jin yadda
soayyarta ke sake huda zuciyarsa ."
Ahankali ya riko tafin hannunta yayi taku biyu ya zaunar daita akan kujera mai
zaman mutun daya ya dawo gabanta ya durkusa a gabanta tamkar mai neman gafara tare
da kafeta da kwayar idanunshi yana kallonta yana nazarin yanayinta ahankali ta
kawar da fuskarta gefe tana qoqarin sake danne damuwarta numfashi ya sauke da karfi
tare da tsarke hannunshi cikin nata ya dawo da fuskarta garesa "am sorry baby !ya
fad'a yana murza tafin hannuta cikin nashi" me kayi ?naunayen ajiyar zuciya ya
sauke yana sake damke hannunta cikin nashi sannan ya motsa labbansa "na haifar miki
da damuwa "wani irin damuwa kuma ?ni babu wata damuwa daka haifar min?na haifar
miki da damuwa mana nayi silar saka zuciyarki shiga qunci na tsaya na saurari nuzla
alhalin ban nemi izini daga gareki ba nasan dole zakiji babu dadi aranki dan Allah
kiyi hakuri ki yafe min ."murmushin tayi wanda yafi kuka ciwo "dan Allah ka daina
fad'ar haka banaso meye aciki dan ka kula nuzla ?karfa ka manta ni matarka ce nuzla
kuma yaruwarmu ce gabad'aya kana da damar aurenta ma ba kulata ba ,karka manta na
baka wannan damar idan har yanzu kana raayin aurenta kofa a bud'e take bazan
haramta halal din da Allah ya halallta ba sai ma nayi maku fatan alkhairi ta fad'a
tana kallonsa shima ita yake kallo yana sake hango damuwa daga gareta ,"
gabad'aya fuskarta ta sauya hankalinta a matukar tashe take maganar da take amman
kaji abinda ta fad'a dan karta haifar da damuwa atsakaninsu "ni dai Kiyi hakuri
bazan sake kulata ba yau ma na tsaya na kawo qarshen komai ne a tsakaninmu sautin
muryarta ne ya katse masa magana "tashi ka zauna please kar qafafuwanka sunyi ciwo
ka daina damun kanka dan baka min laifin kome ba tana gama fadar haka ta mike da
kyar tana cewa "bari na shiga dakin mami yanzu zan fito ta soma daga kafarta da
kyar bayanta yabi da kallo yana mamakin hali irin nata da duka matan duniya haka
suke kamar matarsa da baa samu wata damuwa a gidan aure ba komai nata dabam ne
yasan tana da tsananin kishi akansa amman yanayin kishinta na daban ne kuma yana
burgesa dan sau tari idan ya kira tana d'auka zata ce "an gaishe da mijin nuzla da
nana hauwa'u tun abun na masa dadi har yazo ya fara jin zafin abun dan tun yana
amsawa yazo baya amsawa sai dai kawar da maganar ya shigo da wata ,mata mu sani
wannan d'abia ta nana hauwa'u d'abia ce mai kyau mu dinga kawar da idanunmu da
hankulanmu akan mazajen mu ,mu basu dama kada mu saka ido dayawa akan lamuran su
most especially akan mata domin Allah ya halatta zuciyar maza da son mata dayawa
yayinda zuciyar mata take son nmj kawai mu san irin salon kishin da zamuyi idan
kayi mijinka kawaici tabbas zai dinga jin kunyar aikata wasu abubuwan."
"Tun dazu nake binka akan maganar sultana Adamcy fa sam sam yaki yarda ya dauketa
aiki akarkashinsa amman kaki kayi komai akai aunty abida ta cigaba da bin yaya
ibrahim abaya tana masa magna amman bai ce mata komai ba "yanzu shikenan babu
abinda zaka iya yi akai ?ta fad'a adaidai lokacin da suka tsaya suna fuskantar juna
"na rasa meke damun taunainki kina yi kamar baki san halinsa ba tsawon shekaru kina
cikin gidan nan kuma babu abinda baki sani akansa ba , kinsan yadda halinsa yake
"haka ne nasan komai amman ni nasan yadda zanyi wanda shi kansa bazai ta'ba tunanin
zan iya aikatawa ba ai tunda har nayi niyyar sultana ta auri adamcy kamr anyi
auren nan an gama muddin ina raye "wannan shine dalilinki naso ta kasance kusa
dashi ?ta gyada masa kai alamun "eh! "kina tunanin Adam zai amince da wannan hadin
naki ?" ka tsaya kasa ido kaga ikon allah muddin ina raye sai ya aureta "numfashi
ya sauke "gsky da kin canza shawara kina kallon yarinyar da mahaifiyarsa ma tayi
masa umarni ya aura da kyar ya yarda yayi mata biyayya a qarshe ma sai daya saketa
bare wata sultana can ,dama baa acikin family's dinmu take ba ".
"kai dai ka tsaya kasa ido kayi kallon abinda zanyi tunda shi har yanzu bai
fahimci menene dalilin da yasa nake son sultana ta kasance a kusa dashi ba dan haka
zanyi komai akai tunda kaima har yanzu kana bada umarni a kafani kamar yadda yake
bayarwa ko..."dan allah malama ki bar wannan shirmen naki tun wuri ki dawo
hankalinki idan ba haka ba zaki aikata katoton kuskuren da zai jawo miki matsala
tabbas ina da iko akan kafanin adalili mahaifina kuma shima mahaifina nawa a koda
yaushe cikin bin bayan adamcy yake akan komai he always supporting Adam nayi imani
ko wannan tsarin daya kawo baba babba yasan da komai dan haka a matsayina na
mijinki zan baki umarnin ki cire hannunki ki fita cikin lamarinsa idan ba hk ba duk
abinda yabi yo baya babu ruwana ya qarasa mgnr yana nunata da dan yatsansa sannan
ya kama gabansa shiru tayi tana kallon bayansa tana ystsina fuska ."
Maryama zaune a kusa da mahaifiyarta cikin halin damuwar data tsinci kanta, kullum
qoqarin raba kanta da tunani take amman ta kasa domin da zarar ta runtsa idanunta
yaya sadam dinta take ganin cikin tashi hankali yanzu hk ma jan hankali
mahaifiyarta take mata "ki fahimceni princess wannan matsalar gabadaya ta shafemu
ko nace na fiki shiga cikin damuwa da tashin hankali mai tsananin akan mutuwar
sadam amman me zamuyi daya wuce hakuri mu barwa allah komai hatta mahaifiyarsa ta
hakura ta barwa allah mai yasa Ke bazaki hakura ba "nasan akwai ciwo sosai amman ki
dauka haka taki qaddarar take bawa kuma bai isa ya canzawa kansa qaddararsa
ba ,bamu sani ba ko wani mijin Allah zai kawo cikin kankanin lokaci yasa wannna
lamarin ya faru "numfashi maryama ta sauke mai hade da saitin kuka" dan allah kiyi
hakuri ki daina fad'a min haka babu wani aure da zanyi na gama aure har
abada ."ta jingina bayanta da abun gado ta daga idanunta sama hawaye na zubo mata
"you better eat enough with all this cry cry ..."bazan iya cin komai ba aunty ."
"Common bude baki na baki abinci kinji my princess wasu sabbin hawaye ne ya zubo
akan kuncin maryam ta dube mahaifiyarta gabadaya ta fita haiyacinta adalilin
damuwar data sameta " aunty kin cikin abinci ne ?banci ba ina son sai naga kinci ne
taya zan iya cin abinci alhalin princess dina tana kwance kwana uku kenan bata
sakawa cikinta komai ba ,maryama ta sauke naunayen ajiyar zuciya ta dauki karbi
spoon din hannun mumcy ta dibi abinci ta kai bakinta "kici abinci sannan naci batai
mutsu ba ta bude mata baki ta kai lomar abinci bakin mahaifiyarta, bata kai ga cire
spoon din ba aunty ta dibo abinci da hannu ta kai bakin maryama."
Maryama na hawaye mahaifiyarta hawaye aunty tana matukar tausayawa kanta da rayuwar
yayanta "ina rokon allah yayi min sausauci domin zunubina yake shafar yayata da
basu baji basu gani ba wasu hawaye masu ciwo ne masu zafi sukai zuba a idanunta "in
sha allahu zan koma ga dangina zan rokesu gafara "dan allah Allah ki daina damun
kanki nima na daina damuwa na yarda da qaddarata "aunty ta rungume maryam " yauwa
princess ki kula da kanki kinji ,karki ji komai aunty in sha allahu zan kula miki
da kaina ."
"Me zaki ce da rana ?kinga aunty ba sai kin wahalar da kanki ba wannan abincin da
naci ma ya isheni har gobe aunty ta dan ware idanunta waje "a'a ki fad'a min
kawai duk wahalarsa zan girka miki maryam tai murmushi bata ce uhm ba bare umh uhm
sai ma ta daura kanta akan cinyar aunty yayinda ta saita idanunta akan takardun
zanen jamaa dana kayan sawa a hankali tayi zurfi cikin tunanin makomar rayuwarta ta
rasa komai ta rasa aikin yi duk inda ake bukata zanenta yanzu an daina nemanta ko
tayi ta kai masu ma basanuna alamun ma yayi masu bare su karba dan mijin datasa mu
ya tafi ya barta me kuma ya rage mata yanzu ?mutuwa !zuciyarta ta bata amsa da haka
ta runtse idanunta gam saboda batason mahaifiyarta ta fahimci damuwarta aunty ta
daura hannunta akanta hular kanta ya zame nan kwantaccen gashin kanta ya bayyana
"princess dan Allah ki barwa allah komai kinji da sannu allah zai yaye mana komai
numfashi ta sauke tana riko hannun aunty cikin nata "na gode sosai mamana allah
ya tabbatar mana da alkhairi ."
Zaune suke a babban parlour'n hajiya zulaihert baba babba da babba qarami da uncle
jay sai fahad gabansu kayan motsa baki ne aka kawo masu kowannensu cikin shiga
ta alfarma acikinsu babu wanda bai taba abinda aka kawo masu sai baba qarami wanda
yake cika yake batsewa sannan yake allah allah Adam ya sauko ."ahankali ATA Ke
saukowa daga matattakala jikinsa sanye da kaya light blue kansa sanye da facing
cap fari sol haka ma kafafuwansa wasu hadaddun silifas farare ne sanye dasu sai
kamshi turaren REED ne Ke tashi ajikinsa a natse ya qarasa saukowa ya qaraso inda
suke ya gaishesu gabadaya yana tsaye bai kai ga zama ba babba qarami ya zabura ya
mike a matukar fusace ya soma magana "kai wani irin yaro ne ?"kawai kana son batawa
yara kasuwanci dan kawai kayi certified din kanka ,dama ubanwa ka zauna kayi
shawara ko kuwa kafanin naka ne kai kadai da zaka zarta da hukunci akaron kanka
"?"akan ma wani dalili zaka qara farashin kaya ."
Ganin baba babba da uncle jay yasa bai dauki zafi ba ya kwantar da murya yace "nayi
haka ne saboda ingancin kayanmu bawai da wata man.."karka fad'a min haka domin
wannan maganar banza ce ai sai da yaya Ibrhim ya fad'a masa kar yayi haka amman
yaki inji cewar fahaf " wani mugun kallo ATA ya daukesa dashi wanda yasa babu shiri
yaja bakinsa yayi shiru "duk wasu yan kasuwa ku barsu suje wasu compaing su dauki
kaya daga ingancinsu zasu rasa abokan kasuwancinsu ni nasan abinda nake ba yau na
fara kasuwanci ba koma nace kasuwanci ajinina ya....."enough Adam karka wuce gona
da iri yadda kake taimaka da kasuwanci muma itace silar zuwanmu duniya ba kuma zamu
yarda ka batawa yayanmu kasuwancinsu dan muma munyi business sama da shekara
talatin , so munsan kasuwanci dan haka bamu amince da wannan tsarin naka ba domin
tsari ne da zai korewa kanfani kasuwa daga yanzu da nake maka wannan maganar ka
janye kudirinka akai "wannan shine magana ta gasky baba abinda yaya Ibrahim yayita
fama dashi kenan Faaha ya fada yana hura hanci abinda ma ya kamata da zai dauki
wannan mataki ya zaunar daku gabadaya ya tautauna daku ba wai ya yanke hukunci a
qaron kansa ba nan fa baba qarami ya dinga zuba ruwan bala'i ta inda yake shiga
bata nan yake fita ba ,sauran yan'uwansa na bashi hakuri da kokarin kwantar da
fushinsa dan bai iya fushi ba mutun ne mai tsananin zafin rai zuciya ".
"Ku daina bashi hakuri yayi duk abinda zai yi ".ATA ya fad'a a fusace sannan ya
tsaida kwayar idanunshi akan baba qaramin "baka da wannan cikakken iko akan wannan
kafanin magana ta karshe ka janye jikinka akan wannan kafanin ka maida idanunka
akan wanda yake naka ne kai kadai "ni kake fadawa haka saboda baka da mutunci ?"
Ata yayi shiru yana hura hanci tare da soke hannuwansa cikin ajihu "dan banza yaron
kawai mai banza zuciya ni wallahi bansan inda uwarka tasamoka ba dan ubanka bashi
da mugun hali da mugunta ,yaro kamar sheidan idan anyi nan yayi can dan iskan yaro
kawai wallahi maza maza ka tattara ka kama gabanka kabar masu kamfani su cigaba
da kula dashi ka tsaya iya mallakinka dan kai ne zaka hakura ka bar mana ."
shiru ata yayi yana kallon baba qarami zuciyarsa na tuttukin bakinciki wani irin
tsanarsa yaji ya darsu acikin zuciyarsa ransa idan yayi dubu ya baci wallahi yaci
darajan babba babba dake zaune da girman mahaifinsa da kuma uncle jay da yau ya
gane kurensa domin kuwa da ya nuna masa ya zarta dan iskan daya kirasa dashi cike
da fushin zuciya ya juya zai wuce baba babba ya kira sunansa "Adam ..!
Cak ya tsaya sakamakon jin sautin muryar baba babba "dawo nan Adam a gama magana
gabadaya ya juyo a sukwane fuskar nan tashi ta sake rikicewa ta hade kwata kwata
babu wani alamun annuri "me zance tunda ya zarta da hukuncin da yake so kuma ga
dukkanin alamun yayi maku daidai ,"baba qarami ya kallesa ya watsar"ba haka bane
adam !" baba babba ya fad'a tare da mikewa tsaye yayi taku zuwa inda yake tare da
yin kasa da muryarsa "kafi karfin duk wannan adam ka janye hannunka tunda sun kasa
fahimtar dalili dayasa kayi haka "kenan ka yarda da tsarinsu ?yes saboda zaman
lafiya ne domin bazasu ta'ba fahimtarka ba idan ma da hali ka cire hannunka gbdy
dan bana son na rasaka ,rayuwarka nada matukar amfani a gareni ."ata bai sake cewa
komai ba ya juya a matukar fusace ya haye sama yana taka step cikin sauri sauri."
Mmn sudai
💗💗💗💗💗💗
MAR'ADAMS
💖💖💖💖
💗💗💗💗💗💗
*AYSHA A BAGUDO*
WATTPAD @HAUESH
AREWABOOKS USERNAME
AYSHAABAGUDO
bismillahirrahmanirrahim
Wannan littafin na kudi ne mai bukatar karantashi byn na kammalashi zai biya
1000 ta wannan account number din 1438775094 Aishat abdullahi access idan an tura
sai a turawa wannan 09136918331 alert domin tabbatar da an tura domin sauraron
littafaina a tuntubi chaneel dina (Hausa bakwai ) a YouTube.
Page 29
Zuciyar ATA cunkushe da haushi tare da takaicin baba qarami ya tura kofar
parlour'nsa ya shiga yana shiga kai tsaye bedroom dinsa ya shige ya rike kugunsa da
hannu d'aya yayinda yasa d'ayan hannunsa ya dafe goshinsa da yaji yana masa wani
irin mugun sara sakamakon'bacin ran daya shigo dashi ,babu abinda yake gani sai
fuskar baba qarami ita ke masa gizo cikin tsananin 'bacin rai saurin runtse
idanuwansa yayi yana mai sake jin bakincikinsa na nunkuwa wani irin zafi da suya
zuciyarsa keyi,duk da ya murje idanunshi ya fad'a magana son ransa amman hakan bai
masa ba yaso ya zage kunjinsa ne ya zabga masa rashin mutuncin da har ya mutu bazai
manta dashi ba .kusan mintuna shabiyar yana tsaye yana zariya acikin d'akin tamkar
wanda yayiwa sarki karya ."a can parlour'n kuwa baba babba ne a gaban baba qarami ,
bai damu da cewar shine babba ba ya kwantar da kai cike da tausasawa yake masa
magana "dan girman allah baba qarami kayi hakuri karkayi fushi da adamu tunda ka
rigada kasan halinsa kuma ... "ba maganar hakuri bane yayi saurin dakatar dashi ta
hanyar fad'ar haka "kawai kasashi yayi abinda ya dace shine zaman lafiyar kowa idan
ba haka ba zaayi wacce za'ayi "in sha allahu zai yi biyayya a gareka "dole ya
sauke ra'ayinsa yabi naka domin kai uba ne agaresa "wannan haka ne dole yabi
umarninsa "inji cewar uncle jay "kayi hakuri da duk ma abinda adamu yayi maka
d'anka ne babu yadda zakayi dashi sai ma fatan alkhairi daka masa
arayuwarsa .""baba qarami ya katse uncle jay ta hanyar d'aga masa hannu "dakata
jamilu ya isa haka karka cika ni da surutu "adamu ba d'ana bane kune dai kuka
d'aukesa amatsayin d'a dan d'an cikina bazai ta'ba maida min magana ba kamar yadda
yayi a yanzu a gabanku adamu yasan ubansa ni kuma nasan ya'yan dana haifa ,sai abu
na qarshe wallahi wallahi kunji na rantse ku gaya ma wannan gantalallen d'an naku
ya kiyayaeni kar ya kuma yin gigin shiga hurumina dana ya'yana yayi lamarinsa muyi
namu yayi na farko yayi na biyu kar yayi kuskuren aikata na uku domin idan yayi na
uku bazai ji dadina ba "baba babba yace "shikenan in sha allahu bazai sake ba "baba
qarami yace "da dai ya fiyye masa dan wallahi idan ya kuma yunkurin shuka min
rashin mutunci ba wannan mgnr zaayi ba dan zan shuka masa wanda yafi nasa ."
" da kyar uncle jay da baba babba suka rarrashesa suka samu ya d'an sauko
sai dai duk da haka ya fita yana zage zage tare da tsinewa ata din wanda shine
abinda yafi komai konawa mami rai dan har sai data ta zubar da hawaye dan bakinciki
."
Ahankali baba babba ya numfasa ya cewa uncle jay " tashi muje mu samu adamu shima
mu kwantar masa da hankali dan a samu komai ya wuce atare suka mike suka haura
saman d'akinsa alokacin ata ya samu waje ya zauna a gafen gadonsa ya had'e fuska
tamkar hadari duk wanda ya kalli fuskarsa alokacin sai tsoro da firgici ya
kamashi ,suka tsaya a gabansa suna kallonsa na tsawon lokaci kafin su fara
magana .ahankali baba babba ya fara da nasiha mai ratsa zuciya da shiga jiki akan
yayi hakuri da yan' uwansa "shiyasa a kullum yake qara ganin kimar dattinjon domin
dattijo ne da yasan yakamata bayan baba babba yayi shiru shima uncle jay ya soma
nashi "kayi hakuri ata hakika mun san komai mun san kamfani na mahaifinka ne
alfarma kawai yayi wa yan'uwa alokacin da yake raye hasalima babu wanda yasan cewar
nashi ne sai mu shakikansa dan tun kafin rusuwarsa kamar yadda kasani ya fitarwa
kowa da hakinsa amman kasan halin kawunka sam baya kyautawa kanshi kuma baa isa a
fad'a masa gaskiya yaji ba duk da yasan gskyr aka fad'a masa kai dai abinda nake
so da kai ka cigaba da hakuri dashi, kasa aranka duk abinda ya aikata agareka
tamkar mahaifinka ne yayi maka ,kayi hakuri ka zauna lafiya da kowa wannan shine
muradinmu da kuma kwanciyar hankalinmu dana mahaifinyarka" jiki a sanyaye ata yace
"naji kuma a gode sosai da kulawarku "Allah yayi maka albarka sukai masa sallama
suka fice daga gidan gabdaya."
Bayan fitarsu da kamar mintuna talatin sai ga mami ta shigo inda ta iskeshi a zaune
a parlour'n akan one siter hannusa rike da waya yana daddanawa a yadda yake
operating din wayarsa zaka d'auka kwata kwata baya tattare da wata damuwa ne
ballanatana wani abu makamancin matsala amman ala hakikanin gaksy kallo daya zaka
masa ka fahimci yana tattare da zallar damuwa masu tarin yawa cike da tausayawa
mami take kallonsa .
ahankali ata ya d'ago tsumammun idanunshi da suka gama canza kala tsabar tashin
hankali da yake ciki ya tsurawa mahaifiyarsa ido yana kallonta cike tsananin
qauna ,waje ta samu ta zauna a gefensa murya a raunane ta kira sunansa"adamcy !
gabadaya ya juyo bangaren da take zaune ya natsu sosai domin yaji abinda zata fad'a
itama dan ya rigada yasan taji komai daya faru kawai fitowarce taki yi shima yasan
dan gudun abinda zai biyo baya ne yanzu ma yasan fad'a ne da nasiha ya shigo
daita "yayi maka kyau adamcy da duk abinda ka janyowa kanka ."shiru yayi kawai
yana sauraranta kafin ahankali ya runtse idanunshi ya kasa cewa komai ,mami ta
cigaba da magana "wallahi adamcy ka rage wannnan zafin zuciyar karta jawo na rasaka
. ina umartaka ka janye hannunka bazan so wani mummunar abu ya sameka ba domin duk
abinda ya sameka ya sameni dan sai yafi min ciwo akanka bazaka san yadda iyaye
suke ji akan ya'yansu ba sai randa ka mallaki naka wallahi bana son nayi kukan
rashinka dan allah ka hakura ."
"yanzu sweetheart kina ganin akwai abinda zasu iya min ?ya fad'a ransa a 'bace ta
gyada masa kai alamun "eh !"kinyi imani da allah sweetheart ?"sosai kuwa nayi
imani da allah "to kisa aranki babu abinda zasu iya min ni ban ma yarda akwai wani
dan Adam din da zai iya cutar da wani ba fashe da izinin allah ya qaras maganar
yana furzar da iska mai zafi daga bakinsa "tabbas nasan da haka amman dai fita
hanyarsu "shiru yayi mata "kenan bazakayi abinda nace ba ?tayi maganar cikin zafin
rai "wallahi da ana canza mutun adamcy da tunin na dade da canzaka kowa ya huta
acikin danginka dan kwata kwata baka da kirki "ata dake zaune yayi shiru tare da
cigaba da duban mami batare da yace mata komai ba dan ya ma rasa abinda zai ce
mata ne yasashi yin shirun
sai dai cikin zafin rai ya kamo lips dinsa na kasa ya soma cizawa da karfi "ina
sake umartarka da ka sausauta komai idan ba haka ba zaka ruguza gida d'ayan da
amafinka ya had'a "
" kada kayi Kuskuren ruguza ahli dangin mahaifinka adamcy domin cikar muradinka
idan ka aikata haka mahaifinka bazai ji dadi ba dan girman allah ka bar ruhinsa ya
samu salama "ta qarasa maganar muryarta na rawa alamun tana son yin kuka
"sweetheart zaki fara ko ?ya fad'a yana riko tafukan hannunta cikin nashi "kai din
ne adamcy baka da kirki wallahi ban san wani irin zuciya gareka ba sam sam baka da
tausayi "sweetheart ba haka bane kema kinsan adamcy dinki na iyakar kokarinsa akan
ahlin mahaifinsa yana yin komai dan jin dadinsu ne ,babu abinda bana masu suna jin
dadi ta koina tare da qoqarin sanyasu farinciki burina mu amafana da wannan
kamafanin gabdayanmu nayi qarin kudi ne domin suji dadi ba dan mugunta ko dan jin
dadina ba amman sweetheart ki duba kiga abinda baba qarami yayi ,wallahi banyi
haka dan zalinci ko son rai ba kayanmu suna da ingancin da ko nawa muka saka
farashinsu zaa siya idan baa siya ba wallahi tabbas zaa dawo daga baya saboda
ingancinsu ."ya qarasa maganar zuciyarsa cike da rauni ."
jikin mami yayi mugu mugun sanyi da gane da jin abinda ya fad'a ta matso sosai kusa
dashi tare da d'aura hannuwanta duka ta riko fuskarsa dashi tana kallonsa wani irin
matsanancin tausayi ne mai tattare da qaunar d'an nata taji ya sake nunkuwa acikin
zuciyarta yayinda taji kuka from no where ya kufce mata, kawai ta rungumesa
ajikinta tana wani irin kuka mai ban tausayi "wallahi nasani adamcy duk abinda
zakayi akan agc babu mugunta acikinsa amman bana jin dadin furuncin babanka akanka
haka zalika bana jin dadin yadda kake masa ko babu komai uba ne agareka kanin
mahaifi ne albarkarsa albarka mahaifinka ne haka zalika tsinuwarsa tsinuwar
mahaifinka ce ,ina neman alfarma agareka ,na rokeka dan allah kada ka sake fad'a
masa bakar magna akan komai shi din ubanka ne halak malak duk duniya baka da kamrsa
ka cigaba da hakuri da yanayinsa haka halinsa yake tmkr naka duk da dai yace bai
san inda na samoka ba bayan ya manta cewar duk wannna halin naka shi ka d'auko
amman in sha allahu zaka canza ,zaka canza da izinin Allah,allah yayi maka albarka
ina maka addua allah ya baka abinda kake so duniya da lahira wannan yarinyar
mafarkinka da kake so ina maka addua Allah yasa gaskiya ce.
wani irin yanayi ya tsinci kanshi ciki mai wuyar misaltuwa wanda bai ta'ba jin
irinsa ba babu alokaci d'aya zuciyarsa ta tsunduma cikin tunanin princess dinsa
nan da nan kuma yarinyar data zanashi ta fad'o masa tun daga ranar farko daya soma
ganinta har zuwa had'uwarsu a ogun, shiru yayi zaune tare da rungume hannuwansa
duka a qirjinsa yana tunaninta, muryarta sak irin muryar yarinyar da yake mafarki,
yaso kwarai yaga fuskarta a wancan ranar sai dai cewar ita din matar aure ce
yasa ya hakura amman wasu wurare ajikinta duk irin na princess dinsa ne hatta
yatsun hannunta irin na princess ne haka ma yatsun kafafunta kawai fuskarta ce ta
rage masa ya gani ya tabbatar da ko ita ce. oh my godness god ! allah karka sa
yarinyar nan tazo min amatsayin matar aure dan ban san yadda zanyi da rayuwata
ba"kayi shiru ." bai motsa ba dan bai ji abinda ta fad'a ba "ka daina zurfafa
tunani ni dai a kullum ina maka adduar idan mutunce kuma alkhairi ce arayuwarka
Allah ya gaugauta had'aku idan ba gaskiya bace Allah ya kawar maka da tunaninta ka
huta "
Agogon tsarka hannuta daya zamo hannusa lokacin daya matso kusa daita yana shafa
zanen lallen hannunta tayi baya da sauri sauran kadan ta kai kasa yayi sauri riko
tsintsiyar hannuta sosai alokacin suke kallon juna ido cikin ido suke kallon cikin
kwayar idanun juna nan ma sai da yayi kokarin bude nikaf din tayi saurin kawar da
fuskarta ."ahankali ya mike tsaye ya shiga bedroom dinsa ya d'auko agogon tsarka
ya fito ya tsaya yana qarewa agogon tsarkan kallo mai cike tsananin sheki yana jin
kamar suna tare daita ne a lokacin a hankali ya shiga kai kawo acikin dakin yana
cikin wannan halin mami ta mike ganin kamar ma ya manta da zamanta acikin
parlour'n "Adamcy ta kira sunansa ya dan gigice ya waigo yana dubanta "meye
damuwarka ?daga magana ka fita haiyacinka "ya girgiza mata kai alamun babu komai
"ta sauke numfashi tace "ya babu komai daga magana ka shiga tunani daga tunani ka
bazama ka d'auko agogo kana kallo agogon waye kamar na mata ?"bai ce mata uffan ba
illa ya samu waje akan three siter ya kwanta tare da lumshe tsumammun idanunshi
"ka fad'a min agogon wacece a hannunka ?kwanciya sosai yayi ya mike akan kujera
batare daya bata amsar tambayar data masa ba ya damke agogon sosai ahankali
ahankali ya qara runtse idanunshi yayi pretending like kamar yana jin bacci "adamcy
me ya kawo agogon mace hannunka neman mata ka fara ko me ?" "sweetheart I'm feeling
sleepy ""Feeling sleeping?"ta maimaita abinda ya fad'a "yes sweetheart bacci
".mami taja numfashi ta sauke ahankali sannan tace "alright !amman karkayi dogon
bacci dan laasar ta kusa idanunta akanshi ta fice daga parlour'n sai dai zuciyarta
cike take fal da mamaki da zarginsa ."
********
"Maryama taso kizo gareni maryama ta mike da kyar dan gbdy jikinta babu laka ta
dawo kusa da granny wacce ta kawo masu ziyara a safiyar yau din ta zauna granny ta
kamo hannunta daya ta rike gam cikin nata cike da matsanancin tashin hankali ta
soma magana "wai meke faruwa da rayuwar yarinyar nan ne ?gabadaya na kasa
fahimtar abinda ke faruwa daita duk lokacin da zaayi mgnr aureta ko tayi saurayi
sai wani mummunar abu ya samesa? yanzu kuma gashi wanda ya aureta shima ya mutu ya
barta , maryama tai saurin girgiza mata kai " granny bai mutu ya barni ba fa an
dai binnesa amman nayi imani bai mutu ba zai dawo domin ina cikin son yaya
sadam dan duk cikin wad'an da suka nemi aurena babu wanda zuciyata ta yarda ta
kuma amince dashi kamar yaya sadam ni kaina na kan zauna nayiwa kaina wannan tunani
granny "why abubuwa suke faruwa dani haka ? daga wannan sai wannan tayiwa kakar
sadam tambayar tana sheshekar kuka “ya allah laifin me nayi haka da wannan jarabawa
tamin yawa ?yanzu ni nasan haka zan qare rayuwata matukar na rasa yaya sadam babu
mai kuma Kuskuren sake zuwa neman aurena ". tayi shiru hawaye na zuba daga cikin
idanunta "me yasa kuka min haka ? me yasa kuka nisanta da mijina wallahi
zuciyata bazata iya d'aukar wannan tashin hankalin ba?me yasa ? Why why !!! ta
qarasa mgnr tana wani irin kuka nan take suka rufa akanta har mahaifiyarta suna
bata hakuri ".
ahankali zuciyarta ta tsaidaita daga kukan da take tare da bata kwarin gwiwa "sadam
dinki bai mutu ba sannan bai barki ba zai dawo gareki ki bawa zuciyarki kwarin
gwiwa ki kwantar da hankalinki domin kwanciyar hankalinki shine kwanciyar hankalin
duk wani masoyinki Kiyi masa addua da yarda allah zai dawo gareki ."tun lokacin da
granny ta kirata zuwa gareta ya qaraso bakin kofar shigowa parlour'n da fuskarta
ya sama cin qaro tana zubar da hawaye wanda ke fita daga kasan zuciyarta kamar ance
ta d'aga idanunta dan daman tana fuskatar kofar shigowa ne idanunta ya sauka
akanshi ."shiru tayi tana dubansa tana ganin tamkar a mafarki ne kallon juna suke
ido cikin ido kafin a hankali ta motsa bakinta ahankali tace "kai ne a gidanmu sir
!?bai ce komai ba haka zalika bai shigo ba ya cigaba da tsayuwa "maryama! umma ta
kira sunanta ta sauke numfashi tana duban umma "Kina bukatar wani abu ne ?batace
komai ba ta sake yunkurin maida idanunta inda ta gansa sai dai wayam tagani babu
shi babu alamun sa byn kmr minti goma ta sake ganinsa wannan karon mikewa tayi da
sauri ta nufi kofar d'akin wanda hakan ya maida hankalinsu gurin cike da tsananin
tashin hankali aunty hassana da aunty suka biyo bayanata haka umma tayi kokarin
danne damuwarta ta biyosu "sannu da zuwa oga ammar ka shigo daga ciki mana ." yayi
shiru yana kallonta dan gabadaya bata haiyacinta yaso ya wuce a tun ganin farko da
yayi mata amman ya kasa "waye shi maryama ?umma ta tmbyeta "shine wanda ya taimaka
ya bani aikin dana barwa subaia a Z&A .”
nan take murmushi ya dan bayyana akan fuskar umma "Ke ki rufewa mutane baki da
shegen karyar tsiyar "wannna ai mai gidan sadam ne " umma ta dubi aunty hassana
cike sa mamaki a ina tasan ogan sadam ?amman dai tayi mata alamun tai shiru sai
dai aunty hasana taki shiru ta cigaba da zuba magana " mai gidansa ne dan haka
naji anata fada ranar sadakar bakwai hatta kayayyakin daakaita amfani dashi shine
ya kawo yanzu nasan da wani abun arzikin yazo ,fuskar maryama bayyane da murmushi
tun bayan rashin sadam datai sai yau annuri ya bayyana akan fuskarta kuma tayi
imani na ganin oga ammar ne dan bata ta'ba expecting zai zo gareta ba to me ma ya
kawosa ?ta jefawa wankakki yar kwakwaluwarta kafin ahankali ta mayar da kanta Ta
sunkuyar a kasa "yallabai amar sannu da zuwa dan allah ka shigo daga ciki bai
dace ka tsaya a bakin kofa ba cewar umma da kyar ya ra'ba ta gefen maryama ya
shigo still tsayawa yayi kamar yadda maryama tayi ya tsura mata idanunshi masu
shigar da mutun cikin wani halin " .
Ahankali ya kai dubansa inda take kallo nan yaga tangamemen hoton mijinta sadam
take kallo tana murmushi hankalinsa yayi matukar tashi nan take daidai zuciyarsa ya
dinga bugawa da karfi tamkar ana buga masa guduma hankalinsa ya sake tashi macen
da abokinsa kuma danuwansa ya dauki tsawon lokaci sama da shakaeu shabiyar yana
renon soyayyarta amman yau ga abinda sakacinsa ya janyo masa yasani idan ata yasan
itace yake ta qoqarin ganin sun had’u to zai yi nadamar har qarshen rayuwarsa .ya
furzar da numfashi yana jin wani irin zafi acikin zuciyarsa dan ya san da ata ya
yarda ya ganta a tun farko a lokacin da ita din ba matar aure bace da ko sama da
kasa zasu hade babu mai aurenta sai shi .waigawa yayi yaga babu kowa a parlour'n
alamu sun basu wuri "dukkanin alamun sun nuna kina tsanin son mijin nan naki da
sauri ta juyo ta tsura masa ido jin abinda ya fad'a ahankali ta lumshe masa
idanunta tana tuno yaya sadam dinta byn kmr minti goma sai kuma ta fashe masa da
kuka "yaya sadam his very special to me ya fiyye min komai dake cikin duniyar nan
zuciyata zata rayu da qaunarsa ne kawai .”yayi shiru kawai yana kallon qaramin
bakinta da take motsawa a natse a ransa yace “idan ata ya sameta sai yayiwa wannan
bakin kaca kaca kai bama iya bakinta ba ita karon kanta sai ta gane kurenta sai ta
gane tashiga hannu .”oga ammar ka kuwa san abinda ake kira da soyayyar gasky ?
karkace kai yayi kawai yana sake tsura mata ido dan da alamun soyayya ta zautar
daita abokinsa zai sha aiki ba qarami ba “tô yaya sadam yana mun fiyye da soyayyar
gsk ...."sorry allah ya jikansa allah yayi masa rahma naso na qara dawowa tun bayan
sadakar uku amman sai wata tafiyar gaugauwa ta sameni yau kwanaki goma kenan da
dawowata nace nazo naga lafiyarki fatan dai kina lafiya baki da wata damuwa ?”
“bani da wata damuwa sai ta rashin mijina” miji miji !! ya fad’a acikin kasan ransa
gbdy sukai shiru a tun bayan data furta haka bai sake cewa komai ba dan yana taya
abokinsa jin haushin yadda take nuna son mijinta a fili parlour'n ya dauki shiru
kafin ahankali maryama ta dago ta tsura masa idanunta "nasan subaia ce ta fada maka
abinda ya faru ko ?yes itace zuciyata ta kadu sosai ban san sanda na janye fushin
da nayi dake ba "na gode sosai allah ya jikan iyaye "ameen !”ya furta a fili wannan
kalmar nata na cikin abinda take qara burgesa dashi ya dauki kamar awa daya tare
daita sannan yace ni zan wuce daman nazo naga yanayin jikinki dan lokacin danazo
ance bakya cikin haiyacinki shiru tai tana kallonsa kafin tayi wani hanzari har ya
mike tsaye tare cewa " idan kina bukatar wani abu ki bari nasani yana gama fadar
haka ya juya har ya kai bakin kofar fita ya juyo ya tsaya yana kallonta yana sake
jin tausayinta na mamaye zuciyarsa ta yunkura ta mike da kyar tayi taku biyu ta
tsaya tana watsa da yatsun hannunta "take care !"taji ya furta ahankali daga saman
lip's dinsa kai kawai ta gyada masa bayan fitarsa da wasu yan mintuna sai ga yara
suna ta shigowa da kayan abinci aunty hasana tayi tsalle cike da murna tace "kai
gsky wannan mutumin ba qaramin mai kudi bane kaga abun arziki tunda akayi mutuwar
nan yake aiko da kayan abinci bata rufe bakinta ba sai ga yaronsa ya shigo da
bandir din yan dubu dubu guda biyar ya mikawa aunty hasana kasancewar itace a kusa
dashi "gashi inji yallabai "da sauri ta kar'be tana zuba uban godiya aunty kinga
wani sabon abun arziki ? gsky mutumin nan yana da matukar kirki sosai ai da gobe
nayi niyyar zuwa gidan aunty fatima nayi kwana biyi amman yanzu gsky babu inda
zani wannan abun arziki haka ai sai an gama lashewa dani tasss sannan zan..."haba
hasana ke mutuwar nan ma kamar dadi kikaji daakayita karki manta duk wannan abun
bazasu taba kwantar min da hankali ba d'a fa na rasa sukunta guda dan ma kwaya daya
amman kike murna dan an kawo abun duniya gsky idan haka zaki cigaba ni da kaina
zan sallameki ki koma bangarenki dan zuciyata bazata iya d'aukar wannan cin fuskar
ba.”
“ baki yiwa wannan yar iskar fada ba ko ki koreta a gidanki alhalin itace silar
jefa rayuwar d'akin ciki halin mutuwa sai ni ?ai idan kora ne ga wacce ta fini
cancatar ki kora bani ba, kai ni me ma nayi tukun ?tayi mata tmbyr tana dubanta a
dage babu abinda tayi ita din yarinyar kirki ce datasan mutunci kuma har yanzu dana
rasa d'ana bana jin komai akanta sai tsananin soyayya yadda nake matukar qaunar
sadam haka nake matukar qaunar maryama domin ita din tamkar diyar cikina take."
bata da wani bambamci da sadam a wajena hawaye ya zubo akan kuncinta "fatan kin
fahimceni wannan family na bukatar kwanciyar hankali idan kuma kikayi kokarin kawo
min tashin hankali wallahi zan ajiye duk wani zumunci agefe fatan kin fahimta,ina
bukatar zaman lfy acikin gidan nan tana gama fadar haka ta nufi kofar d'akinta bata
kai ga shiga d'akin ba ta jiyo sautin muryar maryama "tunda dai har zamana a gidan
nan yana kawo tashin hankali atsakaninku ina ganin lokacin barina gidan
yayi ."granny ta girgiza mata kai haka ma aunty wacce jikinta har rawa yake tsabar
tashin hankalin maganr maryama .”
“kowa da yanayin rayuwarsa hasana ni haka tawa rayuwata take da d'ana da ba nawa ba
duk abu d'aya ne agurina qaunar da nake ma maryama yasa na hadata aure da dana duk
da na fahimci yanayinta a tun farko na nakin auren amman daga baya ta amince
saboda qaunar da take min kuma da ina da wani dan a duniya bayan sadam wallahi zan
sake aurawa maryama shi kuma ina da tabbacin ko itace ta mutu bilkisu zata
sake daukar diyarta ta bawa sadam ya aura "dan hka kije kiyi abinda ke gabanki ko
ki bar min gidana na rasa me yasa hasana kike yin haka shin maryama ba diyarki bace
ba ,idan ma baki dauketa matsayin diya ba wannna qaddarar da ta sameta idan ta samu
diyarki ya zaki ji ? "wannan shine karo na biyu da kika ce na bar miki bangarenki
to zan bar miki bangarenki amman karki sake hada yayana da maryama domin diyata
bazata ta'ba tursasa mijinta lallai sai ya kaita har wani gari kawai saboda wani
zanen banza da wofi ba kar ma ki sake hada maganrki da diyata banaso amman ki
rubuta ki ajiye dai maryama zata juya miki baya tunda dai bakece kikawota duniya ba
."naji komai zakice allah ya raka taki gona “a’a abun bai kai ga haka ba duk kuyi
hakuri Ke hassana kiyi zamanki amman fur tace tafiya zatayi da kyar granny ta shawo
kanta ta hakura sai dai duk sanda zasu hada ido da maryama harara ne ke biyowa baya
“
*****
Maryama zaune shiru duk da zuwa yanzu hankalinta ya dan kwanta amman bata wani cin
abinci yadda ya kamata haka ne ma yasa jikinta yaki dawowa daidai umma da granny
suka zo suka sakata a tsakiya "maryam taso muje kici abinci ta sauke naunayen
ajiyar zuciya tana girgiza kai "bana jin yunwa "haba maryama ina lura dake tun jiya
baki sakawa cikin komai ba karki cutar da kanki domin rayuwa babu ci babu sha akwai
matsala idan wani ciwo ya kamaki yaya kike son muyi da rayuwarmu “. tayi murmushi
kawai tana duban umma “idan ma bazaki tausayawa kowa ba ki tausayawa ummanki cewar
granny umma bata ce komai ba ta koma hannunta daya fuskarta dauke da murmushi
granny ta riko dayan hannunta suka nufi kan kujera mai zaman mutun uku daita atare
suka zaunar daita "umma da kun barni wallahi bana jin cin komai Aa bazai fa yuwu ba
ko bakya jin cin komai ya zama dole ki sakawa cikinki wani abu kafin ta sake yin
magan granny ta kai spoon din abinci bakinta murmushi kawai maryama tayi ta karba
ta soma ci granny na bata umma na bata ."ta kai hannu ta karbi spoon din hannun
umma” nasan kema baki ciki komai ba ta dibi abinci ta kai bakinta "umma nah kici
abinci “ta girgiza kai tana shafa fuskar maryama sannna ta bud'e bakinta fuskarta
dauke da murmushi.”
****
Maryama zaune a parlour'n ummah sanye take cikin wondo da riga yan kanti kanta
babu dankwali yayinda gashin kanta ya zubo gadon bayanta gabanta qaramin table ne
wanda ta daura farar takardar zane kasancewar ta samu aiki ta hanyar wata abokiyar
aikinta yusira ,gefenta kuma tarin fararen takardu ne datai zane bata samu abinda
take so ba ,sosai ta dukufa gurin ganin ta zana abinda ake bukata ,tana nan zaune
umma tazo ta wuceta ta shiga kitchen byn wani lokaci ta fito ta dan tsaya tana
dubanta kafin daga bisani ta koma ta cigaba da abinda take duk maryama bata dago ba
dan sosai tayi nisa sai dai har zuwa wanna lokacin bata samu nasara ba ."har yanzu
banga kinyi abun arziki ba keda zane baya baki wuya “ta dago a galabaice tamkar
zatai kuka "wallahi umma bansan dalili ba na kasa samun abinda nake so ni ma rasa
abinda Ke damuna gabadaya na manta komai umma ta qaraso ta dafa kafadarta” karki
damu yarinyarta ki ajiye ki huta zuwa wani lokaci zaki samu abinda kike so
Suna Cikin haka kawarta yusira ta shigo bakinta dauke da sallama sam maryama bata
dago ba , ta dai amsa sallamar ta cigaba da abinda take umm ta fito daga kitchen
tana murmushi "yusira ce agidanmu ? .
"Nice umma ina yini ?Lafiya lau yusira ya mamanki ? tana lafiya ta fad'a tana
zama kusa da maryama maryama kardai har yanzun baki qarasa ba gashi dashi nake son
na wuce ?ta fad'a tana leka zane jirgin sama ne " uhm wallahi gashin nan fa
yusura har yanzu ta kusan awa daya kenan banga alamun zata gamasa ba, kai tunda
nake daita ma ban taba ganin zane data bata lokaci irin wannan ba”. cewar umma tana
gama fada ta nufi hanyar kitchen .”
Yusira ta biyota abaya "umma me zai hana da zaman nan da maryama take ta nemi aiki
tunda ta gama tabarta,banki maganrki ba yusura amman maryama ce wani lokacin
akwai taurin kai cewar umma “da kuwa datayi kokari ta sake applied din aiki daya
fi, kinga akwai wani compaing AGC dake bukatar ma'aikata nima zanyi applied
kinga da sai munje tare abinda ma ya kawo kenan amman sanin yanzu bata bukatar yin
aiki yasa nace na fara miki magana dan kinsan yadda zaki shawo kanta ciki sauki ta
amince” da zata amince hakika da naji dadi tunda zaman hk bashi da wani amfani
banda tunani dake sa mutun amman Kinsan halinta idan tace bazatai abu ba to fa sai
ahankali "Allah ya kyauta cewar yusura "amman Kinsan wani abu zan tura masu
applications batare da saninta ba sai dai taji ankirata idan sun dauketa
shikenan .” gaskiya umma hakan yayi kuma naji dadi sosai ina son duk inda zan
kasance muje mu kasance tare ai kwanaki yayi min ciwo data bawa subai,a aikinta
wallahi umma da ina gari bazai yiwu ba "to Ke kuma banda abunki ai taimako tayi
kinga tafi maryama bukatar aikin duk halin tsananin dasu maryama suke ciki sunfi
subaia tunda su ko babu komai muna nan kuma bazamu bari su rayu cikin kunci ba
amman subaia da abinda zasu ci ma wahala yake masu ?."
"Haka ne kuma allah yasa mu dace mu samu aikin nan dan aikin a kafanin AGC ba
karamin albashi ake samu ba ,samun aiki ma awurin yana daga darajan mutun shiyasa
kullum cikin addaua nake akan na samu aiki a wajen ,” bari na baki mail dinsu da
zaki tura masu sako tayi maganar tana kokarin ciro wayarta "to shikenan yusira na
gode amman me zai hana ki tura min ta Kan waya kawai kamar zai fi sauki ? .""Eh !
Haka ne kuma bari idan na koma gida sai na turo miki duk wannna maganar da suke
babu wanda maryama taji domin tayi busy akan zane
Mmn Sudais
💗💗💗💗💗💗
MAR'ADAMS
💖💖💖💖
💗💗💗💗💗💗
Book 2 end
*AYSHA A BAGUDO*
WATTPAD @HAUESH
AREWABOOKS USERNAME
AYSHAABAGUDO
bismillahirrahmanirrahim
Wannan littafin na kudi ne mai bukatar karantashi byn na kammalashi zai biya
1000 ta wannan account number din 1438775094 Aishat abdullahi access idan an tura
sai a turawa wannan 09136918331 alert domin tabbatar da an tura domin sauraron
littafaina a tuntubi chaneel dina (Hausa bakwai ) a YouTube.
Page 30
Granny zaune akan kujera mai zaman mutun biyu rike da qaurin qafafuwanta tana
mammatsawa tana runtse idanunta alamun tana jin ciwo sosai muryarta a sanyaye tace
“ wayyo allah qaurin qafata, wallahi qaurin qafar nan yana damuna da ciwo sosai
umma dake zaune tare da aunty hasana najin haka ta tashi daga inda take zaune ta
shiga d’akinta aunty hassana ta dubeta kana tace “sannu hajiya “yauwa hassana na
gode, amman mai yasa bazaki dinga kunsa lalle ba yana maganin ciwon qafa sosai “ina
yi amman wani lokacin idan ya tashi dole sai na had’a da man zafi .”bata kai ga
rufe bakinta ba sai ga umma ta fito daga d’akinta ahankali ta qaraso inda granny
take zaune hannunta rike da man zafi “sannu hajiya bari na shafa miki man zafi
nan zaki d’an ji saukin zugin da suke miki, kinsan abu idan ya had’e maka da girma
sai a hankali “ai kuwa na gode allah yayi albarka daman yanzu nake son tambayrki
aboniki dan nasan bakya rasawa umma na qoqarin tsugunnawa sai ga maryama ta shigo
bakinta d’auke da sallama .”tana ganinsu tayi murmushi ta qaraso da sauri ta tsaya
kusa da umma tana cewa “umma mai ya samu granny naga kamar bata da
lafiya ?”wallahi maryama qafafuwanta ke mata ciwo shine zan shafa mata man zafi
“.“ayya sannu kinji granny Allah ya baki lafiya umma kawo man na shafa ma yar
tsohuwar nan dan nasan ke ahankali zaki yi mata ni kuwa da iya karfina zanyi mata
amfani dashi na durza sosai man zafin ya shiga ko….”
“sannu muguwa! “Inji cewar Aunty hasana “maryama ta kalleta a natse batare da
tace mata komai ba “nace sannu muguwa ko karya nayi da kike kallona a
wulakance ?”daman babu abinda kika iya sai tsiya da mugunta muniyar banza kawai
kin wani kafeni da wasu gwala gwalan idanuwa ko zaki cinyeni? still maryam bata ce
mata komai ba idan da sabo ta rigada ta saba da halinta sai dai abinda take mata
ita da mahaifiyarta yana matukar damunta koma tace ya fara isarta amman tasan duk
runtse duk wuya baza ta’ba iya maida mata magana ba yadda batayi magana ba haka
umma da granny basu ce ci kanki ba ,maryama ta cigaba da abinda take tana bawa
granny labarai masu dadi da kwantar da hankali granny ta lumshe idanunta tana cewa
“yauwa diyar albarka ya isa haka ma na gode sosai Allah yayi miki albarka allah ta
jikan mahaifinki Allah ya rabaki da mahaifiyarki lafiya walalhi har naji saukin
zugin da yake min allah yayi miki albarka allah yasa ki gama lafiya .”maryama ta
amsa da “Ameen”. fuskarta da bayyanan ne murmushin na farinciki dan idan akwai
abinda ke sakata jin farinciki da natsuwa bai wuce taji kana mata fatan alkhairi
ba .”
ATA tsaye acikin office dinsa sanye da wasu hadaddun suit wondo da riga ash colour
haka ma takalman dake sanye a qafafunsa ash colour ne masu kyau da tsada yayinda
jikinsa ke fitar da wani sanyayyen kamshi turare mai sanyi da kwantar da
hankali .muryarsa a dake ya kira sunan sectary dinsa “Some !da sauri ta amsa masa
da “ yes sir!” tana mai dubanshi cike da girmamawa da tsananin tsoro bai ce mata
komai ba ya cigaba da aiki a system dinsa . yayinda itama ta cigaba da tsayuwa
tana kallonsa da bayyanan ne tsoro a saman fuskarta ,fuskarsa babu walwala ya sauke
kwayar idanunshi akanta tare da mika mata system dinsa “gashi ki duba sakonin masu
neman aiki ne yau tsawon sati d’aya kenan ban samu dama dubawa ba yanzu haka ina
son na d’an huta kad’an . “okay sir angama yanzu zanyi komai na gama ,ya dawo kan
kujera ya zauna yana lumshe idanunshi yayinda some ta soma abinda ya sakata tana
kallonsa ya mike a kan doguwar kujera da yake zaune ya kwanta tare da yin pillow
da duka hannuwansa yana kallon saman office dinsa .”
Bayan kamar mintuna talatin ya mike ya shiga bayi ya d’auro alwala ya shiga
d’akin dake cikin office dinsa domin gabatar da sallama bai fito ba sai around
2 :30 yana fitowa ya kirata da wayar office ,ta shigo da sauri still rike da
system din dan sauran kad’an ta gama duba wad’an da suka cancata tace ” sir gani !
“ya ake ciki ? ta d’ago da sauri tana
dubansa sakamakon ganin sunan maryama cikin jerin masu neman aiki “sir !! na duba
duka sakonin amman wannna sakon na qarshe akwai ….” kinga kiyi abinda ya dace
kawai hanyar fita yayi daga office din “but sir!” kinga akwai abinda zanyi yayi
saurin katseta ta hanyar fad’ar haka ya qarasa ficewa ”
D’aya bayan d’aya take bin number masu neman aiki har ta kawo Kan number maryama,
ta kira number ya kusan sai uku ba’a daga ba a karo na hud’u ne ta d’auka tare da
cewa “hello!daga can bangaren aka amsa mata da” hello ko muna magana da maryam
hussein ne ? “Yes of course itace muna kiranki ne daga nan AGC company bisa sakon
neman aiki da kika tura mana mun duba takardunki da safur din zanenki duk babu wata
matsala yanzu dai sai mun ganki domin yin interview ta qarasa maganar a lokacin da
ATA ya dawo office din ya zauna ya janyo system dinsa yana dubawa ”nan take
maryama ta rud’e ta shiga kallon umma a rikice “aiki kuma ?”ai ni ban tura wani
sakon ai …”umma ta matso kusa daita da sauri ta dafa kafad’anta “ki ce kinji ni na
tura masu sako neman aiki .”
maryama tayi shiru tana duban umma tana jin wani irin bugun zuciya” ki natsu
kiyi magana dasu da girmamawa” nan take maryama ta ‘bata rai amman babu yadda ta
iya dan bazata iyawa umma mutsu akan komai ba ,numfashi ta sauke da karfi tace
“shikenan yaushe Zanzo domin interview din ?On 28 march tana gama jin haka ta katse
kiran tana duban umma “why umma wani aiki kuma nifa wallahi babu wani tsarin aiki
arayuwata tunda yusira tana samo min zan dinga yi a gida “.murmushi umma tayi tana
cewa “a’a maryama Kiyi shiru kiyiwa kanki fatan alkhairi karki ja da ikon allah
“bazan yi jayayya da ikon allah ba amman ni wallahi umma …” kar ma ki rantse idan
kika ga bakiyi aikin nan ba mutuwa nayi amman muddin ina raye sai kin ci amfanin
karatunki “maryama ta shagwabe fuska kamar zatayi kuka tace”zanje ne kawai saboda
son da nake miki babu yadda zaayi kice nayi abu nakiyi “nima ina sonki maryama
shiyasa ma na tura miki neman aiki domin nasan shine cikar burinki wani dalili ne
dabam yasa kika ce bazakiyi aiki ba ta qarasa maganar tana riko hannun maryama
cikin nata tana jin wani irin a zuciyarta yayinda idanunta suka cika da ruwan
hawaye sadam dinta ta tuna .”
ahankali maryama ta zare hannunta cikin na umma ta shige dakinta da umma ta barma
ta fad’a kan gado ranta duk babu dadi tunanin rayuwarta ta shig yi sannu ahankali
har bacci ‘barawo yayi awon gaba daita .”
“sir ina son nace wani abu shiru yayi bai amsa mata ba sai qarar daddana system
dinsa kawai akeji sai data maimaita maganarta sannan yace “okay ina jinki na gama
duk abinda kasani na kira wad’an da suka cancata “nasan zasuyi matukar murna dan
babu wanda zai samu kiran daga kamfanin AGC bai ji dadi ba “sai wacan banzar
yarinyar ba .” ya fad’a aciki ransa amman a zahiri cewa yayi “okay !sectary dai
tayi shiru taso ya bata dama tun kafin ta kira number maryama amman yaki ,alamarin
mai gidan nasu ne sai hakuri shi kawai zaiyi abinda yake so kuma alokacin da ya ga
dama amman wani bai isa ba .”parlour’n mami dauke yake da manyan baki domin kuwa
baba qarami ne tare da uncle jay da mami da aunty shahida har ma da aunty abida
tare da sultana ,table din gabansu cike yake da kayan motsa baki wanda mami tasa
aka kawo masu hira tayi dadi sosai inda aunty abida ta sako batun aikin sultana
nan take baba qarami yace “ kai diyata karki damu ta shirya kawai ta fara zuwa
aiki bama ita ba idan kina da masu bukatar son aiki akarkashinmu ki kawo muna
maraba dasu “.
“wani irin murna tayi tana mai jin dadin maganarsa ita dai mami bata ce uffan ba
aka cigaba da hira har sanda ATA ya shigo mami na ganin shigowarsa ta mike zuwa
kusa dashi dan tasan baya son azo acika masu gida da hayaniya kuma baqaramin
aikinsa bane yayi abinda zai korasu gabadaya “abinda ya bawa mami mamaki bai wuce
yadda sultana ta mike tazo ta tsaya gabansa ba tana wani irin rausaya da lumshe
masa ido “thank you so much for giving me the job ,gsky naji dadi sosai zanyi aiki
a qarqashin AGC company “what ?ya fad’a a matukar tsawace yana kallonta kafin
ahankali ya motsa lip’s dinsa “ina ganin kamar kin fara shaye shaye wa ya baki
aiki a company “?baba qarami !”tayi mgnr tana duban inda baba qarami yake zaune”ni
na bata kuma zatayi aiki alokacin dataso saboda itama uwarta nada ‘yanci acikin AGC
“gsky baba qarami kana da matukar kirki amman shi wannan d’an naka ya fiyye jin kai
ya manta cewar ni dashi asalin mu d’aya “to ai shi Adam bai da wannan kirki kuma
duk cikin zuriarmu babu mara mutunci kamarsa amman wannan karon ko yana so ko bai
so yarinya dole kiyi aiki a kamfani kwana nan ma zan dawo na cigaba da kula da
kamfani dan nasan kan kamfani fiyye da wannan gatalallen yaron mara kunya idan ma
naga dama zan iya dakatar dashi dan dama bai iya tafiyar da kasuwanci ba hauka da
shirme kawai yasa a gaba saboda rashin sanin kan kasuwanci komai cikin zafin rai da
fushi yake.”
ATA yayi shiru yana dubansa a kaskance har ya soma taku zai isa inda baba qarami
yake aunty shahida tayi sauri ta mike tare da rike masa hannunsa gam cikin nata
tana masa alamar kar yace komai “amman da kin bari nace wani abu saboda yarinyar
sam bata dace da aiki a company dinmu ba dan babu abinda ta iya sai hauka “koma
dai menene kayi shiru ka barsu qanin mahaifi ne kuma tmkr mahaifi ne abinda kasan
baza kayi wa dad yana raye ba karka yi masa albarkasa albarka dad ne ,dan haka ka
tafi d’akinka ka huta” mami tace ko akawo maka coffe “no !ya bata amsa a fusace
tamkar itace ta ‘bata masa rai, me zakaci ko sai zuwa anjima ?”bana bukatar cin
komai ni kawai ku bani dama nayi magana da wancan mutumin” ina mai baka umarni
adamcy karka ce masa komai dan Allah kaje d’akinka kuma a yanzu idan kace masa wani
abu ban yafe maka ba .”
shiru yayi kafin daga baya ya nufi hanyar d’akinsa har yayi taku uku yaji sautin
muryar abida ta kira sunansa da isa ,da kamar bazai tsaya ba sai yayi wani tunani
ya tsaya bata tsaya akoina ba sai a gabansa ido cikin ido take kallonsa tana masa
murmushin gefen baki mai nuna alamun sunyi nasara daman da biyu suka shirya zuwa
dan su aiwatar da nufinsu uncle jay ne kawai tafiyarsa dabam “ya kaji umarni da
baba qarami ya zarta nasan baka ji dadin haka ba ko? amman dai aikin gama ya rigama
ya gama ko kana so ko baka so kamar yadda ya fad’a sultana sai tayi aiki kuma a duk
inda take so koda kuwa acikin office dinka ne baka isa ka tsaidaita ba, tunda ka
kasa bata aiki wanda yake da iko akanka da kuma kamfani ya bata dama yanzu sai kayi
duk abinda zaka..”ai bata kai ga qarasa maganarta ba taji saukar wasu lafiyayyun
mari ji kake tass tass !! har guda biyu ajere akan kuncinta “enough..!ya fad’a a
matukar tsawace gbdy mutanen da ke zaune a parlour’n babu wanda hankalinsa bai
tashi ba cikin tsananin tsoro da tashin hankali aunty abida ta tsaya cak dafe da
kuncinta tana dubansa fuskarta da bayyanan ne mamaki “Adam ka mareni ? “kad’an
kika gani muddin bazaki daina shiga rayuwata ba “
ya fad’a a matukar tsawace .”
Hankalin aunty shahida a tashe ta qaraso inda yake tsaye jikinsa na wani irin tsuma
ta dafa kafad’ansa
tare da fad’in “kana da hankali kuwa ?”ka kusan wacce ka mara ?matar aure ce kuma
matar shakikinka tana magana tana nuna masa aunty abida da hannunta “.iskar
bakinsa ya fesar yace “nasan ko wacece kuma nasan matsayinta kuma itama tasan ko
waye ni bana cikin irin wadan mutanen da zuciyarsu Ke jurar raini wallahi idan
bata daina enter dinta ba wata rana dukan mutuwa zan mata zaro ido aunty shahida
tayi jikinta na wani rawa kamar yadda na mami ke rawa kana hauka ne adamcy ?”I
don’t know but I fell like na haukace “wai meke damunka ne da kake abubuwa
haka ?”dan Allah shahida ki barni kin cika min kunne abinda ya kamata kiyi ki ja
mata kunne ta fita hanyata ta daina shiga lamarina that’s all yana gama fad’ar haka
ya haye sama da sauri sauri yake taka step .”
gabad’ayansu da kwayar idanu suka bisa dashi har suka daina ganinsa .”aunty shahida
ta soma taku zata bisa mami tayi saurin riko mata tana girgiza mata kai”karki bisa
shahida kinsan halinsa “an san halinsa mami amman shikenan sai a zuba masa ido ya
dinga abinda yaga dama .”?ai daman ita ke daure masa gindin yin iskanci da
wulakanci da taka duk wanda yaso dadin abun itama bai barta ba shegen yaro mara
tarbiya kawai “inna lillahi wa inna ilaihi rajiun abinda aunty shahida ta furta
kenan alokacin da taji abinda baba qarami ya fad’a tayi data sanin yin maganarta,
da kuma tasan kalmar da zai fad’a kenan da wallahi bazatace komai ba jiki a sanyaye
mami ta nufi hanyar bangarenta aunty shahida ta juyo ta kalli baba qarami dake
qoqarin mikewa tsaye zuciyarta na wani irin tafasa taso kwarai ta furta koda kalma
daya ce akan kalmar shegen daya furta ga adamcy amman sai zuciyarta ta gargadeta
domin a yanzu ma kuskurenta ne ya janyo ya fad’a abinda ya fad’a bazata so ta sake
aikata wani kuskuren ba ranta a ‘bace ta juya tabi bayan mami .”
Zaune ta isketa mami a baki gadonta tayi shiru idanunta na kallon sama d’akinta ta
samu waje kusa da qafafunta ta zauna cike da girmamawa ta kira sunanta “mami ! mami
ta sauke idanunta tana kallon aunty shahida fuskarta da alamun damuwa aunty
shahida tayi kasa da kanta kana ta soma magana cike da biyayya “dan allah mami kiyi
hakuri bisa kuskurena sam ban ji dadin abinda baba qarami ya fad’a ba domin idan
mutun yace wa d’anka bashi da tarbiya to kai yake son ya zaga ya fake da zagin
d’anka “numfashi mami ta sauke tana cewa “karki damu shahida idan da sabo na rigada
na saba da halinsa kuma hausawa sukance dan kuka mai jawa uwarsa jifa duk wa ja
min koda zagina yayi ?ni dai fatana allah ya canza adamcy allah kuma ya tsaresa
daga sharrinsu Allah yasa kafin mutuwa naga canzawarsu aunty shahida ta share
hawayen daya zubo mata “menene kuma abun zubar da hawaye ?wallahi mami kalmar tayi
min zafi bansan me yasa yanzu baba qarami yake nunawa adamcy kiyayya haka ba ,ji
nayi kamar na tanka masa “gara da baki tanka masa ba ai sai ya tabbatar da rashin
tarbiyar da yace allah dai ya sawaka kawai zamu ce ahankali suka dinga tautaunawa
wanda kusan duk akan adamcy ne .”
*******
On 28 cikin sauri sauri maryama tayi abinda zatayi ta shirya cikin riga da siket
blue da ratsin yellow ta dauko after dres ta daura akan kaya tayi rolling din kanta
da mayafin after dress din ta rufe koina ajikinta ga kyau ga qarancin shekaru wanda
yasa tayi looking very attractive ta fito zuwa parlour’n sai dai duk ranta babu
dadi , da granny ta soma cin karo ta durkusa har kasa ta gaisheta “barka da safiya
granny “barka maryama fatan kin tashi ?”Lfy ina umma? bata rufe baki ba umma ta
fito daga dakinta ta qaraso ta tsaya kusa da maryama ta dafa kafadanta “har kin
shirya masoyiya ? maryama tayi murmushin jin dadin sunan da umma ta kirata dashi
tace “na shirya umma barka da safiya “kin tashi lafiya ?ta gyada mata kai tana cewa
“ alhamdulillah gamu zamu yakin karshe grany ta matso sosai kusa daita “maryama ki
bi komai a hankali ki kiyaye banda shiga abinda bai shafeki ba allah ya baki saa a
dukkanin abinda kike sa gaba .murmushi maryama tayi tana “cewa Ameen angama kakata
ta kaina zan kula da duk abinda kikace, ta juya bangaren umma tana kallonta “sai
ku tayani da addua, in sha allahu zakiyi nasara amman kamar kinso kiyi late ?” Aa
banyi latti ba zamuyi daidai sai na dawo umma “ai baki karya ba ta fad’a tare da
mikewa ta janyo hannuta bata tsaya koina daita ba sai inda ta ajiye mata plet din
abincin data zuba mata ta zaunar daita ta soma bata abinci a baki tana ci tana duba
mata lokaci har ta koshi ta sha ruwa ta mike tsaye tare da jiran adduarta “fatan
alkhairi diyata karki sawa zuciyar karaya ki karfafa zuciyarki kisa aranki
matsalarki tazo karshe da yarda allah ki kula da kanki please “in sha allahu ta
kalli inda Aunty Hasana take zaune akan kujera wacce ko kallon inda take batayi ba
a tun sanda ta fito daga daki sai man karanta wani littafi take .”
jiki a sanyaye kamar kartace mata komai tunda tasan ba fatan alkhairi take mata ba
amman dai ta barwa allah komai kuma ko babu komai kanwar mahaifinta ce sai datai
adduar samun nasara akanta sannan ta bude bakinta da kyar tace “aunty hasana ni
zan tafi interview” fuskatar ta babu yabo babu fallasa ta dago tana cewa “in sha
allahu bazaki samu aikin nan ba yadda kika fita da murna in sha allahu da
bakinciki zaki dawo gidan nan kinyi sanadin kashe mana d’a amman Ke har kin manta
kin fara neman aikinyi jikin maryama yayi sanyi hawaye ya cika kwarnin idanunta
“hasana bai kamata ki dingawa diyar danuwanki haka ba “to mama ni meye nayi mata
bayan gsky na fad’a aiki ne a gabanta ko zama tayi tunanin abinda Ke damun
rayuwarta muddin kina son zaman lafiyarki damu ki kiyaye takurawa yarinyar nan
kinji na fad’a miki “ai daman nasan duk kun tsananeni akan wannan yar iskar
yarinya irin tsiya irin jaraba kawai masu mugun jini taja tsaki ta dauke kanta
akansu .”
Shiru maryama tayi tsaye ta kasa kwakkwaran motsi tana duban Aunty hasana cike da
sarewa gbdy sai taji zuwa interview din ma ya fita ranta domin tana ji ajiknta
kotaje bazatai nasara ba granny ta janyota zuwa jikinta “maryam ki maida hankali
lokaci na tafiya fa karki damu da maganar wannan mayar in sha allahu zaki samu
aiki “okay granny na gode sosai “abinda granny ta fada in sha allahu haka ne zai
kasance karki manta cewar hasana ba itace takawoki duniya ba dan haka babu abinda
bakinta zai miki inji cewar umma idanun maryama suka kawo kwalla muryarta a
raunane tace “ni dai ku bata hakuri idan wani laifi nayi mata ta yafe min dan
banason tana fadar mummunar kalamai akaina umma idan kin sani bayan babu ran
iyayenka addaur yanuwansu tamkar adduar iyayenka ne “.
“haka ne amman ita mummunar adduarta bazatai tasiri akanki ba saboda baki mata
laifin komai ba ai baza ta’bawa yiwa diyar cikinta mummunar addua ba “Aunty ki
daina hada diyar cikina da wannan yarinyar ita din ba diyata bace ya kamata ki
fahimta “allah dai ya ganar dake gsky dan ni banga amfani kiyayyar nan ba , idan
uwarta tana da laifi dan ta auri danuwanki ai danuwanki ma yana da laifi daya nace
sai daya aureta .”inji cewar granny “Ni wallahi umma da nayi zamana dan ina ji
….”bazaki zauna ba kuma babu abinda kike ji sai alkhairi maza kama hanya ki wuce
fatan alkhairi allah yayi miki albarka “Ameen ta juya cike da sanyin jiki take daga
kafafunta .”
Ganin haka yasa umma ta mike ta biyota tana cewa “ki shiga wajen Auty ku gaisa
kafin ki wuce amman kiyi sauri karki yi latti kinji masoyiya maryama tace” to umma
na wuce sai na dawo “to sai kin dawo allah ya tsare “fatan alkhairi maryama allah
ya bada saa ta fito bangaren mahaifiyarta ta shiga bayan ta gaisheta tayi mata
sallama itama fatan alkhairi tayi mata “aunty ina after dad?yana ciki yana bacci
“okay ki fad’a masa na tafi interview ku tayani da adduar samun nasara tana
qoqarin fita daga part din aunty ta kira sunanta “princess ! ta tsaya cak tare da
juyowa ta fuskanci mahaifiyarta tana mai gyara zaman Jakarta a kafadarta“kinyi
breakfast kuwa da kike kokarin fita ta qaraso gabanta hannunta rike da cup din tea
mai kauri tare da bread bata tsaya jiran mai za tace ba ta kai cup din tea
bakinta “bude bakinki ki sha ko kadan ne bana son kina fita batare da kin sakawa
cikinki komai ba .”ahankali ta bude bakinta tace “naci abinci daga hannun umma kuma
na koshi amman bari naci daga hannunki ta soma kurban tea ba wani mai yawa ta sha
ba tace “ya isa haka na gode sosai ta rungumeta tare da yi mata sallama tana
fitowa daga part dinsu ta rufe fuskarta da qara min nikaf .”
********
Babban hall ne aka tanadar masu ,suna zaune gefenta yusura ce itama sanye cikin
shiga ta kamala kowanne ka gani acikin hall din rike yake da takardunsa na
makaranta wasu acikin jaka, wasu rungume dashi ,tun daga Kan matakin diploma har
zuwa kan digree na biyu .bayan wani lokaci aka fara kiran suna daya bayan daya har
aka kawo Kan maryama da addua ta shiga inda zaa mata interview tana shiga ta yaye
nikaf din fuskarta kasancewar taga mace ce ,sectary ta sakar mata murmushin dan ita
tun ranar data soma ganinta taji ta kwanta mata arai yarinyar tana da natsuwa gashi
tana shiga ta mutunci ko yanzu duk masu neman aiki babu wanda yayi shigar mutunci
kamarta “ga guri ki zauna “na gode” maryama ta fad’a a natse tare da zama tana
ma kanta addaur samun nasara .” bayan awa daya aka gama daita tare da daukarta aiki
“maryama hussein idan allah ya kaimu gobe zaki fara zuwa aiki amman wannna abun
da kike rufe fuskarki dashi ba lalla sir ATA ya yarda dashi ba .”
shiru maryama tayi tana jin da kamar wuya ta iya fita babu shi a fuskarta domin ta
rigada ta saba tsawon shekaru haka ta taso idan ma bata saka shi ba bata jin dadi”
muryarta can kasa tace “zan dai gwada zuwa dashi idan ya bukaci na daina zuwa dashi
zan kiyaye na gode sosai.” ta fad’a tana mikewa ta bar office din a wajen ma’akatan
ta jira yusira itama cikin ikon allah ta samu suka nufo gida cike da murna
yanayinta ya tabbatar ma yan gidansu ta samu aiki ta rungume umma cike da
farinciki.”
“alhamdulillah umma mun dace “kai masha allah masoyiya gsky naji dadi sosai da
kyakkyawan albishiri da kika min ,zuwanki aiki zai rage miki damuwa sosai allah
yasa ki fara a saa” maryama ta qarasa ta rungume granny” na gode matuka da
adduarku da bani kwarin gwiwa ta shafa kanta “babu komai maryama gabadaya
parlour’n umma ya cika da murna aunty da habib ma murna fal anan yusura ta wuni
currr suna murna sai yamma tayi masu sallama ta koma gida da zumar sai sun had’u
gobe .”
Washegari da misalin karfe bakwai daidai a AGC company tayi masu babu ‘bata lokaci
aka nuna kowace office din da zata dinga aiki tare da basu file file da zasu fara
aiki akansa basu kasance guri daya da yusura ba ,tare da sultana suka kasance a
office daya sosai maryama ta dukufa aka aikinta tana Kan aiki sectary ta shigo ta
mika ma maryama wasu file “please ki cike yanzu ki kawo min office dina “okay ma”!
ta fad’a tare da amsa ta ajiye aikin da take ta fara wanda aka bata .”sultana kam
ko ta Kan aiki batabi ba wayarta ma take opereting can ta soma magana da alamun
vioce note take yi “kinsan wani abu qawata gani zaune babu abinda nake takardun
banza daakawo gasu agabana haka zasu karaci yininsu bazan cike komai ba kuma bazan
zana komai ba dan ba abinda ya kawoni kenan ba.” ta tura tai shiru tana murmushi
can sautinta ya sake karade office din “wa wannan mutumin ai bai yi ba wani office
aka kaini dabam ba idan yake ba amman duk bata ‘baci ba komai zai tafinmin yadda
nake so ai bari Ke dai qawa mutumin nan ya hadu fiyye da tunaninki sai ma kin
gansa a zahiri sai kin kusan sumewa .”ta qarasa mgnr tana kam kamkame
jikinta .”alamun tana jin shauki akansa .”
Maryama na ciki aiki sai ga subai ta shigo office din hannunta rike da wasu file
yayinda wuyata ke makale da ID card mai dauke da cikakken sunanta da tambarin Z&A
da sauri ta qaraso gurinta tana dafa kafadanta“wa nike gani haka kamar maryama ?
maryama ta dago a natse tana dubanta “a’a subaia wallahi nice ya kike ya kwana
biyu ? lafiya kar dai kina cikin sababbin ma’aikatan daaka diba?maryama tai
murmushi tana gyada mata kai alamun “eh !”kai gaskiya naji dadi dana ganki a
matsayin maaikaciya anan .” Maryama ta maida hankalinta ta cigaba da abinda take
ai nasan daman allah bazai barki haka ba kullum ina sakaki cikin adduarta na gode
sosai da taimakonki gareni “kai karki damu ai yiwa kai ne fatan alkhairi “thank you
dear .”har subaia ta juya maryam ta mike tana kiran sunanta
ta tsaya “Yauwa subai’a ina ne office din madam some?muje na nuna miki suka fita
tare tana sauke nikaf dinta suna qarasa fitowa ta nuna mata da dan yatsanta”gashi
can sai mu sake haduwa nima wani aiki ne ya kawoni sukai sallama ta karya kwana
“.
ita kuma maryama tayi kokari shiga office din data nuna mata ta tura kofar glass
sannan ta sanya jikinta ciki adaidai lokacin da idanun ATA ke Kan cctv “wacece
wannan data shigo yanzu “?ya tmby yana dauke idanunshi ya maida kan fara takardar
dake gabansa ya juyo mata compute daake ganin shiga da fitar mutane .”
Some ta sauke idanunta akan computer maryama ta gani muryar some na rawa tace
“maryama hussein!”
“wace ce haka ?”sabuwar maakaciya ce “baki fada mata baa zuwa mana da irin wannna
shigar bane ? “na fada mata sir “!yayi shiru yana maimaita sunan acikin zuciyarsa
maryama hussein sannan yana sake kallon cctv tabbas itace yarinyar “ wannna ba
yarinyar da muka bukaci zanenta bane watanin baya ba ?“muryarta na rawa tace “ita
itace sir .” what ! ya fad’a tsawace “nan take jikin sectary ya dauki rawa “dan
allah kayi hakuri sir “ itace yarinyar da akayi interview akan kasuwanci daita ,
yarinyar da take da kwarewa sosai akan zane itace yarinyar da kace anemo ta
watanin baya “ kenan the same person ce “? ya fad’a yana ciza lips dinsa da
karfi “yes sir duk mutun daya ce itace take zane but sir yarinyar tasan kan
aikinta duk a rud’e take masa wannan bayanin.”
shiru yayi yana jin wani irin mummunar faduwar gaba from no where sai dai bai dago
ba ya cigaba da typing din da yake cikin zafin rai .”kana kallon yadda yake daddana
keyboard din system din kasan baya cikin natsuwarsa “bana ce kar a Kuskura a
dauketa aiki ba ?kuma kikayi son ranki har ma kina min dogon bayani akan yadda ta
wulakantamu”sir !sir !!kayi hakuri nayi ta kokarin na fada maka saboda gudun
faruwar haka amman kaki bani dama “.
“me kke nufi ni ban fad’a miki ba karta samu aiki har karshen rayuwarta ba bama a
wannan company din ba har other companies?Ke ma kinsani bana bawa kowani irin mutun
second chance dan haka kije ki sallameta bana son ganinta acikin company din nan
“oya go out ! ya nuna mata hanyar fita jikinta na rawa ta fito .”tana fita ya
zabura ya mike tsaye ya daura hannunsa daya akan hannun kujerar daya tashi gabansa
na wani irin mummunar faduwa zuciyarsa na tuttukin zafin kamar ya dakatar da some
amman bakinsa ya kasa furta komai .
ya bar wajen ya koma jikin window yana kallon haraban maakatan yaso kwarai ya samu
nasara sake ganawa daita amman ina bazai iya daukar iskancinta ba har kamar shi ya
sauke girmansa ya kirata amman taki daukar wayarsa har ma da kashe masa waya ga
mummunar sako data fadawa james bayan haka ya nemi ganawa daita a ogun shima
batayi masa abinda ya bukata ba sai ma qara masa damuwa datayi jin abun yayi kamar
alokacin ya faru babu wani sausauci da zai mata wanda ya wuce ya koreta daga
karkashinsa .”
da sauri sectary ta fito zuwa office dinsu tana shiga ta isketa zaune da farar
takadar agabanta tana zana mutun sanye da suit da wondo har ma da takalmi acikin
mintuna da basu wuce ashirin ba ta tsaya tana sauke numfashi, ganin ita kadai ce a
office ta qaraso sosai ta tsaya akanta tana tunanin yadda zatai mata magana dan
sam babu dadi ka samu aiki ranar da ka fara zuwa ace an koreka tsayuwarta batasa
maryama ta dago ba dan bata ma ji alamun shigowarta ba kokari take ta kammala aikin
da ta fara dashi amatsayin aikin farko .”muryar some a sanyaye ta kira sunanta
“maryam hussein ! maryama ta dago da sauri tana cewa “yes ma ,akwai wani aikin da
zan miki “?”No you’re fared cak numfashin maryama ya nemi ya dauke sakamakon jin
mummunar labarin datayi nan take dakin ya dinga jujjuya mata wani irin tashi
hankali tashig mara misali kafin a hankali ta janyo numfashinta dake kokarin
barinta ta dawo dashi gangar jikinta ta fuskanci sectary sosai hankalinta na qara
tashi “wannan hukuncin MR ATA né “.
“Hukuncin Mr ATA”. ?ta furta da karfi tô kaifin me nayi masa nida yau na fara aiki
anan ?tayi mgnr Kmr zatai kuka cike da tausayawa sectary ta dafata sai dai ta kasa
cewa komai “ko zan iya magana dashi dan haka kawai bazaa dakatar da mutun batare da
wani laifi ba ?tayi mgnr a fusace .”no no !! ba sai kingansa ba ,dan ni kaina a
halin yanzu ina cikin matsala dan allah ki bar nan yanzu kafin ya shigo “ba maganar
na bar nan bane ko kina cikin matsala ina son nasan dalilin da zai sa akoreni tunda
nasan sai da dalili akewa mutun irin wannan korar lallai sai nasan meye matsalar
kafin na bar maakatan nan ,”ki natsu please maryam sir bazai ganki ba a yanzu .”
“Kema kiyi hakuri kiyi min iso Ke bari ma naje da kaina .”fuuuuu ta nufi kofar
fita da sauri some ta biyo bayanta tana kiran sunanta “maryama ki tsaya karki sake
yin wani kuskure ta riko hannunta cikin zafin rai “bazai yuwa ma ki shiga inda yake
ba wannan ya sabawa doka .”
“Doka wani doka kuma ?wallahi kusani kun tafka babban kuskure na korata ,bari ma
kiji bani nayi applied din aiki a kamfaninku ba yi min akayi dan haka yanzu ma ban
damu ba kije ki fad’a masa ko bansamu aikin a anan ba zan samu aiki adalilin
baiwar da allah yayi min kuma bare ma zan samu aiki da takarduna” dan allah kiyi
hakuri nima ba laifina bane .”shiru maryama tayi kafin ahankali tace”madam some ko
zansa exactly laifin me kika min da kike bani hakuri ?ai nice yafi dacewa na baku
hakuri ku da ake nema a wurinku ,amman ku kuwa wani irin tsarin ne da maakatarku
hk ?a dauki mutun aiki rana daya da fara aikinsa a koresa ?kiyi hakuri maryam ki
wuce kawai karma kisa rai ko a wani guri ma zaki samu aiki domin sir nada karfin
iko a koina “to ni laifin me nayi masa haka ?ki tmbyr min shi laifi me nayi masa
haka ?tai mgnr tana kuka “ai ban isa najewa sir da wad’an nan tamvayoyin naki ba
“to shikenan amman wallahi kisani bazanje koina ba har sai naji dalilin dayasa ya
koreni muddin bai fad’a min laifin da nayi masa ba anan zan qarar da rayuwata ..”
ta samu guri ta zauna tana kuka mai matukar cin rai “.
“okay maryam bari na gwada saata ko allah zai sa ya saurareni ta juya da sauri ta
fice yayinda maryama take zubar da hawaye masu zafi bata san sanda ta zamo kasa
bisa gwiwowinta ba ta hade tafukan hannunta guri daya “ya allah meke shirin faruwa
dani kuma ?wani irin tashin hankali ne wannan ?daga zarar na fita cikin wata
maseefar sai wata ta bullo ya allah ka taimakeni .”a can gida ma hankalin aunty da
umma har da granny duk a tashe yake umma ta qaraso da magani da ruwa a hannunta
hajiya yau baki sha maganinki ba ga lokaci na wucewa “ni gbdy na ma manta da wani
batun shan magani dan bana da natsuwa ban san halin da maryama take ciki ba wallahi
hakan nan nake jin damuwa ya allah ka taimake yarinyar nan kasa karshen wahalarta
ne yazo “karki damu in sha allahu alkhairi ne zai biyo ba tunda an dauketa aiki ai
sai fatan albashi su fara shigowa to allah yasa alkhairi ne zai biyo baya .”ameen
ta karbi magani ta kai bakinta .”
ATA na tsaye har lokacin ya kasa zama sectary dinsa ta shigo “sir na fad’a mata
hukuncinka amman tace baza tafi koina ba har sai ta gana da kai “no way !” ya
fad’a yana jin wani irin faduwar gaba mai tsanani ”I won’t meet her ki koma ki
fad’a mata haka” sir na fad’a mata taki tafiya ne wai sai an fad’a mata laifin da
tayi daaka koreta aiki daga farawarta yau “kije ki fad’a mata ta bar kanfanin nan
dan bazan ganta ba kema da kika dawo min da banzar maganarta idan kika sake zuwar
min da mgnrta zaki samu matsala dan kinfi kowa sanin laifin datai ko ba da kanta
taki amsar aikin da muka bata a tun farko ba ?”sannan na bukaci zanenta shima taki
yarda ta ganni sau nawa ina kiran wayarta taki daga wa ta saurareni sannan nayi
qoqarin tayi min aiki a ogun shima babu wani biyan bukata,yanzu kuma ta kwaso jiki
tazo neman aiki kamfanina ?kema kinsan bazai yuwu ba ya fad’a a matukar a tsawace
.”
Nan take sectary ta kame jikinta na rawa dan duk lokacin da yake mgn cikin fushi
itama fita haiyacinta take ya sauke numfashi kana ya dunkule hannunsa ya naushi
iska “aikin har yana arha haka ka kisa alokacin da kaso sannan ka samu alokacin da
kaso “idan ma baki fad’a mata laifinta ba ungo nan ya zaro wata farar takarda ya
mika mata kije ki bata amman ganina ko magana dani abu ne da zai mata wahala acikin
wannan kafanin ke qarshen rayuwarta bazata sake ganina ido da ido ba “okay sir tasa
hannu ta karba ta juya ta soma tafiya “idan aka sake halittarta a duniya aka bata
aiki bazata ki karba ba nonsense girl kawai ya fad’a yana furzar da iska .”
Da sauri sectary ta shiga office din da maryama take tana mai kiran sunanta ta
mike da sauri ta qaraso gareta tana cewa”laifin me yace nayi masa.” mika mata
takarda tayi tana qara mata da bayani abinda tayi hawaye ne suka zubo mata” wayyo
allah wallahi bana ki amsar aikin bane a wancan ranar dan yin kaina wata kawata ce
tafi ni bukatar aiki shine na bar mata amman badan banason aikin bane” wanna shine
dalilin da yasa mr ATA ya koreki kema abinda kikayi bai kamata ba bayan shi ma
akan zane shima haka kika masa wulakanci bayan saboda abinda ya faru aranar da
kikazo kawo zanensa yaji babu dadi aransa shine ma yasa James yayita kiranki
akarshe shima ya kiraki baki dauka ba ,da kuma kika dauaka me kika ce ?”maryama
tayi shiru tana dubanta “kikace bazakiyi ba !” Muryarta a sanyaye tace “am sorry !”
Babu wani maganar sorry zaki iya tafiya dan bazaki samu wata dama ba “is okay na
gode Kwarai da gaske tunda da farko nice naki amsar aiki sannan nakiyin aiki daku
yanzu kuma na dawo kuka kini bani da yadda zanyi tunda ku kuke da kamfaninku tana
gama magana ta juya da niyyar barin office din idanunta ya sauka akan kawarta
subaia “kin rasa aikinki akaro na biyu maryama akaina ?”
“karki damu subai ba akanki bane haka allah ya qaddaromin Kiyi min fatan
alkhairi.““ dan allah kiyi hakuri nasan duk laifina ne “nace karki damu ko na karba
da farko haka zasu min dan da gani mai kanfani har wadan da suke aiki karkashinsa
duk mahaukata ne na ma gode da ban samu aiki akarkashinsa ba suna cikin wannan
halin sai ga yusura ta fito daga office din daakaita ,kusa da maryama taje ta tsaya
tana tmbyarta “aikinta ta rasa adalilina aikinta da bar min “wata uwar harara
yusura ta maka mata “ai gsky ne adalilinki ta rasa wancan aikin yanzu ma ta rasa
wanna kenan ?subai’a ta gyada mata kai “a wani dalili ?”Ke !me ma ya kawoki ma
tunda ai baa nan kike aiki ba ?karki manta da mai wannan kamfanin da A&Z duk mutun
daya ne wani mahiman aiki ne ya kawoni “karku tsya bata lokaci please zaku iya
wucewa kuje kasa ku cigaba da magana inji cewar some“maryama bari na dauko jakata
mu tafi tare kawai zaman me zanyi ?no yusura karki damu kiyi zamanki bazan zama
sanadin rugujewa farincikinki ba ,ina miki fatan alkhairi all the best to both of
you tana gama fadar haka ta juya ta soma taku ,da kyar take iya d’aga wafafuwanta
saboda nauyin da suka mata ,wani matashin mutun ta gani tsaye bata bi ta kansa ba
ta raba ta gefensa ta wuce shi tana sauke nikaf din fuskarta shi kam kamewa yayi ya
kasa kwakkwaran motsi shin mafarki yake ko kuwa zahiri yake gani ?.”
ya kai second goma yana kallon bayanta har ta kusan ‘bacewa ganinsa sannan ya juyo
ya dubi some “ kinga wata doguwar yarinyar ta wuce yanzu ? “ yes sir ! da sauri
yace “ mutun ce ko fataluwa ce ?mutunce sir sunanta maryam hussein “.maryam hussein
!? ya furta a dan razane adaidai lokacin da yusura ta fito ta tabi bayan maryama da
sauri tana kiran sunanta hankalin salim a matukar tashe yace “Adam ya ganta kuwa ?
No sir aiki tazo nema har an dauketa yace akoreta” da sauri yace “kai bari naje
na sake tabbatarwa itace ko kuwa dai kama ce ya bi bayanta da sauri ya sauka har
kasan kamfanin yana nemanta bai ganta ba tsaki yaja yana cewa “ amman Adam ya
cika hauka me yasa bai tsaya yaga yarinyar nan ba yana tsaye sai gasu ita da
yusura maryama tana magana muryata da alamun tayi kuka sosai “karki damu yusura
ki tsaya Kiyi aikinki karki yi Kuskure irin wanda nayi ,kin dai ga yadda abun
alkhairi ya zame min ko? to ki tsaya kiyi aikinki ina miki fatan alkhairi “ta
fad’a tana tsaida yusura tare da rike hannunta cikin nata .”Ahankali salim ya kara
taku ya matso kusa dasu “shikenan maryama naji kuma na gode da shawarki allah yasa
haka shine mafi alkhairi arayuwarki sai mun hadu a gida dan allah karki saka damuwa
aranki komai yana da lokaci kuma in sha allahu zai zama alkhairi .”
numfashi ta sauke sannnan ta saki hannun yusura dake cikin nata ta juya itama ta
juya ta soma tafiya da sauri kawai taga mutun agabanta yana sauke numfashi bai
tsaya wata wata ba kawai ya daga nikaf din fuskata tare tsura mata ido byn Kmr
second biyu ya saki wani irin murmushi wanda bashi da maraba dana farinciki
muryarsa cike da in.. ina.. ya soma mgn”itace wallahi tabbas itace wallahi itace
wacce danuwana ya dade yana nema yayi maganar yana riko tsintsiyar hannunta “dan
Allah kiyi hakuri mu koma ciki akwai wanda zan nuna wa ke .”bai gama rufe bakinsa
ba ta fixge hannunta tare da daukeshi da wani gigitaccen mari tana cewa “itace
wa ?”
“Akan wani dalili zaka kai hannunka jikina ?”ammm but da kin ..”“kar kace min komai
bana bukatar jin komai dan baka zo da siffar da zan saurareka ba daga ganin mutun
sai ka wani kai hannunka jikinsa kasani koni matar aurece ta fad’a a fusace tana
sake juyawa ya sake shan gabanta”wallahi babu inda zaki sai na kai ki
gurin ..”“wallahi ka sake kuskure tabani sai na maka wulakanci da har ka matu
bazaka manta dani ba ,matsa ka bani hanya na qara gaba da rayuwata “.
“to to ki bani numberki ko address dinki “i cant! ta fad’a tana bin gefensa zata
wuce shi sam sam marin da tai masa bai damesa ba kamar tafiyar da zatai Adam bai
ganta ba da sauri ya sake shan gabanta “kinsan allah bazaki bar nan ba batare da
danuwana ya ganki ba wuce mu koma sama maryama ta dafe goshinta cikin tsananin
tashin hankali “wannan shine karo na biyu da ta fuskanci irin wannan matsalar “
kafin ta ankare taji ya rike tsintsiyar hannunta ya soma tafiya daita cikin sauri
sauri gudu gudu ya dinga tafiya, tana ya sakar mata hannu amman yaki da kyar da
bala’i ya shigar daita lifter ya fad’a office din ATA daita a tsaye ya gansa rike
da kugu ya juyawa kofa baya yayinda cup din coffee ke rike a hannunsa yana kurban
coffe a hankali bai juyowa ba har sai da yaji salim ya soma mgn “ATA…”ya kira
sunansa cikin wata irin muryar mai cike da tashin hankali ATA ya juyo a natse
yana fuskatarshi alokacin da salim ya cire nikaf din fuskarta maryama yana rike a
hannunsa wani irin bugu qirjinsa da zuciyarsa yayi alokaci daya bai san sanda cup
din hannunsa ya subuce kasa ba. take ya tarwatse zuciyarsa ta tsaya cak ta daina
aiki na wuncin gadi ,duk yadda ATA ya kai ga son motsa sassan jikinsa bun ya
faskara,tamkar wanda bai da numfashi a ganganr jikinsa haka ya dawo saka makon wani
yanayi mai sarkakiya da wuyar faasarawa ya ziyarci zuciya dama gangar jikin ATA
abangaren maryama ma wani irin mummunar bugu zuciyarta keyi da mugu mugu sauri
“la haula wala kuwata illa billa” babu tsumi babu dabara sai na Allah haka ATA
yake ta faman ambata acikin zuciyarsa dake karkarwa yayinda maryama wacce bata san
dalilin dayasa mutumin dake tsaye a gefenta ya shigo daita ba sai dai ganin fuskar
mutumin dake tsaye a gabanta yasa ta nemi natsuwarta ta rasa .”
hakan nan damuwar dake cunkushe cikin ranta ta ninku yayinda soyayya da kaunarta
ya dinga bin dukkan sassa na jikinshi ji yake kamar acikin mafarikinsa ya Allah
kasa a zahiri nake ganin komai ba mafarkin dana sabayi daita bane ,wani irin so mai
zafi ya dinga huda zuciyarsa yana bin jinin jikinsa wanda ma'abota so da shauki
kadai ne suka san zakinta,yana son yarinyar kamar ranshi shikanshi yana mamakin
zazzafar soyayyr da yake mata mai tafiya da dukkan wani motsi na bugun numfashinsa
“adam kayi maza ka dawo haiyacinka karka biyewa soyayya dake kutimemeniya da
rayuwarka gizo ce ba zahiri ba “to Salim dake tare daita fa ?shima gizo ne ko me “?
tsaki taja tana duban fuskar salim a wulakance cike da tarin bakinciki mara
misaltuwa muryarta cike da sheshekar kuka tace “Allah ya isa tsakanina da kai bazan
ta’ba yafe maka ba “.sautin muryarta ce ta dawo da mr ATA cikin haiyacinsa tun bai
kai ga bawa kanshi amsa ba ya ware idanusnhi sosai ya zuba mata kwayar idanunshi
yana kallonta tamkar zai cinyeta “.
Alhamdulillah
Anan zan dakata sai mun had’u a littafi na uku wanda zai zama na qarshe ina maku
fatan alkhairi
Mmn suka